Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
3 / 9
daga dakin. Dakinshi ta tunkara sha biyu ta gota, kofar a bude take tana ta6a handle din ta bude. Bai samu ya yi bacci ba a lokacin yana dauke da iPad suna magana da wani abokinsa ta social network daga kasar Saudiyya. Kwatsam! Yaga ta shigo masa, abin ya ba shi 48 WAYE ANGON? Maryam Ja'afar mamaki matuka, yarinyar da ta tsane shi ko kallonsa ba ta yi, to me ya kawo ta dakinsa a wannan lokacin? Daga shi sai shortniker ba ko singileti. Ya yi saurin mikewa yana cewa, "Subhanallah! Mabaruka lafiyarki ki ka shigo min daki babu sallama?" Ya jawo jallabiyarsa ya saka don kare mutuncinsa. Ya ci gaba "Ba kya tunanin a ya za ki same ni wanda ba zia miki dadi ba?" Ta zumburo baki daga in da take tsaye jikin kofa ta ce, "Ni ina ruwana, wannan ba shi ne gabana ba." Ya yi murmushi ya ce, "Ok! Naji to meye gabanki?" Tayi mai banza tana turo baki. Ya sake cewa, "Mabaruka menene?" cikin kulawa. Ta ce tana kumburi "Magana nake so muyi." Ya ce, "Da ni kuma?" Ta yi masa banza. Ya sake cewa "Ni makiyin naki?" Yana murmushinsa mai kyau. Ta ce cikin fada, "To in ba da kai ba da wa zan yi? Dakin wa ka ga na shigo?" Ya ce, "Kiyi hakuri to dakina ne, naga ko muryata ba kya son ji bare ki ce kina son 49 WAYE ANGON? magana da ni." Maryam Ja'afar Ta ce cikin kufula ba tare da ta kalle shi ba. "Ni ba nazo nan don in ja magana ba da surutai marar ma'ana ba, kawai nazo ne na taimake ka." Ya kalleta da kyau ya ce, "Ok, bismillah zo ki zauna ga kujera."Ya nuna mata kujerar da ke facing din shi. Ta juyo tana harararsa ta ce, "Ba zama ya kawo ni ba, ka daina tunanin zan iya zama dakinka." Ya yi murmushi ya ce, "Maganar ba ta da muhimmanci kenan tunda a tsaye za a iya yin ta. A zatona tana da girman da za a girmamata." Yana rufe baki ta dauka. "Na gaya maka ban zo nan ba don surutai marar ma'ana ba, ka saurare ni kawai." Ya nisa ya ce, "Ok, kin ce ni za ki taimaka, to na gode kije kawai idan har ba za ki iya zama ba, ba zan iya saurararki ba kin atsaye ina zaune, kin gane ko?" Ta harare shi cikin tsananin jin haushinsa har ita zai wa barazana, don haka ta kulu kawai ta juya fuuu ta fice 50 WAYE ANGON? Maryam Ja'afar tana cewa "Kai ka sani ba damuwata ba ce." Ta buga masa kofar ta fice. Ya bita da kallo cikin tsananin kaunarta, hakan da tayi burge shi tayi, ya kasa dauke kansa daga kofar kamar tana gani. Can ya yi ajiyar zuciya ya ce a bayyane. "Ya Allah idan har Mabaruka ba alkhairi ba ce gare ni, in kuma ba za ta taba sona ba kamar yanda nake sonta na damu da ita, nake tausayinta. Ya Allah ka cire min sonta kada ka bar aurannan ya yiwu tsakaninmu, ka zaba min mafi alkhairi ga rayuwata, ita kuma ka bata wanda take so ya zamo alkairi gare ta." Ya koma ya jingina jikin gadon ya yi lamo yana jin zafin sonta na kara zafafa a zuciyarsa, yana kara yaduwa. Koda ta shiga dakin ta shige toilet tayi zaune kan abin kashi ta dinga rizgar kuka, wai me yasa zuciyarta take mata zafi har haka? Wallahi ba ta sonshi ko kadan, tsanarsa ce dankare a ranta. Me yasa ba zai kyaleta da 51 1 WAYE ANGON? Sulaiman dinta ba? Maryam Ja'afar Taci kukanta son ranta sai kuma ta koma yi wa kanta fada, to kukan me ki ke don me ba ki fada masa abin da ya kai ki ba? Ke fa za ki cutu, ki sauke girman kanki ki danne tsanar tasa ki roke shi, me yiwuwa ya fahimce ki, shi kenan ki huta da kuda. Amman in ba haka ba ki kai wasa aka daura aurenki da shi.za ki mutu da bakin ciki, kullum za ki dawwama da kuka kina ganinsa kina kara tsanarsa da takaicin zama da shi, wai a matsayinshi na mijinki. Ai kuwa tazo wuya, ba za ta taba yarda tayi rayuwa da makiyinta ba ya nakasa mata rayuwa ba. Lokacinta na kurewa, daga yau ba wata damar, gwanda taje kawai ta ceci rayuwarta. Don haka ta nutsu da hakan ta mike ta kara ficewa ta tunkari dakinshi. Har za ta tura ta shiga sai kuma ta tuna yanda ta tarar da shi dazun. Don haka sai ta fara knocking har ya kwanta amman bacci bai dauke shi ba, ya ji ana bugawa. Ya tambaya 52 د WAYE ANGON? Maryam Ja'afar "Waye?" don sam ranshi bai kawo za ta dawo ba, yasan halinta. Ta yi shiru kamar ba da ita yake ba. Ya kara tambaya. Cikin masifa ta ce, "Ka zo ka bude sai ka gani." Jin ita ce yasa ya mike ya nufo kofar, ya murza key ya bude. Ya ce, ,"Menene kuma?" Tayi masa banza tana kumburi, ganin ba ta da niyyar ba shi amsa kuma ta ki shigowa yasa ya ce, "To shigo." Ta shigo din ta jingina da bango har da harde hannuwa a kirji. Ya bar kofar bude ya tsaya gabanta ya ce, "Menene wai?" Ta ce a kufule, "Na ce zan yi magana da kai." Ya nuna mata kujerar again, ya ce "Toje ki zauna." Ta dago ta harare shi ta kuma kauda kai don bata iya jurar kallonsa saboda kiyayyarsa, tsawon dakiku. Ya ce, "Mabaruka!" Tayi shiru, ya kuma cewa "Wai me ke damunki ba ki jin magana ko?" Ta zumburo baki tana gunguni. Ya ce, "Na ce kije ki zauna muyi maganar, ina son na kwanta dare yana yi fa." Ta ce, "Ni ba zan zauna ba." Ya ce, "Ok, to zo ki tafi 53 WAYE ANGON? Maryam Ja'afar mun yi maganar gobe." Taki tafiyar. Ya dubeta da kyau ya ce, "Mabaruka!" Ta amsa cikin makoshi. Ya ce, "Ме ke damunki?" Tayi shiru, ya ce "Kije ki zauna muyi maganar to."Ta ki ko da motsawa. Ganin za ta bata masa lokaci yasa ya janyo hannunta har gaban kujerar ya zaunar da ita. Tana zama ta mike tsaye, ya kara zaunar da ita ta sake mikewa tana turo baki. Ya dubeta cikin ido ya ce, “Kin iya kafiya ko?" Tayi masa banza. Ya saki hannunta ya ce, "Ok, mike din tunda kin raina ni ba ki jin magana."Ya koma ya zauna kan gadon ya yi shiru, ransa ya 6ace amman babu alamar yaji haushi. Ba tun-yau take tare da shi ba, ta san shi sosai tasan halinsa lokacinta da yake mutuminta abokinta kan ya ce yana sonta ya zama makiyinta. Ransa zai 6ace a zuciyarsa amma saboda hakurinsa ba za ka gani ba a fuskarsa. Sai in ya kai iyaka za ka gani a idonsa su sauya launi zuwaja. 54 WAYE ANGON? Maryam Ja'afar Don haka ta fahimci ya yi fushi ne, don haka a sanyaye ta koma ta zauna din. Bai ce komai ba dai ya yi shiru. Ganin hakanne yasa ta ce, "Daman um daman..." ta kasa fada. Ya dubeta cikin kulawa ya ce, "Fadi mana, kar kiji komai zna suarare ki na kuma yi miki kyakkyawar ".fahimta י, Don haka ta ce a marairaice, idanunta sun kada, ta ce "Wallahi ban taßa sonka ba, ba na sonka, kai ne namijin da nafi tsana a rayuwata..." Kai maganganun sun masa zafi da nauyi a rai, tamkar ta fesa masa wuta ya ji, duk da ba yau ta fara fada masa ba amman duk sanda zata nanata sai ya ji yafi sanda ta fada a baya zafi. Murmushi ya yi a fili ya dubeta ya ce, "Na sani Mabaruka." Taci gaba "To me yasa ka nace sai ka aure ni bayan ka san ba na sonka ko ka aure ni haka zan dawwama za ka cutar da ni ka tauye ni? Kaima ba za ka 55 WAYE ANGON? Maryam Ja'afar yi farin ciki da aurena ba, bare ka samu nutsuwar da ango yake smau in ya yi aure. Kaga da ni da kai zamu yi rayuwa cikin kunci da hakuri da juna tun da kuruciyarmu mu gagara moreta. Amma idan kayi hakuri da ni sai Allah ya sauya maka, ya baka wacce ta fini, wacce za ku yi rayuwa ta farin ciki da ita, ni ma in auri wanda nake so in yi walwalata da nishadina da shi a kan mu kasance da juna ba cikin farin ciki da walwala ba, mu rasa samun nutsuwar da ma'aurata ke samu. Auren tursasawa ba shi da dadi Imran, sai bacin rai da takaici." Ta saurara tana sauraron me zai ce. Ya numfasa ya ce, "Mabaruka kenan, maganarki gaskiya ne tabbas! Amman abin da nake son ki.sani, wannan-son da ki ka ga ina miki ba ni na sa ma kaina ba, Allah ne ya sa min shi, da zan iya cire shi wallahi da tuni ya dade da fita a raina, tun kan lokacin nan don na sami sauki kema na barki ki huta..." Ta katse shi cikin fada. "Kaso hakanne, tun yaushe 56 WAYE ANGON? za ka cire shi in ka sa wa ranka?" Maryam Ja'afar Shi ma ya ce "To naji, ke me yasa ba ki cire tsanar tawa ba ki ka sa son nawa in har ni zan iya cire sonki?" Tayi shiru tana harararsa. Ya ci gaba “Wannan ba shi ne abin da yasa na nace da auranki ba, illa dalilina daya. Tabbas! Ina sonki amma ni ma ta wani 6angaren zai iya zama tursasawa daga mahaifina kamar yanda mahaifiyarki ta tursasa ki. Da zan fada miki yanda muka yi da shi me yiwuwa da kin fahimce ni, amman akwai abu daya da zan miki, Momy ita ta haife ki nasan za ta fahimce ki, kije ki same ta ki fada mata ra'ayinki a kaina, ki ce ma ni na turo ki. Idan ta amince ta janye aurenmu to wallahi nayi miki alkawarin na janye na hakura, gwanda na mutu da sonki, nayi miki wannan alkawarin." Ta marairaice kamar zata yi kuka ta ce, "Wallahi na gwada haka amman ta ki yarda, nayi mata kuka na roketa, na nuna mata amman ta ki fahimtata, tayi rantsuwa sai na aureka, tunda naje ni kai sai ka gwada 57 WAYE ANGON? mu gani." Maryam Ja'afar Ya kalleta ya yi murmushi ya ce, "Ba zan iya ba Mabaruka, hakan yana daga cikin alkawarin da nayi wa mahaifina, ba zan iya karyawa ba." Ba juyin duniyar da bata yi da shi ba amman ya nace a kan alkawarinsa, har biyu na dare suna abu daya, tayi masa kuka ta durkusa gabansa tana rokonsa. Hankalinsa ya tashi, ya tada ta shi ma ya bata hakuri ba zai iya ba, amman taje ta gayawa Allah shi ma zai yi addu'ar ya zaba musu abin da zai fi zama alkairi kafin jibi. Mikewa tayi a fusace ta harare shi son ranta, sannan ta wuce. Har taje bakin kofa ta juyo tana kallonsa. Ta ce, "Shawarar da zan ba ka, kada ka yarda a hada wannan partyn da za ku yi, don ba zan je ba wallahi. Idan kuma a ka tursasa ni naje, na rantse za ka sha kunya gaban mutanenka da abokanka, sai kayi kuka wallahi!" Daga haka ta doka masa kofa ta fice a fusace. Yaja ajiyar zuciya ya ce, "Na bar maka komai a 58 WAYE ANGON? Maryam Ja'afar hannunka Ya Allah, ka kawo min agaji da mafita." Daga haka ya mike ya shiga bandaki ya dauro alwala ya zo ya shimfida darduma yana kai kukansa ga Allah. IMRAN KENAN. Yayin da ita kuma ta koma dakinta tana tafe tana bala'i, "Wallahi za ka gani, ba ka san wacece ni ba, za ka sha mamaki in halinka kafiya." Bacci dai ba ta yi ba a ranar, haka ta kwana tana juyejuye tana doka tsaki, tsanarsa tana kara ruruwa a ranta. Yayin da shi tunda ya gayawa Allah ya sami nutsuwa, nan da nan bacci ya kama idonsa, a nan ya 6ingire har asuba. Washegari ana gobe daurin aure a gidan su Sulaiman tunda safe karfe bakwai ya fito ya shiga dakin Inna (mahaifiyarsa) tana zaune tsakiyar daki tana daura suga a leda na sayarwarta. Ya tsugunna yana gaisheta, ta bishi da kallo ta ce, "Sulaimanu ina za ka haka tun da safe?" 59 1 WAYE ANGON? Maryam Ja'afar Ya ce yana mikewa, "Wallahi ina da uzururruka yau kasancewar gobe daurin aure, shi ne nake ta sauri naje na aiwatar kar ranar ta min kadan." Ta tabe baki ta ce, "Um, sai ka ce kanka aka fara aure, sai rawar jiki ka ke na rasa dalilin rawar kafar nan da ka ke wa yarinyar nan, kai ba auren farko ba bare ka ce ba ka taba yi ba." Ya yi murmushi yana sosa keya a kagarce yake ya fice kar ta hana shi fita, duk yanda yake kokarin boye dokinsa sai da ta gano. Ta ce, "Ko kokon ba za ka tsaya ka sha ba? Ga shi can Sameera ta dama." Ya ce, "Inna sauri fa nake kin.." ta katse shi "Yau naji ikon Allah! Yau aure zai hanaka shan koko Sulaimanu? Wai wannan wace yarinya ce za ka auro mana?" Ya yi shiru tamkar saman kaya yake, a tsorace ta ce, "To zauna sai ka sha sannan ka tafi, so ka ke kaje ka fadi?" Ya sani ba shi da ikon cewa uffan a kan abin da ta zartar. 60 WAYE ANGON? 1Maryam Ja'afar Ya ji kamar ya yi kuka şaboda takaicin tsare shi da tayi, da tuni ya yi nisa da tafiya. Kuma bai isa ya tafi ba ba tare da ta sani ba, dole sai ya ce zai fita. Ta ce, "Za ka zauna ko sai na mike nima?" Ba shiri ya koma ya zauna, sam ba yunwa yake ji ba, dokin da yake ma bai bar shi ya ji yunwar ba. Ta kwalawa Samira kira, budurwa ce kanwarsa ta shigo tana gyara daura zani, kanta ba dankwali sai gashi da ya tashi buzuzu, ta ce "Gani Inna." Ta ce, "Zubo mishi kokon da dumamen.” Ta се, "То." Тa fice tana kwalkwalar tasona. Shan koko da cin fumame dole ne farilla sai ya ci shi sannan ya tafi duk in da za shi, duk da yana da mata bata yarda yaci na matar ba sai dai nata. Sai dai ya ci wancan a 6oye, sannan ka'idarta ba a mata sauran abinci in ta zubo maka dole sai ka cinye shi. Ta dawo dauke da kofi na roba cike da kokon, sai kwanon dumamen tuwo miyar kuka shar sai kwandalakwandalan waken da ka ke hangowa, da ganin shi bai 61 WAYE ANGON? Maryam Ja'afar dahu ba, guda-gudanshi yake. Ta ajiye a gabansa ta fice. Haka ya ci gaba da karyo tuwonnan yana ci saboda dan banzan taurinsa kamar ya fasa ihu. Sai da ya tura tuwonnan duka tumbinsa, ya wanko hannu ya dawo yana cewa, "Nina tafi." Ta ce, "Ina kayi kenan?" Yayi jim! Sannan ya ce, “Akwai wasu abokaina da zamu hadu da su to can nayi." Ta ce, "To jeka Allah ya tsare." Ya ce, "Amin." Har yana hardewa wajen sa takalmi, kar ta kara tsayar da shi. Har ya wuce ta kira shi ya ji kamar ya runtuma kar ya dawo, ya dai daure ya dawo din. Ta ce, "In ka fita ka ce wa Saddiku mai shago in yaga yara da kwanon siyen יי koko ya turo su." Ya ce, "Koko kuma Inna? Ana bikin ba za ki hakura ba?" Ta dago da bala'inta ta ce, "Ka ji min dan iskan yaro, auranka din banza zai hana ni neman kudi, za ka ba ni ne?" Ya yi saurin cewa, "A'a yi hakuri.” Daga haka ya juya. Ta ce, “Kai zo nan.” Ya juyo ta ce, "To in gaya 62 WAYE ANGON? Maryam Ja'afar maka ko ranar da aka kawota sai nayi ba fashi ka ji ko?" to." Ya ce, Naji sosai Allah ba da sa'a." Ta ce, "Amin, jeka Ya juya har ya kai zaure ta kara kwala masa kira. Ya dafe kai "Oh ni Sulaiman! Na shiga uku." Ta kara dago murya, "Sulaimanu kana jina kayi shiru ko nasan ba ka isa ficewa ba." Ya juyo dole yana kumburi. Ta dube shi da kyau ta ce, "Wai saurin me ka ke ne, in fa kayi wasa wallahi za a daga bikinnan." Ya zaro ido "Dagawa kuma Inna?" Ta ce, "Eh! Ko ban isa ba? Sai a fasa ma gabadaya." Ya yi saurin cewa "Kin isa mana sosai, ayi hakuri." Tayi kwafa ta ce, "Jeka to Allah ya tsare, ka duba in mai kosan nan ta fito." Ya ce, "To." Da sauri ya wuce. Ta dago murya "Kar ka yi dare fa." Shi ma ya dago "To an gama Inna." Da gudu ya karasa fita. Ya saki ajiyar zuciya da dafe kirji. “Wai, Allah ya fito da ni! Inna jaraba." Bai saurari ya duba mai kosan ba, don ba dawowa zai yi ya gaya mata 63 WAYE ANGON? Maryam Ja'afar. ba abin da ya gani. Ya tare mashin ya bar unguwar zuwa hidimominsa. Koda suka tashi ita da Rafi'a, tun sannan mai gyaran jikin da aka dauko ta fara aikinta, in da ta hau darzar mata jiki tana yi tana zo6ara baki da musu. Idan mai gyaran ta ce tayi haka ta ce a'a, ita ga yanda za ta yi. Abin ya kai matar bango ta ce, "Shin ke wace irin yarinya ce da kafiyar tsiya? Na ce haka kin ce haka, a gyara ki ne ba kya so ba ki ga kuďaden da Mamanki ta kashe ba a kan gyarannan?” Ta turo baki ta ce, "Yo ina ruwana." Rafi'atu ta ce, יי "Don Allah kiyi hakuri kar ki ga laifinta." Ta dube ta ta ce, "In tambaye ki don Allah?" Ta се, "Ina jin ki."Ta ce, "Amman auren dole za a yi mata ko?" Ta kasa bata amsa, sai dai Mabarukan ta ce "Kwarai kuwa, auren dole auren maza biyu kuma." Mai gyara ta kasa fahimta. Rafi'ar ita ta mata bayani, abin ya bata mamaki matuka, ta dubi Mabarukar ta ce, f 64. WAYE ANGON? Maryam Ja'afar "Eh lallai kam dole kyayi kumbure-kumbure, Allah ya sawake." A dakin da suke kusa da na Imran ne, ya shiryo tsaf cikin dogayen kaya farare sol yasha hula da farin glass, ya zauna a saman dogon hancinsa. Haka kuma ya yi wa kyakkyawar fuskarsa kyau, mai haske. Dakin bude yake suka yi ido biyu da ita lokacin da yake tsaye a falo suna magana da Momy. Tayi masa kyau sosai, ya saki fuska yana mata murmushi, ya yi mata alama da "kin yi kyau" daga can ta gallo masa harara tasa kafa ta banko kofar ta rufe. Ya yi dariya abinsa ya wuce. Motarsa tayi ready wanke an goge, ya shiga ya zauna ya turo mata text. an Kin yi kyau my light, you will receive millions kiss from me, Insha'Allah. Urs husband, Imran Umar. Ya yi dariya yaja motarsa, Maigadi ya bude masa Gate ya fice. 65 WAYE ANGON? Maryam Ja'afar Lokacin da taji shigowar text a wayarta ta jawo ta duba ta karanta, ta ce "Allah ya isa, mugu!" Idanunta suka ciko da kwalla. Suka juyo suna kallonta ita da Rafi'a, ta ce "Menene? Ke da wa?" Hararar Rafi'ar tayi. Suka gaji suka kyaleta. Karfe hudu tuni an gama gyarata, tayi wani irin kyau. Daman ga ta fara ta kara rikidewa kamar ba ita ba, jikinta har santsi yake, ga lallan da aka zuba mata ya yi wa farar kafarta kyau a kai mata kwalliya. A ka bata kayan da Imran din ya aiko mata bayan fitarsa, wanda zata sa suyi anko a nan aka dinga rigima da ita ta ce wallahi ba za ta sa ba, har Momy tazo. Ta ce, "Ba za ki sa kayan ba saboda me?" Kai tsaye ta ce, "Ba zan je ba ne." ta ce, "Saboda wane dalilin kenan?"ta ce, "Don ba na sonsa, ba na son abin da zai hada ni da shi." Ran Momy ya baci, ta fidda hannu ta mareta ta ci gaba da fada. "Uban wa ya haife ki? Ke ki ka haifi kanki da ki ke 66 د WAYE ANGON? na fada kina fada? Kina gaya Milvaaga son ranki? Wa yake da alhalin zaba miki miji? Cutarki a kai aka hada ki da dan iska bare ki min rashin kunya? Kin fi ni hankali ne?" Ta saurara. Yayin da ita kuma take cizgar kuka kamar ranta zai fita. Momy ta ci gaba. "To don ubanki kar ki sa kar kuma kije, idan naji labarin kinje sai na taka miki wuya, kici gaba da mishi rashin kunya." Daga haka ta fice mutane na ta ba ta hakuri. Ita kuma ta ci gaba da kuka kamar ba za ta daina ba. Rafi'atu ita ke rarrashinta, amman ta ki sauraron kowa bare ta bari sai don kanta, idanunta suka yi ja sun kumbura sannan ta bari, ciwon kai ya dameta. Rafi'atu ta ce, "Kinga ran Momy ya baci har ta kai ga taba ki, kin fiye kafiya Mabaruka, ki mata abin da take so zuwa party ba zuwa gidan Imran ba ne, kije awa daya ya yi yawa ki dawo sai ki samu sauki daga fushi. Don wallahi tayi fushi sosai, ga mutane suna taruwa 67 WAYE ANGON? WA Ċ S Maryam Ja'afar ana kallon kuna sa'insa da mahaifiyarki kina gaya mata magana son ranki, wanda ba tarbiyya ba ce sai a tafi ana yi da ke. Kiyi hakuri don Allah Mabaruka kar ki bata kunya, kar a daura miki aure tana fushi da ke, kiyi kokari ku rabu lafiya tana sa miki albarka." Ta ci gaba da share mata hawayen, da kanta ta dauko kayan tasa tana yi tana turo baki a ka sake mata kwalliya. Masha Allah kowa yake cewa, tayi kyau fiye da tunanin mai tunani, tamkar ba ita ba, kayan sun mata cas! Kamar an gwadata. Less ne hadin fari da pink riga fara sikyat pink sai gwaggwaro pink tayi cas! Sai walainiya take cikinsu an zubo da gashin gefe guda ga sarka wacce ta dace da kayan, agogo zuwa 'yan hannu. Aka dinga daukarta hoto duk da ba fara'a a fuskar sai zumbura baki da harare-harare, ji take kamar tasa kaya jikinta saboda amfani da tayi da kayan makiyinta. Tasan kudinshi yasa ya siyo tabbas hannunsa sun 68 WAYE ANGON? Maryam Ja'afar taba kayan. Zuciyarta ta dinga tashi ta dinga yatsineyatsine tana tara miyau. Abin mamaki kawayansu suka ga suna ta tururuwar zuwa sun cika dakinta kowaccensu tasha kwalliya, akwai masu shirin kwana ma kowa in tazo da tsegumi wai a ce ba a gayyace ta ba. Rafi'ar ke cewa da ba za a yi komai ba suma sai yau suka sani, haka dai kawaye suka yi dandazo, wasu har kan gado. Kowa sai da suka yi hoto da ita daga wayoyinsu, still dai fuskarta ba walwala. Sai suke tsokanarta ta fara kukan aure ne? Ba a sami tafiya ba sai bayan sallar Magriba, sannan a ka zo aka dinga daukar kawaye da wasu iyayen zuwa tsararren hotel din da a ka tsara aka yi kwalliya da kalar kayan ango da amarya, Duhu ya fara sanda za a dauke ta aka tsayar da motar gabanta har wani walainiya motar take da ganinta sabuwa ce dal. 69 WAYE ANGON? Maryam Ja'afar Aka ce ta shiga, to da duhu ba ta san akwai wani ciki ba, da shigarta ta ji ta ta fada jikin wani abu mai laushi, zata yi ihuya yi saurin sa hannu ya dode mata baki, dole tayi shiru tà kasa kwatar kanta. Ya kunna hasken wayarshi ta haske mishi fuska, kawai taga Imran ne. Ta fiddo idanu tana kallonsa cikin tsananin haushi da takaici, ta ci gaba da harararsa. Yayin da shi yake dariya ya yi kyau cikin irin kayanta, kamshinsa yana dokar mata hanci, ta yunkura zata kwace kanta ya riketa gam! Ta harare shi ta ce, "Sake ni."Ya ki, ta kakalo miyau (yawu) ta tofa masa a fuska, tare da cewa "Allah ya isa." Ba shiri ya sake ta, yasa hannu ya shafo miyan. Ya yi murmushi ya kalleta da take harararsa ya ce, "See." Kawai taga ya lashe shi ya kara gogo wani ya lashe shi. Sannan ya ciro handkchief daga aljihunsa ya goge fuskarsa. Yasa a hancinsa ya shake shi har da lumshe idanuwa. Ya bude yana kallonta ita ma duk tana kallonsa. 70 WAYE ANGON? Maryam Ja'afar Ya ce, "I will keep it, ba zan taba wanke shi ba nayi miki alkawari, don in dinga shakar kamshinsa ina jin dadithanks." Ya maida aljihu. Ta kauda kanta tare da jan tsaki. Rafi'a ta shiga gaba direban daya daga cikin abokansa yaja motar suka yi gaba. Ta koma jikin kofa ta rabe, bata son jikinsa ya hadu da nata, gefe kuma tana jin wani takaicin yanda jikinsu ya gogu har ya ta6a ta, ta ci gaba da yin Allah ya isa a ranta har suka isa. Suka fiffito, suka tsaya aka sa kawayanta gaba don suyi mata rakiya zuwa wajen zamansu, wasu kuma bayansu aka saka su tsakiya ita da shi. Sunyi kyau matuka, in ka gansu zaka ce wallahi babu masoyan da suka dace da juna irinsu, abin ya burge mutane sosai, aka ci gaba da daukar su hotuna zuwa bidiyo. Aka ce su kamo hannun juna su shigo hall din. Ta juyo ta harare shi ta ce, "Wallahi ka kuskura ka taba ni a 71 WAYE ANGON? Maryam Ja'afar sai ranka ya 6aci." Ya yi murmushi ya ce, "Ni ma ba zan fara ba." Bayan sun zazzauna aka fara abin da ya tara su. Abubuwa sun yi kyau matuka, kowa yana yabawa, duk 'da ita amaryartana yin nesa-nesa da angon. Kamshin turaransu daddada mai tsada dan waje, shi ya zamar mata kamar tana shakar kwan da kaza ta fara kwancinsa ya fashe, haka take ji ta koma tana dode hanci har zuwa lokacin fuskarta babu annuri. Wasu sun fahimci wani abu, yayin da wasu ba su lura ba. Amman da mamaki amarya ranar partynta bata fara'a sai gumtse-gumtse da 'yan harare-harare. Idan abokansa sun zo suna gaisheta sai taja tsaki ta kauda kanta, ba wanda take amsawa. Wannan shi ne kadai abin da tayi ya 6ata masa rai, amman hakuri irin nasa sai ya share kawai. Jikin abokansa ya yi sanyi, duk sun fahimci wani abu game da amaryar tasa. Lokacin da suka dawo ana tsayawa zata fice ya yi saurin tsayar da ita ya ce, "Ba za ki min sallama ba?" 72 $ S WAYE ANGON? Maryam Ja'afar Harararsa ta yi kawai ta fice tana cewa, "Don Allah ka sakar min mara nayi fitsari, na dai yi abin da ka ke so ko, to ka kyale ni."Ta fice tare da turo kofar. Ganin yanda ta fito ne yasa Rafi'atu ta biyo ta. Da shigarta ta fara yakice kayan tana wurgarwa, "Tir! Da kayannan, ba zan iya ci gaba da zama da ku jikina ba." Rafi'ar ta shigo ta tsaya tana kallonta, daga ita sai under wear tayi sama da shi, ta ce "Wannan wane irin hauka ki ke? Ai suma na jikinki din

Chapter 3 of 9