Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
3 / 8
dama kuma dan shi nake yi, na mike muka tafi tare da Mustapha. Har makayi nisa da tafiya, bai ko kalli inda nike zaune ba, balle wata magana ta hadamu da shi. Titin da zai fitar damu daga unguwarmu, mai tama dai dai nan naga Mustapha ya kashe mota, ni kuwa sai ma na kalli bangaran marfin sashena, tsawon minti biyu tukuna ya fara magana. Kin san saboda ke na tsaya, amma kika kalli wani 6angaren, duk dan ki kara mani wani hasuhin," "haushin me zan kara maka, kai ba mijina ba?, ni nayi zaton ko motarce ta lalace shi yasa, sannan ganin in na kalleka haramun nake kallo, shi yasa na juyar da kaina gefe, amma tunda magana gareka, kayi kokarin kayita da wuri saboda kasan fa aroni kayi, wanda ka aroni a hannunsa fa yana can yana ji. "Bana san wannan maganar ta isa haka nan, "just looking at me" na waigo na kallshi, "me kika gani a idona da jikina?" "banga komai ba," "ki kalleni sosai Hamida," jin ya rage sautin miryar yasa na kalli bangaren wajan motar. "ki kalleni sosai Hamida cikin tsakinina duk na rame saboda ke, Hamida bazan iya auran da zakiyi mani ba, dan Allah ki yafe mani shi, nasan zuciyarki za tayi kuncin naki auran kawarki ba "Me yasa kake mayarda zance baya Mustapha, na fada amma fa nima sai naji miryata ta rage zakin da takeyi a dazu, "saboda ina kaunarki sosai a zuciyata, dan Allah ki kalleni Hamida, 21 pa dan na isa ba, na juyo na kalleshi muka hada ido da shi, wanda sai a lokacin naga kwayar idansa ta koma ja, sumar gashn kansa ma tasan jikin Mustapha ba lafiya. Me kika gani? na kawar da fiskata gefe "ba komai sai ciwon ido da naga idan ka nayi," "yayi wani dan murmushi mai tashi da dan kadan din sauti, "kinsan abinda ke damuna, nayi imani kinga abinda kwayar idona ke so, kin san ke take so Hamida. "to yanzu duk me ya kawo wannan maganar, ka san, "is too late," "wallahi is not too late,' in kin bani izini yanzu in je in mayar a daura mani auran da ke," "kenan mun zama maciya amana ko?" "sam ba cin amana bane, san kaine, kin san kuma duk duniya ba farkon abinda ya cancanci dan adam ya so, illa ya so kanshi, kafin son kowa." Amma ni wallahi zuciyata tafi sonki fiye da kaina kinga kuwa don naso kaina a kanki ai na yiwa kaina adalci kenan""yanzun dai zaka wajan Halimatu ko ka fasa?" "ni dama ba wajanta zani ba. Wajanki na zo,". "Amma kasan bai cancanta ba ko?" "saboda me kikace haka?” "saboda yanzu na zama matar wani," "walla'i kika kara fadar wannan kalmar sai na wulakanta maki rayuwa yanzun nan". Ni zan koma gida," "sai kin dawo," ya juyar da kansa gefe, ni kuwa kokawar bude kofa nike, amma taki budewa, na dawo da kallona gareshi. "Why?" "da akayi me?" "da ka rufeni," "au baki san wajan budewa ba ne? ko da yake ba mamaki, baki faye shiga motata ba, tsaya in bude maki," gaba dayanshi ya kwanto jikinshi a jikina, mai makon ya bude, sai naga gelas din motar duk sun rufe," "me ye haka Mustapha, jikinane da ya hadu da mahadinsa, sai ya ji ba zai iya rabuwa da shi ba, ni ba ruwana, jikina ne, Hamida." "Mustapha bai dace kayi mani haka ba, kasan fa in hali Hannunsa naji a bakina, ya rufe maganar da zanyi, "Hamida ilove you, I cant marry your friend", amma kina son bata mani raina 33 da yawan yi mani maganarta. 25 Na saukar da ajiyar zuciyar da ta dan fito fili, "yasa danyatsansa yana zagaye la66ana, "kiyi hakuri, na baki haushi ko?" nasa hannuwana na tureshi, sam na manta da ciwona sai a lokacin, hakan yasa na famashi sosai, na dinga yarfe hannuna ina wash! Wash!! "Kaga ni kaja na fama hannuna, dama zuwa kayi ka karasa gutsure mani shi." "Wayyo mu gani, mugani!! Har kinsa hankalina ya kara tashi sosai, "naki nuna masa har sai da ya kamo hannun da tsiya, "kai! Kai!! Kai!!! Yanzun Hamida kika zauna hirar banza da hannunki kumbure haka, kila ma karaya ce. Jaki mahaukaci, wai shi yana son mace amma bai iya kula da rayuwar ta ba," "waye shi, "na fada ina wash, mahaukacin da kika baro yana jiranki," ya fada a dai dai lokacin da ya tashi mota, hankalinsa a tashe bai zame ko ina ba sai asibitin dake kusa damu." Da shiga abinka ga babban mutum, nan da nan aka yı mana jagora sai wajan likita, muna shiga yace wai matarsa ce ya kawo, ta samu matsala a hannu, nan likia ya tayashi murna, da Allah ya sawake, sannan yace yaga hannurı. Yana fara taba hannun nace wash! Wash!! "dacta da zafi fa" "to sannu! Sannu!! Sai kin daure," ina kallan Mustapha kamar yasa ihu, ko ban sani ba nasan abu biyu Mustapha yake batawa fiska, shine zafin da nike ji wanda ba zai iya cire mani shi ba, sai lagwaiwaita mani hanun da likita ke yi. Likita ya saki hannuna ya kalli Mustapha, "Yallabai ina jin sai dai a kirawo mai gyaran hausa, amma na duba ba karaya bace, ba tsagewar kashi ba kila dai targade ne, ko gocewa, wannan sai masu aikin gargajiya, ya danyi shiru. "Yauwa, inji likita, "a kwaı wani yaro da muke kira yana yi mana ire-iren wannan aikin in ya taso, in ka amince a kira shi," "ba komai, ba komai a kirawo shi amma ai zata warke, zuwa anjima ko?" likita yayi dariya wadda nima har kunya sai da ta kamani. Cikin zaman minti ashirin sai ga wani yaro ya shigo, shekarunsa na haihuwa sayi ashirin da biyar bakine, amma da gani bakinsa mai kyaune, ya shigo ya zauna shima tare da gaishemu, Lanka amsa, sannan ya gaisa da likita. 26 "dama wannan hajiyar zaka duba mana hannunta ka gano mana me ya same hanun nata, saboda muji dadin bata magani," "to tallabai. yaron yana zuwa ya tsuguna gabana, Mustapha na tasowa daga kujerarsa shima, ya tsuguna gefena, kamar inyi dariya, sai dai na dan dakc. "Irin damkar da yayiwa ya tsuna, tasha ban ban da ta likitawajan zafi, ai kuwa nace, "kai! Kai!! Wash, kai da zafi fa sosai, kayi a hankali," sai yasa hannu daya a tafin hannuna, dayan kuwa ya fara taba 'yan yatsuna. "Dakata dakata!! Dakata!!! Kaga da zafi fa, ga mani yarda akayi inji mta, "alhaji hakuri zakayi ya duba mana, saboda abun ne sai wanda yake aikin shine za iya ganewa," likitane yake baiwa Mustapha hakuri. "To! To!! Shi kenan kayi mata, ni ba ruwana ısaya in fita, ni ba zan iya gani ba, da ciwo fa," ba wani zancen ciwo kishin tsiyane na kada a taba mani hannu, ke damunshi, amma duk da haka, sai gashi ya kasa fita. Wanda ni kuma tun ina daurewa, har sai gani ina zubar da hawaye, a haka mai gyaran hannu ya gayawa likitu cewa targadeee yan yatsun uku sukayi, dayan kuwa gocewa ce, nan take likita yace ya kama mani targaden, ko ince ya gyara mani hannun gaba daya. Sai gani ina kuka ina rike Mustapha, saboda wani irin tsananin zafi da naji yana ratsa mani jiki, da kyar na samu na daure aka gama mani, sannan likita ya rubuta mani magunguna, har da na shafawa a yan yatsun. Muna shiga mota, dukewa nayi, na cigaba da zubar da hawaye da suka rage mani na zafin ciwon hannuna, jin Mustapha nayi ya daga kai na, baice mani komai ba, sai dai yasa gefan rigasa yana goge mani hawayen fiskata, "da zafi ko?, sannu dan ba yanda za'ayi in cire shi daga jikinki ya dawo kaina, da nayi maki. Yayi shiru, da nasan haka zaki sha wahala, da ban kawoki ba ni na janyo maki ciwo har haka ko? Sannu, sannu haka ya dinga lallashina, har ya samu nayi shiru, sannan yada mota muka tafi. Mai makon mutafi wajan Halimatu, sai naga mun tsaya a .SAIHAD STORE' sai naji yace in jirashi, minti goma sha biyar da 27 shigarsa, sai gashi ya fito da yar bakar leda, a hannunsa, sai da ya shigo ya zauna tukuna ya miko mani ledar. "Kayan gyaran fiskatane ki gyara fiskarki, gudun kada mu koma a dinga tambayarki" "na dan harareshi, "ni ba zan gyara ba," "Hamida tausayinki nake ji yanzu, da sai na biya ki kudin kallon da kike yi mani kinyi mani shi a ofishin likita, yanzu ma kin kara zan rama, ne Nayi shiru bance kõmai ba, ki gyara mana, "sai ka fita," "ina zani ni da matata "ni ba matarka Bace Halimatu ce mat Kafin in karasa ya fice daga motar, bayan kamar minit goma, sannan na fito nima, na. gama," bai kalleni ba ya bude mota ya shige, na shigo nima, ko rufe wa banyi ba, ya kanayi imani fada. "Ban gaya maki in muna tare kada ki Kara ambatar-stınan wata ko wani ba, na lura-ke dai Hamida kullum kin, tison kiga raina a bace," "Allah huci zuciyarka ni das yanzu mayar dani gidanmu don Allah," "yaushe ne kuke fatin naku?" Karfe biyar na yamma in sha allahu mun fara, "a ma zakuyi? A BUK Gust INN. Bai ce komai ba ya ja mota, zaka zo ne?" inna samu dama." "zan iya gaya mata hakan?" ko na zo ba dan ita zanzo ba." "dan wa zaka zo? ke "ni Mustapha waigo ya kalleni, sai naga yayi murmushi. "Hamida ina son in ji kin kira sunana, sai inji sanyi a zuciyata, yanzu har naji bacin raina ya kau. zanzo wajan fatin na ku, amma kada ki kurkusara kiyi mani abinda zai bata mani ra, "to ni kuwa ina ruwana da zuwanka balle in kai ga bata maka rai, kai da ka zo saboda matarka." "Wacece matata?" "ita ha "Ya kalleni, "to ba zan ce Hamida ba kuma ya tuntsure da dariya, "sai tsoro da kinsa vanzin na kara yi-maki wani kamun hannu, na harareshi ba sai in some maka ba yanzun wai kila maki Sani hawan jini," mu kayi dariya ya kawoni har gidan mu ya ajiye da tabbatar mani zaizo wajan fatin mu Hankalina gaba daya yana ga Kofar shigowa dakin taron fatin namu, ganin kowa ya gama shigowa, har an fara addu'ar bude taro, amma ba Mustapha, duk da nasan ban gayawa Halimatu yanda 28 mukayi da shi ba, amma duk da haka sai naga yau Halimatu tanata fara'a ta saki jiki sosai, ba kamar baya ba. A zuciyata ba abinda nike cewa, sai yaya Mustapha zai yi mani haka?" bayan angama addu'a an shafa cikin abokan sufiyanu wani ya mike kenan zai fara magana sai kawai naga fiskar Mustapha ta shogo dakin taron, ban san lokacin da na mike tsaye da sauri ba, tare da fadar Halimatu ga angonki." Gaba daya kallo ya koma ga Mustaphan da ake takewa baya, wani abun da ban fahimta ba, shine Mustapha na shigowa, naga nan take ana canja, mazauni, ma'ana sai naga sufiyanu ya tashi daga kusa dani, mazauninshi na ango ya koma kusa da Zulahatu, yaya Usman naga ya koma mazaunin kusa da Halimatu, mazaunin sufiyanu shi kuma Mustapha ya zauna. Kafin in gama mamaki, har mai magana ya fara da cewa "jama'a kada kuga anyi haka ku dauka wani abu, ba komai muna tafiyar da tsarin ne tamkar tsarin turawa, saboda kara hada zumunci. Anyi taro lafiya, an kuma tashi lafiya, wanda mu duka hankalinmu a kwance, saboda Mustapha bai nuna wani abu ya shiga tsakanina da shi ba, ya saki jiki sosai da Halimatu, sii dai abu daya da ya so ya bani haushi shine, yawan shigewa sufiyanu da naga Zulahatu nayi, wanda na kasa daurewa, har sai da nayiwa sufiyanu magana. Amma sai yace mani, ba wani abu, saboda ni Zulaihatu ke yin haka, dan gani raina ya dan sosu, har na dan samu waje daya ni kadai na zauna, yasa Mustapha, ya zo ya tambayeni ko lafiya, gudun kada Halimatu taji yarda naji yasa ban tsaya bashi wata amsa ba, nace ba komai, kawai na mike na shige cikin mutane. Komai lafiya kalau, har ranar daurin aure tą zo, ranar asabar da yamma karfe hudu za'a daura auranmu, wanda yan masari da mai maiduguri suka bada lamanin, ayi a nan garin abuja, saboda kada a baiwa jama'a wahala da yawa. Karfe goma na safe, zuwa karfe uku na rana, akayi walima ta musamman wacce Mustapha ya hadata a matsayin walimar iyaye da manayan baki, wacce za'ayi a naicon, mada din in an dawo daga daurin aure, saboda in an dawo daurin aure, zamu zauna a nan 29 naicon hotel din har su dawo, a in da mu kuma zamu kara shiryawa da angunanmu, zuwa hotel din Prince hotel. Domin tamu dina fatin wanda zamuyi yamu-yamu yara, wanda zai iya daukar mu har karfe sha biyu na dare, hakan yasa anguna, suka roki alfarma abar kai amare sai lahadi, wanda itama ranar lahadin za'ayi karatun Qur'anic and Recitation da yar fadakarwa, zuwa la'asar a masallacin Abuja, watau National Mosque. In an fito za'aci abincin iyaye na Allah bada zaman lafiya da a zahar bayan sallah, a koma har zuwa karfe biyar sai a tashi bayan nan ne da dare za'a kai amare gida jansu. *** *** Taro yayi taro a Hotel dan naicon wanda ko ban fada ba kasan an hada manyan Nigeria a wajan, sa da aka dinga gaisawa da jama'a, mu yara da su iyayenmu kansu, wanda hakan ya dauki awa daya lafiyayya, takuna aka bayar da izinin a zauna. In da duk tebir mutum hudu ne, da kayan sha, a gaban su, mu kuwa tebir din mu, mu hidda ne ni da sufiyanu, sai Halimatu da Mustapha, sai bAbbar kawarmu Zulaihatu, da yaya Usman a gefen mu, mun zama shida kenan. Wanda muna can saman fakin taron, "gefen da iyayenmu suke, sai dai ba'a jere da su muke ba, Mai makon in ga an fara kawo abinci sai naga manyan kasa sun fara tashi suna magana daya bayan daya da turanci, abinda ya daure mani kai shine in da iyayen anguna da amare suka dinga magana daya baya daya. A wajan kalaman Daddy na sai naji yana cewa ya gode Allah da ya kawoshi auran yayansa uku gaba daya, saboda dole yayiwa Baban Halimatu kara yasata cikin yayansa biyu su cike uku kenan. Ban damu ba, saboda ina tunanin, ni da sufiyanu yake nufi, sai ita Halimatu Alhaji Nafi'u Sani, shi ya zamo madadin mahaifin Mustapha, bayan sane Hajiya Hindatu ta fito tayi nata bayanin godiyar ga Allah, bayan nan sai Alhaji Yusufari Abba Ghana mahaifin Halimatu, in da yayi godiya ga Allah da Allah ya kawoshi auran yarsa, da kuma yayan amininsa su biyu. 30 Sai kuma mahaifin safiyanu yayi shima in da naji yana mika godiyarshi ga mahaifin Zulahatu, da iyayenmu, nan take nace, oho dai sufiyanu yariga ya zama nawa, Zulaihatu sai dai ta samu wani. Shishshigi nace a zuciyata, da naga mahaifin Zulaihatu ya tashi yana bayanin wai ya gode Allah da Allah ya kawoshi bikin yarsa Zulaihatu, nan take, sai nace a zuciyata, to ko yayana shi zai auri Zulaihatu, sai naji wani irin sanyi a zuciyata, saboda Zulaihatu ta na da halaiya mai kyau tun muna makaranta. Bayan nan ne aka danyi yan kide-kide da yan wasannin kwaikwayan turanci, wanda zuburdaya, yayi da mutanansa bayan su, sai Papa Ajasco shima yayi da mutannansa, yan waka kuwa har da yan koroso da Bodan katsina su Dan maraya, sani Dan indo. Sai da aka samu wajan awa uku anayi tukuna aka bude taro da addu'a aka fara cin abinci, inda da aka gama aka yi sallah a zahar aka dan bata lokaci wajan kara gaisawa zuwa uku da rabi na yamma, daga nan, aka dunguzuma sai daurin aure. Sai aka barmu yan mata kawai, in da mu kuma muka shiga dakunan hotel din muka huta, wasu kuma suka fara yin wanka, gudun kada azo ana jiranmu, iyayenmu mata kuwa tuni an kaisu gidajansu. Kamar a mafarki naji mai magana da lasifika a cikin talabijin din da muke kallo sama-sama yana cewa, yau Allah ya kawo ranar da aka daura auran (HAMIDA DA MUSTAPHA NAJIB BAUCHI) wanda mutane suka fi sani da (MUHAB), Har tashi nayi na tsuguna gaban talabijin, amma mai magana sai kara mai-maitawa yake dalla-dalla. Har ya zamu na dagowa ragowar kawayenmu masu surutu, cewa suyi shiru in ji, amma mutumin nan da ya fada Halimatu da yaya Usman, ya fada sai inji yace wai sufiyanu da Zulaihatu, karshe sai na karajin yace Hamida da Mustapha. Na dinga kwallawa Halimatu kira a rude, ina cewa," zo kiji mai rahotan nan yana shirme, muyi sauri muyi waya a gayawa su daddy su sa ya gayara, wai sai naji Halimatu ta ce mani, "Hamida kenan, (baki san reshe ya juye da mujiya ba)". "Ke da Allah ana maganar kwaba da dan rahoton daurin aure keyi ke kina wani zakwalo wata karin magana can," cewa fa yake 31 wai keda yaya Usman, ni da Mustapha, shashasha, kinga, bari in yi saurin yin waya kada duniya tayi zatan da gaskene. "Ai ba karya banc ba fa Hamida, abinda yake fada shine gaskiyar magana, cewa an daura maki aure da Alhaji Mustapha Muhab, wanda ni kuma gurina ya cika na auri wanda nike kauna yayanki Usman, shi kuwa sufiyanu, ya samu sakaiyya da Zulaiha." "Wace irin maganar banzace kikeyi haka? Kin san kuwa abina kike fada Halimatu?" " Sani kuwa, kuma ni ba maganar banza na fada ba, maganar gaskiya na fada, kuma magana ta riga ta kare, tunda an riga an daura, sai ki sani daga yau Mustapha ya zama mijin Hamida Haruna Masarin katsina. Bata karasa ba na mike, "wallahi bai isa ba, abinda kuka kulla mani kenan ke da Mustapha, wallahi bai isa ba, shi din me" "a dai iya baki, saboda miji ba wasa bane kada a kwashi lodin zunubi tun yau." a "Wallahi Halimatu bani son wulakanci, in bakiyi mani shiru ba zan gungunduma maki ashar yanzu, banza,banza marar hankali." "sannu Hamidar hankali, kinga in zaki je ki shirya ki shirya, kin san tunda an daura yanzu za su zo mu tafi ko kin manta muna da sauran abubuawan yi a gaban mu? Hamida matar Musta. nayi saurin dana mata duka a cinya da karfi wanda yasa tayi shiru dan dole. Mayafina na samu na yafa na samuna dauki jakata na rataya sai hanyar fita, ina kaiwa kofa wata kawarmu saude mudi ta biyoni wai mayafinta ne na dauka, na waigo nace mata," in kineda karfi, fizge daga jiikna, nayi gaba ina jinta tana cewa tsaya mana ki gani in ban fizge ba," ban kulata ba nayi gaba. Ni nasan banzo da mota ba, ga filin hotal din ba kowa sai tsirarin mutane, sai kuwa masu gadi, amma hakan bai hanani taka kafata in fita daga harabar hotel din in samu mota ba, ina kawowa get din hotel din, motocin mustapaha da na jama'a gaba daya suna kawo kai. Jin anyi wani jan birki da duk wanda ke kusa sai da ya razana da ko haďarine za'ayi, hakan yasa nima nayi saurin waigawa sai naga Mustapha ya fito daga mota da tayi haka da saurin sa ya nufoni, ban fasa tafiyata ba, har yazo yajera dani. 32 "Hamida kada ki bani kunya a gaban jama'a zanyi maki bayani daga baya, nasan dama dole ki ji abin a bazata kiyi hakuri, ki daure ki nunawa mutane, dama kinsan komai, saboda abin nan da ya fara na family ne ba dole ne ba jama'a su sani," "ka sa a kaini gida," "muje in kaiki, "bana so" "to naji! Naji!! Zo mu je in sa akaiki, "don Allah ki saki fiskarki." Na dan juyo har da murmushina, kamar dama muna cikin hirar soyayya da shi ne, sannan nace, muje kasa a kaini gida," don Allah kiyi mani arzikin in kaiki, ko mai zakiyi mani kiyi mani shi a mota, kada ki bani kunya, ki duba jama'ar da suka taso daga nisan duniya duk saboda mu". Duk magiyarsa ban amince ya kaini ba, sai na wayance masa da jama'ar da ya tara, da kyar ya amince da hakan. Ina zuwa gidanmu, gidan a cike makil da jama'a na samu na ratsa na shiga dakina na kulle kaina a ciki. Tambayoyi na dinga jirowa kaina na ya akayi haka ta faru? Shin ko dama can tarko Halimatu tayi mani ta turani wajan Mustapha?, ko da hada baki suka yi da Mustapha bar sani ba? Amsoshin tambayoyina nasan sai Halimatu ce kawai zata. iya amsa mani su. Hakan yasa na koma na kwanta a gadona, ba abinda nike tunani, sai ya ma za'ayi in auri Mustapha, wanda har yau zuciyata bata gama amincewa da shi ba, me nayi kenan ina zauna da Mustapha a matsayin /mijina?, daga bangaran gefan zuciyata naji ance mani cin amana. Nayi tsoki, wai an daura mani aure da Mustapha abinda zuciyata ta fada kenan, to ya akayi har haka ta faru ban sani ba? Kenan ban cikawa haliamatu alkawarinta ba? Sai naji hawaye sun cika mani ido, saboda tunanin duk wahalar da nasha ta zama ta banza kenan tunda gashi a karshe ya zamana naci amanarta, tAbbas ba zan auri Mustapha ba, sai dai yasan yarda zaiyi da auransa da ke kaina. Kara naji dai-dai lokacin da hawayena suka karasa gangaraowa, na daga kallina na kalli gogon gefen gadona, karfe biyar da rabi na yamma, kenan na samu minti talatin da baro hotel din. 33 Karfe shida da mintina uku, naji an kwankwasa kofar dakina, kiran sunana da naji anayi shi ya tAbbatar mani da miryar Halimatu ce, ina jin shirun da suka ji nayi ita tasa suka daina, amma bayan yan mintina kadan sai naj wayar gefan gadona tayi kara, ban ki dauka ba, saboda ban sanko waye yayita ba, na dauka tare da sallama ta, miryar mustapha da naji ya ambaci sunana a sanyaye. Tare da cewa, "Hamida kada kiyi mani haka, please ki zo mu tati," ita tasa na kife kan wayar, tunanin zai kara bugowa,yasa na daga kan wayar na ajiye gefe, bai fi mintina goma ba. Sai naji miryar Daddy yana yi mani magana. "Ba zata bude ba ko me?" "E daddy mun kwankwasa ta ki bude mana," miryar Halimatu kenan, "bude mana," na mike da rawar jiki na bude kofa, mai makon inga daddy na shi da su Halimatu sai nagashi tare da musatapha, "baki san mutane ne ke jiranki ba, shine za'a buga maki kofa ki ki budewa, wani irin rashin hankaline haka, kai kuma kayi tsaye kana kallanta,ba zaka zabga mata mari ba, shashashar kawai shirya ki fita ko in dawo maki yanzu," yayi baya da saurinsa, na koma da baya ni kuma zuwa cikin dakina, jin an rufe kofa shi yasa na juyo, Mustapha ne ya rufeni a dakina," "dalilin tambayar da nayi masa kenan, "kada a gane mani mata, kinsan fa kaya zaki canja ko?. Na harareshi, kada ki kuma yi mani wannan kallan, in kika kara zan zo in biyaki yanzu ko kina musu?," bance komai ba, na bude akwatina na dauko kayan da zansa, ina jin tafiyarsa ya nufoni, amma hakan bai san na daga kaina ba. "Karbe wadannan ki sa, "ya miko mani yar karamar jakar matafiya, "ina da kaya ni ma wanda mahaifina ya din ka mani" "nasan da su amma wadannan nike son ki sa a matsayina ni kuma na mijinki," sai ya ajiye ya koma gefen gado ya zauna," mutane na jiranmu a waje, nasan kinsan da haka." "To ka fita in sa kayan ki," "ba in da zan fatia in zaki sa ki sa," "da wannan fadan ba kara ka zo ka dakeni ba" "Allah baki hakuri na daina, bari in runtsi idona saiki saka," yasa tafin hannayensa duk viyun a fiskarsa, na figi jakata na shige ban faki na kulle, ina jinsa yana cewa yau ne karshe, gobe kamar haka sai yarda nace," a zacıyata nace ba dai ni Hamida ba. 34 Sam wajan 'happy day na kasa hada ido da Halımatu sunar fatın namu kenan, to balle sufiyanu bawan Allah, wanda shi naga ma ya hakura va ungumi Kaddara, shi walwalarsa yake cikin jama a ni kuwa tun da na zauna a kujerata ta amarya ban tashi ba har yanzu, tun ana rokona in yi wani abu, bar kowa ya kyalcni, suka kama harkonkinsu Shu kanshi ango Mustapha, yana can cikin jama'a yana ta hidimarsa, kamar ance daga kanki, sai na hango Mustapha da wasu yan mata hudu, sai dariya yake yi masu, na tafc bakina, a zuciyata nace, "dawa zalayi haka kana gida nan can ana sharholiya da 'yan mala. Amma kuma sai na kasa kawar da kaina daga kansu, ina cikin kallansu naga duk ragowar ukun sun tafi, sun barshi tsaye da wata, can naga ta bude jaka ta miko mashi yar karamar takarda, duk da ba a kusa nike ba, amma na fahimci katin adreshine ta bashi. Ina kallo dai naga yana waige-waige, da alama wani yake nema, can sai naga ya kira daya daga cikin yaransa, sai naga ya bude weta yar jaka ya mika wa wannan budurwa farin abu, hakan ya tabba.ar mani shima nasa katin ya bata. Wai anan take sai naji wani mugun bakin ciki ya taso mani a zuciyata, shin wai me Mustapha ke nufi da baiwa budurwa katinsa?," nan take haushin kaina ya dirar mani a zuciyata, na me Уг ва г02. me yasa ua zuwan ya kamani dole ban taho da motata ba. Ma yaudart ya sanıi ya sameni, shine har ya fara hirar wata, na mike na fice daga dakin taron hotcl din, na fita na samu tsakiyar wasu bishiyoyi fulawa na zauna, na mayar da kaina na kife a cinvavina. wai sai naji kamar zanyi kuka, na dago kaina nayi kwata. Bae Ja 1sokyarda kaina na kifa a cinyata. Hamida! Hamida!! Naji yana kira, ko ban daga kaina ba nasan Mustapha ne, ke kirana, inaji yana tambayar mutane tare da cewa daya daga cikin yaransa va je ya tambaya masu gadi ko sun ga na Bike Ina jinsa ya dawo yace masa masu gadi sunce ba wanda va fita, ina ji yace duk su shiga cikin hotel din su nemoni, shi kuma zai duba a harabar hotel din. 35 n a a Γ Kanshin turaransa da nike kauna sosai shi naji a hancina,hakan yasa na daga kaina yana tsugune a gabana, "kin tayar mani da hankali sosai, why," "saboda bana sonka bana son abinda kayi mani,"ya taso ya zauna kusa dani, "nace zanyi maki

Chapter 3 of 8