Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
7 / 8
na jiyota shine abin ya dauremin kai nake son in tabbar da maganar daga gareki. "Amma jeki kiyi sallar ina jiranki”. "To" nace dashi yayin dana hanzarta ficewa daga dakin, ka'idar gidan ne a duk lokacin da aka idar da sallar magariba, akan zauna ayi ta karatun Alkur'ani kowa yake zuwa ana biya masa war lokacin sallar isha'i tayi dan haka yau dinma haka aka yi sai bayan mun yi sallar insha. Addu'o'i muka fara yi sannan Alhaji ya juyo gareni, yace Humaira yan makaranta, tun da dai ba'a kawomin sakamakon ba (result) bari to in tambaya na sunkuyar da kaina don hakika har ga Allah na manta tunda babu wanda- aka ma maganar sakamakon na yi dariya nace, la Alhaji mantawa na yi bari in je in dauko maka Na mike na nufi dakina na dauko jakata na fito da takardar na kaiwa Alhajin yana gama dubawa ya shimin albarka ya shiga yabamin. Hajiya ta tambaye shi ko na nawa na yi? A'a kaddai in ce tun da tazo baki gani ba haba Safiya, ai shi dan makaranta kamar wanda ka aika ne da zarar ya dawo ai aiken da ka masa zaka tambayeshi ni kaina dana yi shirui na zaci ke zaki kawomin shi yasa, to ta uku ta zo sai kisawa abin albarka. Alah yasa nan gaba tafi haka dan hakika tayi kokari. Ai ni nayi zatan ta dainayin karatun ne yanzu saboda yadda anaga tayi kiba sai naga ai mai akratu baya kiba. To Allah dai ya taimaka, ya kuma kara bude mata kwakwalwar ya linke takardar yasa a cikin Aljihunsa ni dai dag anan na tashi an nufi dakina na barsu Yaya Auwal-ya shigo yana tambayar Khadija, ina ina tace Yaya ai Yaya Humaira ta yi bacci ina jin shi ya doka uban tsaki. 61 Lubabah! Alhaji ya yi kiransa yace tsakin me ka kc yi, Auwal ko wani abu kake nema ba sai ka hakurcewa safiya ba? in Allah ya kaimu da randa lafiyar. Nan dai Yaya Auwal ya koma dakinshi, amma har ga Allah in banda Alhaji ya sa baki ina ganin da sai ya shigomin dakin. Ina kwance na yi fakarc naji Mama na tambayar Alhaji ko tana wa nazo yace a'a mantawa kika yiw ai meye yake damun kine, an tabbata wannan zuciyar akwai magana, tayi dariya,t ace babu wata magana ji nayi kana ta yabanta, ina tayi kokari a nan Alhaji wancan hutun fa ta biyu tazo, mai makon ta tsaya a ta biyunta ko ta tafi ta daya sai ta cilla har ta uku, kuma ace tayi kokari. Haba Safiya ai yaci a yaba mata kin san shi yadda karatu yake nan dai suka zauna suna ta tattaunawa. A safiyar yau na tashi da matsananciyar ciwan mara, saboda a duk lokacin da zan yi al'ada nakan fama da hakan mama ta shigo ta riskeni ina ta juyi a gado, tace "Ke lafiya?" da kyar na iya buda baki nace da ita "mama marata. Kasancewar ta sanni da ciwon mara sai nan danan ta rude, tace, "Kai na rasa yadda zan yi da wannan ciwon mara naki, bari in kirawo Auwalu ya zo ya kaiki asibiti gashi babu kowa a gidan, kaini dama ba'a tafi da Khadijaba. Ga Alhaji ya fita tun da dukuduku ni dama maganin hausa aka gwada miki, tunda na yi na asibitin a banza. Maryam! Maryam!!" Mama ta kwala mata kira, da gudu Maryam ta shigo tace, "Mama fitsari nake yi" "То maza ki kirawomin yayanku, kice ya zo ya kai Humaira Asibiti. A rude Yaya Auwal ya shigoda ga shi sai gajeren wando da yar T. Sheat yace, "Me ya same ta Mama?" "Cikinta ne yake mata ciwo dan Allah yi maza ka shiryo kazo ka kaita asibiti, akwai Allurar da ake mata kawai ka kaita wajen doctor Sa'ida kwai allurar da yake mata ako da yaushe. Da sauri yaje ya ziro doguwar riga irin jallabiyyar nan ko T. Sheat din ciki bai fiddaba. Cak ya daukeni kamar wata 'yar yarinya. Dama tuni Mama, ta dagani ta shiryani tsab, saboda haka ko da jinin ya zubo babu matsala, ba zai bata ni ba. A asibitin ma bamu bata wani lokaci ba muna zuwa muka ci karo da likita Sa'id yana ganina yace. "Waww Humaira time is coming ko?" bai jira wata magana ba ya jamu zuwa daya dakin dake kusa damu duk abin nan ina rungume a jikin Yaya 62 Duk Wanda Ya ce Namiji Uba Ne...... Auwal likitan ya fita da sauri zuwa can ya shigo rike da allura a hannu ya kalli Yaya Auwal yace, to Auwal dan gyarata kafan zata karbi Allura cikin sauri ya dan bude gefen duwawuna kadan aka yi min. Amma hakika da ina cikin hayyaci na ne da ban amince ba shi kansa likitan ya zaci uwar mu daya Ubanmu (faya dashi, tun da ba kowa bane ya san dangantakarmu dashi. Daga nan ya umarci Yaya Auwal da ya kwantar dani nan da minti goma sha biyar zan ware in sha Allahu. Hakan kuwa aka yi ban kai bama minti goma sha biyar din ba jinin ya tsinke nan da nan marar tawa ta lafa saı da na dan dara hutawa sannan muka taho gida. A hanya ne yake cewa dani, Dama haka kike fama da ciwon cikin nan, har likita yasan matsalarki amma ni da nake gidan ban sani ba?" na sinkuyar da kai cike da matsananciyar kunya dan ni a zatona yasan abinda ya sani ciwon cikin danni in banda ya gayamin ma shi ya bude gurin da akamin allura da ban sani ba balle ya yi tunanin ko saboda haka ne na ke jin kunyarshi. "Amma fa gaskiya na tausaya miki gaskiya ya kamata ace an yi wani abu, bawai a sami magani na lokacin cuta ba kawai, wallahi Alhaji na zuwa zan gaya masa, gara a nemo maganin da zan rabaki da ciwon kwata-kwata. Nan dai yaci gaba da surutanshi, amma ni nayi shiru in banda tunani babu abinda na ke yi. A haka muka karasa gida. Muna zuwa na wuce dakina dan in yi wanka, in kwanta in huta. Tun da na fito daga wankan na fada gado na yi kwanciyata ina bacci. Bant ashi tashida ga bacci ba sai da yamma likis misalin karfe hudu. Ina tashi na kara fadawa ban dakin na dan watsawa kaina ruwa na sake shiri sannan na zauna na shirya kai na tsab, na dauki wasu kayana na fakistan, irin wadanda ake yayinsu a yanzu. Na tsuke kaina, dai dai da sheap din da Allah ya bani Gaskiya kayan sun bala'in yimin kyau na fito tsakar gida na zauna kai bakace nice nasha fama a dazuba. Nace "Mama wai ina Mary ne?" "Ta fita ina jin ta shiga gidan makota, ba taga yau gidan shiru ba". "Amma Mama bata bin 'yan gidan su bila ko dan wallahi yaran fitinannu nc. Sam basu da kunya. "Ina ai tun rannan da wannan yarinyar ta gidan wacce suke kiranta Abulle ta kwada 63 L.ubabah! mata dutse a kafa har tayi targade, shi ke nan ta daina zuwa gidan. Alhaji ya fito daga dakinshi, nan da nan na durkusa har kasa na gaidashi, danni ban san yana gidan ba yace ya jikin na sukuyar da kai cike da kunya nace da sauki. Dan hakika nasan ya sani nace kai Allah kai ka doramin wannan ace sam mutum bashi da sirri, kai Allah ka yayemin yaci gaba da cewa Humaira ki shirya gobe da safe manu Direba ya kaiki saban gidan Abanki, dazuma muka gamu dashi yake cewa ya har yanzu baki zoba? Alhalin kwana biyu dayin hutu? Shine nake masa bayanin ciwan naki. To amma nace gobe za ki zo ki wuni ko maman taku bata gaya miki cewa Abban naki ya yi saban gida bane?" "Alhaji ni ban sani bama a wacce unguwar ya koma?" "Yana can Ribado Road Gaskiya gidan ya yi kyau Allah kuma ya sanya alkhairi. Ai Maman taki ce wani lokacin sai ita. Na yi juyin duniya taje ta masa Allah ya sanya alkhairi taki. Dan hakika wanan gidan da ya yi duk wani mai kaunar sa ya masa murna. Don wallahi ko alondon gidan sai haka. Amma Mama bata ce da shi komai ba, amma da ganin yadda bakinta yake motsi kasan akwai magana a zuciyarta, dan haka tsagar na tashi na bar gurin ina shiga daki tun kan in shige ciki sosai na ji yo muryar Mama tana cewa, "Haba dan Allah Alhaji, duk abinda yake tsakanina da mahaifin yarinyar nan ai bai dace a gaban ta ka ringa nuna ma taba, meye na cewa wai kayi-kayi in je in masa Allah ya sanya alkhairi naki kana tunanin cewa, ita yarinyar abin zai mata dadi ne? kuma in ca aka yi in banje ba nayi Allah sanya alkhairi gidan zai ruguje to sai dai ya ruguje din. Dan babu in da zani ita dai da ya zame mata dole taje. Dan haka kada ka karamin haka a gaban yarinyar nan. Abin da ke tsakanina daita daban, abin da ke tsakanina da mahaifinta da ban". A nan ne naji wani makokon bakin ciki, kishi mai tsanani ya trnokomin, wai har yanzu uwata bata san ubana kishin Alhaji ya kamani, na ji kamar in tafi in bar masa gidanshi sai na ji ma kamar da gayya yake gayamin cewa mamana taki zuwa, gidan mahaifin nawa wato shi ya nuna min cewa yana so in san har yanzu uwata ba kaunar ubana take ba Nan take nace wai ni 64 Duk Wanda Ya ce Namiji Uba Ne...... mc yasd da ta nuna bata san shi ma ya dage, ya aurcta. Rabonki sjiw ata zuciyar ta bani amsa fakat wanan shine amsa. A washegari da wuri na kammala da shirina cikin wani hrdadden dinkin shadda da ake mata hadi da code lace. Hakika dinkin ya hadu, duk yadda akc tsammani ya wuce nan. Na fito shirye tsab, yayin da mukaci karo da yaya Auwal a tsakar ida yacc, "a'a Humaira manya ina kuma za'ad osa yau. Na dan kaleshi gami da dan kauda kai nace, "Yaya Auwal kenan sai ka ce wata mai yawan yawo. To gidan Abba zani. Zamu dai, wa ai kaiki? Alhaji yace Mani ne zai kaini wane Manun bayan gani, aikin me nake? Bari in karbo mukullin motar ki jirani, hari in yis auri in yi wanka. Nima jiya nake jin labarin sun tare a sabon gidanshi kai amma ina tayashi murna Allah ya sanya Alkhairi amin. Amin nace adede lokacin da mama ta fito daga dakin girki, yayin da shi kuma ya shige dakin Babansa ya gaidashi, ya kuma tambayeshi mukullin motar, yana fitowa ya daga mini mukullin motar yayi gaba yana dariya. A lokacin da ya kammala da shirin shi sai ya fito ya umarceni da in fito mu tafi Maryam ta fito a gujc tace "Yaya Auwal dani fa za'aje ka tsayani in shirya", Yace, "da kinsan zaki kika tsaya wasa, yi sauri ki shirya ina jiranki". Mama tace "Ji yadda ka bata rai kana magana sai kace mai magana da sa'arsa ke kuma kiyi sauri ki fito ku tafi ke kuma Humaira ai kun je kya gaida Baban naku ki kuma gaida lya da kyau. A zahiri wannan abu yakan dauremin kai, sam mama bata son Abbana, amma tana tsananin san mahaifiyarsa, yayin da ita kuma lya tana nan tana ciki da bakin cikin yadda Mamana taki danta fafur, duk da irin wahalhalun da yake sha a kanta. Nan dai na amsa mata, muka yi mata sallama muka tafi. A hanya ne Yaya Auwal ya shiga yimin shirarraki, yace, "Yauwa Humaira wato shine rannan kika shanyani daga kije kiyi sallah, shi kenan ban kara ganin kiba" "Amma fa yaya Auwal kasan in muka idar da sallar magariba anan muke zama muna addu'o'i da karatu har lokacin sallar insha'i. To yanzu ana zazzaune, sai in tsallako in taho Yaya ai sai sù Alhaji ma su zargi wani abu. 65 Lubabah! A'a to in sun zarga meyc? kika sani ko ayi mana zargin alkhairi a'a Yaya irin haka ai sai kasa a zargeni ko ma soyayya muke (Hakika ni na san abinda Yaya ya ke nufi kenan, to amma na yi kodarin in nuna mas aban san inda yasa gab abane, dan kada yayi saurin gane ni mai wayoce) Ya dan waiwayo ya kalleni, gami da kashen ido, kasancewar a gidan gaba nake da zama yace, "Allah ko?" Ashe dai kin san soyayar da har kike zargin za'a zargeki da ita. Ni na yi zatan ma baki san taba. Nan da nan na ga ne cewa lallai yaya mai wayo ne,w ato ya dagoni ke nan. Nan da nan na sunkuyar da kaina. A hankali muke tafiya sautin kida mai ratsa kwakwalwa yana tashi, ya sake lumshe ido yana murmushi yace, "Uhm, ina tambayarki shin ita soyayyar kala nawa ta kasu? A'a ni yaya wallahi ban sani ba. To shi kenan abar maganar wata rana zan turaki gonarta, in kinje kya gayamin kala nawa kika noma". Na tuntsire da wata mayaudariyar dariya nace "Kai yaya ke nan" ita kanta magana ta wata siga ta daban nayita. Haka muka tafi muna hira har muka karasa kofar gidan. A falon Hajiya lya muka fara masauki, bayan mun gaidata ne take cewa, a'a. Ni wannan shirin ya yi min, ni badan bama kada ace na yis aurin karaya, daba sai ince na yafe auren naka ba, in maka can ji da wannan kwakyalarba. Na kwashe da wata irin dariya mai sanyin sauti, nace. "Amma fa Hajiya Iya kin gama dani, kuma gaskiya kin sai dani arha, in banda abin ki ina ni ina auren Yaya. Yaya ai Yaya nane ni kuma kanwarsace, ko Yaya, ai bama haka da kai ko? wani irin matsiyacin kallo ya watsomin mai hanzarta ratsa zuciya, baice dani komai ba ya juyar da kansa, zuwa ga Hajiya Iya yace Hajiya in kinga hakan ya dace ba sai ayi ba. A nan dai muka dan taba hira sannan muka karasa cikin gidan. Zaune a falon Hajiya Rabi Nasir ne kishin gide yana ganin mu ya hanzarta, tashi zaune tamkar marar gaskiya. Nan da nan ya shiga kwalawa Hajiya Rabi kira, wai tazo tayi baki, da ganin idanshi kasan akwai munafunci a cikinshi, dan kuwa kiran da yake kwala mata wata siginace ya ke mata, t ahanyar yaudara wato duk abinda take shirin kawo masa ta san dai akwai baki. 66 Duk Wanda Ya ce Namiji Uba Ne..... A nan ne ya shiga wangalc baki, yayin da ni kuma nasha kunu babu wata alamar fara'a a fuskata na zauna kan kujcra na gridashi, tunda g anan ban kara cewa komai ba. Shi kuwa yaya Auwal hannu ya mika masa suka gaisa. Yayin da suna cikin gaisawa hajiya Rabin ta fito. Na durkusa har kasa na gaida jta (Dan hausawa suna fadin durkusawa wada ba gajiyawa bane). Na zauna kadan ina jin su yaya suna hira shi da Nasir. Nasir ya dago kai yana murmushi, yace Malama Humaira 'yan makaranta. Ya karatu?" Na doka masa harara nace lafiya lau. Yayin da na mike gaba daya na nufi waje kai tsaye na lura da wani dan bangare da ban wanda aka kawatashi, babu tantama bangaren Abane. Dan haka sai kawai na nufi dakin kai tsaye rike da Maryam a hannuna ita kanta Hajiya Rabi tasan jiya ba yau bace shi yasa in taga na nufi dakin mahaifina bata min katsalandan kamar da. Nasir ya leko yace dani Humair ain kung ama da Abban, ina son ganinki in na kalleshi hakika zanso Alade a zuciyata. Na yi banza dashi. A hankali nayis alama, gami da kwankwasa kofar gaba daya. Yayin da Abba ya umarceni da in shiga. Na shiga na durkusa har kasa na gaidashi yace, "Humaira yan makaranta nayi murmushi, yace "Ya karatu?" Nayi murmushi nace "lafiya kalau". "Ya jarabawa?" "Alhamdu lillahi" "an yi abin kirki ko?" E babu laifi Abba nice na zo ta uku Ba laifi kam amma a kara dagewa Allah ya bada sa'a nace, "Amin". "Amma gaskiya Abba gidan nan ya hadu kai Allah yasa rai a ka yiwa. Allah kuma yasa mai amfani ne yayi murmushi yace Humaira Bahauishiya lallai kin iya addu'a to na gode kin ga dai yadda Allah ya yi damu kuma? E wallahi, ai da ma shi Allah babu abinda bai iyaba, Allah dai ya rabaka da mahassada. Amin Humaira yauwa dama ina son in yi miki wata magana, to amma na fi son sai mun sami kamilallan guri, tun da na ga ba ke kadai bace, kuma hakika maganar sirrice, tsakanina da ke to Abba yaushe zan zo duk sanda kika sami dama, dan yanzu bana fita sosai koma bana nan ba sai ki jirani ba. Amma ni dai Humair aina son in ga kin fitar da gwaninki tun yanzu dan gaskiya ina son in ga da zarar kin kammala karatunki an yi miki aurenki, dan gaskiya dukw ata mace bata 7 Lubabah! mutanta sai tana da aure. Kuma nima hankalina yn fi kwanciyа, tun da ke kadai Allah ya bani. "Au wai shin ina takardar sakamakon na kine?" "Tana gurin Yaya Auwal, muna cikin maganar saig ashi ya shigo. Ya durkusa har kasa ya gaidashi ya dan kalleni ba tarc da sakin fuskaba sosai yace, ke kije Nasir na kiranki". Abba ya dan kalleni ya kawar da kai gefe guda, yayin da ya kira Maryam yace, zo nan maryam tawa. Ni duk naga yau kinyi sanyi sai kace wacce aka yiwa wani abu yau ko gaisheni ban ji an yiba. Maryamt aje ta zauna kusa dashi tana murmushi, amma ba ta ce ko mai ba. A hankali na kara kallan Abba muka hada ido, yace, "Ke ba kiranki ake ba? "Na dan bata rai nace Abba to ni in naje mai zan masa? Ya yi 'yar dariya yace "nasir ya kasa ganewa, nace dashi ya guji mace da sharrinta, na fada masa ba daya ba ba biyu ba. Nace in har ya nemi yarinya ta nuna bata sonshi, to ya rabu da ita. Dan wallah in har ya dage, tofa karshensa shine a wahale, dan ko ta dawo tace tana sonka aikin banzane yaudarace kawai. Amma ai shikenan. Hakika naji dadin wannan magana ta mahaifina, dan hakan ya nuna bazai min auren dole ba. yayin da na lura da yadda Yaya Auwal yake fara'a ganin cewa Abana bai goyi da bayan abin ba. Abba yace da Yaya Auwal ina takardar Humairar ne? tace tayi na uku ko?" Yaya Auwal ya yi murmushi yace E Abba amma kuma na manta takardar a gida, in mun koma na kawo maka yace 'to'. Abba yaci gaba da cewa Auwalu kai namiji ne in har kuna shiri da Nasir ka gaya masa gaskiya. Dan gaskiya ni ba zan yiwa 'yata auren dole ba Yaya Auwal yayi murmushi ya kalleni. Abba ya dan doki Maryam a baya yace ke dai Maryamw ani lokacin kin cika muskilanci. To ku tashi in zaga daku ko ina a gidan ku gani kai ammafa wallahi gidan ya bala'in tsaruwa yadda baa tsammani dan ni komai kwancemin ya yi, hakika, duk wanda yaga gidan yasan mai gidan ya gama hadewa, ta ko ina. Dan kam babu ce kawai babu agidan, amma komai ya gama tsaruwa. Nan dai muka kara sawa abin albarka daga nan muka zarcc dakin Hajiya iya harşhi Abban. Nan ma mun jima 8 Duk Wanda Ya ce Namiji Uba Ne...... muna hira ta dubi Abba tace, ni Alhaji, ai da kiran Alhaji Safiyanu kayi kuka shirya yiwa yaran nan aure, Abba ya yı dariya yace haba Hajiya, ai ni an daddara da yiwa aure katsalandan in har suna son junansu har sai mun yi shawara Hajiya ai su za su je su shirya kansu, tukunna. Aini Hajiya da hakan zai kasance da nafi kowa so. Don wallahi yadda Alhaji Safiyanu ya rikemin jinina tamkar nasa, ai kowani na shine yace yana son 'yata, kuma suka dai-daita ai ba zan hana shi ba balle kuma 'yar cikinshi. Ni dai auren dole ne kawai ba zan wa 'yata ba. A zahiri ba karamar kunya bace ta yayyameni, shi kansa Auwal din na lura da irin tsananin kunyar da ta kamashi, nan dai muka mike gaba daya muka fice, Hajiya lya tace, "Ja irai suna so suna kaiwa kasuwa" Aini Alhaji tuni na ganesu". "Tо Hajiya mudai fatanmu Allah ya hada kawunansu. 69 Lubabah! un daga ranar Yaya Auwal ya shiga nunamin wasu T alamu amma ya kasa tunkarata gaba da gaba ya gayamin komai yake tsoro oho? Ana saura kwana shida mu koma makaranta ne Aba ya aika a gayamin cewa Hajiya lya bata da lafiya. A rude naje na sami Alhaji na gaya masa, a lokacin direban Abban ne ya zo ya sanar dani Yaya Auwalu na falon nan yace wa Alhaji ai sai mu taho tare dashi. Gidan baya na shiga na yi zaton zai shiga gidan gaban da yake a motar Abban zamu tafi amma sai naga ya shigo bayan shima, Alhaji ya biyo mu abaya yana bawa Auwal sakon ya gaida masa da Abban nawa, ya kuma yiwa Hajiya Iyan sannu suma suna nan tafe shi da Maman da daddare. Ta yi dare-dare bisa gado na shiga ina murmushi nace, a'a duk ciwanne haka? Ya jikin tace da sauki nace ni nayiz atan zan zo in same ki a kwance sosai, Abba duk yabi ya rude, ashe ma murace kawai take damunki? Y ajikin tace da sauki yayin da ta kama tari nace, ke wallahi hajiya lya haka kike, shekara sittin da hudu kawai duk kin bi kin kwararrabe wannan in kika kai dari kuma ya ke nan? Ta dan yi murmushi tace karfin hali tace, kai ya dai 'yar nan shekara sittin nan take? Yaya Auwal yace, Ai kuwa yanzu take ganiyar ta, ni dana shirya auren yanzu, ba ita zan kwasheba. Tace ni na yafe gadai wacce na bakanan dan in fanshi kaina. Na dan yi dariya nace, ke Hajiya Iya in banda abinki an taba fansar kai da maganar aure ne?" "E ni na fanshi kaina ta bani amsa. "Yanzu dai kam jiki da şauki Allah ya kara lafiya amin summa amin mun jima muna hira da ita, sannan na koma cikin gidan muka gaisa da Abba sannan muka tafi. Tun da muka dawo Yaya Auwal ya tsayar dani a kofar gida yake tambayata a kan lallai sai na gaya masa saurayina. Na yi dariya nace, "wallahi Yaya bani da saurayi". Yayi murmushi yace, "Kai Humaira ki gayamin gaskiya. Allah nasan ba zaki rasa ba koda a boye ne, yanzu shi Nasir a wane matsayin yake? "Ni wallahi Yaya Auwal ka daina yimin maganar Nasir Nifa ba saurayina bane makwawącina ne shi kawai. Ni kuwa wallahi 70 Duk Wanda Ya ce Namiji Uba Ne...... yayi ya gama ni fa na gaya maka bani da wani saurayi". "To ai shikenan tun da baki da saurayi zan yi kokari in samo mikı bai dace ace kyakkyawar mace, kamar ki ba ta zauna bata da saurayi". Nace "Allah ya kaimu lokacin. "To Yaya ni zan koma gida" "Au haka ma zaki ce muna tsaye muna hirarmu shinc zaki gudu gida?" Amma shi ke nan sai an jima da yamma ma hadu. Ni dai na shige cikin gida yayin da shi kuma ya shige dakinshi. Tun da na shiga gidan zaunc muke a tsakar gida ni da Mama da Maryam muna hira Nace Mama ni na rasa abin da yasa yanzu Maryam in mun je gidan Abba bata sakewa sosai. Tayi tsagal tace, "cab bayan hajiya Rabi ce tace wai na cika shishshigi, sai kace Ubana, wai in ta kara ganin na zo gidan ina damun mutane da surutu sai ta yankani". "A'a bazata yankan keba Maryam (Mama ta fada) wannan ankwai mahaukaciya, to in banda shirme irin nata Maryam dinma abar ayiwa kishi ce. To ai sai ki dana zuwa, kiyi zamanki gidan Ubanki, bamu gaji da keba, dadin abin kema da na ki Uban. (Da farko abin ya dan sosa min rai sai naga kamar da gayya Hajiya ta fadi hakan). Na yi murmushin, karfin hali nace, "amma Mama bai kamata ki biyc mata ba tun da dai kin san sam ba wani tunani take da shi ba ai ni tuni na dawo daga rakiyarta, don hakika nali lajiya Rabi tunani na rasa abinda yake damunta". A to ai gashi nan har yanzu jiya wa yau. haka dai muka zauna muna ta hira, a kalla mun fi awa daya a tsakar gidan saboda ko mun shigama babu wuta. Taci gaba da irin rurin kidan da ta saba, wato wayar salula Yaya Auwal Hajiya tace kai ni na rasa dalilin da yasa Auwalu yake barin wayar nan a kunne kuma yayi nisa da ita su kuma masu bugowa ga shegiyar kwawar tsiya, in sun jima ba'a dauka ba sun ringa yi kenan. Humaira maza ki je ki dauka in kuma bata kusa shi kenan in sun gaji sa daina. To gida ne babu kowa Maryam ma in tana nan me ye in ba shirme ba. Ai shima Kawun nasu yayi shirme da yaga an kusa komawa ba sai ya dawo da suba amma yabar yara ko sai ana gobe za su koma zaida wo dasu. Tun da Hajiya tace in je in dau waya naji gabana ya yanke ya fadi. Ba dan komai ba sai dan ina gudun 'yar gidan jiya wato 71 Lubabah! kada in ganshi ayanayin da na ganshi ran nan. Na shiga falon hade da sallama, amma ba'a amsa min ba, shiru na duba ko ina a falon babu alamun ga daga inda karan yake, dif na ji wayar ta daina rurin. Na juya zan tafi,s ai da na zo daf da kofar fitar sannan na kara jiyo sautin kidan ta daga cikin daki, na yi kamar in share wato in fice kawai sai na yi wani tunani ya zomin ta iya yiwuwa bama ya fakin yana can waje dan haka kai tsaye na dama kai cikin fakin. a Turkashi, mai zai faru ai Yaya Auwal na gani ya kwanta bisa gado yayi dai-dai dashi da shigar da n aganshi rannan wato kwance ya ke daga shi saig ajeren wando. Na yi kamar in koma sai na tuna cewa in har wayar taci gaba da kida tofa Mama zata iya tambayata dan me ban dau wayar ba? koma tace dani in tashi in dawo in dauka. Na dauki wayar a hankali na

Chapter 7 of 8