Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
4 / 8
bayanin yarda akayi haka ta faru, amma har yau kinki kwantar da hankalinki balle in ji dadin gaya maki komai." "Bana son ji, ni dai abinda nike so kawai kace ka fasa aurena ka sakeni yanzu, ni nafi jin dadi a zuciyata. .""ni kuwa tawa zuciyar ta buga?, ki cire wannan tunanin kwata kwata a zuciyarki, saboida kinsan abinda ba zai taba yiyuwa bane kika fada. "ni kuma abinda nike so kenan", "Allah baki hakuri don Allah ki daina wannan maganar haka nan ta isa," "ni kuma ita nike son ayi," "dama ba nace a dainata kwata-kwata ba, a'a kiyi hakuri gobe sai in gaya maki duk yarda akayi, in kuma baki iya daurewa ki tambayi Halimatu yanzun dai kiyi hakuri ki taso mu shiga ciki kada a nememu. "Ko dai kada ta nemeka," :ita wa kenan?" "ita wacce kace ta sameka a inda kake son ku hadu," "Hamida ban gane ba," "ka gane in tabi katin ta karanta ta sameka inda kace ku haďu," "ohoo!! Yanzu na fahimta, ya mike tsaye, ina zuwa jirani don Allah". ya tafi har da dan saurinsa, sai gashi ya dawo da Abdulrashid so gabana, yasa hannu a aljihu ya dauko katin da ta bashi yacewa Abdulrashid ya kai mata ya karbo masa nashi da ya bata, nan take yace okey sir, ya juya ya tafi. Minti kamar biyar a tsakani sai gashi ya dawo ya mika masa, ya iso ya zauna kusa dani, "gashi an karbo, kiyi hakuri daga yau ba zan kara yin haka ba, tunda baki so," "me ye na ban hakuri, in kana sonta kasa a warware áuran dani a mayar da ita. "Wai ni ya su, yau da naga samu naga rashin Hamida ni dan alkaki," na tuntsire da dariya, ganin yarda ya fada da miryar mata kamar irin yan daudun nan har da dukan cinya da tafa hannu, cikin dariya nace Mustapha wa ya koya maka maganar mata haka?." Yayi murmushin da ya daga kai sama, alamar ya ji dadin dariyar daya sani. "Ba wanda ya koya mani, nayi ne kawai saboda in ganki cikin farin ciki, Hamida, kalli sama ki gani," na daga kaina sama, "me 36 kaika gani?" "taurari,""amma sunyi maki ky ko?" "na tsaya na kura masu ido. Saman yayi bulu-bulu wanda turawa ke cewa "sky blue" taurari sunyi haske sosai, "sunyi kyau sosai," "Allah ya haliccesu suma kamar yarda ya haliccemu, ya haliccesu, suma dan su bauta masa kamar yarda ya halicce mu domin mu bauta masa, kinga ko maganar nan da mukayi bautar Allah ce mu keyi, to balle ke da zakiyi biyayyar aure a gareni, kinga lada biyu kenan." "Ban gane ba," ko maganar da kike yi mani yanzu cikin natsuwa, zuciyata nayi mani dadi, shima bautar Allah ce, "tashi mu tafi gida, kaga dare yayi," "ba kya son magana tane?," ni kuwa bakiji yarda nakejin dadi a zuciyata ba, wai ni ne yau Mustapha zaune kusa da mtata tanayi mani magana a hankali mai kwantar mani da zuciya." Sai naji ya lalubo hannuna dake saman cinyata yasa a gefen kumatunsa, saboda dukkanmu kawunan mu na kallan sama, "bai dace ba fa Yallabai," "in kika kirani da Mustapha, zuciyata tafiyi mani dadi," "amma kasan bana sonka, ba zan iya auranka ba", "aure fa ya kare mani Hamida, sai dai inyi kokari yanzu ki soni kawai," "to ka sakar mani hannu," "bautar Allah fa kike yi. Fiskarsa kawai naji a wuyana, ya kwantar tare da sumbatarsa, nayi dan hanzarin mikewa tsaye, "yana mikewa, sai kawai naji ya rungumeni jikinsa, "mijnki ne ni fa ko kin manta?" naji ya fada a gefen wuyana, nayi kokarin kwace jikina naja baya, "ka zo kasa mayar damu gida," na fada cikin rawar mirya tare da sa hannu in shafa fiskata kamar mai share hawaye. Hannuwa na yayi saurin matsowa ya kama, anan take nasa yar kara, saboda zafin fama mani ciwo da yayi, "me ye?" "hannuna" "sorry, wallahi na manta da shi, sannu," "kai ma naci da rashin zuciya yasa kake like danij nace bana sonka, ka sakeni, bazan aureka", "duk naji, na gode, ni na janyowa kaina dana fama maki, sannu, zo muje mu kara gaisawa da jama'a, zuwa sha daya da rabi sai a tashi hakannan." "Sha daya da rabi yayi yawa," "to sha daya sai a tashi sabosa kinga yanzu goma har da mitina," yanda yake maganar, sai naji banji dadin yarda nayi masa ba, kamar in ce yayi hakuri sai kuma 37 a wata zuciyar tace "ke da ke neman saki," sai kawai nayi gaba zuwa komawa cikin dakin taron fatin. *** *** *** Duk bayan kowa ya watse an gama walimata a gidan Mustapha, an kawoni wajan karfe bakwai da rabi na dare, wanda dama tuni yan uwana na gidan nashi domin walimat 'budar kai" da akayi mani, sai ya zamana, wajan tara na dare gida ya koma ba kowa sai ni kadai. Ango Mustapha kuwa tun takwas da yan mintina ya zo da abokanan shi, ya gabatar dasu, a gabana, da sauran yan surutansu na abukan anguna, da yan nasihohinsu, wanda ni bata mani rai kawai sukeyi, tunda har yau ba abinda nike so Mustapha yayi mani, sai ya sakeni in huta. Ni kaina duk wata hanyar da zanbi in ga an raba auranmu nabi ta, amma kowa sai dai yace inyi hakuri, har daddy na samu ina kuka, amma sai ma na sihohi yayi mani yace in hakura. Bayan sun fita ne har dashi dan rakiya, ba abinda ni kuna nayi kokarin yi sai rufe kofar cikin dakina na sam.u gefen gado na zauna na rabka tagumi na, ba abinda nike tunani sai ya akayi reshe ya juye da mujiya haka, yau gani gidan Mustapha ba Halimatu ba, Kwakwasa kofar da akayi ita tasa na katsi tunanina tare da faduwar gaba, "Hamida don Allah ki bude mani, ba wani abu zanyi maki ba, iyakata da ke magana, ina so ne in gaya maki abinda ya faru a tsanina da kawarki har ya zamo an juya na aureki. Please, kada kiyi tunanin dan ni, ki bude dan Allah, sannan kiji tsoraonsa bani ba, kiyi tunanin shi ke bayar da aljannan ga wanda yaso, ya kuma aikata aikin kwarai, sannan kiyi tunanin shi fa ke bayar da wuta ga wanda ya kaucewa umurninsa. Kiyi tunanin nifa na zama miji a gare ki, saboda haka duk abinda na lissafa baya biyayya gareki zata iya janyo maki dadi haka, kin biyayya a gareni zai iya janyo maki kishiyar haka, amma in kin zabi abinda kikaga yafi alheri gareki, to ni dan addua ne, in nan take na tuno irin nasihohin da akayi a babban masallacin Abuja wanda akayi a (international mosque abuja.) 38 Ba tare da na barshi ya karasa ba, na zo na bude kofa daga kullewar da nayi mata, yana tsayc, ban tsaya kallansa ba, na juya na koma jin shiru bai shigo ba yasa na juya na kalli kofa, sai naga ya jingina jikin bangon cikin dakina. Magana a hankali ya farayi mani, "wallahi Hamıda banyi niyyar canja manufa ta ba, saboda inji dadin rayuwata ba, a'a Allah ne ya kaddari kece matata, Hamida ina son duk wani abinda kike so, ko da kuwa zuciyata bata sonshi, in har nasan in nayi makishi zaki ji dadi, to zan so koma meye shi. Sam ni bani naje nasa a canja aurena da na kawarki ba, ki je ki tambayeta ya akayi, ina son in ga ni na gaya maki yarda akayi, amma ganin har yanzu gani kike kamar ni mayaudari ne, shi yasa nike ganin ko na fada maki ba zaki amince da ni ba, saboda ba so ko daya a zuciyarki nawa." a Kawarki tace kince in har akayi maki auran da ni, sai kinyi sanadiyyar rayuwata, saboda tace kince bakya kaunata ko kadan zuciyarki, amma ina mai tabbatar maki, gurina ya gama cika, tunda duniya gaba daya tasan nayi aure, kuma zuciyata tasan wacce ta ke so ce ta sa'nu, saboda haka, ina mai godiya ga Allah in har akace wacce nike so, ita ce sanadiyyar mutuwata, sannan kuma tayi mani takaba, ko da kuwa ta kwana bakwai ce. Amma don allah ina son in roki wata alfarma a gareki, ta ki dan bani lokaci kafin ki kasheni ko da na kwana uku ne, saboda ki gani, ki tabbatar, cewa ina sonki so na gaskiya, son da nasan ke ba zaki taba yi mani irinsa ba, kawarki tace kince inkin ganni ranki baci yake, saboda kuna da zuciyarki keyi. "Wai ni yaushe na fadi waDannan maganganun? Sharrin da Halimatu zatayi mani kenan, yanzu ba sai an kwana ba sai naje na sameta ta gaya mani ranar dana fada mata wadannan maganganu." Na nufi hanyar fita daga dakin "Hamida" na waigo na kalleshi, "kina nufin baki fadi cewa bakya sona ba? Kina nufin baki fadi wadannan maganganun ba,?" "wallahi ni ban fada ba," "in har da gaske baki fada ba zo wajena yanzu," ya miko mani hannuwanshi duk biyun daga in da yake jingine da bango. Nayi tsaye ko motsi na kasa yi, "kin fada kenan cewa bakya sona, zaki kasheni ki huta ko?" "ni ban fada ba, "me zai hana ki zo 39 gareni yanzu, alhalin kinsan ni mijinkine mai kaunarki," yayi shiru tare da mayar da kansa ya kwantar a jikin bangon. A hankali na dinga tafiya har na zo dai-dai kusa da shi amma sai ya zamanto na kasa karasa isa jikinsa, na kura masa ido ina kallan fiskarshi wacce idanuwansa ke lumshe yana mayar da numfashi a hankali, nan take naji sonshi ya dawo mani sabo. Kyawun fiskarshi ya bai yana sosai, nan take sai naji gashin dake kwace a fatata duk ya tashi, na tambayi kaina shin ina son Mustapha ko kuwa bana sonsa?, nan take sai naji jikina ya bani amsa da cewa, son Mustapha ne a cikinsa. Maimakon in isa in shafa kyakkyawar fiskar mijina, sai naji na tsuguna kasan Kafafunsa, jin yayi shiru yasa na dago kaina na kalleshi, amma yarda yake dazu, har yanzu ma haka, na sa hnnuna na shafa yan yatsun kafarshi, sai a lokacin naga ya sunkuyo a kaina. "Baki fada ba?" na daga kaina, yasa hannuwansa, ya dagoni na mike tsaye hannayensa yasa ya tallabi kumatuna, " you love me, now" maimakon in- amsa masa, sai kawai naji hawaye masu sanyi sun zuba a kaumatuna, tare da ajiyar zuciya na mayar da fiskata na kwantar a jikin hannunsa. "Zaki zauna dani yanzu?" "Halimatu zata ce na ci ama ", "don't to say that" itama tana gidan mijinta yanzu," yasa dan yatsa yana wasa da hawayen da ke zuba a fiskata, nasa hannuna na dauke hannunsa, a hankali naji ya hadani da jikinsa, ya rungume, wanda ya kwantar da kaina a jikinsa. Karfe shidda da rabi na safiyar litinin na farka, naji ni mane a jikin Mustapha, na samu na daga hannunshi da yake saman bayana, na mike a hankali, naja wani zane dake kusa dani na daura na nufi ban daki, amma ina zuwa sai naji na kasa yin komai, wanda hakan yasa na samu gefe daya a cikin ban dakin na zauna dirshan kasa. Bayan kusan mintuna sha tara, sai naji Mustapha na kiran sunana a hankali, maimakon in amsa sai ma na tura kaina a cinyata saboda tunanin da wane idon zan kalli Mustapha ni Hamida, ina haka ya iso ya tsuguna agabana sai naji ya danyi yar dariya "uwar gida Hamida," nayi shiru na kyaleshi, ya dago kaina, sai na harareshi. 40 "Kai yau ya cancanci in biya kudin wannan kallon, sai ya chukumoni, ya dura a jikinsa, inda ya zame ya zana kasa shima a bandakin, ya dago kaina, wai tsotsar bakina zaiyi, na dinga gocewa, har na zame na kwanta kasa, ya dinga dariya shima ya kwanto, ya rungumo bayana. "Wanka ko kin yafe?" na daga kaina alamaar E, "kudin kallaki ko shima kin yafe?" na daga kaina, to ni ban yafe ba sai na biyaki da kudin da ba'a rikonsu a hannu," "wadanne kudine su kuma?"na fada kai a kudundune da hannayena," "kallansu ki gani "me zan kalla?" "kudin" na samu da kyar na juyo, wai sai naga ya turo mani halshensa, da yawu a jiki, "ina kudin?" "Gasu" ma'ana dai yawun da halshe yake nufi, na dan sa hannuna na daki bakinsa, ya kara wargajewa kwance a kasa yana dariya. Ko abinci bamu tsaya munci ba don gajiya, bamu farka ba, sai karfe daya na rana, na samu na kwakwale Mustapha daga kirjina na mike, wai ni abinci zanje in dora, wanda nike tambayar kaina me zanyi, inna shiga kicin daina ma'ana, abincin safe ko na rana. Na bude: firij din sashena naga ba komai ciki na ci sai kayan sha da na makulashe, ina haka mustapha ya biyo bayana," madam" haw are you to day? Nayi murmushi kunya ya lakaci hancina," "yunwa nike ji," "yanzu zan dora kicin zan shiga yanzu, ba kaine ba," "ni ne nayi me?", "kace ayi barci," "ba gashi kin huta ba." Wai yarda nike magana, shima haka ya keyi, ya ja hancina, kadan, "zo muje sashena in gani ko na fiki abinci," muna shiga bAbban falashi, naji kanshi na tashi, nan take yawona ya tsinke, har sai da muka isa falonshi na dakinshi sai naga tebirinshi jere da kayan abinci. "Kai," nace, ke", shima yace," "wa yayi haka?" "kukuna" da agida kake cin abinci?" "da a ina zan dinga ci?" "ba kunada hotel ba?" "a'a ni in.kinga naci abincin hotel to wata kasar naje, amma in dai a gida Nigeria ne, tare da mai dafa mani abincina nake yawo." "Sannu" nace masa yayi dariya, "kinsa mu manya a ko ina muna da abokan hamayya, shi yasa gudun kada a hada baki a zuba maka wani abu ta lemu, ko abinbci, shi yasa bana cin abincin kowa, 41 sai na mamata kawai, sai kuwa in yarona ya dafa mani, yanzun kuwa sai na Hamida ta. Muna hira yana cin abincinsa, a haka ya lura ni banaci shine fa naga ya taso ya zauna saman tabirin a gefena, sai da ya tilastani naci nima. Gaba dayan yaransa, har da masu gadin duk get din biyu, da gadin gidan, da ma su ba ruwan fulawa ne da sauransu, sai da ya tarasu ya gabatar da su a wajena, da aikin kowa, su kuma ya kara gabatar da ni a wajasu. A karshe ya nuna mani Abdurashid yace mani shine bAbban su gaba daya, kome nike so in bayanan, Abdulrashid zan tambaya, shima haka ko me yake so, ya tambayeni, da na lissafa masu aikin gidanshi sai naga sun kai kusan arba'in saboda talatin da bakwai, ga arba'in kalilan ne babu, Karfe biyar saura na yammar ranar, yace muje in ga wani abu, ni kuwa na bishi a baya, har wani loko na gidan, wanda bansan dashi ba, muna zuwa ya kaini ga wata mota, yar karamar mai kyan gaske, an rubuta," is for my wife,"happy marriage". "Ni Yallaßai?," ya daga mani kai alam,ar e,' haka da yayi mani yasa nayi baya, bayan ya shigo falona ya samwni ya zauna kusa da ni, "me nayi maki kuma Hamida", nayi maki wani laifi ne na daga kai alamar e, meye gaya mani "Ni fa ba dan kudinka na hakura zan zauna da kai ba, kuma kasan ba ban kudinka ba nike so. ."nayi shiru na kasa karasawa, "naji nagane ba dan kudina kike sona ba ko?," na daga kai, "to cigaba" "shine amma zaka! Zaka!! Yi mani haka." "Oho! Na gane wallahi ba haka nike nufi ba, nayi ne kawai saboda godiya ga Allah da nuna maki murnata da na sameki "fine Woman" ina fatan kin ganc?" nayi saurin kife kaina a cinayata saboda kunyar da ta kamani, ya matso kusa dani," "kin fahimceni yanzu ko?" na mike na nufi cikin dakina *** *** *** Watana biyar kenan a gidan Mustapha, tun ina jin kunya da nauyin ya ma za'ayi in cigaba da zama da shi, sai gani har na sake 42 na saba.ni ma balle ganin yarda Halimatu ta sake a gidan nata mijin, har wani nuna mani take, ita fa tayi auran soyayya, ba tasan ni ma ina son nawa mijin ba, kawaici kawai nake mata lokacin, yanzun kuwa mun niga mun goge a gidan Yallabai dina. a Kauna kuwa wajan mahaifiyarsa kamar ta hadiyeni, haka ma da mukaje indiya yan uwanshi suka nuna mani kauna, balle lokacin da bani da wata isasshiyar lafiya. Samun cikina kuwa yasa Yallabai ya kasa fita ko wace kasa saboda kula da lafiyata da debe mani kewar girman gidanshi ni kadar, sai dai yakan fita ofis, ko wasu jahohin da yasan ba kwana zai yi ba. Amma duk wani aikin da yasan kwana za'ayi ko ya haure nan Kasar, sai dai ya tura jabir, wanda ni kuma ko wash nace tamkar ya saka ihu dan kulawar da yake mani, sai dai abu daya da ya dan damar mani zuciya, shine tunda yaga ina da ciki shekenan ya daina dokina da nuna hutawarsa gareni. Wanda na tambayi halaimatu, tace ita nata mijin a koda yasuhe bai ki ya huta ba, sai dai in ya lura bata jin dadi sosai, naga itama fa tana da cikin ıan kamar ni, amma ko zuwa nayi gidan sai inga yaya nata rawar jikin da ita kamar ya hadiyeta. Ni kuwa in kaga Yallaßai na rawar jiki, to yaga bani da lafiya, ko zanci in cin wani abu, to lokacin zai dinga rawar jiki yaga ya kawo mani shi, nasan duk bayan awa daya ko lokacin da ya dan samu dama a ofis, yakan buga mani waya yaji ya nike. Haka kuma na tambayi Zulaihatu wacce itama yanzo take laulayin nata ciki, tunda mun rigata samun ciki, amma tace ita wani lokacima, sai mijnta yaga tana kuka, tukuna zai saurara mata, ko yaganta akwance sosai, bata jin dadi. Ni nasan yallabi na kulawa dani Dari bisa Dari, amma wannan abun daya shine ke damuna saboda tunanin ko dai ya samu wasu a waje ne shi yasa ya manta dani, wannan abun ne kawai ke damuna, wanda na kasa yiwa Yallabai magana a kanshi. Wai ko irin wani garin mukaje muka samu kwanaki, in mun dawo, a tunanin, ya kamata ya nuna doki a akaina, amma sai in ga shiru wanda farkon aurena da shi ba haka muke ba, nasan farkon na kwanta jinyar laulayi amma yanzu cikina wata hudu kenan, na samu 43 na daina duk wata matsananciyar rashin lafiya, amma har yanzu ba wani canji. Bayan na gama gyara jikina da ruwan kunun kanwar shadda na kallin kaina a madudi naga nayi kyaun gaske, anan take ne na kama tananin kwaliyar ma da na zauna na bata lokaci na nayi ta, nasan mijina ba yabbawa zai yi da ita ba, amma duk da haka ban taba kinyi kwalliyata ba. Na fito ina taku a hankali zuwa bayan gida inda muke hutawa duk yamma ni da Yallabai na, ina dososhi, naga alamar kamar maba a hankalinsa yake ba, saboda tunanin da naga ya nutsu a cikinshi. Har na iso na tsaya bayanshi, amma bai san na zo ba, hakan yasa na sa shantala shantalan yan yatsuna na rufe mashi idanunwanshi ta baya, sai a lokcin naji yace, wai Allah, kin tsoratani, my love," yasa hannuwansa ya janye hannayena, ya zagayo dani ya kwanta a cinyarsa. Kina son kiyi wasa da jikinki ko Hamida? Na dan langwabe ki," to ya kake son inyi yallaßai, in daina tafiya? ko kuwa in daina wanka gaba daya?, "ni ba haka nike nufi ba, ni dai ki daina yawan wasa da jikinki, ni fa ko gani nayi kina tafiy. da karfi sai naji hankalina ya tashi." Ya danyi shiru, "Hamida tunda kika samu cikin nan naji hankalina ya tashi mutuka," "saboda baka sin haihuwa ko kuwa saboda me?," "ba haka nike nufi ba, Hamida waye zai haihu duniya, sai wanda bai yarda da kaddara ba." cikin nawa?" a "Kenan nice kaddara ko "a'a kada kiyi saurin sawa zuciyarki wata fassara ta da ban," "to da nice kenan baka son haihuwa?, ai da ka gaya mani haka da tuni na san. "kada ki ce komai don Allah. Ni ba haka nake nufi ba, Hamida tunanin yarda akace mani haihuwa da wahala, shiya ke tayarmani da hankali," "waya gaya maka haka?" "mahaifina yace mani wajan haihuwa mata na wahala harma mutuwa akeyi wani lokaci. To a yanzun ya ikake son ayi da cikin?" "ba komai, amma koda yaushe na kallleki, sai inji hankali na ya tashi matuka," "ashe shi yasa ka mayar da ni bola a gidanka?" 44 "Sam ba haka bane Homida," "to me ye?" "yanzun dai abar wannan maganar, Allah ya baki hakuri shi kenan ko?" "shi kenan a wajanka, amma ni a nawa wajan ya zama dole in yi tunanin matakin da zan dauka a kan lamarin," haba Hamida don Allah ki bar maganar nan ni a wajena ta wuce har a bada." "Ni ma ta wuce a gareni." Har kusan sallah magariba muna wajan shan iskan mu, gannim an fara kiran sallah magariba yasa muka kwashe kayan mu, muka koma ciki. Bayan sallah, isha ne mun gama cin abinci, na taka zuwa shashina, daga shashin Mustapha, wanda nayi haka ne domin ni har yanzu zuciyata na cikin ciwo da kunar maganganun da Mustapha ya fada na game da cikin jikina Ban tsaya yi komai ba, na mayar da kofar dakina na kulle, bai fi minti sha biyar ba tsakani, sai naji yallabai na kwankwasa mani kofa, ina jinshi tun yanayi a hankali, har yakai ga bugawa da dan kafinsa, tare da ambatar sunana. Ina jinsa ya kwana zirga zirga daga shasen shi, zuwa nawa, har ya gaji ya koma ga waya, amma ni ma sai na dauke duk kan wayar da ke shashena, na ajiye da ban Kwana mu biyu a haka, wanda ni tuni na rayawa zuciyata ni da Mustapha ya saka ni idanunsa sai na haihu, shima dan asan mai yiyyuwa, saboda ba zan iya zama da mutumin da baya son, haihuwa ba. Ranar cikon na uku ne, kamar ance mani in mayar da kan wayoyi na saboda tunanin kada a dinga bugowa daga gidan mu, ko wani bangaren aji shiru, ban fi minti biyu da mayar da kan waya ba sai naji wayar na kara, har na vi niyyar kada in dauka can kuwa wata zuciyar tace in daure in dauka. Ina kangawa a kunnena sai naji Halimatu nan muka sha hirar mu ta wayar tarho, har ta tsayin mintuna talatin, wanda ina ajiyewa naji wayar tarho din ta kara sakin sauti miryarshi kawai naji na gane Yallabai din na ne, "Hamida ke ce akan waya "kana iya cigaba da maganarka ina saurarenka" "dama ina son yin magana da ke don Allah," "dama ni ban hana ka yin magana dani ba, na baka lokacine kayi shawara a kaina." 45 "Ba wata shawara Hamida da zanyi ina son don Allah ki huce haka nan, ni ma na gane nawa kuskuran please ayi hakuri gimbiya, kwana biyu fa Hamida ban ganki ba banga beby na ba" "waye kuma bebinka?" "Allah huci zuciya." Daga tambaya sai ban hakuri," "ni dai a ce an huce a gani yanzun in zo," "au dama ka damu da sha'anin mu?" "ba zan iya baki wannan amsar ba sai in kin bani izini zuwa gareki, ke da kanki zaki gane amsarki, in har kin tsaya mun hada ido da ke." "yanzun yaushe zaka zo?" "in yanzun ki kace in zo sai dai in ce ki jirani nan da minti goma," na kalle agogon da ke manne gefan bangon arewa, karfe sha biyun rana saura minti goma sha uku, "kana iya zuwa wajan karfe biyu na rana." Ina jinsa yana fada, "a rage Hamida yayi mani nisa," amma ma sai na ajiye kan wayar tarho na juya abina. Cikin gudu-gudu sauri sauri, na samu na gama dura mashi yar jalaf din taliya da farfesun kayan cikin rago, banda dan lemun dana hada mashi a gefe, ma'ana lamun da nasan ya fi so a duk cikin lemuna da nike hada masa. Watau lemun kwakwa, ina sauke wa tare da wankana, gidana kuwa a tsabtacensa ya ke saboda duk safiya da kwai mai yin aikinshi na nusamman a cikin yaran Yallabai na. Shaddace ruwan cincin bale turare nasa ajikina, na mayar da kofar bAbban falo na rufe da madaninta, ma'anata, sai ya kwankwasa tukuna a bude masa, karfe biyu dai dai naji an kwankwasa kofa. Da dan hanzarina naje na bude masa, Abdulrashid ne hannayensa lode da kaya har naji zuciyata tayi ba dadi kadan saboda rashin ganin Yallabai na. Bayan hankalina ya dauke ga yiwa Abdulrashid magana, sai naji wani kamshin turare ya ratsa hancina, da sauri na juya zuwa ga kallan kofa, sai naga Yallabai na, tsaye yana dan murmushi. Abdulrashid na fita sai kuma yana matsowa dab da ni, ya kama hannuwana duk biyun tare da fadar (I miss you, you and my beby)" "na dan daki kirjinsa da kaina wanda hakan yasa ya kara hadani da jikinsa 46 sayan na tAbbatar ya ci abinci ya koshi ni kuma na tashi na koma sha shina saboda har yanzun ina jin haushin maganganun da ya gayamani kwana biyu da suka wuce. Ina jin shogowarsa, a lokacin ni har na riga na kwanta, ina jinsa ya kwanta bayana "Hamida har yanzun baki hakura ba?" "kai ma ai kasan bakayi mani dai dai ba "baki fahimceni ba ne Hamida, sam ni ba manufata bana son ki haifa mani yara ba, manufata shine tausaya maki da tunanin ya za'ayi in dinga takura maki, alhalin kina יי cikin hadare kamar wannan." Yasa hannun ya rungumani jikinsa ta bayana, "amma dan Allah kiyi hakuri, daga yau nayi maki alkawarin ba zan kuma yi maki haka ba Cikin sigar tausaya masa na miko hannuna ta baya na shafi gashin kansa, "ni ma dan Allah ka yafe mani, 'tsayin lokacin dana dauka ina cutar da kai, har tsayin kwana biyu, kayi mani afuwa don Allah," "Na yafe maki Hamida nıma ai nasan rashin fahimtar juna ta kawo mana haka, nayi imani da kin fahinceni haka ba zata taba faruwa ba tun karfe bakwai da rabi na safiyar ranar na tashi na shiga kicin domin shiryawa Yallaßai dina kalacin safe, saboda nasan ya dauki lokaci bai ci kalar abincin matar sa ba, tunda na kwanta rashin lafiya da daniel ya shiga kicin, a ranar kuwa Yallabai ko kofar gida bai fita saboda shagwaßa da sangarta da ya yini yi mani. Misalin karfe shidda na yamma

Chapter 4 of 8