Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
7 / 8
ka, saboda karfin naushin sai da hular karfen da Sarki sultan ya Saka ta tsattsage tamkar an doka Sanda a jikin gilashi. Faruwar hakan keda wuya sai Sarki sultan ya sulale Kasa sumamme. Nan take nutse a cikin jinin dodannin nan, aka dena hangoshi. WAYE ZAI SAMU NASARA A WANNAN YAKI? SHIN SARKI SULTAN ZAI SAMU NASARAR KASHE DODANNIN NAN GABA DAYA? ME ZAI FARU TSAKANIN SARKI SULTAN DA SAURAN SARAKUNAN DUNIYA IDAN YA SAMU NASARAR KARAR DA DODANNIN? INA LABARIN ALJANI RA'UFUL KALLUS? SHIN ALJANI RA'UFUL KALLUS ZAI SAMU NASARAR TSALLAKE DUK MASIFUN DA KE CIKIN KURKUKUN DA AKA SANYA SHI? Domin Jin Amsar wadannan tambayoyin sai mu hadu a HATSABIBIN ALJANI na TAKWAS 8. Daga Mai debe maku kewa a Koda yaushe, wato NAJIBULLAH MUHAMMAD βœοΈβœοΈπŸ™ **HATSABIBIN ALJANI** LITTAFI NA TAKWAS 8 ✍️✍️ PART A ❀️❀️✍️ AUTHOR: NAJIBULLAH MUHAMMAD ✍️✍️ POSTING: Najibullah Muhammad πŸ₯·πŸ₯· GORON JUMA'A 🀝❀️ Muna fatan Allah ya sadamu da Alkhairin wannan Rana Mai albarka tare da kare mu daga kowane irin bala'i πŸ™πŸ™ Cigaban littafin... Lokacin da daya daga cikin dodannin nan ya samu nasarar gabzawa Sarki Sultan naushi a ka, har ya sulale Kasa cikin jini a sume. Sai gaba dayan DODANNIN nan suka watsa hannuwansu a cikin jinin, da niyyar lalubo Sarki sultan. Sai da dodannin nan suka shafe dakika dari da arba'in suna laluben Sarki sultan Amma ko alamarsa babu a cikin kogon Nan. Koda ganin haka sai Katon dodon nan ya fusata ainun, ransa ya harzuka. Nan take ya kwarara uban ihu Mai tsananin razanarwa Wanda har sai da gaba dayan Duwatsun kogon suka fara tsattsagewa saboda tsananin Karar rurin dodon. Bayan shudewar dakika arba'in ne dodon ya tsuke bakinsa, sannan komai ya natsu. Kawai sai akaga wannan dodon ya jefa tafkeken hannunsa Mai kama da Katuwar bishiyar kuka a cikin jinin Nan. Faruwar hakan keda wuya sai ya fara hautsina jinin kota'ina Yana mai fatali da shi. Yana cikin hakane kawai sai yaji karamin Dan yatsansa ya sargafo rigar karfen da ke jikin Sarki sultan. Nan take ya dago shi sama, sannan ya sagale shi a jikin Saman kogon dutsen yana Mai kura Masa idanu cikin tsananin mamaki. Babban abinda yafi bawa wannan dodo mamaki shi ne, ganin yadda bil'adama guda daya tal, yayi masu mummunar barnar da gaba dayan Aljanun duniya ma sun Kasa yin Koda rabinta. A bisa ganin irin wannan Jarumtaka da wannan bil'adama ya nuna ne, yasa wannan dodon ya ayyana a ransa cewa bazai kashe Sarki sultan ba. Amma zai barshi a haka kamar yadda ya sagale shi, har sai mai-gidansu ya dawo wato HATSABIBIN ALJANI RA'UFUL KALLUS domin ya Yanke Masa hukunci da hannunsa. Batare da Bata wani lokaci ba wannan dodon yayi wa sauran kananun dodannin inkiya akan suci gaba da aikinsu, na sauraron shigowar wasu abokan gabar. Nan take dukkansu suka Kara gyara makamansu sannan suka jejjera sahu-sahu suna jiran Wanda zai Kara afkowa garesu. Wannan shi ne abinda ya faru a Kogon BAHAR DURGAFUL KALLUS bayan an fafata kazamin yaki a tsakanin wadannan dodanni, da Kuma rundunar mutane da Aljanu.. ALJANI RA'UFUL KALLUS βœοΈβœοΈπŸ‘‡πŸ‘‡ A bangaren ALJANI RA'UFUL KALLUS kuwa lokacin da ya samu nasarar kubuta daga cikin daki na farko, a kurkukun da aka Sanya shi. Sai yayi sauri ya tube kayan daya daga cikin masu gadin kurkukun ya Saka a jikinsa. A tunaninsa tunda gaba dayan Aljanun birnin kama suke yi da shi, to babu ta yadda za'ayi a gano shi. Uhm! Wai an ce rashin sani yafi dare duhu. Abinda RA'UFUL KALLUS Bai sani ba, shi ne duk wadannan Aljanu da yake gani ba na gaskiya bane tsafaffu ne, Kuma ba wani bane ya tsafasu ba, face wannan bakon Bokan Aljanin nan. Haka Kuma duk irin abubuwan da suke faruwa Yana gani ta cikin madubin tsafinsa. Koda ganin RA'UFUL KALLUS ya kubuta daga cikin daki na farko, sai ran Bokan Aljanin nan ya Baci ainun. Nan take ya runtse idanunsa ya fara wasu surutai irin na tsafi, fara hakan keda wuya sai RA'UFUL KALLUS yaga wasu zabga-zabgan Aljanu masu mummunar siffa da kirar karfi, sunyi Masa Kawanya. Da zuwansu basuyi wata-wata ba, sai suka cukuikuyi RA'UFUL KALLUS suka jefa shi a cikin daki na biyu, dake Jere a cikin Kurkukun. Da shigarsa, sai yayi arba da wadansu kananun Aljanu masu falka-falkan Kunnuwa da kwala-kwalan idanuwa kamar tulu ne aka lillika masu. Su dai wadannan Aljanu adadinsu ya Kai dubu hamsin, Kuma suna da zako-zakon hakora wadanda duk abinda suka Kafa mawa, to cikin dakika biyar kacal suke zuke Masa jini kaf, su jefar da Gawarsa. Komai tsananin girman halitta, muddin wadannan Aljanun suka yanyame ta sai dai kaga sun zuke mata jini, cikin kiftawar Ido sun jefar da Gawarta. Bugu da Kari wadannan Aljanun basa magana, Kuma basa fahimtar wani yare. Abu daya kawai suke fahimta, shi ne duk abinda suka ga an jeho masu a cikin dakinsu, to hakan na nufin abincinsu ne na wannan ranar. Bayan anyi kallon-kallo tsakanin RA'UFUL KALLUS da wadannan kananun Aljanu. Sai kawai yaga dukkansu sunyi fitar burtu daga inda suke, sun rugo garesu tamkar tsuntsayen duniya ne sukayi hijira zasu sauya wuri. Cikin tsananin zafin nama Mai Kamar walkiya, RA'UFUL KALLUS ya fiddo makamansa ya tunkari Aljanun Nan. A zuciyarsa yasan cewa Abu ne mawuyaci ya fita daga daga cikin wannan daki a raye, domin a rayuwarsa bai taba ganin Aljanu irin wadannan ba. Koda zuwan Aljanun sai suka rinka kawo masa caka da tsinin bakunansu, shi kuwa ya rinka karkade su da takobinsa tamkar ana girgizar kanya. A wannan lokaci RA'UFUL KALLUS Yana yaki ne da dukkan karfinsa, domin ya San cewa muddin ya sake Koda Daya daga cikin Aljanun Nan ya samu nasarar Kafa bakinsa a jikinsa, to shikenan tasa ta kare. Nan fa RA'UFUL KALLUS ya dage iyakar karfinsa wajen make Aljanun nan, suna makuwa a jikin garun dakin. Babban abinda yafi bashi mamaki shi ne, ganin yadda yake zubar da su Kasa suna faduwa kamar matattu, Amma Kuma sai su tashi su Kara rufar Masa tamkar babu abinda ya same su. Nan fa ran RA'UFUL KALLUS ya Baci, Nan take ya tuna da duk irin wahalhalun da ya Sha a rayuwarsa. Ya tuna cewa shi fa gwarzon jarumi ne, Wanda ya zama abin kwatance ga mutane da Aljanun duniya. Nan take yaji wani sabon karfi tare da kwarin gwiwa ya shige shi. Faruwar hakan keda wuya sai ya sauya salon yakar Aljanun. Nan take ya dena amfani da kaifin takobin wajen kashe Aljanun, sai ya koma caka masu tsinin takobin a cikin tsakiyar kawunansu. Fara hakan keda wuya sai sai ya fara samun nasarar kashe Aljanun Nan, Koda ganin haka sai ya Kara zage dantse wajen yakar dodannin. Sai da aka shafe sa'a guda da rabi ana wannan gumurzu sannan RA'UFUL KALLUS ya samu nasarar kashe gaba dayan Aljanun Nan. Yana gamawa sai ya durkushe Kasa Yana haki saboda tsananin Gajiya. Yana cikin wannan hali ne, daya daga cikin Aljanun nan Yana gargarar mutuwa yaga RA'UFUL KALLUS ya ajiye kwaurinsa a kusa dashi. Ai kuwa Koda ganin haka bayyi wata-wata ba sai ya gartsa Masa cizo a kwauri iya karfinsa, Nan take ya Luma hakoransa sai gashi ya cisgo lafceciyar tsokar nama daga jikinsa. Cikin tsananin rudewa RA'UFUL KALLUS ya kwarara uban ihu saboda tsananin zafi da zogin da yaji. Nan take jini ya kama bulbulowa daga jikin kafar. Bayan kamar dakika goma da faruwar haka sai ya ga kafar ta fara rubewa har tsutsotsi sun fara cin Naman jikin kafar. Nan fa RA'UFUL KALLUS ya Kara rudewa kamar yayi hauka. Abinda Bai sani ba, shi ne duk abinda hakoran wadannan Aljanun suka caka take abun yake zagwanyewa ya rube ya lalace Koda kuwa karfe ne. Haka Kuma duk duniya babu wani magani da zai iya warkar da Wanda Aljanun Nan suka ciza, face Naman su kansu Aljanun. ( Ma'ana dole sai dai mutum yaci namansu ) sannan zai warke. RA'UFUL KALLUS Yana kwallara ihu ya samu ya jawo Daya daga cikin gawarwakin Aljanun nan sannan ya fara cizgar Naman jikinsu da tsiya Yana ci. Yana fara hadiyewa sai yaga kafarsa ta dena Zogi Kuma jinin ya tsaya. Nan take yaci gaba da cin danyen Naman Aljanin nan, Sannu a hankali har sai da yaga tsutsotsin da suke shawagi akan kafar sun bace bat, kafin cikar dakika hamsin raunin kafar ya cike kafar ta koma sumul tamkar wani abu bai taba samunta ba. Koda ganin haka sai RA'UFUL KALLUS ya Mike tsaye cikin tsananin mamaki, sannan ya kekkewa Yana Mai tattaka kafarsa da karfi domin tabbatar da warkewarsa. Bayan wani lokaci Yana tunanin mafita, zuwa can sai dabara ta fado Masa. Nan take ya tattaro gawarwakin kananun Aljanun Nan guda Dari, sannan ya rinka 6ara bakunansu ya ciccizgo hakoransu Yana Tarawa. Ashe hakoran wadannan Aljanun mugun tsawo garesu, domin girma da tsawon kowane hakori ya Kai kamu uku. Sai da RA'UFUL KALLUS ya ciro hakoran Aljanun Nan dubu, sannan yayi masu wasu kananan hudoji daga karshensu, sannan ya rinka dura su a cikin wani siririn zare Mai kwarin tsiya. Sai da ya jera hakora dari biyar a jikin wannan zare sannan yayi damarar dashi, sauran hakoran kuwa sai ya kwashe su ya fuskanci bangon daki na uku. Da zuwansa duk da cewa babu kofa a ciki, sai ya rinka Luma ragowar hakoran da ya kwaso a hannunsa a jikin bangon dakin Nan. Faruwar hakan keda wuya sai kawai akaga Katangar dakin ta tsattsage tamkar danyen ginin da ruwa ya buga. Zuwa can sai gaba dayan Katangar ta ruguje, kawai sai tsintar Kansa yayi a cikin daki na uku. Da shigar wannan dakin sai yaga babu komai a cikinsa, face wata Katuwar rijiya a tsakiyar Dajin. Ita dai wannan RIJIYA tana da tsananin girma, domin ta kusa cika fadin dakin gaba daya. Babu ta yadda za'ayi a wuce gaba dole sai anbi ta samanta. Haka Kuma wannan RIJIYAR anyi mata wani Katon murfi da wani mulmulallen bakin karfe Mai tsananin kauri Wanda Koda Karti Dari biyar zasu taru bazasu iya daga shi ba. Nan take RA'UFUL KALLUS yayi nufin ya hau ta Saman murfin RIJIYA ya wuce. Fara tafiyarsa keda wuya, sai halittar Dake cikin wannan rijiya ta fahimci cewa lallai an jeho mata abun kalaci. Kwatsam ba zato ba tsammani sai kawai RA'UFUL KALLUS yaji an Doki murfin RIJIYAR Nan daga Kasa. Murfin da RA'UFUL KALLUS sukayi sama tamkar an watsa ledoji sunje sun maku a jikin Saman rufin dakin sannan sun fado Kasa can gefe guda. Nan take RA'UFUL KALLUS ya dafe keyarsa saboda tsananin zafi da yaji sakamakon buguwar da yayi da rufin dakin. Yana cikin haka ne, kawai sai yaga an miko wani lafcecen hannu daga cikin RIJIYAR, girman wannan hannu yakai na Katuwar bishiyar kuka. Zuwa can Kuma sai yaga an sake Miko dayan hannun a wajen RIJIYAR an ajiye. Kafin RA'UFUL KALLUS ya yi wani yunkuri tuni wani zabgegen dogon mutum Mai shantala-shantalan hannuwa da kafafu ya fito cikin wannan RIJIYAR. Shi dai wannan mutum Yana da matukar tsawo na gaban kwatance, domin har ma yafi dakin da yake tsawo, dole sai dai ya rinka rankwafa wa. Bugu da Kari Yana da rafkeken Kai tamkar Katon Dutse ne aka lika Masa. Haka Kuma wannan dogon mutumin a rayuwarsa babu halittar da ba ya ci, walau mutum ko Aljan ko Dabba duk abinda ya shigo dakin da yake, to Nan take yake Amfani da lafcecen hannunsa ya matseshi rugu-rugu sannan ya rinka cizgar sassan jikinsa Yana ci a hankali-a hankali har ya koshi, daga bisani sai ya zuba Kasusuwan halittar a cikin RIJIYAR da yake kwana. A halin yanxu ya zubawa wannan RIJIYAR Kasusuwan halittu mabambanta sama da guda Milyan arba'in, Amma saboda tsananin zurfin RIJIYAR tamkar ba a taba Sanya mata komai ba. Amma wani abun mamaki shi ne, duk girman wannan wannan RIJIYAR idan wannan dogon mutumin ya shiga cikinta, to cika ta yake taf, har ma sai ya tsuguna sannan murfin RIJIYAR yake iya rufewa saboda tsananin girman wannan mutumin. Koda wannan shantalelen mutumin ya bayyana a gaban RA'UFUL KALLUS sai ya kyalkyale da wata mahaukaciyar dariya Mai nuna tsantsar mugunta da rashin Imani. Shi kuwa RA'UFUL KALLUS tuni hantar cikinsa ta kada saboda ganin irin bala'in wannan mutumin. Kafin RA'UFUL KALLUS ya gama Yanke shawarar abinda ya kamata yayi, kawai sai yaga wannan shantalelen mutumin ya Miko hannunsa guda da nufin ya cafko shi, Nan take hannun ya taho sululu Yana ta Kara mikewa tamkar ana Jan dafaffiyar roba. Koda RA'UFUL KALLUS yaga wannan rafkeken hannun yayo Kansa, sai ya falfala da gudu yana Mai tsalle-tsalle sama domin gujewa wannan hannun. Amma sai ya ga mutumin Yana iya lauya hannunsa izuwa duk yanda yake so, tamkar yadda ake Sarrafa kwayar hatsi a turmi. Koda RA'UFUL KALLUS ya fahimci cewa ba zai iya gujewa mutumin Nan ba, sai ya daka tsalle sama ya haye kan gwiwar hannunsa ta hagu, sannan ya falfala da matsanancin gudu yana Mai tunkarar Saman kan mutumin. Shi kuwa wannan shantalelen mutumin sai yayi tsaye ya zuba Masa idanu, Yana Jira ya karaso kusa da bakinsa kawai ya Ida tura shi ciki ya cinye.. Sai da RA'UFUL KALLUS yayi gudun dakika dari da tamanin sannan ya iso kan kafadar mutumin Nan. Da zuwansa sai ya cisgo biyu daga cikin hakoran kananun Aljanun nan da ya fafata da su a daki na biyu, sannan ya Luma hakoran nan a cikin idanuwan mutumin Nan. Nan take hakoran suka lume a jikin idanun, shi kuwa RA'UFUL KALLUS sai yayo Kasa luu kamar Wanda ake jeho daga sama ta daya saboda tsananin Nisan Dake tsakaninsa da Kasa. Cikin tsananin rudewa da firgicewa shantalelen mutumin Nan ya rinka magowa Yana dukan ko'ina hannu da kafa. Duk inda ya buga sai dai kaga wurin ya Burma yayi gaba. A hakane wannan mutumin ya samu nasarar mako RA'UFUL KALLUS da hannunsa yayinda yake fadowa Kasa daga wuyansa. Saboda tsananin karfin dukan sai da RA'UFUL KALLUS yayi sama tamkar an janye shi da majaujawa sannan ya manne a jikin rufin dakin. Ala'marin wannan shantalelen mutumin kuwa, Bai gushe ba Yana rushe dakuna da katangun birnin har sai da ya ruguje gaba dayan ragowar dakuna dari Tara da casa'in da bakwai, duk da haka Bai Dakata a Nan ba sai da ya rushe gaba dayan gine-ginen Dake cikin wannan kurkukun. A sannan ne aka ga ya Yanke jiki ya fadi Kasa matacce Nan take tsutsotsin Nan suka rufarwa jikinsa da ci ko'ina ya rube Nan take, tamkar Gawar da tayi shekaru ba a rufe ba. Ala'marin RA'UFUL KALLUS sai da ya shafe dakika hamsin a manne a jikin bangon dakin, sannan ya fado Kasa a sume. Bayan ya farfado ne yayi arba da irin mummunar barnar da wannan shantalelen mutumin yayi. Batare da Bata wani lokaci ba, RA'UFUL KALLUS ya rinka bin duk Inda wannan shantalelen mutumin ya ruguje Yana wucewa. Bai gushe ba Yana tafiya har sai da ya keta dakuna guda Dari Tara da casa'in da bakwai sannan ya iso ainihin farfajiyar gidan kurkukun inda anan ne ya riski Gawar wannan mutumin. Nan take ya cika da tsananin mamakin karfin wannan mutumin. Tabbas yasan cewa inba don yayi dabarar dauko hakoran Aljanun Nan ba, da babu ta yadda za'ayi yaga bayan wannan shirgegen mutumen. Yana gama wannan mamaki ne, sai yayi duba izuwa bangaren yamma na gidan kurkukun. Ba zato ba tsammani sai yaga gaba dayan Dakarun gidan kurkukun sunyi cirko-cirko rike da muggan makamai. Su dai wadannan Dakaru adadinsu yakai Milyan Dari, Kuma kowannensu ya ninka Aljani RA'UFUL KALLUS girma da kauri sau goma. Kafin RA'UFUL KALLUS yace wani abu tuni gaba dayan wadannan Dakaru sun rugo gare shi da nufin yagalgala shi... A dai-dai wannan wuri ne nikuma na gaji ainun, nake cewa mu hadu a part B don Jin cigaban wannan Kasaitacce Kuma Kayataccen labari ✍️β™₯️πŸ₯° Ina maku fatan Alkhairi β™₯οΈβœοΈβœοΈπŸ™πŸ™**HATSABIBIN ALJANI** LITTAFI NA TAKWAS 8 ✍️ PART B βœοΈπŸ’― AUTHOR:- NAJIBULLAH MUHAMMAD ✍️✍️ POSTING:- Najibullah Muhammad πŸ₯·πŸ₯·πŸ₯· BARKANMU DA JUMA'A 🀝❀️❀️Muna fatan Allah ya sadamu da duk alkhairan da ke cikin wannan rana Mai albarka β™₯οΈπŸ™πŸ™ Cigaban littafin......πŸ‘‡πŸ‘‡ Idan baku manta ba, a baya mun tsaya ne inda gaba dayan Dakarun gidan kurkukun suka taru da nufin yakar RA'UFUL KALLUS. Su dai wadannan Dakaru adadinsu yakai Milyan Dari Kuma kowannensu na rike da muggan makamai masu matukar girma da kauri. Kafin RA'UFUL KALLUS ya ce wani abu tuni gaba dayan wadannan Dakarun sun rugo gareshi da nufin yin filla-filla da sassan jikinsa. Cikin tsananin zafin nama na gaban kwatance RA'UFUL KALLUS ya finciko takobinsa ya tari gaba dayan Dakarun Nan Yana kururuwa mai tsanani da razanarwa. Suna haduwa suka kacame da sabo Kuma masifaffen yaki mai tsananin ban tsoro. Amma abun mamaki shi ne, duk Aljanin da RA'UFUL KALLUS ya Sara da takobinsa sai yaji jikinsa tauri tamkar ya sari Dutse domin ko Kwarzanewa bayayi. Koda yaga wadannan Aljanun suna kokarin cukuikuyeshi su kama shi, sai yayi wurgi da takobinsa sannan ya zaro gaba dayan hakorin Aljanun Nan da ya maΖ™ale a jikin wata murtukekiyar igiya. Yana fiddo hakoran nan ya rinka wurwurata Yana Zane Aljanun nan da dukkan karfinsa. Fara hakan keda wuya sai Aljanun Nan suka fara kamawa da wuta suna konewa kurmus. Idan RA'UFUL KALLUS ya Kai duka da wannan igiyar a lokaci guda Yana iya mako Aljanu dari biyu da arba'in, Kuma duk Wanda bulalar Nan ta taba jikinsa nan take yake kumbura ya fashe tamkar an Saka batir a wuta. Nan fa Aljanun Nan suka zage dantse wajen kawowa RA'UFUL KALLUS mugayen hare-hare. Ta kawone Hali so suke su kashe shi. Sama da Aljanu Milyan biyu ne suka yanyame shi suna Mai Kai Masa Sara da suka ta kowace kusurwa.. Nan fa RA'UFUL KALLUS ya wanzu mai kashe Aljanun Nan cikin tsananin zafin nama juriya da bajinta. Babban abin mamakin ma shi ne, komai hatsabibancin makami indai yaci karo da wannan igiyar ta Aljani RA'UFUL KALLUS sai dai aga makamin ya ratattake ya zama toka. Duk da cewar RA'UFUL KALLUS Yana kashe Aljanun ta ko'ina, Amma sai Kara ciccidowa suke suna Kara rufe shi. A duk cikin dakika goma RA'UFUL KALLUS Yana kashe Aljanu dubu arba'in, Amma saboda tsabar yawan Aljanun tamkar matattun ne ke sake tashi suna tunkararshi. Lokacin da bala'i ya Kai bala'i, sai tashin hankali ya baje kolinsa a filin yakin. Mutuwa ta zamo abun siye da siyarwa domin giftawa take ko'ina a cikin Aljanun nan tamkar yadda kamshi ke ratsawa ta cikin hancinan mutane. Duk inda mutum ya duba sai dai yaga sama da Aljanu dubu sun kama da wuta sun kone kurmus. Yayinda kisan Aljanun ya yawaita, sai gaba dayan birnin ya fara girgiza tamkar zai ruguje saboda bala'in yaki. Nan fa tsawa da girgizar Kasa ta yawaita, hasken da cikin birnin ya yaye, duhu ya maye gurbinsa. Amma duk da haka Aljanun Nan Kara rukunkume RA'UFUL KALLUS sukeyi. Hakika wadannan Dakarun sun cika masu nacin tsiya da taurin zuciya, domin komai yanda bala'in mutuwa ke giftawa a tsakaninsu baya hanasu tunkarar abun harinsu. Shi kuwa RA'UFUL KALLUS Koda yaga haka, sai ya rinka jujjuya bulalar ta ko'ina sama da Kasa, gaba da yamma, kudu da Arewa hagu da dama yana mako Aljanun. Kuma babban abin mamakin ma shi ne, duk da cewa garin dundum yake, wannan igiyar ta RA'UFUL KALLUS a haskake take da hasken wuta. Saboda haka Yana iya ganin duk abinda ke gabansa. Nan fa RA'UFUL KALLUS ya rinka maka bulalar Nan a Kasa, faruwar hakan keda wuya sai akaga Kasar wurin ta fara tsattsagewa, kafin cikar dakika hamsin da fara hakan, sai gaba dayan Kasar birnin ta fara ruftawa, manyan-manyan ramuka suka wanzu a ko'ina. Nan take gaba dayan Aljanun suka rinka ruftawa cikin ramukan Nan suna mutuwa. Kafin wani lokaci sai gaba dayan birnin ya fara tambal-tambal zai nutse karkashin Kasa. Koda ganin haka sai RA'UFUL KALLUS ya falfala da matsanancin gudu domin barin garin. Gudu yake iyakar karfinsa, Amma duk Inda ya dauke kafarsa sai dai yaga Kasar wurin ta rufta. Haka ya wanzu cikin azababben guda har tsawon sa'a biyar sannan ya iso karshen birnin, Yana ajiye kafarsa ta farko izuwa wajen birnin sai yaga komai ya tsaya, girgizar Kasar ta dena sannan hasken ya dawo. Nan fa RA'UFUL KALLUS ya tsaya yana tunanin hanyar da ya kamata yabi, domin ya debo Kasar wannan birni da Kuma ganyayen bishiyoyin nan. Tayaya zan iya mallakar wadannan abubuwan alhalin birnin ya ruguje gaba Daya? RA'UFUL KALLUS ya tambayi Kansa a cikin zuciyarsa. Yana cikin wannan tunani ne, sai kawai yaga ba zato ba tsammani Kasar birnin da ganyayen bishiyoyin nan sun taso Saman iska sun shige a cikin battarsa, Nan fa ya cika da tsananin farin ciki. Faruwar hakan keda wuya sai wannan igiyar ta kama da wuta ta kone kurmus. A wannan lokaci ne gaba dayan birnin ya rinka nutsewa a karkashin Kasa. Nan fa RA'UFUL KALLUS ya rinka ganin yadda manyan gine-ginen birnin suna dulmiyewa a cikin Kasa, Kai hatta bishiyoyi da komai dake Saman turba sai da ya nutse karkashin Kasa. Hakan na gama faruwa sai Kasar birnin ta shafe gaba dayanta ta komai dai-dai tamkar babu abinda ya taba faruwa da ita. Har ya juya zai ci gaba da tafiya, sai ya rinka ganin komai Yana farfadowa Yana dawowa sabo, duk sababbin gine-gine suka wanzu bila'adadin a cikin birnin, daga bisani sai bishiyoyi kala-kala da ciyawa nau'i-nau'i gasu Nan birjik ko'ina. Haka ya rinka zuba Ido yana mamakin faruwar wannan Ala'marin har sai da komai ya dawo dai-dai, hatta gidan kurkukun Nan da Dakarun gidan kurkukun da komai da ke rayuwa a birnin sai da ya dawo sabo tamkar wani abu bai taba faruwa a cikin birnin ba. Nan take RA'UFUL KALLUS ya juya ya tunkari birni na Sha Daya, Yana mamakin irin yadda duk abubuwan Nan suka faru tamkar a mafarki. Bayan RA'UFUL KALLUS ya shafe sa'a biyar yana gudu, sannan ya iso birni na Sha daya. Tun lokacin da ya iso wannan birni kanshi ya kulle gaba daya sakamakon ganin abubuwan Al'ajabin da suka fi karfin hankalinsa. Gaba dayan yanayin zubi da tsarin birnin sunsha bamban da na dukkan biranen da ya taba ganin a cikin wannan duniya. Kai hatta a duniyar mutane da Aljanu Bai taba gani ko jinin labarin abubuwan Al'ajabin da ke cikin wannan birni ba, duk da cewa ya taba yawace duniya kaf! Kuma ya shiga ko'ina da Ina a cikin waccan duniyar, yasan sirrinta sosai tamkar yadda mutum yake sanin sirrin cikin gidansa. Shi dai wannan birni komai nashi yasha bamban da sauran birane. Tun farkon shigowarsa ya fara yin arba da taurarin garin manya-manya girman kowace tauraruwa ya Kai na Katon Dutse. Bugu da Kari gaba dayan taurarin sun sauko kasa-kasa suna yawo a cikin iska, tamkar yadda tsuntsaye ke jerangiya a sararin samaniya. Haka zalikha su ma bishiyoyin birnin a Saman iska suke yawo, Kai komai dai ka sani da yake rayuwa, sai dai ka hange shi cikin iska yana yawo Yana harkokinshi. Hatta gidaje da Duwatsun birnin duk a cikin iska suke yawo. Ma'ana dai babu wani Abu Mai Rai da yake Saman turba, duk suna sama suna yawo cikin iska. Shi kanshi RA'UFUL KALLUS Yana ajiye kafarsa ta farko a cikin birnin, sai wata zukekiyar iska Mai tsananin karfi ta sure shi tayi sama da shi. Ba zato ba tsammani sai kawai yaga kanshi a duniyar wadannan taurari Shima ya shige cikin Al'ummar garin kawai sun ci gaba da yawo a cikin iska. Faruwar hakan keda wuya kawai RA'UFUL KALLUS yaga wata mummunar tsohuwa yankwananniya Mai tsananin Muni da ban tsoro ta bayyana Tsulum a gabansa cikin iska tana Mai kyakyata dariyar mugunta.... Ita dai wannan tsohuwa tana da rafkeken Kai tare da wadansu kahonni guda hudu a Saman kanta. Haka zalikha iduwanta guda hudu ne, biyu daga cikinsu suna maΖ™ale a Saman goshinta, Kuma jajawur suke kamar garwashin wuta, babu sirkin fari ko kadan. Sauran guda biyun kuwa suna mammanne a jikin kurmin idon da na kowa yake, Amma Kuma kalar su ta sha bamban da wadancan domin farare ne tass, babu ratsin Baki ko kadan. Haka Kuma tana da zako-zakon hakora masu tsananin tsini, harshenta sai faman dalalar da yawu yakeyi, dalalaa.... Gaba dayan fuskar ta a yamutse take ba kyan gani, komai dakewar zuciyar mutum inda yayi arba da wannan tsohuwar Aljana baya marmarin Karawa, domin zuciyar mutum na iya tashi yayi amai. Koda bayyanar wannan yankwananniyar tsohuwa a gaban RA'UFUL KALLUS sai ta dafa shi da Dan yatsa guda ta bace tare da shi tana Mai kyakyata dariyar mugunta 😁😁😁😁😁😁 ME ZAI FARU TSAKANIN RA'UFUL KALLUS DA WANNAN MUMMUNAR TSOHUWAR ALJANA? TA YAYA ZAI SAMU NASARAR TSALLAKE WANNAN BIRNI? INA LABARIN YAKIN DA AKEYI A TSAKANIN DODANNI DA SAURAN SARAKUNAN DUNIYA? Mu hadu a HATSABIBIN ALJANI na Tara 9 don Jin cigaban wannan Kasaitacce Kuma Kayataccen labari ✍️β™₯️πŸ₯°πŸ˜πŸ˜πŸ˜ **HATSABIBIN ALJANI** LITTAFI NA TARA 9 ✍️ PART A ✍️✍️ AUTHOR:- NAJIBULLAH MUHAMMAD ✍️✍️ POSTING: Najibullah Muhammad πŸ₯·πŸ₯· GORON JUMA'A β€οΈπŸ€πŸ™ Idan baku manta ba a wancan satin mun tsaya ne a inda wannan tsohuwar yankwananniyar aljanar nan ta dafa ALJANI RA'UFUL KALLUS da Dan yatsanta guda na hagu ya bace tare dashi tana Mai kyakyata dariyar mugunta... Koda wannan mummunar Aljana ta bace tare da RA'UFUL KALLUS, Bata bayyana a ko'ina ba sai a wani mummunan gida mara kyan gani. Gidan

Chapter 7 of 8