Reading ALAƘAR ZUCI by Mai Dambu Chapter 1 | TKNovels


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

ÿþ"[12/4, 10:51 AM] Firdausi Salis: *ALA˜AR ZUCI*"

Na

Mai_Dambu

Ramlat Abdulrahman Manga.

EJ-1D' FE- DI' 'DDG E3(

"*Wanda ya ce ilimi na da tsada, ya je ya taya jahilci ya ji nawa ne kudinsa?*"

ŠAYA

ATB TEACHING HOSPITAL.

"Aunty Hindatu tayi tana kallona, yadda nayi shiru har likitan ya gama bayani bata ce kome, kafin ta"

"juyawa gare shi tana faWin. ""Yanzu likita ya zamu da ita? Shin zata cigaba da shan magani ne ko zamu barta tana ganinta."" ""Mrs Jama'are abinda nake son ki fahimta, kanwarki bata yi magana ba, don yadda zamu taimaka mata dole sai tayi magana. Sannan zamu san yadda zamu taimaka mata. Ki sani akwai mutane ire-irenta dole sai mun ji meke damunta, shiru da rashin son magana ba zai saka mu san meke damunta ba."" A hankali ta sauke Ajiyar zuciya kafin ta ce mishi. ""Yanzu babu yadda za'a yi kenan?"" ""Ku zaku fara sakata magana, kafin ni na fahimci Matsalarta, a yadda take dai kana ganinta kasan tana"

"bukatar taimako idan tak'i magana haka zamu hakura da ita tunda bata son magana."""

"Mikewa tayi tana faWin. ""Shi kenan Doctor na gode sosai, idan da wani abu zan kara tuntuban ka ko"

"na kawo ta."" ""Ba kome Mrs Jama'are!"" ""Na gode sosai! Muje Lubnah!"" Shiru da nayi kafin ta kara cewa. ""Muje Lubnah!"" Firgita nayi tare da kallonta ina faWin. ""Tow tow!"" Na mike ina mai Waukar jakata. Kura min ido likitan yayi ya tashi tare da nufo ni, ganin yadda ya nufo ni yasa ni yin maza na koma bayan Aunty Hindatu, jikina yana rawa. Itama kallonshi take, d'aga hannunsa yayi nayi maza na n rufe idanuna tare da cewa. ""Kayi hakuri ba zan kara ba, kayi hakuri don Allah kada ka dake ni."" Sauke hannu yayi ya sake murmushi ya ce mata. ""Dawo ku zauna."" Zama tayi nima na zauna ina zare idanu. ""Mrs Jama'are! Kanwarki ce kuwa?"" Kallonshi tayi tana son magana amma ta kasa sai gyad'a mishi kai take. Kafin tayi motsi da bakinta ta ce mishi. ""Kanwata ce Doctor Hadi."" ""Tana da aure?"" ""Kamar yadda na gaya maka tana da aure."" Zai sake magana wayata tayi ™ara, jikina yana rawa na shiga buWe jakata. Bakina yana rawa jikina kamar an saka min wuta na Wauka. Kamar zai fasa min dodon kunnena ya daka min tsawa."

"""Kina ina? Da izinin wa kika fita?"" ""Kayi hakuri Aunty Hindatu ta ce na rakata asibiti gani nan dawowa"

"don Allah ka yi hakuri! Kayi hakuri ka yi hakuri!"" Na fada kamar zan yi kuka, jikina sai rawa yake. ""Na baki"

"minti goma kacal na ganki a gida!"" ""Na gode sosai, Allah ya huci zuciyarka."" Na fada da sauri ina mikewa na dauki jakata. ""Ina zaki?"" ""Zan koma gida ne Ya Hafiz ya dawo;"" na fada ina kokarin barin office din. ""Kamar ya?"" Ban tsaya saurarenta ba. Nayi waje ina kallon agogon hannuna ba shiri ta biyo ni tana min magana. ""Dama baki gaya mishi ba ne?"" Shiru nayi ban bata amsa ba, muka cigaba da tafiya. Riko hannuna tayi da ™arfi. ""Magana nake miki!"" ""Me kike so na gaya miki? Tun da kika ce mun na shirya zamu fita na gaya mishi, kawai baya son ya ga bana gidan ne."" Murmushi nayi na cigaba da tafiya har inda ta Ajiye motarta, muka isa ta bude da key Win motarta, na zaga na zauna itama ta shiga wayata ce ta kuma kara ji nayi kamar zuciyata zata buga. Dauka nayi na saka a kunne. ""Ke wacce irin jaka ce? Har yanzu kina asibitin ne ko ina?"" ""Kayi hakuri gani nan a hanya!"" Na fada ina kallon Aunty Hindatu da taki tadda da motar. ""Ni zaki renawa hankali ki ce kina zuwa."" Amsar wayar tayi da ™arfi ta saka a kunne daidai yana zagina. ""Jaka dabba wacce bata san ana rufa mata asiri ba, akan me Hindatu zata dauke ki? Itama yar kutumar uba, wallahi kin san halina sai na haWa ki da shi tsohon da ya nace sai kin zauna da ni zaki dawo ki same ni, Yar iska me kiba kamar Aladiya!"" ""Alhamdulillahi Ubangiji ya nuna min halinka, Hafiz rashin mutuncin har kan Mahaifinmu ya sauka kenan? Idan aka gaya min ba zan tab'a yarda ba, amma da kunnena na ji wannan ka sani Lubnah ba zata tab'a dawowa gare ka, Hafiz mai kake yi mata ta koma haka?"" Kashe wayar tayi ta cilla min wayar, ta tadda motar muka bar asibitin. Gidanta na ga zata"

"nufa da ni na ce mata. ""Ni ki sauke ni na wuce gida!"" Da mamaki take kallonsu"

"""Gida zaki wuce?"" Na lumshe idanuna, na bude a kanta. Mamaki da abinda nayi take tana kallona."

"""Yanzu duk wannan zagin da ya miki?"" Wayarta ce tayi kara, shi yayi sanadin da tayi shiru ta dauka. ""Assalamualaikum!"""

"""Ki rike sallamarki, wallahi ki wuce mishi da Matanshi, ban da son kai da son zuciya irin naku,mutumin"

"nan ya zauna da yar uwarki bata haihuwa, bata kome sai kishi da yunkurin hallaka mishi mata da Yara zaki dauke ta. Hindatu idan kina son ganin Daidai ki mai da mishi matarsa, idan ma kashe ta zai yi ya kashe ta ai ni na bashi Lubabatu, ko kece? Ka ji min mara kunya? Duk abinda yake mata baku gani kun dauki maganar mutane kun daurawa ranku, kowa ba haka ya zauna a dakinshi ba."" Ranta yayi bala'in b'aci, har Baba ya kashe wayar tana jin wani irin ciwo, haka ta nufi hanyar gida dubu, ni dai na san yau na lahira sai yafi ni jin dadi, wani irin tashin hankali nake ji, ni daya na kasa zama da duwawu na, tsabar tsoro da tashin hankalin da zan gani, a kofar gida na same shi. Ba kunya ko tsoron Allah, tana parking ya zo ya bude min mota, yana kallonta fuskarshi dauke da murmushi. ""Lulu tawa ce, tana cikin rayuwata sai naso tayi dariya ko kuka, sai na so ta ganku daga ita har dattijo da Baban Bauchi, suna tare da ni. Kafin ki iso ga Lulu sai kin fara isa ga Baban Bauchi da Baba Malam, sannan ni mai gayya mai aiki. Ke tinkiya muje, an rufe mata asiri duk da bata haihuwa haka bai saka kun gode min ba, oya muje jakata akwai aiki da"

"hukunci me girma!"""

"""Kai dakiki jahili. Dabba a cikin riga ka sani muna nan tafe bisa kanka ko da mutum kake tsafi muna tare"

"da Allah, na jima ina addu'a Allah ya nuna min wannan lokacin kuma na gani da idanuna, ka sani kayi"

"kuskure, ka fara shiri domin farautar da zamu yi akanka sai ka gudu zuwa kauyen gyatumarka, ai baka yada a kasa ba, ka tsotsa a nono."""

"Daga haka ta koma motar, cike da bakin ciki da damuwa."

Lubnah

"A lokacin da muka shiga cikin gidan, kallona yayi yana girgiza kai. ""Me kika gayawa wancan munafukar?"""

"Ban iya bashi amsa ba, domin abu daya ne zuwa biyu imma ya dake ni ko ya min wulakancin da ba zan manta ba. Kaina a kasa na cigaba da tafiya, a hankali muka bude kofar shiga cikin gidan, kafin kofar ta bude ya wani haWa kaina da kofar ya wanda yayi dai-dai da buWewar kofar. ""Sannu faduwa kika yi?"" Ya fada min, yana kokarin mikar da ni, ya damko hijab dina muka wuce bangarena. ""Tambayarki nake? Me kika gaya mata!"" Ya fada yana ture ni can na fadi kasa. Har lokacin ban yi magana ba. Wayarshi ce tayi ™ara ya Wauka yana me zama a kan kujerar parlourn. ""Na'am Baban Bauchi, wallahi na gaji ina ga zan rabu da ita kawai idan yaso Yaya Hindatu ta nima mata wanda ya fi ni, haba Baba me nayi da zafi haka? Me yasa suka tsane ni? Me yasa basu kaunata? Idan har akan Luluna ne na hakura, yau shekaru hudu kenan tun auro Karima suka juya min hankalin Luluna, waye bai san yadda nake son Luluna ba, Baba kasan me na shirya mata? Umara na je na biya mana ni da ita zamu tafi watan Mauludi amma tunda haka bai musu ba,.na hakura dama tuntuni Ummana take cewa na hakura amma saboda zumunta da kuma karfin soyayyar da nake mata!"" Ba sai ya shiga share kwalla ba, alamar zai yi kuka kamar yadda ya saba, yadda yake jan hanci da shirin kuka yasa na tashi a hankali na wuce dakina, na rufe kofar na zube a bakin gadona. Ban san lokacin da ya gama waya ba, sai dai yadda yake buga kofar dakin da ihun kiran sunana, yasa da gabana ya fadi sai da naji duhu ya lullube min ganina. ""Lubnah!"" Ya kwala min kira, tsoro da fargaba suka kara cika min rai kamar wata marainiya na amsa mishi a sanyayye na tako bakin kofar na bude ina jingina da kofar, wani irin bangaje kofar yayi da kafad'arshi, na zube a kasa kamar wata guna."

"Bina yayi da karfi zai mare ni daga waje aka ce mishi. "" Da dai kada ka wahalar da kanka, dukarta dai ba zai cigaba da yadda muke so ba, ka sake ta mana darling."" A fusace ya juyo yana kallonta. ""Da kin kyale ni na taka yarinyar nan, ta saka sai kukan karya nake a gaban wancan tsohon nata, kina tsammanin akwai mai cire ki daga wannan ukubar nawa ne? Kaf duniya babu yarinyar baki ga kome ba, sai kin ji dama mutuwa kika yi da wannan rayuwar!"" Ya saka kafa ya shure ni, sannan ya bar dakin, shigowa Matarshi tayi tana murmushi ta ce min. ""Ki tattara naki ya naki, ki bar gidan nan kafin dare ya miki"

"domin Hafiz nawa ne ni Waya, ina dakatar da shi ne don ni ce uwar Yaransa."" Daga haka ta fita daga dakin, har aka kira sallah azhar ina wurin wani irin jiri da ciwon kai nake ji, a hankali na rarrafa zuwa ban daki na kama ruwa nayi alola sannan na fito, abin sallah na shimfida sannan na tadda sallah, ina cikin sallah Yaransu suka shigo min daki. Ina idarwa Babbar yarshi Yusrah ta ce min. ""Lulu yunwa nake ji, ki bani abinci!"" Karamin ya ce min.. ""Lulu Golden mo zan sha. "" A tsawon zamana da Ya Hafiz Allah bai ba ni haihuwa ba, ko nace na biyewa son zuciya irina shi na kashe kaina da kaina. Shafa addu'a nayi na mike tare da cewa. "" Tow ku zo muje parlourn sai ku na baku. "" Tasowa suka yi suka biyo ni a baya, ina son Yaran ko don Yaran Ya Hafiz ne, mutumin da nayiwa wata irin makauniyar so, har yau bana ganin laifinsa duk abinda zai min tow na san idan ya nutsu da kanshi zai gaya min rashin kyautatawa da ya min, haka yasa na shiga kitchen din parlourna, na shiga hada musu musu abinda zasu ci, a parlour kuwa Yaran suka shiga fada akan remote din tv, daga cikin kitchen na ce musu. "" Ya isa ku bari ko na zo na kwace!"" Shiru suka yi na hada musu na kawo na ajiye musu kowa ya dauki nashi, nima na koma kitchen na hada nawa na fito parlourn na zauna a hankali, ina sha ina kallonsu. Wayata da take daki tayi ™ara da sauri na ajiye"

"kofin na nufi dakin, bude jakar nayi na dauka a hankali, na saka a kunnena. ""Na'am Aunty Hindatu!"""

"Murmushi nayi na ce mata. ""Mun shirya ai ba kome fa, kawai dai baki fahimci abin ba ne"" na fada ina"

"dafe kaina da yake min ciwo. ""Amma nasan baki da lafiya!"" Ihun Yaran da naji a parlourn yasa ni mata sallama babu shiri na fito, wanda yayi shigowar Iyayensu, Yusrah da Yasir suke ihu lokacin da Yasir ya dauki kofin tea na, ya watsawa Yusrah wani abu ne ya dake ni cike da tsoro mara iyaka. Na zuba musu idanu, Allah yaso ruwan ba zafi na tashin hankali, amma yadda yarinyar ta kwala ihu zaka rantse ruwa ta fasashe ne jikinta. ""Me kika aikata Lubnah?"" Kasa magana nayi Uwar ta ce. ""Wai ke me yasa kike haka ne?"

"Yaran nan suna sonki amma shi ne kike azabtar da min da Yara."""

"""Wallahi!"" Tass ya wanke min fuska da mari, ""ku yi hakuri, ku yi hakuri, ku yi hakuri ba zan kara ba,"

"don Allah ku yi hakuri don Allah ku yi hakuri!"" Na shiga fada ina tattara kofin Yaran da nawa, ina basu hakuri na nufi Yusrah da ta daina kukan sai ma wasanta da take, zan riko hannunta. Ya Hafiz ya ture ni, ma fadi can. ""Kayi hakuri ba zan kara ba, don Allah ka yi hakuri wallahi ba da gayya ba ne."" ""Ki tafi da Yaran gani nan zuwa!"" Jan hannun Yaran tayi suka fita, ya zuba min idanu yana sauke ajiyar zuciya ya ce min. ""Kin kona min Yara ya kike so nayi?"" ""Kayi hakuri wallahi ba da gayya ba ce!"" ""Ok kina son ki gaya min ba haushina kika ji ba kenan kika kona min Yarana ba?"" ""Wallahi na rantse da Allah!"" Kifa min mari yayi a kan fuskana sai da na daina gani na hucin gadi, kafin na bude idanuna ina kallon kasa. "" Kayi hakuri"

"Ya Hafiz ka fadi duk abinda kike so zan yi, don Allah kada ka dake ni."""

""" Na ji ba zan dake ki ba, amma idan na saka ki aiki zaki yi?"" Da sauri na d'ago kai ina gyada mishi kai. """

"So nake ki kira Baban Bauchi ki gaya mishi, kome a kan idanuna dangane da fitar da Hindatu tayi da ke saboda ina zaton kashe min aure zata yi yasa ta fita dake!"""

"D'ago kai nayi ina kallonshi, "" ba zaki fada ba kenan? Na kira Baban Bauchi na gaya mishi yadda kika"

"kona min Yarana? "" Girgiza kai nayi ina faWin.."" A'a bata ce min na kashe Aurena ba! "" "" Ok kenan ba zaki fada min gaskiya ba kenan? Kin san ina sonki ina kaunarki amma shi kenan! "" Tunda ya fara faWin haka tuni ya kashe min jiki, sai na nemi duk wani abinda ya min na rasa, kaina a sunkuye na ce mishi. ""Asibiti ta kai ni, saboda ciwon kan nan da nake fama da shi, bayan nan wallahi babu abinda ya faru."" Ajiyar zuciya ya sauke a bayyane, tsaki yayi yana faWin. ""Dama shine abinda ya faru baki gaya min ba? Kuma"

"idan asibiti ne ai ni nafi dacewa na kai ki ko? "" Daga haka ya fita zuwa dakinsa, ni kuma na gyara parlourn."

"Haka na wuni raina babu dad'i, kitchen na nufa na daura tuwon dare, da miyar yakuwa. Ina cikin aikin"

"Yaran suka shigo, sai da gabana ya fadi, ihu da wasan banza suke nayi musu fada amma sun ki bari, na musu tsawa, sai suka kama min dariya, karshe haka na kyale su nayi na cigaba da aikina, amma idanuna yana kansu. Ana kiran Magariba na gama abincin, tsoron kada wani abu ya kara faruwa na gama na rufe"

kitchen din.

"""Lulu zan ci abincinki!"" ""A'a da zafi!"" Na fada ina kallon yadda suka zuba min idanu, da gudu suka fita"

"zuwa bangaren Uwarsu, sai gasu tare da ita. "" Lulu ba zaki zuba musu abinci sai ki ce musu babu, idan baki basu ba, uban waye zai zai basu? Ni bana son bakin ciki domin ni ba girkin nayi ba! """

""" Tow dama da zafi ne, kada ka basu ne su kona kansu! "" Na fada mata a sanyayye, cikin jin haushi ta ce"

"min. "" Dalla ki min shiru kina wani magana kamar wata Mutuniyar kirki, idan da kina da zuciya da tuni kin bar gidan nan, amma kin wani zauna kina tsammanin zaki samu hafiz ne kamar da!? "" Wuce ta nayi na dauko mata abincin na bata. "" Don Allah dubi mace sai kace saniya! "" Ta fada tana kallona, fita tayi daga parlourn Yaran suka bita, ni yanzu magana baya min ciwo ko tashin hankali. Alola nayi na gabatar da sallah magariba, ina kan abin sallah ina addu'a na gabatar da sallah isha, tare da shafa'i da wutir, ina idarwa Ya Hafiz yana shigowa, abincin na fita na hada mishi ya zauna ya fara ci, yana ciro wasu kwalayen magani, ya zuba min a kan kujera. ""Gasu nan kina sha zaki ji sauki!"" Murmushi nayi na ce mishi. ""Na gode sosai Allah ya saka da alkhairi, Na gode sosai Ya Hafiz!"" Dama nasan duk abinda yake yi, zai dawo mu shirya, uwar dakina na wuce na ajiye maganin na shiga wanka na fito na shirya cikin doguwar rigar barci, sannan na fita na dauko ruwan sha na, koma dakin na zauna har ya gama cin abincin, sai da na sha magani sannan na dawo na kwashe kayan da yaci abinci na kai kitchen na wanke na wanke wa sannan na dawo parlourn na cigaba da kallon ina cin abincin na, dakyar na gama na wanke hannuna, sannan na dawo parlourn akan na jira shi, ina zama a kujeran parlourn barci yayi gaba da ni, wani irin barci me karfi da yasa ban iya farkawa ko sallah daren da na saba yi, shiga sallah asuba ya farka da ni, na zubawa parlourn idanu. Dama a parlourn na kwana? Sai naji na muzanta, me yasa Ya Hafiz bai shigo ba? Bayan yasan girkina ne? Ko da yake yaushe rabon ya kwana a bangarena? Idan ba son kai irin nawa ba. Daki na wuce na fada ban daki nayi alola nazo na sauya kaya na gabatar da sallah asuba, ina zaune a wurin na ji motsin bude kofar bangarena, ban yi mamaki ba nasan sai shi. Ina azkar ya shigo da sallama, ya zauna a bakin gadon. ""Malama ki sallame ki zo nan!"" Tunda ya fadi haka, nasan ba wani abu ya zo nima ba, sai ya"

gaya min magana ta hanyar hakkinsa.

"Haka na tashi na cire kayana na nufe shi, babu wani abu ko sako a'a kawai bude min cinya yayi ya"

"shiga tsakanin ya shiga biyan bu™atarsa, yana shiga ko minti goma bai yi mai kyau ba, na ga ya fara kakkafe min tare da matse ni, yana wani danne ni. Can na ji ya fito bakiWaya yana nishi, kafin ya dauki wandonsa ya saka ya bar dakin, a hankali na mike tare da nufar ban daki, flast dina na wanka na juye ruwan zafin na yi tsarki na yi wanka, sannan na fito na shirya zuwa kitchen, na daura abin karyawa da sauri sauri. Na gama wainar fulawa da ruwan tea, na fita na dauko kular makarantar Yusrah, na zuba mata sannan na nufi bangaren Karimah na buga kofar, bude kofar tayi tana hamma daga ita sai kayan barci. ""Dama abincin makarantar Yusrah na kawo!"" ""Tow ko zaki shigo ki shirya ta ne?"" ""A'a ina da wani aiki da zanyi, zai fi kyau ki shiryata!"" Na mika mata abin makarantar na dawo bangarena, ina shirin zama na karya sai ga Ya Hafiz da Yarinyar. ""Ko Karimah bata haifi Yara nan ba, ai na kine, gashi maza ki shiryata."" Haka na mike na amshe na wuce dakina da ita na mata wanka tana ta min kukan banza, har da ihu, ina shiryata Uwarta ta shigo tana faWin. ""Wai me kika mata ne take ta ihu?"" Ni dai ban ce kome ba, tana ganin abin karyawan da na ajiye ta zauna ta fara ci, har na gama ita kuwa ta cinye. Sannan ta kamo hannun Yarta suka fita. ""Yawwa wannan abin ya yaji dayawa, sannan me yasa kika sake garlic karshe yau sai na sha wani abu domin Yayanki baya son wani abu me tashi!"" Ta fada tana murmushi, ni dai ban ce mata kome ba, kitchen na nufa na kara dibo abincin na fito na zauna na fara ci, ina kallon tv, ban gama ba sai ga Ya Hafiz da Yasir, ""shima ki mishi wanka!"" ""Tow"" nace mishi na cigaba karyawa. "" Sai yaushe"

"zaki tashi zan kwana ina jiranki ne? "" "" Kayi hakuri! "" Na mike da sauri ina kwashe sauran wainar fulawa."

""" Jaka ban san me ATBU suka gani suka baki first class honors ba, dube fa baki san kome ba sai ci, dalla ki"

"mishi wanka ki bashi abin karyawa. "" "" Kayi hakuri! "" Na fada ina amsar Yaron bayan na dawo daga kitchen, na wuce na mishi wanka na shirya shi nazo ina bashi tea, ya fara ihu yaran kamar ana gaya"

"musu , wani abu da zasu yi a lokacin Uwar ta shigo ta ci kwalliya kamar mai shirin zuwa gasar kyau. "" Lulu me kike mishi ne?"" Sauke shi nayi ya wuce wurin Uwar, tana kallon kayan parlourna, lokacin haihuwar wannan Yaron Abba ya sauya min. "" Kayan parlournki kamar basu tsufa! "" Ni ban ce mata kome ba, domin tun fil azal haka Allah ya halicce ni, bana son yawan magana, a shekarun baya ina da yawan tsokana da zolaya, amma baya bayan nan bakiWaya kamar an sauya min rayuwa,. Haka nake bana son Magana ko damuwa. ""Yaushe zaki sauya wasu?"" Na gaji da tambayar renin wayo na ce mata. ""Sai kin"

"sake haihuwa!"" Rike baki tayi tana faWin. ""Wai sai dai ko ke?"" Yake na mata ban ce kome ba."

"Haka ta fita, ina zaune a wurin na gaji gyara parlourn na fara tare da shirya kome a inda yake, ina aiki"

"aka kira wayata, dauka nayi Ya Ado ne, mutanen Lagos dauka nayi ina murmushi na ce mishi.. ""Barista ya aiki?"" ""Auta"" ""na'am!"" Na amsa mishi a hankali, ""Hindatu ta kira ni, akan wani batu ya abin yake?"" Tsintar kaina nayi da cewa.. ""kawai zato take amma wallahi ba

Please Login or Register in order to submit comment