Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
5 / 9
ya koma. Sai bayan shekaru uku sannan na sami 'ya mace, muna ce mata Salaha. Watanta hudu Allah ya amshi abinshi. Muna nan muna nan dai kamar ba za a kuma ba can sai ga wata haihuwar, a nan muka samu haihuwar Mabaruka, to Allah ya rataya Alhamdulillah wannan shi ne a takaice." Alkali ya kira Mahaifiyarta ta tsaya a dayan gurin ya ce, "A takaice ko za ki fada wa kotu tarihinki?" Ta ce, "Eh! Sunana Halima Bello, 'yar nan garin ce ni, mahaifina shi ne Mallam Bello, gidanmu duk mata ne ni ce mace ta farko 'ya a gidanmu. Ina da kanne biyar, nayi aure tare da Mal. Yusufa kamar yanda ya ce, Allah ya bamu 'ya'ya hudu tare da shi amman Allah bai sa sun tsaya ba sai Mabaruka." Alkali ya ce, "Meye rayuwar aurenku da shi?" "Eh, lallai kam an sha fadi-tashi na rayuwa tsakanina 100 WAYE ANGON? Maryam Ja'afar da shi, dangane da wuyar rayuwa na talauci. Mun yi yawon haya gida-gida a lokacin kudin hayar ma gagararmu yake sai dai mu biya rabi kan ya kare zamu harhada da 'yan kasuwancin da muke ni da shi mu biya. Tun bayan barin wajen aikinsa inda yake wankin hula. Kwatsam sai ga wani sabon kamfani an bude ana neman ma'aikata. Don haka bai yi wasa ba yaje cikin sa'a aka dauke shi aikin. Ba laifi albashin da albarka, na daya na biyu ana uku ya harhada ya sai fili. Muna nan dai rayuwa ta fara sauki shi kanshi ginin yana yin shi gutsin-gutsin in an samu ayi, yanayin dai ginin talaka bai gama ginin ba aka samu matsala kamfani a ka kulle, don haka sai dai ya koma sana'ar wankin hularsa. a Haka dai rayuwar ta ci gaba da gangara mana ganin mun kusa gama ginin mahaifiyarmu ta rasu, to gadona da shi nayi amfani na sayar da dan abin da ke gare ni daga kayan daki da 'yan canjina na tattara na ba shi ya 101 WAYE ANGON? Karasa ginin, Maryam Ja'afar Daki biyu ne shi daya ni daya, muka tare hankalinmu kwance, lokacin Mabaruka na yayeta. Ban fasa sana'a ba ina yi mu kanci abinci da kyau shi ma ya kawo abin da ya samu, don haka sai rayuwa tai mana sauki, ga shi ba yawon haya a gidanmu ne ga sana'a muna yi ni da shi. Wata rana, ranar Asabar ina zaune ina yankewa Mabaruka farce ya shigo da kaya niki-niki a hannunsa, na bishi da kallo ina cewa. "Malam daga ina haka afujajan da kaya?" Ya zauna tare da mike kafa yana cewa, "Ke dai bari, daga kasuwa nake." Na ce, "Kasuwa kuma?" Ya ce, "Eh! Na bude na gani. Atamfofi na gani har guda uku, sai leshi daya da hijabi da takalma sai 'yan kayan shafa. Na dago ina kallonsa na ce, "Wadannan kayan fa?" Ya ce, "Kanwarki taja min sayensu, haki ne." Na ce, "Ban fahimta ba, wace kawar?" Ya ce, "Ku fa mata 102 WAYE ANGON? Maryam Ja'afar akwai ku da basarwa, wace kanwa ki ke tunanin zan kawo miki? Abokiyar zama mana wacce Mabaruka zata sami 'yan kanne." Ya fada yana jan kafar Mabarukar yana mata wasa. Idanuwana suka fito na ce, "Aure ka ke nufin za ka yi?" Yayi dariya ya ce, "Yawwa 'yar gari ashe kin gane, aure fa. Jibi take tarewa." Matuka raina ya 6aci, saboda ganin ya raina min wayau, yana kallon wuyar da muka sha na rayuwa duka yaushe muka fara samun sauki, amman ko shekara ba mu kulla ba ya fara zancan aure. Wai har jibi zata tare, kenan an daura aure tunda har ana maganar tarewa? Na dai daure na ce "An daura kenan?" Kai tsaye ya ce, "Wallahi yau mako daya kenan, anjima masu yin farar kasa za su zo su dan shafa mata a 29 dakin, in ya yi ragowa kya samu. Na ce, "Allah sa alkairi, na gode da fenti ita dai da yake sabuwa ce a mata tafi bukata." Ya ce, "Ah to ba 103 WAYE ANGON? laifi bana tunanin ma zai isa." Maryam Ja'afar Na kara cewa, "Amman kana ganin adalci ka min har a daura maka aure ba ka sanar da ni ba sai ana jibi ba ni da wannan kimar da zaka sanar min?" Ya ce, "Kiyi hakuri bana son ki tayar da hankalinki ne, amman yanzu tunda an riga an yi damuwarki da sauki."Daga haka ya mike yasa takalma ya fice. Koda amarya ta tare nasha mamakinsa matuka, kirikiri ya canza baya jin komai gabana yake rawar jikin matarsa kamar bai taba aure ba. Hatta cefane ya fara canzawa idan ranar girkina ne sai ya dauko Naira dari ya bani ya ce ba shi da lokacin zuwa kasuwa in sai abin da zan siya ayi maneji. Idan kuma ranar girkinta ne haka zai shigo da ledoji fal da kayan miya, kaji da cefane ko kifi tayi girki gajegaje ta juye musu a ledar da naman ni ta bar min saura a tukunya. Duk idan nayi magana ya hau fada, ai ba ni da hakuri shi ma ba daga shi ba ne kawai dai abin da ya sani ita ta 104 WAYE ANGON? Maryam Ja'afar shigo da kafar dama shi yasa duk ranar girkinta aljihunsa yake jinsa da nauyi. Wata ranar girkina zai fita da safe ya miko min Naira dari ya'ce "Ga shi nan in sai kayan miya yana sauri ne. Naki karba na ce "Ka ba yaro ya siyo ai ba a rasa mai siyowa ba, ba lallai sai ni naje na siyo ba." Ya ce, "Wane yaron nake da shi zai siyo?" Ya jefo min ya wuce yana cewa, "In kin ji yunwa kin siyo." Ya ficewarsa. Dole tunda ina jin yunwar da rana tayi na dauka naje na siyo wake gwangwnai dayan da dan barkono da manja na dawo na girka. Abincin nan da na gama na ba Binta matarsa ko kallonsa bata yi ba bare taci, ni dai naci haka zalika shi ma da ya dawo na kawo masa ya ce a koshe yake. To a ranar ta karßi girki tun da ya shige dakinta ban kara jin motsinsa ba. Washegari tunda safe ya fice, ashe kasuwa yaje sai gashi da kaya dam a hannunsa, ya wuce dakinta ya kai 105 WAYE ANGON? mata. _ Maryam Ja'afar Ta fito tana gyarawa, kayan miya ne da kifi lodi guda, duk ina kallo ban ce komai ba, sai da ya fito muka gaisa na ce. "Amman abin da ka ke ya kamata kenan? Yau ka sami lokaci kuma aljihunka da nauyi a kullum in dai ni ce da girki ba ka da kudi sai ranarta? Malam kar fa ka manta baya ka nutsu ka gyara kuskurenka." Ya 6ata rai “Ni matsalata da ke kenan bakin ciki, kina bakin ciki ana kawo mata ni ba daga ni ba ne kuma abincin nan in an dafa ana baki kin fi ma kowa ci amman kullum kina bakin ciki da haka." Raina ya 6aci, na ce "Kai kasan ban taba maka bakin ciki ba da samuwarka ba, ina son dai ka gyara kuskuranka don ka zamo mai adalci, ka tashi gobe kiyama babu alamar rashin adalci a tare da kai." Ya ce, "To ba zan yi ba, ki dauki mataki. Daga haka ya fice. Abin kullum gaba yake karawa, musamman da ta 106 WAYE ANGON? Maryam Ja'afar samu ciki abin da yake nema kenan, don haka rawar jikinsa ta karu na koma bora a cikin gidansa, ba ni da matsayi a idonsa ko kadan sai dai ita ke juyinta son ranta. Kullum ita ke yin daidai amman ni ko ya nayi kuskure duk makota sai sun ji saboda fadansa. Zaman ya koma min na hakuri, ko kadan bana jin dadinsa, ko yana dakina babu wata mu'amula tsakaninmu idan ni na neme shi sai ya ce shi ya gaji, don Allah na kyale shi ya huta sai yai ta sharar bacci ya banni zaune cikin tsananin bukata. A kullum haka muke, ta kai ga na fara masa kuka amman ko sau daya bai taba saurarata ba. Kamar wata rana mun yi haka da shi da dare, da safe yana tashi ya'ce in je gida na huta zai neme ni, na tambaye shi dalili sai ya ce naje dai kurum. Haka nan ba da son raina ba saboda bukatuwar mijina na tafi gida, koda mahaifina ya tambaye ni dalilin zuwana, na ce shi ya ce na taho gida. 107 WAYE ANGON? Maryam Ja'afar Ya dube ni da kyau ya ce, "Halima." Na ce, "Na'am Baba!" Ya ce, "Kin tabbata ba ki masa komai ba ya turo ki?" Na ce, “Wallahi ban masa komai ba, kai ma ka sani Baba a tsawon zamana da shi ban taba zuwa ko yaji ba, ban taba karo maka kararsa ba, lafiya muke zaune da shi ban taba jin ya yi min korafi nayi masa wani abu ba. Ya yijim cikin gamsuwa sannan ya ce "Amman abin da mamaki Halima, a ce haka nan miji ya turo mata gida wai ta zo ta huta?" Nayi shiru dai. Ya ce, "Amma zan neme shi yazo in ji me ke faruwa?" Na ce, "A'a Baba kada ka neme shi tukunna ka bari muga me yake nufi kenan? Idan abin nasa ya wuce misali sai a tuntube shi." Ya ce, "Haka ne kuma, shi kenan Allah ya tabbatar mana da alkhairi." Haka na zauna gidanmu tun ina jiran zuwansa mu tafi har dai na mike kafafuwa, idanuwana kullum a kofa, duk sanda Babanmu ya shigo ina bin bakinsa da kallo ko zan ji ya ce "Ga mijinki yazo ku tafi." e 108 ☑ WAYE ANGON? Maryam Ja'afar Amman shiru nake ji ba shi ba alamarsa, ga jarabar son mijina da yake damuna, kullum mafarki nake na koma gidan har dai mahaifina ya fahimce ni. Wata rana ya kirawo ni dakina. Bayan na zauna ya ce "Kiyi hakuri Halima, nasan kina son komawa gidanki, amman kin ga har zuwa yanzu bai zo ba, bare ya bukaci hakan. Amman na yanke shawarar zan neme shi sai naji dalili. Idan laifi ki ka yi masa ki ba shi hakuri ki koma, idan kuma dai wani dalili ne duk zamu ji." Na gamsu da hakan, don abin da nake nema kenan fada ne dai ban yi ba. Don haka kwana biyu da maganarmu, kwatsam na tsinkayo maganarsa zaure tare da Babanmu, farin ciki ya bayyana gare ni, ba tare da naji ya suka yi ba, na hada kayana inajiran a kira ni. Ba wani dalili ba ne nashi illa kame-kame, wai na fiye kishi, tunda naga ya yi auren nan nake kishi da matarsa na takura mata da sa mata ido duk abin da take 109 WAYE ANGON? Maryam a'afar idona na kai bare da ta samu ciki wai na dinga jin haıshi ina mata mugun baki, wai dan ai ba zama zai yi ba, nima haka nayi. Maganganu dai ga su nan da ji kasan tsara su acai, koda mahaifina ya ji bai yarda da zan yi hakan ba, amman dai ya ce "To ya yi hakuri zai min fada ba zan kuma ba insha Allah." Ni kaina nasan ya fada ne amman ba haka ba ne, nayi hakuri kawai na bar shi eh a kan hakan ne, muka tattara ya wuce da ni. Koda na shigo gidan kallon banza ta min, tare dajan tsaki. Cikinta ya turo sosai, plate din farfesu a gabanta tana sha. Ta harare ni ta ce, su karya dai an ji haushi ba zuciya an dawo dai to kizo ki zauna ba za ki samu kima da daraja ta matar gidan na ba za ki ga wane matsayi za ki zauna. Raina ya 6aci zan yi magana ya daga min hannu, "Ba na son rashin hakuri da Allah wuce kawai." Ba na son mu fara daga dawowata hakan yasa na 110 WAYE ANGON? dauki jakata na shige dakin. Maryam Ja'afar In da tsari ake bi tunda na kwana da yawa ba na gidan to yau ni ke da miji, amman ina ganinshi ya shige dakinta. Na kyale shi ayi kwana biyu kamar yanda muke yi, don haka na share. Akai kwana biyu duk yana dakinta a zatona zai dawo dakina, amman naga yana kokarin shiga dakinta, na dakatar da shi na ce. "Ka manta ne yau a dakina ka ke?"Ya juyo ya harare ni tare da jan tsaki ya bude labule ya shige, na kara daga murya na ce baka ji ni bane yau fa a nan kake kwananka biyu a dakinta. Ji nayi an turo daki bam! A wannan ranar nashi kuka iya karfina na tabbatarwa kaina lallai a yanzu ba ni da kima a gidansa, ba ma da son ransa ya dawo da ni ba mai yiwuwa saboda mahaifina ne. Sai da na gaji sannan na bari na fito nayo alwala ina jiyo dararrakunsu daga daki na goge kwallar dake son taruwa a idona na shige dakina. 111 Π WAYE ANGON? Maryam la'afar Tun daga sannan na daina kasancewa da mjina dawowata wata biyu kenan, yana gidan amman ya manta dani ya ma daina maganar girkina, kullum ita ke yi kayan abinci suna dakinta in ta gama ta yafo min a plate ta shige musu da saurah dakinta. In ya dawo ina masa magana ya ji tsoron Allah sai dai ya wuce ya bar ni tsaye sa shige daki har da banko kofa. Lubabatu kanwata ce ita ke bina wata rana tazo min ziyara. Wuni guda ta gama fahimtar me ke faruwa, musamman da taga an turo min plate daya na abinci ta shige daki ta rufe. Ta kare dubana yanda na rame nayi baki kashi har a fuska, ta ce Yaya! Na kalleta ta ce, "Fada min me ke faruwa?" Abu daman yana cina a raina kamar jin nake kun san in kana cikin damuwa idan ka fadawa wani ko ya ya ne zaka samu sauki, ban yi niyyar fada mata halin da nake na fada mata. Hankalinta ya tashi ta dinga kuka, tayi bakin cikin 112 WAYE ANGON? kasancewata a wannan halin ta dinga fada. Maryam Ja'afar Ai ba kallonsu za ki dinga yi ba Yaya, gidanki ne fa nan tazo ta same ki taje tayi 'yan abubuwanta ta anshe miki miji sai ki sa ido kina kallonsu. Na ce, "To me zan yi Luba?" Ta ce, "Nuna mata za ki ita karamar 'yar iska ce, ba tare da kinje gun boka ba ko Mallam, nasan kina addu'a amman dabaru hikima za ki janye hankalin mijin na ce to ba sai in ina ganin mijin ba ma. Та се, "Кo yana dakinta ne banka ki shiga ki zare mata ido ki nuna mata ke ma 'yar bariki ce, ba a fiki wayau ba, don ma tana ganinki laka-laka shi yasa. amman in irina ce ai ba inda zataje wallahi. Na ce, "Ba mai maganin abin nan sai addu'a, Luba wani rashin kunya duk ba mafita ba ce, ke dai ki taya ni da addu'a kurum." Haka dai Luba ta tafi tana ta fada akan zata dawo kwana biyu taga ya abin ya sauya, lallai dai in yi abin da ta ce. 113 WAYE ANGON? Maryam Ja'afar Har nayi bacci kamar daga sama naji saukar bulala a jikina na mike ba shiri bai saurara da dukana ba sai da ya min liga-liga sannan ya kyale ni yana huci wai na fara zama 'yar iska, wato an zo an zuga ki kun hadu ke da ita ku ka dinga ci mata zarafi zagi ba wanda ba kuyi mata ba, har da duka. Na kalle shi cikin mamaki na ce "Ni aka ce maka?" Ya ce, "Ko zata yi miki karya? Yanzu gata can kwance bata da lafiya, sakamakon dukan da ku ka yi mata har ya shafi cikinta. Na dube shi hawaye na zuba na ce "Wallahi-wallahi ba abin da ya shiga tsakaninmu, ko magana bare zagi har ya kai ga duka na rantse me yasa zan dakar maka mata in kuma kallon halin da take ciki." Ya ce, "Za ki iya ai, sau nawa kina nuna adawarki saboda kin kasa ki haifa su zauna gatanan shekararmu nawa da ke, me naci riba da ke sai wannan wai 'ya mace guda daya tal? To meye ma amfaninki? Ni ba farin ciki nake da ita ba wallahi. Ina son magaji namiji, wannan shi ne musababbin aurena, kuma gashi 114 WAYE ANGON? Maryam Ja'afar nan da alama zan samu, yarinya mai albarka tana kyautata min fiye da ke, ina jin dadinta amman kina kokarin nakasa min ita." Na ce, "Komai na Allah ne, ba ka fi ni son na haihu ba su zauna, ba daga ni ba ne ko ita ma hakan yana iya faruwa da ita don Allah ya nuna maka ikonsa." Fadin wannan magana yasa ya kara hassala yaci gaba da duk na sonr anshi sai da yaga bana motsi sannan ya kyale ni ya fice yana maida numfashi. Darennan ban iya ci gaba da bacci ba, na ci kuka har na gaji hawaye suka kafe sai a sannan na fara nadamar dawowata gidansa bayan tunda na dawo har zuwa yau ban kasance tare da shi ba. Haka naci gaba da zama gidansa ba wanda yasan halin da nake çiki sai Luba, tana yawan kawo min ziyara duk sanda tazo sai mun sha kuka ni da ita, ta so ta yi wani kokari a kaina amman na hanata, ni nasan komai lokaci ne, ba abin da ke dauwama. Na cutu a gidan Baban Mabaruka nayi kuka nasha 115 WAYE ANGON? Maryam Ja'afar duka na wulakanta a idonsa na koma shara me aiki tafi ni daraja. Allah cikin ikonsa, matarsa ta sauke a ranar da ta haihu a ranar dan ya koma, wannan shi ne dalilin rabuwata da shi. Saboda hakan na faruwa ya ce ni ce na kashe masa da don na yi masa baki cewar ita ma dan ba zai zauna ba, don haka a ranar yai min kora ta wulakanci gaban iyayenta da 'yan unguwa, yasa bakin wuta ya dinga dukana gaban jama'ar ina kuka ina rokonsa har ya tillo ni waje bai fasa dukana ba rigata ta yage zani na kwance amman ya kasa saurara min. a Da kyar 'yan unguwa suka kwace ni ta hanyar rike shi. Wani mutum ya cire babbar rigarsa ganin tsiraicina ga mutane dankare, don haka ya rufe ni da ita a nan ya min saki uku gabadaya. Wata makociyata ta fito ta ja ni gidanta, ta ba ni suturarta nasa har zuwa lokacin ban fasa kuka ba, cike da takaicin wulakanci da tozarcin da ya min gaban maz 116 WAYE ANGON? Maryam Ja'afar da mata yara da Kanana, ta dinga lallashina da ban hakuri, ta ba ni waya na kira Luba. Lokacin da tazo taji me ya faru ta harzuka matuka ta nufi gidansa taci masa mutunci ni na hanata. Tun daga wannan ranar mahaifin Mabaruka ya fice min a rai, ina masa matsananciyar tsana babu wanda ba na son jin ko maganarsa, irinsa bare na gan shi muka yi rabuwa ta har abada. Dole ina ji ina gani ya kwace Mabaruka ta ci gaba da zama gun matar Babanta wacce ba kalar wuyar da bata sha ba gunta. Na dawo gidanmu da zama tare da matan Babana zamanmu lafiya har hankalina ya kwanta damuwata ta wuce, mahaifina yaci gaba da min addu'ar samun miji na gari. Haka Allah ya hada ni da Alh. Umar mahaifin Imran kenan, tun ban amince da shi ba har na yarda muka yi aure. Ban taba tunanin ana samun namijin da ke nunawa 117 WAYE ANGON? Maryam Ja'afar matarsa so da kulawa ba irinshi. Ya damu da ni da matsalata, ya zame min tsani, rayuwata ta canza tayi kyau farin ciki ya zauna tare da ni zamana lafiya da mijina cikin tattali da kulawa. Alh. Umar Allah ya azurta shi da tarin dukiya yanda da kasuwanci kasashe-kasashe da gida Najeriya shi kanshi bai san adadin dukiyarshi. - Mutumin kirki ne me fara'a da son dariya, yana bada taimako ga talakawa koda yaushe ya ware wani abu daga dukiyarsa da yake rabawa mabukata a kullum. Matarsa ta rasu da dadewa, Imran da Sharifat sune kadai ta haifa, Balarabiya ce a wajan kasuwancinsa ya hadu da ita a kasar Saudiyya, mai kamala da addini, 'yar babban Malami ce a can akwai tarbiyya da nutsuwa tare da ita. Ta ba su Imran tarbiyya da ladabi daidai gwargwado, sun fita daban, ko bayan zuwana sun dauke ni tamkar mahaifiyarsu ban taba fuskantar wulakanci ba, ko rashin kunya ba gurinsu. 118 WAYE ANGON? Maryam Ja'afar Imran ya yi karatunsa a (England) na Pilot har ya kammala yanzu haka yana aiki a nan gida Najeriya. Sharifa kuma ta bukaci tayi karatunta a Saudiyya a kan Arabic, hakan yasa ta koma hannun dangin Mamanta taci gaba da karatunta sai ta samu hutu take zuwa gida Najeriya. Ban taba ganin 'yan uwa masu son juna ba irin su Imran da Sharifat mai sunan mahaifiyarsu. Imran ya damu da Kanwarsa da damuwarta haka zalika ita ma koda yaushe Yayanta. Ta zauna tare da su Imran tamkar 'yan uwanta, shakuwar da ke tsakaninta da Imran ya wuce misali, ya dauke ta jininsa kanwarsa, zai fitga da ita yawo wuriwuri. Ita ma tana jin dadin kasancewarta da shi, sai su wuni tare suna wasa. Ta dubi Alkali "Wannan shi ne takaitaccen tarihin rayuwata." Alkali ya yi 'yan rubuce-rubuce sannan ya ce yana 119 WAYE ANGON? kallon Baban Mabarukar. Maryam Ja'afar "Ka ji abin da ta ce, da gaske haka ne ko ka musa?" Ya sunkuyar da kai sannan ya ce, "Eh haka ne." Mabaruka ranta ya 6aci, hawaye suka dinga zuba ta dinga kallon mahaifinta mugu azzalumi wanda ya wulakanta mata uwa, ya tozartata. Ashe ma ba ya murna da ita a samuwanta 'yarsa? Haba shi yasa a kullum take yawan tambayar mahaifiyarta me ya raba ta da Babanta? Ashe ba komai ba ne a labarin sai wulakanci da tozartarwa, tabbas tasan zata tsani mahaifinta, shi yasa taki fada mata. Haushinsa ya darsu a ranta, ta dinga masa kallon mugu. Alkali ya sake cewa. "Waye Sulaiman? Meye dangantakarka da shi? Sannan me yasa ka hadata aure da shi?" Ya ce, "Sulaiman kamar kani ne a gurina, don kanin matata ne Binta, ubansu daya da ita. Ya kasance yana zuwa gidana, idan ya zo kanshi tsaye yake shigowa 120 WAYE ANGON? saboda tamkar gidansu ne. Maryam Ja'afar Yana yawan tsokanar Mabaruka a duk sanda yazo ita ma takan biye mishi. Tsawon lokaci suna tare da juna tun daga zolayar da suke wa juna har suka fara soyayya tsakaninsu, hakan ta bayyana shi da kanshị Sulaiman din ya min maganarta, ya kuma bukaci da na ba shi aurenta a shirye yake ya aureta. Nayi farin ciki da haka, don nasan waye shi. Yana da hankali da ilimi, matata ta kara karfafa min gwiwa. Na kira Mabaruka na tambayeta ko tana sonshi zata iya aurensa? Ta ce, Sosai ma Baba na gamsu da Sulaiman na lura da shi yana da hankali da ilimi, wannan yasa na yarda da shi. Na ce, Shi kenan kije na amince da aurenku har bayan raina, ko da na mutu ki aure shi, ni ma na yarda da nutsuwarsa. Hakan yasa na shaidawa Sulaiman ya turo 121 WAYE ANGON? Maryam Ja'afar magabatansa na ba shi auren Mabaruka, bai yi wasa ba ya turo su muka yi magana. Wannan shi ne musabbabin da na aura mata Sulaiman." Alkali ya gamsu, yasa aka kira Sulaiman. ed Ya ce, "A takaice wanene kai?" Ya ce, "Sunana Sulaiman Garba, mahaifina ya dade da rasuwa, na taso karkashin kulawar mahaifiyata, ni da kanwata Samira, nayi aure har sau uku ina da 'ya'ya biyu, amman yanzu ina da mata daya ne sai Mabaruka!" sn ssdM LI Aikali ya ce, "Ka ba da sadakinta kuma?" sanoi Ya ce, "Sosai na ba da sadakinta da duk wani abu na aure, kuma Kanin Babanta shi ya daura mana aure da ita." A kakira Baba Hamza. s Alkali ya dube shi ya ce, "Kai ne kanin Mahaifinta?"" Ya ce, "Eh ni ne uwa daya uba daya muke, kumani na karbi sadakinta kuma na daura auren tare da cikakkun 122 WAYE ANGON? L shaidu da waliyyai. 7Maryam Ja'afar Alkali ya ce, "Ya a ka yi ka daura aurenta bayan ka san an daura mata aure da wani?" Ya ce, "Ban sani ba, nasan dai suna rigimar auren shi da mahaifiyarta." Ya kara da cewa, "Kuma lallai na daura kafin su su daura, hakan yasa ban yi was aba na daura din." Alkali ya gamsu, ya dubi Momy ya ce, "Ya a ka yi a matsayinki na mace ki ka daurawa 'yarki aure da wani bayan kin san Babanta ya daura mata aure da wani?" Ta ce, "Ni ba ni na daura mata aure ba, kanin Babanta shi ya daura mata aure, bayan yaga iyayen יי angon sun ba shi sadakin aure.' Alkali ya ce, "Meye dangantarki da angon? Ya kuma aka yi ki ka hada auren?" Та се, "Kamar yanda na ce Imran dan mijina ne, na dade da yabawa da dabi'unsa, nasan idan har Mabaruka ta aure shi zata yi farin ciki ba gidan da zata ji dadi irin BD TDIN SUE gidansa. ВРАве ua'nd idanrm snjswinlsa sua enui an 123 WAYE ANGON? Maryam Ja'afar Saboda yanda yake sonta da kuma ingantaccen ilimin addini da ya samu, kuma yana aiki da shi. Imran yaro ne mai nutsuwa da hankali, yana da tausayi matuka. Idan suna wasa in ta yanke ko ta fadi ina ganin yanda yake damuwa da ita, duk yanayinsa ya sauya duk da lokacin yana shekara sha takwas tana da shekara takwas. Ya taso da sonta da tausayinta, duk in yaje ya dawo zai nemeta, sannan yana da matukar saukin kai da hakuri, zan iya cewa ba wanda yasan Mabaruka da yanda zai tafi da ita sai shi. In ranta ya baci yasan yanda yake lallashinta, ita kanta tana kasancewa cikin farin ciki tare da shi, har ta girma ta kammala Sakandire. Na barwa kaina suna son junansu ne kamar yanda shi ma Baban Imran yake zato, wata rana ya gansu tare. Yanda yaga suna nishadi da walwala fuskokinsu a kan na juna suna sakarwa juna murmushi, ba su san da kowa 124 WAYE ANGON? gabansu ba. Maryam Ja'afar Ina kicin ya shigo ya same ni fuskarsa da farin ciki ya ce, "Kin san me?" Na ce, "A'a." Ina kallonsa. Ya ce, "Wani abu nake gani a gidánnan, ban sani ba ko ni kadai na gani." Na ce, "Me kenan?" Hannuna ya jawo ya kai ni inda suke ya ce, "Kalli ki gani." A lokacin sun koma suna hoto tare, da ka gansu zaka fahimci akwai wani abu tare da su, na juyo ina dariya na ce da shi. "Ai in wannan ne ni na ma saba da gani kullum, kai ne dai ba ka gani tunda ba zama ka ke ba." Ya ce, "Ki ce haka suke amman ba ki taba sanar da ni ba da gaggawa."Ya ce, "Ba ki fahimci komai ba ne?" Na ce, "A'a shakuwa ce tsakaninsu." Ya kara da cewa, "Da soyayya kuma." Na zaro ido ina kallonsa, na ce "Iye!" Yayi dariya ya wuce, ya zauna yana cewa "Yes." Ni ma na zauna ina farin ciki, na ce "Amman ya aka yi haka?" Ya yi dariya ya ce, "Ikon Allah mana, amma fa 125 WAYE ANGON? Maryam Ja'afar zan fi kowa farin

Chapter 5 of 9