Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
5 / 8
tarho gefen gadona ta sa kara, nayi yunkurin in dauka Yallabai ne, ya yi saurin mirginawa ya dauka jin ya tintsire da dariya ya ambaci sunan yaya Usman yasa ayi saurin tashi tare da karasowa wajan sa, saboda nasan Halimatu na kusa Amma da kyar Yallabai ya amince muka gaisa, wai a cewarsa, in muka fara hira dadewa zamuyi in barshi ba abokin hira, amma ta wayar naji yana cewa Halimatu gobe zai kawoni in Allah ya kaimu. Bayan na yini gidan Halimatu har zuwa karfe biyar na yamma sai gashi ya dawo, wanda tunda ya ajiyeni ya tafi ofis acewarsa yanzun ma kutowa yayi ya bar jabir a can. 47 A tunanina gida zamu wuce, sai nagan yayi hanyar unguwa maitama gidan mu kenan da murnata, na shiga gida muka gaisa da su har izuwa karfe shida har da mintuna biyar na yamma, bayan nan kuwa, sai gidan ma'ama wanda acen muka kai har karfe takwas na dare. Amma wani abinda Mustapha yayi mani shine, kiri-kiri ya ki yarda mu biya gidan Zulahatu saboda kishin sufiyanu da na fiskanci Yallabai nayi, ina kallo aka bi ta kofar gidan su da ke unguwar area 4 wuse market. amma yaki yarda ko gaisawa in leka muyi da ita. Kwana ni da Yallabai dina tamkar biyu ne a tsakani, amma ango da amarya, duk da dan cikin jikina yana son ya iakura mani da yan wasu abubuwan ga dan yawan motsi da ya dameni da shi, wai shi ya fara girma, dan wata hudu din da yayi. Kwance nike a cinyarsa a falonsa wajen karfe takwas ko na dare motsi nayi sai ya sumbaci koshina, tare da tambayar yaya dai? Ma'ana nufinsa ko na gaji ne da kwanciya Cikin yar hirar nishadi da muke yi da yan wasannınmu, na samu na sako zancen gidan zulaihatu, anan take sai naga Yallaba ya hade fiska, a cikin wasa na fara zaulayarshi." Yallabai Zulaiha fa, haka ranar ma fa ka ki mu biya gidanta kai Yallabai na lura dai nema kake ka hanamu zumunci da ita aka abinda bai shafeta ba," "ya isa haka nan don Allah." Na mike zaune daga saman cinyarsa da nike kwance, tare mikewa tsaye, saboda nasan maganar da zan fada sai nayi nesa Yallabai, gudun kada insha marin tsautsayi. "Ni bana son in ga ka kullaci sufiyanu, sufiyanu ba ruwans ballanatana matarsa, laifin na gareni ni da nace ina son in aureshi na dan yi murmushi, wai da yanzu fa shike da cikin jikina." Nan take naga Yallabai ya dago kansa da sauri, ni kuwa gan haka yasa na yi saurin tafiya zan shige cikin daki, waigowar zanyi sai naga Mustapha ya biyo ni da saurinsa. Karasa rugawa nayi cikin daki, na kwanta tare da makalka filo, ina kiran na tuba, na tuba," isowa yayi ya cire filon hannuna tsiya ya dagani zaune da dan yatsansa ya nuna ni sannan ya fa magana, 48 "Wallahi kika kara yi mani irin wanwan maganar sai na bata maki rai sosai", na samu na sauka da dan hanzari na ina yar dariya, "amma kasan dai gaskiya na fada ko?" mai makon yayi magana sai na ga ya tashi da saurinsa har wata 'yar rawar, jiki yake yi Ni kuwa sai na kara yin gaba da guduna, "Hamida, "Hamida wallahi kada ki kuskura ki zubar mani da ciki wajan wasan wauta, shine har ki ke gudu, wallahi ." kafin ya karasa fadar wata maganar ni kuwa har na kaiwa kofar dakin sa karo ta cikina Na dawo da baya sai gani kasa kwance wanwar, yayi saurin zuwa ya dagoni, ina ta wani irin nishin wanda na fasarashi, a nishin wahala yanda Mustapha ya nuna mani shine ga haushi a tare da shi na kamar yayi mani dukan tsiya ga kuma tausayi da na fuskanci yana ji nawa. Nasan dole tasa Mustapha ya daukeni ya dora agadonsa, amma sai naga ya koma gefe daya ya tsaya yana kallona, cikin wata irin yanayin miryar da ta zamo kamar ta aro nayi mashi magana. "Iya taimakon da kake ganin zaka iya bani kenan?" "ki kira sufiyanu ya zo ya aimaka manki, wannan ma da kika ga nayi na yi shine kawai saboda bebina da yake jikin ki, wallahi! Wallahi!! Wallahi!!!, in har kika kuskura bebina ya samu wani lahani a jikin ki sai nayi maki abin da duk tunaninki ba zai kawo maki shi ba." Ficewa yayi da saurinsa kamar zai kifa kasa, nan take na mayar da kaina na kwantar saboda bazan iya tashi ba, balle har in samu in bishi domin neman afuwa a gareshi. Karfe uku na dare na farka a firgice saboda wani matsannan cin ciwon da marata da kuguna keyi, haka yasa na dinga laliban Mustapha, amma sai naji ban ji shi ba, hakan ya dan bani kwarin gwiwar lalubo makunnin fitila da ke gefen gadan mu na kwanciya, saboda in kara tAbbatarwa kaina ina Yallaбai na ya tafi. Hasken da ya gauraye fakin baccin Yallabai shi ya tabbatar mani mai dakin baya cikin dakin, na samu na ja jikina na mike a hankali na shiga bandaki, amma wata firgita da nayi na mike tsaye la saurina daga zaman fitsarin da nayi akan farar tukunyar bature ta in bayan gida. Ko daya ban karajin wani ciwo ba saboda tsoro da tashin ankali dana shiga, a lokacin dana zauna yin fitsari, a maimakin Λα fitsarina kuwa sai naga jini ya maye gurbin zubar fitsari, hakan kuwa shine sanadiyyar firigtata, tare da fitowa daga bandakin ba shiri. Zaman da nayi gefen gadan Yallaßai, nayi imani ba zai taba yaye mani faduwar gaba da fargabar dana samu kaina a ciki ba, hakan yasa nayi kokari na mike na samu da wani karamin tawul nayi kunzugu da shi gudun kada jini ya kai ga 6ata mani jikina, A sannu a hankali na dinga labe labe har na fito fatan Yallabai, gabana ya kara faduwa da karfin gaske da naga Yallabai kwance a falonsa saman daguwar kujera. Ya zame mani dole in isa in nemi gafarar Yallabai, hakan yasa na cigaba da tafiyata in karasa in da yake kwance, waigowa yayi ya kalleni, sai naga ya kawar da kansa gefe, nan take sai naji jikina yayi sanyi tamkar na kutsa kaina a firizar kwance. Amma duk da hakan da yayi mani bai hana in isa gareshi ba, ina isa sai naji na tsuguna gabanshi kawai, nayi imanin yana jina, ma ko juyo da kanshi bai yi ya kalleni ba. Kara daurewa nayi na dafa gefan cinyar hanrunsa tare da fadar, "Mustapha," "me ye, ki tafi ki kwnata kawai " ya fada mani tare da ya juyo kanshi ya kalleni na, a take anan dan ragowar karfin da ke zuciyata ya tauye sai dai kawai hawaye naji sun tsiyayo mani a kumatuna. ba Cikin karfin hali na mai kararriyar zuciya nace mashi, "Mustapha jini," "what?" ya fada da karfi tare da mikewa zaune, "me kika ce?" ban iya kara fada ba, sai dai kifa kaina da nayi a jikin kujera na sa masa kuka. Dagoni yayi tare da girgizani da karfi "ki fada mani mana, me naji kin fada? ina magana kinyi mani shiru," "jini", "da gaske ki ke ko kuwa?" "da gaske ne," ya sakeni yayi shiru tare da dafe kanshi da hannayensa biyu. Tashi yayi ya fice daga falon, hakan ba karamin tayar mani da hankali yayi ba, na mike da niyyar in bi bayanshi, amma sai marata taki daukata, dole tasa na koma na dukusa saboda wani azabtaccen ciwo da take yi mani, sai da na sami kusan minti sha biyar sannan na iya dan daddafawa na mike tsaye, amma duk da haka sai naji na kasa daga kafafuwana. 50 Dole tasa na koma na zaman wanda zauni yar ma ta gagareni, sai gani na zame kasa na kwanta, ni kaina ban san iya tsayin lokacin da nayi ina birgimar ciwon da nayiwa lakani da ciwon mutuwata, а cikin wannan halin ne naji Mustapha ya daukeni. Ban yi tunanin bude idanuwana ba, saboda ni kaina nasan ba zan iya daukar nauyin budasu ba, ba abinda Mustapha baiyi mani ba, domin yaga ciwon da nike birgimar ya sakeni, amma ko sauki sauki ma banji ba. Ni dai ina jin muna wuce motoci jefi jefi, amma ba zan ıya cewa ga lokacin ba, ko ince karfen agogon bature nawa ta nuna a lokacin, amma duk da idanuwana rufe suke bai hana kunene jin yan surutai da hayaniyar tashin miryoyin jama'a ba. Ban tAbbatar da in da muke ba, sai da naji tsinin allura ya ratsa fatar hannuna, sannan na tAbbatarwa kaina da asibiti muka zo Ina bude idanuwana ba abinda su ka gani sai wata 'yar madaidaiuciyar agogon bango da ke saitin gadona sai naga karfe uku na ranar, ko ban san iya awanmina ba, nasan dai na jima a asibitin nan. Bayan duk yarı sunnu sun tafi wanda suka tafi da sunan faduwa nayi na samu wannan ciwon, saboda hakan Mustapha ya fada masu, sai na zamo ni daya a dakin asibitin, hakan yasa a nan take sai na fara tunanin ina Mustapha?, kenan Mustapha yayi fishi da ni? ban kara tuna komai ba, sai gashi ya shigo da Abdulrashid bayansa dauke da ledoji Abdulrashid ya matso ya fara yı mani sannu, sannan ya fita, tare da cewa Mustapha, sai kamar karfe nawa zai dawo daukarshi, amma ta harshen turanci, zanyi maka waya, abinda Mustapha ya bashi amsa kenan Abdulrashid ya amsa da okey sir ya fice abinda Abdulrashid na fita Yallabai na ya iso bakin gadona ya tsaya tare da dafa goshina da yar sumbatar goshina, "ya jiki?"ya ce mani a dai dai lokacin da yake shafa gashin kaina. Cikin sanyin mirya na amsa mashi cewa da sauki, tare da ce masa ya gafarceni don Allah, gani nayi Mustapha ya daga kai na ya dora a cinyarsa sannan ya sunkuyo ya kara sumbatan kumatuna. "Ki daina wannan maganar don Allah, Allah ne ya kaddara ta sanadiyyar yinta zaki hadu da wannan ciwon, in dama zamu kara 51 1α godewa Allah, shine da ya bar mana fan bebinmu, sai dai mu kara kiyaycwa kawai. Murna, dadi, su suka dirar mani a zucıyata nan take wanda hakan yasa nayi saurin cewa Yallabai na gode yayi yar dariya tare da dan lakatar mani hanci kada a kuma maimaitawa na dan rufe idanuwana alamun kunya da na dama Shigowar Ma'ama ita tasa naga Mustapha ya daga kaina da ke cinyarshi ya dora a filo, ya mike yana yan soshe soshe wuya wai shi kunya, wanda ni ya sakarwa kunya, tunda na kasa bude idanuwana. Abinka ga babbar mace, sai ma ta nuna ba san abinda ake ciki ba, bata fi mintuna ba sai ga mamana ta shigo da inna tantu dauke da kayan kwnoni a hanunta, idona rufe nayi saurin wajen naji suna gaisawa da ma'ama amma ko kusa dani bata matso ba sai dai sun gaisa da Mustapha har tayi mashi ya mai jiki. Ina jinta tana gayawa ma'ama cewa ga inna tantu nan ita zata awaje na ina ji tayi wa ma'ama bayanin cewa iya tantu kanwar daddy din muce, ni kuwa a lokacin da na dan kyalla idana sai naga ba Mustapha a cikin dakin, hakan ya tAbbatar mani ya fita kenan Karfe takwas na dare su mamana da sauran wasu daga cikin yan dubiya ta suka tafi, wanda fitarsu ke da wuya naji Mustapha ya shigo yana yiwa ma'ama magana da irin yaransu na indiya. Ban iya yaran indiya ba saiu dai kala mai fai daya, saboda haka bansan maganar da suje yi ba, sai dai da maganar tasu tayi nisa naji ana fadar ba ayarda ba, da cewa ko da yaushe da yansauran tsirarin kalaman da Mustapha ya koya mani A haka dai na hada na fahimci a kan kwana wajena suke magana wanda naji Yallabai na cewa shi zai kwana tare da ni ita kuwa ma'ama tana yi mashi gardama a karshe naga ma'ama ta fice ta bar mashi dakin, tare da fadar maganar ta ta karshe da kalmar hausa, "na gaya maka kada in kuskura in ji labarin ka kwana aа sibitin anan sai da safenku. Hajiya ma'ama na fita, naga Yallabai ya zauna daya daga cikin kujerun da aka zagayc dakin dasu, "kushin," a hankali na kira sunan sa, ya dago kanshi sai na ware hannayena alamar ya taho, Bai yi wata gardama ba ya taso ya zo ya zauna gefanm gadona sanna ya dan shiga hannuna ya kwanta a kirjina, a hankali na dinga 52 shafar gashin kansa da magana cikin natsuwa da nuna tausayawa a gareshi, ta ya hakuri ya bi abinda Hajiya ma'ama ta ce. Nan ya kama yi mani miratar wai ko ya koma gida ba zai iya wani barci ba, "ke kinsani ko na koma gida ba zan iya barci ba,"""na sani Yallabai, amma ni a nawa gani kayi hakuri kabi abin da mahaifiyar ka ke so saboda a ganina ko ka zauna nan kayi barci, to barcin kuwa bashi da amfani tunda mahaifiyar ka na kule da kai. Hakurin ka kawantacan shi ne alheri a gareka, haka na dinga lallashinsa harya hakura tare da cewa sai sha biyun dare zai koma gida shima, sai da na cigaba da bada hakuri tukuna aka hakura za'adinga tafiya sha daya na dare. Maimakon dadi sai haushi a wajan Yallabai na, saboda wucewar da za'ayi da ni gidanmu, da an sallameni daga asibiti, domin hutu da likita ya bani, shi ma kuwa sai da nasha sabon aiki a wajan Yallabai na, da kyar na samu na shayo hankalinsa ya hakura. *** 1 Alhamdulillahi, ni kam Hamida ina samun kulawa matuka saboda duk safiya ko dare sai Yallabai ya zo, banda ma'ama ita ma kullum tana tafe a hanyar zuwa gidanmu, a bokannan Yallabai ma haka Abdulrashid kuwa gidan mu ma komawa yayi tamkar nasu saboda komai shi Yallabai ke aikowa ya kawo kafin ya iso Bangaran mamana da daddy ba zance komai ba saboda duk abinda likita ya ce shi kuwa suke bani. Sai da na samu tsayin wata daya a haka, sannan Mustapha ya zo mani da labarin zaiyi tafiyar gaggawa zuwa kasar itali shi da jabir a cikin satin nan, tabbas naji banji dadi ba, sai dai na dan nuna ban damu sosai ba saboda gúdu kada Yallaßai na ya gane ya rushe tafiyar, gata ta karuwar muce itama. Yau kwanan goma sha biyu da tafiyar Yallabai (kasar Itali) domin taron bude wani sabon kafanin takalma, wanda hadin hannu ne da gwannatin kasar. Tafiyar ta kamashi ne a ba zata, wanda ta kuma zama dole ya tafi tare da amininsa Jabir, hakan yasa dole ya bar mani Abdulrashid, domin kulawa da duk wani abun da zan bukata, 53 Abukan Yallabai kuma kullum zirga zirga suke akan dubani, wanda hakan ya kan rage mani tsananin tunanin rashin mai gidana a kusa da ni, wanda Hajiya maama kuwa, duk kwana biyu sai tazo taga yar sirikarta da lafiyar abinda danta ya bari a ciki. Hakan ba karamin dadi yake yi mani ba, ganin yarda aka mayar dani yar gata ni Hamida gashi gidan mu bani aikin ko ninke kayan da na cire, wadan da zan saka jikina ma, sai dai in gan su in saka, wannan kuma duk aikin 'yar Kanwata ce Aina'u Dakin mamana nike kwanciyata ina barci, domin nawa dakin za'a shiga a gyara mani shi ni kuwa dama aikin tsayuwa bai gannin ba, tunda na samu matsalar cikin nan nawa. Karar wayar gefan gadon mamana ita ta tashe ni daga wani barcin da nike mai dadin gaske, cikin fan tsoki na na dauki kan talho din da ke gefen gado na kanga a kunnena, tare da fada, "assalamu alaikum," Amsa sallamar kawai naji amma na gane miryar bakon italiyan, 'sai ka tasheni barcina mai dadi, sai kasa na haifo maka yaro mai gutsurarran kunne," na fada cikin magara irin ta shagwaba. "To"be sorry" banyi zaton kina barci ba, ganin ranace, gashi gidan ku gidan jama'a amma duk da haka, a fuwan, ki kuma gayawa bebi kada yayi fishi yanzun zaki koma barcin, yayi hakuri inzo in ganshi da kunnuwansa biyu.". Na danyi dariya, "baka gajiya wallahi da sa mutum dariya ni ya bakunta?" "bako ai ya kusan dawowa, ki tarye shi yau da karfe uku na dare a filin jirgi, domin bako ya gaji da jama'a garin wasu ba matarshi akusa dashi balle dan bebinsa. Kinga daga filin jirgi ai sai gida ki hadawa bakonki abinci ko?" "a'a bako ya ciko cikinsa tun a garin jama'a, in kuwa na jirgi yake so, to ya ci ya koshi, domin har yanzu matar bako jinyar dan bebin bako take yi." Muka sa dariya gaba daya, "ke matar bako, kada kiyiwa bakon naki haka," "amma ai shi bakon dai in mai hankaline ai yasan ba zai so matar bako ta fito cikin dare taryar bakonta ba, ko bako yana so taci karo da azzalimai a hanyar zuwa tarar bakonta?" 54 Yayi dariya, "Hamida kenan, akwai iya dubara, yanzu dai kinyi wa dan bakonki wayau kenan, ya ji zai rama in ya iso ga matar bako, yanzu dai ki koma ki cigaba da barcinki, ko shima sai bako ya ririgaki ne?" "wallahi da zan samu ina so bako," "to tsaya in fara ririgaki, kina jina, amma kwata ki rufe idonki," to kinyi, to goshin nan zan fara, yar bebina, kiyi shiru, yar lele ta bako, goshinki da haske, kuncinki da laushi wuyaki da gwabi," ni kuwa dariya kawai ni ke, tare da cewa, "kai Mustapha, har kasa na harareka a waya "kai! kai!! kai!!!, to, inazo kuwa sai na biya kudin wannan hararar," "ni ma in biya na raino, gashi kuwa har na soma barci," nayi sauri na kife kan talho din in ba haka ba kuwa,sai mu kai wani lokaci, dan yallabai ba gajiya zai yi ba. Tun asuba, nayi wankana, na gyare jikina, na kawo turaririka na goge jikina da su, tare da daukar rigar baccita na mayar a jikina, duk dan jan fada ga yallabai, gama shiryawata kuwa, yasa na koma na shige cikin bargona, tare da kashe fitulun dakin da nike kwana, waini barci nike. A wannan yanayi ra sanyin watan karshen "december", wanda ni kuma na koreshi da shiga cikin bargona mai laushi domin samun wadataccan dumi a jikina. Karfe takwas da rabi na safe, naji tashin miryarsa a bAbbab falan gidanmu, hakan yasa na juya na baiwa kofar dakin baya waiui a dole barci ni ke yi. Ina jin shigowarsa, har da mayar da kofa da kullewa da makulli, a zuciyata nayi yar dariya, shi kuwa har wani sanda yake wai manufarsa kada ya tasheni, a hankali ya bi har ya hayo gadon ya zauna dai dai in da na mayar da fiskata. Ina jinsa, ya sumbaci kumatuna, tare da janye bargon da na lulluba, zuwa wajen cikina shima ya sumbaci cikina, tare da dan lailayashi alamar yaji ko lafiyarsa kalau, sai lokacin na bude idanuwana a hankali ina mai nuna alama daga barci na tashi. Da saurina kamar gaske nayi saurin tashi na fada jikinsa wai ni murnar dawowarshi. Shi kuwa sai dariya murna da farin ciki yake, ya dagoni, "ya bebina?" na dan bata rai kadan "shi kadai ka sani?". 55 "Na ısa ayi-wa bako afuwa, ya kika wayi gari?", "lafiya kalau" "ina fatan kai ma ka dawo lafiya, da fatan kuma tafiya tayi пasarа???", "Alhamduhillahi, tafiya tayi kyau sosai, amma ni ban tsaya an karasa komai dani ba, kasarce naji duk ta isheni, Jabir na baro in an gama shi ya taho "Kai yallabai yanzu ku tafi tare kai kuma sai ka taho ka barshi can", "to ya zai yi, shi ya dan saba sosai da barin iyalinsa gida, ni kuwa kinga ban saba ba, ina laifi wannan ma da nayi." "Shine kuma sai kayiwa mutane sammako a gida," "su bani matata su gani in zan kara zuwan masu, to balle ta kaini ga sammako," "kenan ko gaisuwa ba zasu samu ba?" "na isa, wannan ai daban, in dai har zanje gaishe da Hajiya maama to zan kuwa gaishe da suma nan gidan, saboda kinsan duk daya suke a gareni. Cikin wata yar yananin sigar wata manufa Mustapha ya yi mani magana, "ni yanzu na zo in biya hararar da akayi mani a waya "wasa fa nake kai ma kasan..... ," kafin in karasa yayi saurin hada bakina da nashi, Mintuna ashirin da kusan biyu daki na ya samu bakuntar shıru, tamkar ba kowa a ciki, wasnnnin shiru kam shi na biyewa Mustapha mukayi amma cikin cikon minti na ashirin da uku, sai naji Mustapha na nema canja wasa Hakan ya sa na nuna masa alamar ba'a hada wasa biyu a lokaci daya a kare lafiya, ba tare da anyiwa wani cikin yan wasa ciwo ba, amma a take sai Mustapha ya nuna mani, shi mai iya shiga cikin wasa kala hudu ne ya fita ba tare da anyi fada da shi ba. Maganata da nayi ita ta kawar da shi run da dakin yayi "Mustapha kasan dai ba zai yiyyuba, ka tuna sharuddan likita "ba komai a duk Allah ya kaddara zai faru zai faru ki kyale managar likita kawa." "A gidamu Yallabai?" "taso mu tafi wani hotel din," "haba kaima kasan maganar da ka fada ba mai yiyyuwa ba ce ba," "to yanzu ya kike son inyi? Wata biyu fa, har da kwanaki," "ka manta likita wata uku ya bayar," "kwana nawa ya rage a wata ukun bai fi ashirin ba." fa Hamida." "Ni dai don Allah abar wannan maganar ma muyi hira kawai 'bazan iya ba," "ni kuma ba zai yiyyu ba," "ko," "gaskiya kayi 56 1 tunani kaima," "ki daice haka kika zaba wa kanki shi kenan magana ta wace. Abin bai kai na zafi har haka ba," "nace magana ta wuce, ayi wata, in kuma ba wata in tashi in tafi, ina son in je in gaishe da maama, ban je gidan ta ba nan kawai na taho daga tashi na. A hankali ya mirgina ya sauka," "ni zan tafi, saboda ina da yan abubuwan yi, wata kilan in dawo an jima, in kuwa ban samu dawowa ba, to kilan sai gobe in Allah ya kaimu" ina zaune ni dai ina kallonshi har ya gama maganar sa, ya sun kuyo ya sumbace ni a goshi ya tafi, ni kuwa na bishi da kallo har ya fita. *** *** *** Wane irin fishi Mustapha yayi dani haka?, harda zai dauki kwanaki har takwas ba shi ba wayar shi, balle dan aike, shin ko ya samu wata ne ban sani ba?. Nayi tsoki na mike daga zaman da nayi a gadona, na shirya jikina, na ficewata falo abina, tunda nasan tunani ba magannin da zai yi mani, tunda bani da ikon fita. Misalin karfe sha daya na safiyar litinin dai ne akace mani ga Abdulrashid, dama mamata bata falon ta shinta kenan ta shiga sashen daddy, a tunanina ko shara zata yi masa, ni da Aina'u ne kawai a falon, ita ma dan ta dauki jarabawar wucewa makarantar gaba da primary" A nan nace tace ya shigo tunda dama da mayafina, a jikina da ma ni da shi nike yini a jikina, saboda kunyar a ganni da tikeken ciki a gabana har na wajan wata takwas. Bayan mun gaisa da shi ne da tambayata ya karfin jikina, duk na amsa masa da lafiya kalau, sannan ya cigaba da fadar sakon da aka turo shi da ya fada. "Madam dama Yalla6ai ne yace in kawo maki sako", ya sa hannu a aljihu ya zaro wata ambulan ya miko mani, "kaya na cikin mota suma ya ce in kawe maki." "Yayi tafiya ne?" "a dai sanina bai yi wata tafiya ba," "1о yanzu yana ina?" ni dai tunda jiya da ya zo ya kawo mani wannan sakon ya i har yau bai dawo ba" "kenan bai kwana gida ba?" "Е, 57 to, gaskiya bana jin ya kwana gida," tunda ya dawo daga tafiya yana kwana gida?" "Hajiya wannan tambayar ba tawa bace, nasan dai anan yake kwana," Abdulrashid ya fada yana murmushinsa, nan take sai naji kaina ya sara dan cikina ya juya take marata ta daure, duk da yanayin sanyi muke ciki, amma hakan bai hana gumi tsiyaya a jikina ba, "Bai gaya maka yana da tafiya zuwa wani gari ba, ko kasa," "bamu yi maganar haka dashi ba tunda ya dawo, ni fa nayi zatan yana nan gidan sai jiya da dare ya zo ya kawo mani wadannan kayan yace a kawo nan." "Tun jiyan kuma bai dawo gida ba?" "E sai dai yau da safe yana bugo waya mun gaisa," "me yasa kuke barinshi fita shi daya, kullum nan yake kwana, dama na tambaye ka ne saboda in nuna maka kuna son kuyi sakaci da aikinku, Yanzu da ba nan yake kwanaba, da ya kenan, ku kuma ba kwai binshi ko abaya ne ku dinga kulawa da shi, kunsan dai irin su oganku, sun tattare da hadari sosai, don Allah ka dinga kiyayewa Abdulrashid." "To madam daga yau zan kiyaye, tunda kin bayar da izini, ni zan koma, yace in da wata matsala ki fada," "ba komai ka koma ma da kayan da ka zo da su kace masa wadan can da ya kawo mabasu kare ba, kuma daddy na ma ya kawo wasu jiya," "to Hajiya ni na koma." Na bude ambulan din da ya miko mani na zari naira dubu biyu na bashi, "wannan a saiwa iyali lemo, ragowar ka mayar masa kace ya tuna fa, jiya ya bani wasu ko ya manta ne?" "to Hajiya ya karba tare da yi mani sallama ya tafi Idanuwana a rufe na isa daki, saboda ba sa ganin gabana sosai, ba abinda na kawo a zuciyata illa na zauna kasa na jingina da gado, tare da yaye mayafin jikina, hade da tube rigar jikina domin in samu in shanya cikin gabana ko dan cikinsa ya samu wadataccen iska. Ni na jayowa kaina komai, tunda lafiyata kalau amma naki arbar bakuncin Yallabai, "innalillahi wani inna ilaihir raji'un," shi kenan mijina ya zama( iska ma biyin mata, na zame jikina kasa 58 na kwanta rasidina ko ba siginta sai mustaphja ya bani shi (saki), tunanin da nike yi kenan Haka na yini a ranar ina ta mirgina a tsakar dakina na gidan mu, har karfe takwas na dare, sallah kawai take tayar dani daga kwanciyata, abinci kuwa, suna jere a gabana ban taba ko daya ba. Sai ma da na gama sallar magaribq ne, sai na ji dan barci na neman

Chapter 5 of 8