kallan saman dakinsa, jin motsi na na fito ma,
bai sa ya dago kanshi ba, har sai da na zo, na tsuguna gabanshi.
"Gani" na fada a sanyaye, wannan maganar da nayi ita tasa ya
juyo ya kalleni a sace, a tunanina, yana zaton har yanzu ba kaya a
jikina, bai ce mani komai ba, sai dai shima gani nayi ya tashi zaune,
ya rarrafo da gwagoyinsa, har gabana.
Kanshi a sunkuyé ya fara magana, "ni nasan kaddara, ba zan
zama jihili ba a bisa, abinda Allah ya tsara mani, Hamida ni nasan
Allah ne ya kaddara mani auran Halimatu, saboda haka ba zanyi ja
da ikon Allah ba zan auri Halimatu Hamida,
Kuka na sa da karfina, ni kaina nasan murna ce, saboda sai na
kama fadar, "nagodewa Allah ni ma yau na cika alkawarin dake
kaina na gode Mustapha, na gode, Allah ya baka tukuicin alajanna
13 firdausi 12
"Ya isa! Ya isa!! Dan Allah Hamida ki jira ingama maganata tukuna, ya dago ya kalleni, "nasan nayi iya kokarina, akan in guje
auran da kike sani inyi, amma gashi yau ya zamanto kin samu
nasara a kaina ta hanyar da ban taba zatan zaki samu ba.
Nayi bakin ciki kwarai da gaske, akan cewa bake zaki zamo
matata ba, nasan kuma zan kasance cikinsa har abadan duniya,
kenan har aranar da rayuwata zata zamo "the end" Hamida nasan
ina sonki, so na tsakani da Allah, amma gashi yau dubarata ta kare
ba yarda zanyi in zamo miji agareki.
Yayi shiru, amma ki sani, ba zan taba son kawarki ba har
abada, sanna abu na biyu, in munyi aure da kawarki kada ki kuskura
ki zo gidana da ziyaça, sai dai in mutuwa nayi, in ba haka ba, duk
ranar da kika shigo gidana, koda bana kasar, to da na dawo zan saki kawarki, wallahi saki uku.
Wanda hakan zaiyi sanadiyyar mutuwar naki auran da tsiya,
saboda haka, tun yanzu ki san dubarar yi ke da kawarki, ya dan
sassauta mirya, Hamida ina neman alfarma a wajenki dan Allah."
Nasan nayi rashin ki, amma don Allah alfarma da za kiyi mani,
ki amince mani inyi sallamar ka:she da ke," "kamar yaya? Nafada
da dan saurina, "kamar ki saki jiki dani muyi sallamar karshe dake"
"ban gane ba har yanzu," "manufata ki amince mani in matso kusa
da ke, jikina ya dan hadu da naki haduwar karshe," duk da nasan
bakya sona, amma ni zaki taimakawa don Allah."
"Wai yaushe kaji nace bani sonka, ni bana son kazafi, na dan
yunkura zan tashi, sai naji yayi saurin roko hannuna, tare da
mikewa tsaye shima, "maganata ta bata maki rai ne? kiyi hakuri ba
da niyyar haka na fada maki ba."
Duk da fiskata bata kallasa, amma jikina naji yana tausaya
masa, ko dan yanayin da naji yana magana, tamkar wanda akayiwa
mutuwa sabuwa.
Hakan yasa hawayen idanuwana suka dinga fitowa da sauri da
sauri, dab da jikina ya matso, "ranki baya so ko?" ya fada mani dai
dai wuyana, nayi alamar zanyi gaba, sai naji ya karasa janyoni
jikinsa ta bayana.
In da yasa hanunsa daya ya runguma cikina, dayan hannun
kuwa yana ga wuyana ya hada da kirjinsa, wuyansa na sama
13
kafadata, hawayen fiskarsa, na tsiyaya cikin wuyana ni kuwa dama
tuni na riga na saki kuka mai tashin sauti, nasa hannuna na rike silin
hannunsa.
Bayan kamar minti goma ne na, kira sunansa, ko ban fada ba,
na san mirya ta a sanyaye ta ce Mustapha, na danyi shiru kadan, zan
tafi," maimakon inji ya sakeni, sai naji ya kara matseni jikinshi.
Ni kaina ban san lokacin da na tura hannuna a gashin kansh
ba, mai taushin gaske abinka da gashi ba irin namu ba, jinsa nayi
yayi ajiyar zuciya, tare da juyowa muka fiskanci juna, yasa
hannuwaya tallabi kumatuna, tare da hada gashina da nasa,
"Hamida imiss you for ever," "zan tafi.
Ina ganin tallabar da yayiwa kumatuna zuwa inda fiskata ta
dagi sama nasa so yake ya hada bakina da nasa, haka yasa na
girgiza kaina alamar a'a "please," yace mani, sai ma na same jikina
nayi gaba, tare da daukar hijabina da take gefe daya.
Har na kai kofar fita ta bAbban falo, sai naji yayi magana, "ki
jira in rakaki mota mana," na tsaya har ya iso, ya karbi jakata da
take hannuna.
Ba wanda yayiwa wani magana a cikınmu, har muka je kofar
fita daga gidan, bayan mun sako daga yar motar lifta mai kama da
motar wasan yara, ta gidan wasan yara, (children's park) ba tare da
yace in tsaya ba, naji yana yi mani magana.
"Ya zakayi akai kaya gidan su Halimatu?, kinsa ban san
gidansu ba," "kawo jakar in baka katin da zai kaika har gidansu, ni
kuma yanzun in na tafi, zan biya ta gidansu in fada, cewa zasu je,
da yamma ko banda yamma bane ba?".
"da yammar ma yayi Hamida tunda kince haka," ina bude jaka
sai naga dunkulin kudin engila" Pound stiling" na dago kai na da
şauri na kalleshi, "bana son wata magana, ni ne na baki, nima
gudunmawa tace, Allah ya baku zaman lafiya."
"Yallabai." ya daga mani hannu, "in bakya so, ki yar ni ki bani
katin kawai nace," na duba na dauko masa katin, "na gode," "ba komai, kigodewa Allah ba ni ba, bawansa, ya zaro hankici daga aljihunsa, "ki gyara fiskarki," na karba, tare da goge fiskata sosai.
14
Har get din gidan shi na biyu ya rakanı a motata sannan ya fita
ta taga ya dan leko, I miss you, kawai ya fada ya ja baya, ban bashi
amsa ba, na ja motata nayi gaba.
Kayan kwalliyar cikin jakata su nayi fakin da motata gefen titi,
na gyara fiskata su, sannan na tashi motata tare da kara kallan kaina
ta madubin gaban direba naga fiskata fas, kamar bata sha kuka ba.
Kai tsaye gida na nufa, ba tare da bata lokaci ba, na cewa
mamana tayi wa momi waya cewa saurayin Halimatu yace yau da
yamma zai turo bakin iyayensa domin gabatar da kansu, nayi mata
bayanin cewa yanzu ya je gidan biki yake gaya mani haka, ba
dubarar da banyi masa ba, amma ya ki saurarata, shine nace bari in
rugo gida in fada.
Amma yanzun zan je in sanarwa halimatun, sannan in koma
gidan bikin, da murna mamana tace sai na dawo kafin in fita, sai da
na bugawa safiyanu waya muka gaisa, a' nan ne nake ce masa, in
yana da hali, ya sameni gidan su Halimatu wajan karfe uku na
yamma saboda wata mahimmiyar magana da nike son nayi da shi,
"dama mai neman kira, to ina ga ance sarki yana kiranka," da
murnarsa yace, zai zo in saurareshi a lokacin, ina isa gidansu
Halimatu, abin mamakin, sai na sameta da yaya Usman sunata hira
harda tuntsirar dariya.
Wani haushi ya kamani a take, da kyar ma na gaishe da yayan
nace mata ta zo ina jiranta, sai ta koma in mun gama da kyar ta taso,
wai ita kada abar yaya shi kadai.
Bayan mun shiga dakinta ne, nake yi mata albishir da yau za'a
kawo kayanta daga gidansu Mustapha har da murnata kamar zan
tashi sama, amma wai sai naga tayi shiru, na dan dafata, Halimatu
ya bakiyi murna ba abinda kike nema ya samu nan da sati biyu kina
dakin Mustapha.
"Hamida ni ba abinda zan iya cewa, face in ce Allah yayi maki
sakaiyya da abinda yafi wanda kika yi mani, na gode, na gode,
Allah ya saka maki da aljanna firdausi, na aikawarin da kikayi
kokari kika cika mani, gashi kuma kin rike mani amanata na gode.
Amma kuma, sai wani hanzari, Hamida, hanzarina kuwa shinc,
tunda Yaya Usman ya dawo daga karatu, naji kuma zuciyata ta tashi
15
daga kan Mustapha, ta koma kan Usman, Hamida ba zakiyi mani
afarma ki auri Mustapha ba?"
Wani wawan duka na sakar mata a cinya, har wata irin kara ta
saki mai karfin gaske, "in ma wasa kike to ki dawo sai ti, in ba haka
ba, zamuyi tashin hankalin da bamu taba yinsa da ke ba, kuma ki
sani, aure ke da Mustapha ba fashi, tunda ke kika riga kika firta kin
a sonshi da farko.
Ke da kinga irin walakanci da zubar da mutuncina da nayi da
cin fiskar da akayi mani duk akanki, har ki fara fadar wannan
maganar marar kyau haka," na kara harararta, "wallahi kin bani
mamaki Halimatu, ban taba tunanin zaki wulakantani ba, ki ci
fiskata ba kamar haka,"
"Me nayi maki kuma Hamida, wallahi ni da zuciya daya na
fadi wannan maganar, kinga ke dama ba wani tsayayyan saurayi
gareki ba, kinga sai kawai muce dama ke kikewa kanki kamfai ba
wata ba, ke kunya kike ji ki fadi gaskiya a baya shi yasa
kik.
"Kinga! Kinga!! Bana son maganar yara, ni fa ba yarinya bace,
shima kuma Mustapha haka, sannan ke baki isa ki sa ni yin abinda
zai zubaar mani da mutuncina ba, kin dai sani da farko, kuma nayi
maki, amma ina tabbatar maki yanzun baki isa ba.
In gaya maki magana ta karshe, shine yanzun haka maganar
nan taje kunnan Abbanki da momi, saboda haka nasan shirin karbar
baki kawai zasuyi, in kuma kika kuskura kikayi musu ko wani ja
akan abun nan, to zan kuwa tona maki asiri saboda haka, shawara
ua ga ke, bani ba.
Ni yanzu haka inada wanda zan aura, wanda ni ma tare da ke
za'ayi komai, tare kuma za'a kaimu dakunan mazajenmu, kinga
ritata ni, bacin munyi da bakona zaizo nan gidan, da gidama zan
afi, amma yanzun zan je mu zauna da momi, ko nasamu wasu yan
shawarwari game da auran da zamuyi.
Ke kuma ta rage ga naki, ki koma wajan wanda ya hure maki
kunne, marar hankali da ke kawai, daga mutum ya dawo daga turai,
ba binkice ba komai sai kice shi zaki aura, wa ya sani ko ya dawo
mana da kanjamau ko wani.
16
"Kinga Hamida ya isa haka nan, ya ishcki hakanan ki fita tun
kafin raina ya kara bасі. "ya baci mana ina ruwana,
ni kinsan iya bacin ran da na samu kafin in samo maki Mustapha,
ranki ya fado don Allah in har kin isa ke sunanki Halimatus
sa'adiya, sai in san kina 6acin rai.
Ni yanzun har da wani abinda zai firgatani kuma, wanda ban
gani ba, lokacin yi maki kamfai, har yau din nan sai da naga abinda
yafi komai tayar da hankali, wallahi Halimatu baki da mutunci ko
kadan," nayi tsoki nayi gabana kyaleta a daki zaune. Bayan mun gama gaisawa da momi ne na gaya mata yau suna da baki, nayi mata bayanin Mustapha dalla dalla, nan take momi ta mike, ta barni, sai dakin Abba ina zaune ko yunkurawar tashi banyi ba, mamana tayi sallama da daddy suka shigo
Baki daya sashen Abba, suka shige, cikin kamar mintina
arba'in da bakwai sai gasu sun fito gaba daya kafin karfe biyu na
rana kuwa, gidansu Halimatu ya fara cika da jama'ar arziki.
Karfe uku saura kwata safiyanu ya baiyana, bakinshi kuwa
kamar anyi mashi albishir din zuwa makka aikin hajin ba zata,
kamar yanda Halimatu da yaya Usman suka tashin tsiya daga
kujerun zancensu, ni kuma haka muka dauki kujerun zuwa bayan gidansu Halimatu.
A inda nike sanar dashi in ba takura ina son ya aiko da kayan
auransa shima, zuwa gobe, saboda gida an takurani wai da Halimatu
za'a hadamu ayi mana aure.
Nan take ya hau murna, harda cewa in bashi izini ya aiko da su
a yau shima da yamma, na nuna masa ya dai hakura sai gobe saboda
gidanmu a yau ba kowa duk ana nan karbar kayan Halimatu.
Yanda naje na samu Halimatu a kwance tana kukan dani nasan
na rabuwa da Usman ne, nima haka na shiga imotata sai gida na
haye nawa gadon na fara nawa kukan rabuwa da Mustapha, da
auran da bansan sunan saba da zanyi.
Ni dai nasan bani son sufiyanu, amma zuciyata ce ta amince
mani da auranshi, wanda har karfe biya da minti goma tayi, sannan
na daure na mike domin in gabatar da salah la'asar din da na kasa
tashi inyi tunda na shigo.
17
*** ***
Saura kwana biyu daurin aurammu, ni da Halimatu, wanda
kullun sai munyi rigima da Halimatu akan auran da zatayi, korafin
kuwa da ta faye yi mani shine na har yau bataga Mustapha ba, wani
nata bai san Mustapha ba, ga fittitika anan ta zuwa, amma ba
Mustapha a ciki.
Wanda tun korafinta baya damuna, har ya zamo yau kam ya
dameni, wanda hakan yasa na duba naga ta fini gaskiya, a baya tana
ce mani ya aiko mata da sakon gaisuwa a takardu, da yan kayan
amfani a ledoji, wai a gaya mata yayi tafiya zuwa indi'a domin gaya
masu bakinsa ya taso.
Amma gashi har yau saura kwana biyu, ba Mustapha, aiken ma
ya daure kafar yisa, ni dama tun farko da ta fada mani, nasan ba
wata tafiyar da yayi, koma yayi ta ba zata wuce kwana biyu ba,
amma ragowar kwanakin yana garin nan.
Bayan mun gama yin fada kace-kace da Halimatu, har da yan
zage zagenmu, da saurinta ta fice ta bar gidan. mu, ni kuwa sai na
dauki kanwaya na danna nabar gidan Mustapha.
Sai da tayi kara ya kai sau biyar, tukuna aka dauka, wanda a
farko nayi masa ne ta talho dinsa ta hannu, amma ba,a dauka ba,
hakan yasa na juya zuwa ta cikin gidansa in ji ko yana kusa.
"Waye ke magana, nan gidan Alhaji Mustapha Mahab ne,"
abinda wanda ya dauka ya fada kenan, "sanu ko," nace masa ya
amsa da yauwa," "dan Allah Alhaji Mustapha nake son magana da
'shi," "Hajiya don Allah kiyi hakuri Yallabai ne yace kowa ya ke
son magana da shi ace masa yayi hakuri sai bayan sati biyu.
Amma don Allah kiyi hakuri ki bugo nan da kwana biyu, a
lokacin sati biyun ta cika kenan, ina fatan ba zaki samu damuwa
ba," "kai waye ke magana?" "Hajiya sunanan Abdulrashid", "au
Abdul rashid ne, kace masa nice Hamida ke magana dashi."
"Nan take ya canja murya zuwa ga ladabi, "sannu sannu
madam rike yanzu zanyi mashi magana, Allah yasa ya saurareni,
saboda yau kwananshi goma sha biyu a daki kwance, ya hana a
ganshi, sai dai lokacin abinci ka wai yake bude kofarshi.
Ina zuwa bari in gwada in gani," "bayan kamar minti hudu sai gashi ya dawo, "hello! Hello!! Madam kina kan layi?" "ina jinka
18
Abdulrashid," "wallahi madam yace nace koma waye ace ya bugo
nan da kwana hudu," "ka gaya masa nice?," "e na gaya mashi, sai
yace wai in wani abu kuke bukata ki fada in kawo maku yanzu."
"Ka koma kace masa nace, magana ce kawai zanyi dashi,
bama bukatar komai daga gareshi," "haka shima bayan yan mintina
sai gashi ya dawo, "hallo madam," "yace ba zai iya sauraren ki ba,
amma wai in maganar ta zama dole, ki baiwa kawarki Halimatu
nambar wayar ta bugo masa, sai ki fadi mata maganar ta gaya
mashi, bayan haka bai kara komai ba."
Kaje ka ce mashi........" "don Allah madam kiyi hakuri
wallahi yace in na kara zuwa kofar dakinsa bakin aikina, ni inaga
wani abu ke damunsa, da zaki iya zuwa da kanki da yafi, mu kanmu
abun yana damunku gashi yace kada a gayawa hajiya," "hi kenan na
gode Abdulrashid, sai anjima."
Wani bakin ciki ne ya taru a kahon zuciyata ya takareni, wai ni
Mustapha zai wulakanta, kamar bani na hadashi da Halimatu ba,
hannuwa biyu nasa na rabka tagumin bakin ciki, nayi kwafa nayi
tsoki sunkai talatin a cikin mintuna ashirin da daya.
Hakan naga ba zata taba sani in hrice ba, sai naga Mustapha
ido da ido a yau ina haka ba, abu uku zan hadawa kaina a lokaci
daya ga bakin cikin maganganun da Halimatu ta ke gaya mani, ga
bakin ciki na Mustapha, ga auran da bazan iya cewa ga sunan sa ba,
zanyiwa kaina shi.
Na mike na yayimi hijabinta, da dan nakullin motata sai waje,
mutanan da suka cika gidanmu yan biki sai magana suke yi mani da
masu tsokanata, amma washe musu baki kawai nayi na wuce abina.
Ba wani canji da ua gani a wajan yaran mustapha yanda suke
mani a baya, yauma haka, hakana wucesu suma ina yake masu
hakora.
Sai da na kwankwasa takai goma, amma ko motsi banji anyi
ba a falon Mustapha, bakin cikin haka yasa nayi ma kofar wani
wawan duka, wanda na jirashi ya kai biyar ba tsayawa.
Allah yasa fiskata gefe take kallo da nasha mari, saboda
hannun Mustapha kawai na gani a baje bakin kofa, har ya dan taba
wuyana "me ye haka kai kuma" "me kika zo yi ke kuma?," sai naga
yana neman mayar da kofa ya rufe.
19
Nayi saurin sa hannuna a jikin inda za'a rufe kofar, amma sai
Mustapha ya datsa kofar da hannuna a jiki, duk da kofar katako ce,
amma bai hanani jin wani mugun zafi da radadi ba,
Karar da na saka mai karfi ita tasa yayi saurin bude kofar,
shima ya kara mirtsike mani yan yatsuna, cikin saurin da bai kai
sakan ba na durkushe kasa nasa ihu ina waiyo Allah, tare da dura
hannuna a kaina.
Da rudewarsa ya iso ya kamani, "sannu innalillahi, mugani na
fizge hannuna, "ni ka sakar mani hannu, bayan kana sane kayi mani
haka sai na samu na mike ina yarfe hannuwana, ji nake tamkar in
ciresu in zubar in huta, na nufi kofar komawa daga inda na fito.
Amma Mustapha ya biyoni a baya, "Hamida Hamida, kada
kiyi mani haka tsaya dan Allah in ga hannunki ko hankalina ya
kwanta" "ba wani mayudari, dama nasan a baya yaudarata kaso
kayi Allah ne ya bani sa'ar gane ka, gashi yanzu tun ba'ayi nisa ba,
na gane manufarka.
Gabana ya tarayye, "dan Allah ki tsaya inyi maki bayanin"
bana son wani bayaninka, ni dama ba wani abu ya kawoni ba,
matarkace take ta kukan baka zuwa wajanta, kuma ba wanda ya
taba ganinka a danginta, in kaga dama kaje in baka je ba kuma dan
kanka, nayi gaba abina.
Har na tashi motata yana tayi mani magiya ko kara kallan inda
yake banyi ba, naja motata.
Ina isa gida na samu sufiyanu zaune abisa akujera da wasu
kawayenmu suna ta hira abisu, yana hangoni gaba dayan hankalinsa
ya dawo kaina, amma na rasa yarda zanyi inyi masa fara'a a fiskata
ganin haka da sufiyanu yayi yasa ya taso da sauri ya taryeni.
"Me! Me! Me yafaru ne na ganki haka?" da kyar na danyi
murmushi na nuna mashi hannuna na hagu, wanda yanyatsun sun
kumbura sosai, "yayi saurin rike mani hannu, hankalinsa a tashe,'
ya akayi haka ta faru? Me ya sameki ne haka?".
Zame hannuna nayi tare da guntun murmushina," motace ta
datse mani 'yan yatsu, a gidansu Halimatu," "muje in kaiki asibiti
kilan ma kin samu karaya ayatsun, "ka barshi, ba komai zai warke,
amma yanzun dama gidan kamu zanje su duba mani ko na samu targade amma bana zaton karaya."
20
3
1
"Sannu yacce dani," na danyi mashi kallon naji dadin tausayin
da yanuna a gabana, "kaji safiyanu kamar wacce ta datse yanyatsun
gaba daya," "ke wannan fa bAbban ciwo ne, gani kike kamar wasa
sai naga ya waiwaiga, sannan ya kara matsowa dab dani har da rage
sautin tashin maganarsa.
"Ba ciwon wasa bane ba fa, zai iya hanaki cın amarcinki fa ya
janyo mani hutun dole," na harareshi nayi yar tafiya ina murmushi
kunya, "kai wallahi. Ya biyoni, "karya nayi? "ni ba
ruwana, "tare da kara hararrarshi, "zan biyaki hararra nan taki bayu
ba sai nan da kwana uku,"
nayi saurin cigaba zuwa shigewa gida, ina mai alamun jin
kunyarsa, "Hamida Hamida tsaya zan biyoki har cikin gidan kinsan
dai nima gidan mu ne" "is left for you" "bata rage garenmi ba
amma zai ragegareki nan gaba kadan ban tsaya bashi amsa ba, na
shigo cikin gida da saurina ga kunya duk da rufeni, saboda mutane da ke kallamu.
Na danji dadin yanda sufiyanu yayi mani wanda haka ya dan
lafar mani da zuciyata, hakan yasa nima nayi wanka na na sake
kayan jikina, domin kawai ya gani yaji dadi a zuciyarsa.
Tabbas nayi kwaliya mai kyan gaske da boyel mai ruwan kalar
kayan sojoji faudata na shafe fiskata da jita, wanda kwallin da nasa,
shi ya boye jan da idona yayi na kuka, jan-jambaki mai turin bakibaki, shi na shafa a la66ana.
Na kawo man gashi na shafe gashina da yasha kunan shampoo
na taję shi na rabashi biyu na tibke, sarkace ta dayimon din ingila
na sa a wiyana"diamond" na kawo zobinanta biyu nasa a hannina,
banda kunnena da nasa dan kunnata.
Gajerun takalmane a kafata, mai ruwan hoda shima mayafin
dana yafa kalar takalimin kafatane, daurin dankwalin da anyi kuwa
yadan langwaba kadan, yafa mayafin kanshi sai da nayi shi yar da
zai birge duk wani wanda yake kallona, ba ma sufiyanu kawai ba,
wanda akayi kwalliyar dominsa.
A karkace ake yafashi, baiyana yafa mayafinnan, sai wanda ya
gani da idonshi ni Hamida, tararan fancy, na fesa a jikina irin
turaranda sai an matso kusa dani, za'aji kanshinsa.
21
Tun daga hangoni sufiyanu ya mike tsaye, daga kujerar da
yake zaune, ba abinda idansa keyi, sai kallona, wanda naso yanga
da 'yan yatsun hanuna, amma ciwon jikinsu shi va hanani sakin
hannuna na haggu ya wataya kamar yarda na so.
Kallan da sufiyanu ke yi mani shi yasa kawayena da ke zaune
suna dabe mashi kewa suka waiga gaba dayansu, kamar sun hada
baki sukayi shewar nan ta yan makaranta, tare da cewa kin fito
kinyi kyau, ki iso ango ya biya ki kudin kwalliyar ki."
Murmushi kawai nake masu, ina isowa sufiyanu ya kauce daga
inda yake tsaye, "sai naji yace, "sanu ga kujera," manufarsa kujerar
da yake zaune zan zauna, nayi mashi kallon da zai sa ya kara sona a
zuciyarshi, nace masa, "in baka zauna ba zan zauna a kasa."
יי" To tsaya! Tsaya!! Ina zuwa in dauko maki wata kujerar,
"meye aikina ni kuma?," "ki zauna in ta kallanki" gaba daya muka
sa dariya har da su, Zulahatu, itace taje ta dauko mani kujerar zama,
tace ango na hutar da kai," "na gode hajiya Zulahatu, kin biya
kema.' Na zauna muka cigaba da hira kafin karfe hudu na yamma,
mu fara shirin tafiya.
A
Mun samu kamar mintuna arba'in da biyu da zama hirarmu,
sai mai gadi ya zo yace ana sallama da ni, a wajan get, na
tambayeshi ko waye, sai yace wannan mai zuwa dan baturan nan,
Yana fadar haka, na gane Mustapha ne, take anan na tambayi
kaina me Mustapha yazo yi kuma? Hakan yasa na mayar da kallona
ga yan yatsun hannuna da na shafesu da Lanis bon ya karasa gutsire
mani su ke nan?, na fada a zuciyata, sannan na kalli angona.
"Angon Halimatu ne zanje don Allah in ji ko lafiya, ya dan
daure fiska, "kada ki dade ina jira" "yanzu zan dawo Zulahatu ga
ajiyar angona nan a hannun ki" na mike na hau taki daya bayan
daya na nufi get.
Ina fita get na faure fiskata har da kashe ido daya dan tsananin
inyi masa kallan wulakanci, ba sallama ba komai na hau magana,
"me ya kawoka gidanmu, ko ka zonan ma ka karasa gutsure mani
ya yatsina, wallahi baka isa ba, ko ka tafi ko insa yaran unguwa su
jefe mani kai." Ya dago kansa da ke sunkuye a jikin sitiyarin
motarsa, "kiyi hakuri dan Allah, dama zuwa nayi ki rakani wajan
22
C
Halimatu saboda zuciyarki tayi maki sanyi, na san yanzu kin dauki
fishi dani
"Sai na rakaka gidansu Halımatu, to kada Allah yasa kaje, ni
dai tunda angona na kusa dani, alhamdulillahi ku kuwa kujecan ku
karata ni baruwana kaga tafiyata wajan angona, saboda minti biyu
ya
"Don Allah ki saurareni ba wani abu yasa na biyo ta nan ba,
saboda kece kika hadamu da ita, kamata yayi kuwa ranar haduwar
mu ido da ido da ita, ace shima ke kika gabatar dani a wajanta, kiyi
mani arzikin haka, in kikayi hakuri saura kwana bai fi hudu ba in
bar maku kasar gaba daya."
"Sai dai kaje ka tambayi angona inya amince, saboda bana son
bata masa rai," "sai ni ki ke son batawa rai ko Hamida?", ban tsaya
bashi amsar komai ba nayi gaba abina.
Ko zama banyi ba, na hango Mustapha ya shigo get din gidan
mu, ban nuna na ganshi ba na zauna kujerata, har da canja salo
zama, da canja kallo da nikewa sufiyanu, ammata wutsiyar idona
ina kallon Mustapha, tare da tunanin Allah yasa a gama lafiya.
Da fara'ar sa suka gaisa da sufiyanu, shima haka angon
sufiyanu, sannan na dago kai nace "Alhaji, wannan shine Alhaji
Mustapha muhab angon Halimatu, Yallaßai wannan shine sufiyanu
angona," ta wutsiyar ido Mustapha ya harareni wanda nasan ba
wanda zai gane hararta yayi, sai ni.
"Dama cewa tayi kuna tare shine na shigo mu gaisa, tare da
tambayar ka bani aronta zamuje mu hadu da Halimatu domin yin
wasu shirye shiryen da dole sai mmu uku zamu yi su, saboda lokutan
baya nayi tafiya shi yasa, jiya na dawo".
"Ba damuwa gatanan ku tafi," "a'a ka tashi mu tafi tare da kai,
kaima ai anyi wasu shirye shiryen da kai ko? Na cewa sufiyanu,
Mustapha ya kara sakar mani wata hararar karkashin ido, nima
take na rama.
a
"Ke dai ki tafi, ina nan ina jiranki, kada ki zauna kinsan dai
yanzu ina bukatar ki kusa dani, "you know "to shikenan, amma da
mun tafi tare, kasan nima banajin dadin barinka kai kadai."
"Gasu Zulahatu da yasira da sauransu, ai kwa tayani zama ko?
Suka amsa da E" "shikenan amma Zulahatu ga amanar agona nan,
23
kada ki yarda wani abu ya 6ata masa rai, in lokacin salla a zahar ya
karasa ki shiga gida ki dauko maku bAbbar dadduma, yanzu zan
dawo
kada ki bar maini shi da yunwa," "kai wannan dokoki naki
Hamida sunyi yawa, ko dai ki saka angon naki aga ba ku tafi tare,
aka danyi dariya sannan na mike tsaye.
Nasan Mustapha na kallona, shi yasa na canja kallo da
magana, har da durkusawa gaban sufiyanu, "sai na dawo kayi mani
addu'a sai in tafi, ya danyi sumi-sumi da baki, sai ya to fa mani a
goshi, ya sunkuyo kadan, "a dawo lafiya," nayi murmushi, "Allah
yasa," "kar ki zauna da yunwa fa," na daga masa kai alamar to.
Mustapha kuwa sai kallonmu kawai yakeyi