Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
5 / 8
ikon Allah Hajiya yana zuwa gaban mahaifin nata sai yayi masa kwarjini, duk abinda Uban yace, sai yace to suka ringa juyashi kamar aikin asirida ga karshe ma sai aka ce an bashi ita, kadama ya matsawa kansa, an ya fe mas akomai, amma sai yace dasu shi dai ya gode amma zai yi iya kokarinsa wallahi hajiya daga kayan lefe sai sadaki kawai ya yi shi kansa lefen ba wani na azo a gani ba yayi sai sadaki da ya bayar dubu goma, da dubu biyar ma zai bayar da kyar muka lallashe shi ya bada dubu goman. Ya karayin dariya yace, to dan Allah Hajiya kowa ya ji yadda auren ya kasance ai yasan daddarace kawai wadda ta riga fata. Ita kanta in banda gata ga yadda take, muni kamar biri wallahi babu yadda za a yi tace zata auri Sulaiman dan yadda take da shegen dogon buri a zuciyarta wallahi hajiya yawanci irinsu sai dai kawai a yi sha'ani, wai mutumin birni ya ga na kauye. 41 Lubabah! Ya juyo da sauri ya kalli lumaira, a lokacin da ta mike tsaye da niyar zata fice daga dakin yace, ke kuma ina zaki ana Zaune ana hira mai makon kema ki kawo mana labarin dakika sani na auren kaddara da ya faru a Kano. Yama sata dariya, ita a ganinta, ba komai bane ya sa ta dariyar face yadda taga ya zauna, sai zuba yake, ya kanyar rani, badan komai ba sai dan ya sami shiga a gurinta, tabbas da yasan yadda dawan garin yake da bai so shirya soyayya da ita ba. Hakika da ya ji labarinta da ya yi wani tunanin, to amam shi mutum in yaga abin da ya ke so idan shi rufewa ya ke, sam sai ya ji shi komai ma ya yi masa dai-dai, shi yasa bahaushe ma ya ke cewa so hana ganin laifi, ba mamaki ko ta bashi labarin nata shi yaga hakan ba komai ba ne a gurinshi. Ya dubeta yana murmushi yace, "tunanin me kike yi? Ко an tuno miki da kanawa, hankalinki ya yi can. Allah ni dai ki shirya dan gobe-goben nan rake son jin labarinki tun daga farko har karshe dan haka ki kiyaye banda ragi, kin ji ko. Dan in kika rage abu daya ko kika boyemin, zai iya ruguza ginin zuciyata guda goma. Yaran banza, yaran wofi ya ji ya doki dodon kunansa, da muryar mahaifiyarsa. Hajiya taci gaba da cewa "Kai yanzu sai ka zo cikinmu ka zauna ka kama surutai na babu gaira babu dalili. Da kake cewa sai ta sanar da kai labarinta, ji nake nice na gargadeku da kada ku takura mata akan ta baku labarinta. Na ce ku bari, in ta kara sakewa ita da kanta, dan kantama zata so ta bada labarin nata. Amma ni na rasa irin wannan naci naku dan Allah tashi ka fita kabawa mutane guri. Ya dago kai ya kalli Humaira yayi murmushi yace Hajiya in na koma gida dawa zan yi hirar, dama Hajiya ina son in bawa Shafa'atu mukullin gidan taje ta share min shi dan sun barmin shi kaca-kaca", "Ka bayar gobe sai su tafi tun da sassafe, ita da Humairar" "To Hajiya yayin daya kara dago kai ya kali Humaira, ya kashe mata ido gami da tsareta dasu. Ya dubi Hajiya yace, "Hajiya wallahi bana son yawan yawo, a wannan lokacin kada 'yan tsegumi su ganni su tafi su kaiwa Khadija labari, duk subi su ishi mutane da magiya, ni kuwa lajiya wallahi na sayar akai kasuwa. 42 Duk Wanda Ya ce Namiji Uba Ne...... "Ya Rasulillahiw ai dan Allah dan nan mai yasa baka da kunya ne, ni kake yiwa irin wadannan surutan kamar an kwence maka takunkumi ko kuwa hirar taka daban? In Humairar ka ke so kabawa labari, ka jata can mana ka bata, ka zo ka cika mutane da shegen surutu, kace wannan kace wancen. Ni dan Allah ku tashi ku bani guri har Humairar, itama dan taga Shafar bata nan ne shi yasa ta shigomin". Ya sunkuyar da kai cike da matsananciyar kunya. Hakika babu tantama Hajiya ta dago shi shin shi kuwa wane irin abu ya ke yi haka, har Hajiya tayi saurin gano shi. Hakika shi so ba'a sa masa shamaki, ya tuna yadda da yake tsananin kunyar ya zauna yana zuba haka, kasancewarsa na fari agurinta, amma sai gashi yau ya zauna yana ta zuba ya kurnar rani maganganu barkatai da wanda ya dace dama wanda bai dace ba. Kuma hakika shi kansa yasan saboda Humaira yake irin wannan surutan, nan dai ya tashi a sanyaye yabi bayan Humaira, wacce tuni ta fice cike da matsananciyar kunya. Ya sameta kwance a dakin su ta daga kanta sama tana tunani. Ba komait ake tunawa ba face rayiwarta da tsohon mijinta an ya kuwa duk maza ba mayaudara banc. 'T'a tuna irin gigin da mijinta ya ringa yi mata amma tashi daya haka ta kasance tsakaninsu wanda take ganin sam Fahad bai kama kafar-kafar irin son da mijinta ya nuna mata ba. Ya yi gyaran murya, yayin da ya yi mata sallama bata ji ba yace Malama Humaira tunanin me ake ne ko kanawa`ne suka murdo kanbunsu. Ni dai ina rokon mutan Kano da su rufamin asiri, su barni in cika burina. Ya kamata ace tun yau kin fara bani labarin ki kinga gobe sai ki karamin. Dan na lura da wannan cikin tabas akwai maganganu masu yawa da suke kunshe a birnin zuciyarki. Gara a daure, a amayar min dasu ko an samaw abayin Allah matsugunni. Ya Salam ta fada cikin siririyar muryarta, da takan yawan rikitashi, hakika ko rankane ya baci da zarar kaji wannan mu.yar, ta wadatar dakai, ka ji bacin ran ya gushe, ko da ba'a lallasheka ba yaci gaba da tunani aransa yayinda taci gaba da magana tana cewa, "Wai mai yasa ka damu da kasan labarina. To amma tunda ni na maka Alkawari, zan fara gutsuro maka 43 Lubabah! labarina. Amma kada abin ya baka mamaki, in ka na canja wasu guraren in anzo bawa su hajiya labarin saboda kunyarsu da nake ji. Amma in sha Allahu kai babu abinda zan boye maka sabdoa na lura da wasu abubuwa da dama da suka ringa wakana ya yi murmushi yace, "Na kwa gode da aka yi saurinf ahimtata yayin da ya sami guri ya zauna taf ar abashi labari kamar haka. a le a fito da gudu daga dakin soron kofar gida, in da N akasari a nan muke haduwa, mu da sauran yara 'yan unguwa muna yin wasa. Yau dinma wasan muke dan a lokacin babu wata makaranta da nake zuwa saboda na gama karatuna na F'iramare. To a yau mahaifina ya zo ya kawomint akarda ta shaidar na ci makarantar gaba da Firamarc. A nan dakin ya sameni ya bani shine na shiga cikin gida da gudu ina murna, dan in nunawa mahaifiyata. Na shiga kwala mata kira ina cewa Mama-Mama. Ban daina kiran sunanta ba har sai da na ganni tsaye a kusa da gadan da take kwance tana bacci. Nan ma ban hakura ba na shiga fadin Mama! Mama!! Mama!!!. Ta tashi ranta a bace tace, "waike wacce irin yarinyar banza ce ba na hanaki tashina daga bacci ba? Na gaya miki muddin kika sameni ina bacci, ki hakura da duk wani abu da kike san gayamin, ki bari sai na tashi. Na yi tsagal nace Mama dama yanzunnan Abba ya zo ya kawo min takardata shaidar naci makaranta ta gaba da Firamare, yace garin Babura naci. Nan take ta bata ranta, na rasa dalilin da yasa ako da yaushe na yiwa mahaifiyata maganar mahaifina sai in ga ta bala'in bata ranta, sam bata kaunar taga ina kula mahaifina. Alhalin ni kuma ina son Ubana, kamar yadda yake nunamin so 44 n n a e Duk Wanda Ya ce Namiji Uba Ne...... A kowane hutu Yaya Auwal ne yakc zuwa daukata, A amma wannan hutun Manu Direba shi ya zo daukata, a lokacin ina aji biyar na sakandire kasancewar Yaya Auwal yana makarantar B.U.K. yana karatun Digiri dinshi na biyu. A ko da yaushe yaya Auwal yakan rubuto min wasika akai, akai dan tambayar lafiyata, da kuma karatu. In kuwa ya zo gida, lokacin muna makaranta, sai ya kawomin ziyara kafin ya tafi wannan hutu ne wanda in na koma aji shida zan shiga. A gaskiya wannan hutun na yi kyau, har na gaji gashi kuma na fara cikar budurci. A wannan hutun ya zo dai-dai da hutun su yaya Auwal, dan haka a ranar da na dawo shi kuma washegari ya dawo ina kwance a doguwar kujera ta falon Alhaji a lokacin mun hadu da yara, suna zaune suna yin Video Game ni kuma ina daga kwance rike da lemon fata a hannuna ina tsotsa. A lokacin na gama hadewa cikin wasu kaya riga da siket farar riga bakin siket. Abba ne ya kawo mana su iri daya ni da Khadija da Maryam. Hakika kayan ba karamin kyau suka yi min ba. "A'a don Allah Yaya Humaira ba na kada shi ba?" Na ji Khadija ta katsemin tunanina a lokacin na shiga tunanin ya kamata da yamma ko gobe in je in gaida Abbana". A'a Habibu nifa bana san wayo" "Ke fa baki gani ba Yaya, gini fa na hada kuma tunkan ya fadi na yis auri an daga shi, shine za ta ce wai an fadi, ni shiyasa bana san yin wasa da Khadija, wallahi ta fiye runton tsiya". "To in dai fafa za ku yi ku hakura haka" Auwal ya shigo yana murmushi yace ku yaran nan babu wanda ya iya yiwa mutum sannu da zuwa tun dazu na dawo amma babu ko sannu da zuwa. Gaba daya muka mide muna dariya gami da yi masa sannu da zuwa. Na koma na zauna adoguwar kujerar, Yaya ya zo kusa dani ya zauna wani irin kallo da ya wurgomin, ban san lokacin da na jefar da lemon hannuna ba saboda kidima. Domin hakika kallan kallo ne mai kunshe da fassarori, daban-daban. Hakika nasha jin labarin irinw anan kallon a bakunan marubuta dan shi suke zaiyanawa 57 Lubabah! a duk lokacin da masoya suka hadu kaji ance an kashe ido ana kallan mutumg ami da murmushi. Amma ni idona bai yi sauring askata hakan ba, saboda ina ganin bata mana 'yar haka a tsakanina da Auwal domin ni a ganina mun zama kamar uwa daya uba daya. Ya lankwasa murya yace, "Humaira 'yan makaranta, tun yaushc aka dawo? Nayi murmushi nace, "tun jiya" yace "yanzu jiya jiyannan kika dawo amma tamkar kin yi,kwanaki kin yi fes dake haka" murmushi kawai nayi yara suka shiga tambayarsa mai ya kawo musu, yace "Ni babu abinda na kawo muku sai kace wanda na bar garin koda n kung ana kwana biyu ban zo hutun karshen sati ba. Ai jarabawa ce ta tsaremu bawai garin na bari ba". Ya kalleni yace gaskiya Humaira kin kara kyau". Habibu ya kaiwa Khadija duka a baya tace. "Aaa... wallahi saina rama Yaya Auwal yace kai Habibu mai yasa ka daketa, yace "yaya tankwabata tayi na fadi". "Shine kuma ka dake ta, to shi kenan ku ajje ku fita wasanku. Nan dai suka fice suna gugunai ya dubeni yana murmushi yace in je muyi aga wanda ya iya. Nace "Yaya ni wallahi ba zan iya yi da kai ba". Ya yi murmushi yac, "saboda me, Humairan Yaya?". A hankali na dago kai ma kalleshi, dan maganar ta burgeni. To amma abin yana dauren kai yau sai wani iri ya ke min kamar yana gaban budurwarshi. Ya ce dan Allah ki sauko mu yi yau sha'awar yin game din na ke yi mama tana can da baki shi yasa na taho nan. A kan dole na zo muka fara muna yi muna hira, ya turkeni akan lallai sai na gaya masa saurayina, wai shi ya gaji da ganina da zarar na gama karatu aurar dani zai yi. Na tuntsire da dariya na ce, "Aure Yaya? Aini Aba da Alhaji duk sun ce sai nacig aba da karatuna, kafin in yi aure dan haka babu wani saurayi da nake kulawa", yace, "Allah ko? To Babban yaya kuma ya ce aurar da kanwarsa zai yi. In ma babu saurayin shi ba sai ya aure ba?" Gaba daya kunya ta kamani. Amma gaskiya Yaya Auwal ya iya dubara da nasan haka ya ke so yace, ai da na ce ma da samari da yawa. Na kwashe da wata mayaudariyar dariya nace, "Yaya ai kana ta dannawa har ka fadi baka sani ba". Na yi hakan dan a bar maganar. 58 Duk Wanda Ya ce Namiji Uba Ne...... haka kuma itama ina sonta a matsayin uwata, kamar yadda take nuna min so amatsayina na 'yarta. Nan dai naci gaba da murnata ta naci makaranta ban damu da laifin da nayi ba na tashin mamanmu dag abacci. Ta dakamin tsawa, tace sakarar banza sakarar wofi. Ai bacin makarantar ba karatun shine. Ba wai kawai a je aci kwaki da kanzo ba a dawo, ba a san komai ba, sai dai a yi ta faman yanga a titi yayin da ta warci takardar a hannuna ta doka uban tsakit ace, "Wai shi Abbań naki har kofar gidan nan ya zo?" nace E mama shi ya kawomin da kansa, ina fada ina murna cike da fara'a a fuskata. Ta kuran ido na dan lokaci sannan tayi kwafa ta shige daki, tana mai gargadina da kada in kara tayar da ita daga bacci". Gikin sanyin jiki nace da ita "to"yayin da na koma can soron kofar gidan na tarar da abokan wasana mukaci gaba da wasanmu. Amma duk da haka ina ciki da tunanin abinda yasa mahaifiyata bata kaunar mahaifina. Ni ba wani bambanci nake nunawaba tsakanin Abbana da kuma mijin da take aure ba. Domin kuwa ya rikeni sosai kamar yadda ya rike 'ya'yansa, babu wani ban banci da yake nunamin. Na fito da saurina, na yi kofar gida sakamakon tsayiwar motar Alhaji da naji muka tare shi ni da yara kannena, muna masa sannu da zuwa. Na karbi jakar dake hannunshi, kai tsaye falon shi muka wuce, Maryam ta fita da saurinta ta sanar da mama dawowar Alhajin, zuwa can sai gata ta fito rike da robar ruwa a hannunta, gami da kofi tayi masa sannu da zuwa ta zauna ta zuba masa ruwan yasha sannan ta sami guri ta zauna sosai. Alhaji da ke zaune a kasa kan kafet ya jingina da doguwar kujera kansa babu hula, wanda sanko yayi masa katutu. Ya dan shafa sankon yana murmushi yace "Naga yau. Humaira sai fara'a take mene ne ya faru ne?" Mama tayi dan murmushit ace," Ai tun tuni in banda ina harararta da tuni ta baka labari, to amma tunda ka tambaya bari a gaya maka dama na bari ne sai ka huta sosai. Daga nan ta bashi labarin samin takardata, ta shaidar cin jarabawata zuwa makarantar kwana". "Ni fa in ce wannan farin ciki yayi yawa". Yana fada yana dariya". To ai shike nan Allah ya bada sa'a Allah kuma yasa hakan shine mafi alkhairi amma dani ina nan ina nema mata 45 Lubabah! makarantar gaba da Firamaren, wacce take cikin garin nan. To amma hakan ma na yi farin ciki sosai, to amma yanzun ma na gamu da Abban nata in yi masa bayani. Ni da na fi son makarantar Shekara, to tsarin makarantar ne baya burgeni wato yadda tsarin ginin su yake amma hakika akwai karatu to amma yanzu in ya bari sai a nema mata Dala ko ba haka ba Mama ta yi murmushit ace duk abinda ka yi ai daidai ne. Allah dai ya zaba mana abinda ya fi alkhairi. Na yi dariyar jin dadı, murna fal cikina yace "Humaira sai ki shirya gobe kije ki gayawa Abban naki, abinda ake shirin yi in sha Allahu nan da litinin ta sama, sai a kaiki makarantar dan bai dace a bari lokaci ya kure ba". Nace "To" yayin da na tashi na fice daga dakin ina ta murna. Gari na wayewa na shiga shirin tafiya can gidan Abbana, Mama tana kalona, amma ko ta tafasa bata ce min ba. Ta dago kai ta kalli Fahad, ta dan yi murmushi tace, ko da ya ke nasan an dan rikita ka. To auren mahaifiyata tuni ya mutu, amma bari dai zan gaya maka komai taci gaba da cewa. Na gama shirina tas da 'yar Atamfata ta Nicam, na dubeta nace, "to Mama zan tafi ta kalleni tace, ke tunda sassafe haka, sai kace wacce za ta je ta tarar da su yabar garin". "Mama ai dan kar in je in tarar ya fita". To in kin je kice ina gaida Hajiya Rabin da kuma Iya. Wato Mahaifiyar mahaifina nace "To". Naje na tarar Abban bayanan duk da tsananin saurin da na ke yi. Da naga baya nan sai kawai na gaida Hajiya Rabin na fito na nufi bangaren Iya. Saboda kwata-kwata matar Abban nawa bata sakarmin fuska shi yasa bana zama a gurinta muyi hira sai dai in tafi gurin Iya in yi zamana in jirashi. Na jiyo tsayiwar motarsa a farfajiyar gidan, dan haka yana shiga cikin gidan sai na biyoshi abaya ba tare da na mása amgana ba mai makon in bishi falon nashi, a'a sai na nufi falon Hajiya Rabin na sanar daita zani gurin Abban, saboda ta yimin gargadi mai tsanani akan kada in sake in je gurin Abban ba tare da na sanar da ita ba, ka jifa yaya Fahad ni da'mahaifina. Sai da ta dan basar dani sannan ta amsamin, ta kuma ce in jirata sai da ta gama abinda take yi tukunna ta tashi tace in biyo ta. Na bita sokai-sokai har falon Abban duk da cewar ya saba ganin rawar kaina da nuna farin cikina a fili a duk lokacin da 46 Duk Wanda Ya ce Namiji Uba Ne...... muka gamu amma saboda tsanan tsoron Hajiya Rabi da na ke yiwannan karan a sanyaye na shiga fakin na durkusa har kasa na gaidashi, ya bukaci in koma kusa dashi na koma na zauna ya tambayeni lafiyar Alhajin. Nace "yana nan lafiya, ya ce ma agaida kai". Yace. "Maman na ki fa da sauran kannan naki suna nan lafiya?" Na ce, "Duk suna nan lafiya. To fa a nan ne Hajiya Rabi ta mugun bata ranta. Na lura da cewa Hajiya Rabi tana tsananin kishin mahaifiyata wanda na rasa dalilin hakan yaya Fahad bafa su taba zama tare ba. Amma bata kaunar taga mahaifina ya nuna kulawarsa ga mahaifiyata. Na sanar dashi sakon da Alhaji ya yomin hakika ba Karaminf arin ciki ya yi ba yace, "wallah ki gaya masa duk abinda ya yi dai-dai ne, ai ya tashi ce ko. nan dai muka zauna muka dan taba hira yace wannan yace wanan ya kuma tambayan wancan ya tambayen wannan. Amma duk da haka Hajiya Rabi bata s amana baki ba. Asalima in ya yi mata maganar kawai sai tace, uhm ko uh-uhm, da ya lura da ita kawai sai ya watsar da ita. Nace dashi ni zan tafi, yà yi murmushi yace, "to Hurnaira Baban naki ya hana in yi miki komai. To amma ga wasu Atanfofi da ha saya mu ke da su Maryam. Ga kuma dubu uku ki ba Maman naku, kice in jini ta biya muku kudin dinkin. Na karba na yi godiya. Amma kallo daya za ka wa Hajiya Rabi ka fuskanci tsananin bakin cikin dake can kasan zuciyarta. Ta hade girar sama da ta Rasa tayi murtuk. Ni dai nan nayiwa Abbana godiya na tashi na tafiyata na abrau ko sallama ban mata ba kamar yadda itama bata yi min ba, amma nasan tsabar bakin ciki ne, sai dai kuya ya kasheta. Tun da tsakanin da da mahaifi sai Allah. Na koma gida cike da farin eiki da murnata na nunawa Mama kayan da na zoda su gami da mika mata kudin nace, "Mama yace yana gaidake, kuma yace in baki wadannan kudin kya bayar da kudın dinkinmu ta ee uhmm, sai kije ki Ajjesu in an bada dinkin an bayar da kudin. Ga yadda ta amsamin aai duk jikina yayi san yi sati daya aka yi ana neman makarantar aka samu, batare da ansha wahala ba. Nan take Alhaji yaee, "А Lubabah! ranar litinin mai zuwa za'a kaini makaranta. Nan na shiga murna ina addu'ar Allah ya kawo ranar. Na tashi tunda asubar fari sabosa tsabar doki, saboda a yaune ranar da za'a kaini makarantar: Tun da duku-duku na shiga wanka na shirya, kafin karfe bakwai na safe na kammala da komai, ni dai kawai ina jiran azo a kai ni makaranta. Na nufi dakin Alhaji don in gaidashi da misalin. karfe takwas na safe ya dubeni ya yi murmushi yace Malama Humaira 'yar makaranta, har an gama shiryawa". Na sinkuyar da kai ina murmushi cike da dokin in ji yace in fito mu tafi, kan ya kara cewa komai sauran yara suka shigo ya dubesu ya yi murmushi yace, "Kun ga har Humaira ta rigaku zuwa nan ya yiwa Maryam wasa, sannan ya juyo gareni yace. "Humaira sai dai kiyi hakuri, don da kyar ne in tafiyar zata samu a yau wato wata tafiyace ta gaggawa ta riskeni. Yanzum nan zan tafi Abuja. Amma a yau zan dawo in sha Allah dan ko siyayyar ban miki ba. Da Auwalma yana nan da ya yo miki, amma ai yau zai dawo dan tun shekaran jiya suka kammala karatunsu. Don haka sai kiyi hakuri sai na dawo koni ko Auwal din sai wani ya kaiki makarantar. Na ji gabana ya yanke ya fadi domin har ga Allah gani nake kamar ba kaini za'ayi ba. Alhaji ya kara dubata yace karki damu kin ji, da zarar Allah ya dawo dani lafiya zan kaiki makarantar. Khadija da Mujahid suka tashi suka nufi dakinmu na yara Nima a hankali nace, "To Alhaji Allah ya dawo dakai lafiya ya ce amin Humaira. Na fito na nufi dakinmu na yara, ina shiga Kadija da Mujahid suka kama yimin dariyar an fasa basu kyaleni ba har sai da suka kular dani. Raina ya yi bala'in baci, Nan da nan na fito fuuu na nufi dakin Mama na sanar da ita abin da Alhajin ya fada, tace to Allah yasa hakan shine mafi alkhairi. Na kara bata rai ya yin da idanuwana suka cicciko nace, "Mama kin ga su Khadija suna min dariya ko?" Tace yi hakuri. To kuma meye na kukan, hako za ki je makarantar kina yiwa yara kuka sa maidake sakarai sam ace baki da hakuri sai saurin fushi ga zuciyar banza. Na góge hawayen da yake a idona. Na ce "Mama dariya fa suke min, ni wallahi bana sonda riya, yayin da na sake ficewa Duk Wanda Ya ce Namiji Uba Ne...... daga dakin, raina a bace, dan ba haka na so ba, naso ta kirawosu ta mammaresu ko tayi musu fada. Na yi wankana tsab da yamma kai ba kace nice na sha kuka dazun nan ba. Na dauki wata doguwar rigata da Abbana ya sayo mana, ni da sauran kannena, na saka, hakika rigar ina matukar santa. Dan in na sata ji nake kamar ba a kasar nake ba. Na dauki jambaki ruwan bula kamar yadda naga manyan 'yan mata na yi na wannan zamanin. Mama ta shigo tace, "Kai 'yar nan da kwainanen tsiya kike, tun yanzu an fara iyayi, irin kune sai shegiyar yanga babu kokari wai ku 'yan sakandire. Na yi dariya na ce, haba dai Mama ai ni ina da kokari, nan dai na gama iya yina a gaban madubi na yi gaba. Na fito tsakar gida na zauna ina shegen kaudi in ce wannan in ce wannan. Na ji gaba daya yara suka shigo gidan suna fadin ga yaya Auwal ga yaya Auwal Nan da nan Hajiya ta dau murna duk da 'cewa ba sosai ba. Amma ta nuna farin cikinta kada ran kada han. Suna shigowa Mama ta tambaye su yana ina?" Suka ce yanzu Saminun bayan gida yace, wai tare suke da Auwalun shi saboda kaya yana can tashar motar yace a turo masa mani ya daukoshi" Tas yi tsaki tace "Shine kuke fadin ga yaya Auwal, ku da ko ganinshi baku yi ba. Ni yanzu bana san in da ya ke ba, amma ku duba can shagon Ema ko yana can gaba daya suka fita da gudu, sai gashi sun dawo tare da Manin, ya karbi mukullin mota a gurin Hajiya. Ya kwashi yara suka tafi,da ga ni sai Habibu kawai aka bari agidan ban damu in jeba saboda na manta dashi hakika na sanshi, to amma tun kan in yi wayo sosai. Nan da nan suka dawo da uban shirgin kayansa, tamkar wanda ya yo cirani. Ni dai na je na durkusa na gaidashi daga nan na kama gabana yace Hajiya kaddai in ce wannan Humaira ce kai amma fa ta girma hutu ta zo muku Hajiya?" "A'a ai ta dawo nan. Habibu ne ya yi karab ya fada ya ce, yauwa Mama ai kinga hakan ya fi. Ni dai nan na barsu. Na ji yara na murnar dawowar Alhaji sama-sama domin ni a lokacin bacci ya fara daukata. Firgigit na tashi, ya lai kuwa ina zuwa yi masa sannu da zuwa ya turo min katan kwali da leda yace, ga kayan tafiya ne, kinga gobe sai ki shirya a kai ki 49 Lubabah! makaranta, amma ina jin mani direba zan bada, da Auwal su kaiki shi kenan ko. Na fito riki-riki da jakar leda a hannu na nufi dakin mama ina murna. Tayi farin ciki gami da murna, tace kin yi godiya ko?" Nace "E Mama, yace ma gobe da safe za'a dauko akwatin da katifar, da kuma bokiti. Na tashi da wuri, a washegari ni na tashi mamanmu, nace ta tashi ta shiryamin kayana, da farko ta dau fada, amma daga karshe sai ma na bata dariya. Bata kulani ba sai da safe misalin Karfe takwas, sannan aka dauko akwatin aka shirya min kayana, aka kuma shiryamin kayan sawar a cikin jaka Mama ta hada mukullan guri daya ta mikomin tace saura ki yadda. Gama naga rawar kanki ta yi yawa Yaya Auwalyace ni na rasa irin wannan murna, karfa kije kwana biyu kisa kwaki a gaba ki cinye ki zo kina kuka ba fa ci muka turaki ba, a'a karatu a ke so ki tsaida hankalinki guri guda kiyi karatu kin ji ko? kada ki zama irin wasu 'yan matan sai shegen ci kamar gara, amma babu karatu. Nan ne aka sa

Chapter 5 of 8