Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
shiga tayi kai tsaye ajinsu tanufa yayinda suke ta shara seda suka kammala sharar malami yashigo wanda suke kira da sir mansir wanda yake daukansu physics mikewa sukai suka gaisheshi yayinda ya umarcesu dasu zauna tambaya yayi akan last topic din dasuka gama bawanda yabasa amsa ganin haka zuhura ta daga hannu pointing dinta yayi yana cewa munajinki bayani tashiga yimai dala dala bashi kadai ba harta yan ajin ta burgesu tunkafin takarasa aka faramata tafi dakatar dasu yayi inda yakalleta yace what's is you name zuhura haruna adamu dakyau zuhura idan anfuta break kisameni staff room to tace yace tazauna yafara lesson dinshi Inna ce takaiwa baba karin kumallo koko ne se dan tuwon data tuka ta kadamai miyar kuka kawomai tayi ci yafarayi bayan yakammala ya futa ya wanke hannunshi yadawo bara natafi kar oganmu yazo banjeba kinsanshi da bala i to seka dawo adawo lpy ameen ya amsa yanafuta bayan yafuta ne tashiga gyare gyaren gidan Iya lami me aikin mamy ce taketa shirya breakfast a dining mamy ce tafuto sanye da doguwar riga tasha duwatsu se kyalli take karasowa dining din tayi inda iya lami ta gaisheta mamy ce tace su muhsin suntafi school eh hajiya suntafi ok jawad fa be futoba ok to ki tasoshi tom hajiya wucewa tayi dakin jawad kwankwasawa tayi waye yafada a hasale iya lami ce to meyafaru hajiya ce take kiranka ok yafada time din yafuto daga wanka sauri sauri yayi ya shirya dan yasan mamy na jiranshi suyi breakfast iya lami ce ta dawo tanafadin hajiya gashinan ok to mamy tafada iya lami wucewa tayi kitchen jawad ne yafuto yana danna wayarsa kujera yaja yazauna yana fadin good morning mamy amsawa tayi tare da cewa school fa se 1:00pm zantafi ok kayi breakfast Bayan an futo break ne tace wa da kawarta sumayya tazo ta rakata staff room sumayya ce tace nidai bazanjeba kije kidawo bara naje na siyo awara to tace mata tanufi hanyar staff room bayan ta shigane ta hango shi a kujerarshi dayake zama gurin tanufa durkusawa tayi tace sir gani yawwa zuhura kinzo kaita gyadamai ok janyo durowar dake jikin table dinshi yayi yadauko littafai dozin daya da biro da pensil da maset ya ajiye asaman table dinshi hannunsa yasa a aljihunsa yaciro yan dari biyar biyar guda hudu dauko littafan da maset din da biron da pensil da kudin yamika mata dagowa tayi tana kallonshi shima kallonta yakeyi ganin yana kallonta yasa tayi kasa da kanta ki karba mana kai ta gyadamai alamar bazata karba ba kikarba nace ah ah sir kabarshi ke namiki kyauta kice nabarshi kokarinki ne yasa nabaki da buki bani amsaba bazan bakiba dan haka ki karba karba tayi tana yimai godiya zuhura yafada yana kallonta kamar zeyi magana se kuma yayi shiru ok tashi kije kici gaba da kokari kinji tom tafada tana dadaimai godiya tafuta tanafutane kai tsaye gurin da suke zama ita da kawarta sumayya in an futo break tanufa tarar da ita tayi a zaune zama tayi itama kusa da ita tana mikamata kayan daya bata sumayya ce ta karba tana kallon zuhura shiya baki wanan kayan eh shiyabani da ni nama ki karba seda yamatsamun sannan nakarba jinjina kai sumayya tayi tace anya kuwa zuhura ba sonki yakeba haba dai so kuma ai yace saboda nabashi amsa shiyasa yabani to ai shikenan aji suka koma sanadiyyar an kada kararrawa ta komawa break se 1:15pm aka tashesu kai tsaye gida tanufa tana shiga tafara kwalawa inna kira inna inna nadawo daga cikin dakin inna tace to sannu da dawowa inna mekikeyine tafada tana shiga dakin gari nake lalube kinganninan nagama miya banga gariba to inna kuma yunwa nakeji sarkin ci saboda ke naketa hanzari nagama inna kumafa ban karyaba to sarkin mita jeki cire unigorm din harta tafi ta dawo tana fadin inna anbani kyauta a makaranta to me aka baki hannunta ta zura cikin Jakarta ta fito da kayan da sir mansir yabata tana nunawa inna karba inna tayi tana fadin wane yabaki wannan kaya haka kuma me kikaimai inna tambaya yayi nabasa amsa shine yabani to ungo boye in babanki yadawo kinunamasa to tace tafuce tana fadin inna ina amira da auta sun fice wasa bama su dade da fucewaba Wacece zuhura Malam adamu abdulahi mahaifin malam haruna wato kakan zuhura yanada mata biyu matarshi tafarko habiba tanada yaya biyar sama'ila se hafasatu se hauwau se idiris se mika'il se matarshi ta biyu suwaiba kakar zuhura danta daya malam haruna mahaifin zuhura yana shekara 5 mahaifinshi ya rasu dan haka ya girma a dangin mahaifiyarshi sanadiyar shine yasa taki aure saboda batasan rabuwa dashi mahaifin malam haruna yabarmusu gonaki har kusan biyar amma sanadiyar Shiba a gidan yakeba yasa kanin mahaifinshi yadage seya karbi kudin ze juyamai ahaka aka bashi tunda aka bashi ko labarin kudin yadenayi sukuma kamar anrufe musu baki seda yakai shekara 11 mahaifiyarshi ta rasu nan aka rinka rigima waye ze rikeshi gashi kakaninsa sun rasu ahaka yayan mahaifiyarshi yadaukeshi ya rikeshi yake tayashi aikin gona da haka har yakai shekara 25 malam haruna yarone me kwazo bashida kiwa sanadiyar haka yayan mahaifiyarshi yadauki son duniya yadorawa yaron da haka har matarshi take jin haushi ta tsaneshi yasha wuya a hannunta, nan ne yayan mahaifiyarshi yace yasamomai matar aure yar gidan abokinshi malam garba wato innar zuhura babanta malamine yana koyar da almajirai nan yaje yaganota yaji ta kwantamai arai macace me kamala da mutunci kuma kyakyawa mahaifiyarta bafulatanace dan haka kana ganin habiba kasan jinsin fulanice anan aka daura musu aure seda tayi shekara kusan 5 bata haihuba har abun yafara basu tsoro inda wan mahaiyarshi yaketa ziryar karbo musu magani saboda acewarsa kan ya mutu yanaso yaga dan haruna, tunda matarshi taga yadda ya kwallafawa dan gidan haruna kota nata jikokin bayayi nan tashiga yawon bokaye nan wata kawarta ta rakata gurin wani boka aka tushewa habiba mahaifa habiba tashiga damuwa ko bacci batayi kullum kuka anan ne mahaifinta yasa aka rubutamata alkur'ani tasha cikin kuddurar ubangiji ko wata ba ai ba tasamu ciki murna ba a magana gurin yayan mahaiyafiyarshi bakin ciki kamar ya kashe matar wan mahaifiyarshi nan cikinta yakai wata 8 a watanne yayan mahaifiyar haruna marikinsa ya rasu yaji mutuwarnan baka danba yaso yaga ya haifarmai jika , habiba bata shiga wata na taraba tafara nakuda inda haruna ya gigice yatafi yakira matar wan mahifiyarshi yadauketa kamar uwa tunda agurinta ya karasa girma yayin da tazo habiba ta jigata sosai dakyar ta haihu ta haifi mace matar wan mahaifiyarshi gwago larai taso takashe abunda ta haifa dangin habiba suka zo anan yarinya taci suna fatima suke kiranta da zuhura yarinyace kyakyawa ga gashi ga hanci ba fara bace tanada farin jini kowa yaganta seya dauketa seda takai shekara 4 anan ne gwago larai da yayanta sukace alallai se malam haruna yabar gidan tunda wanda yakawosa ya rasu haka suka tattara kayansu suka bar gidan gashi basuda gurin zuwa hakan yasa habiba ta tafi gidansu kafun ya nemomusu muhalli nan yaje gurin abokinshi da suka tashi tare tunda shi yanada hali, yaji tausayinsa sosai hakan yasa yabashi gida yazauna ya sanar da yayanshi cewa yabawa abokinshi gida kar wanda yayi yunkurin karbar gidannan sedai bayan ranshi anan suka koma gidan suka cigaba da zama inda malam haruna yake fafutukar neman aiki dakyar yasamu awani gareji aka daukeshi aikin gadi shize dinga budewa kuma yana rufewa, zuhura takai shekara10 habiba tasamu cikin amira, a lokacinne mahaifiyyar habiba tarasu, amira takai shekara 5 ta haifi halifa, mahaifin habiba ya rasu bata da kowa daga ita se yayarta suka rage, halifa ayanxu yanada shekara 5 amira na shekara 10 zuhura kuma nada shekara 17, zuhura kyawunta yafuto sosai tanada dogon hanci fatarta chocolate colour ce tanada manyan idanu da dan karamin baki zuhura nada gashi dan idan tasakeshi yana kaiwa gadon bayanta bata da kiba kuma ba doguwabace can sedai tanada diri sosai inda inna ke mamakin yarinya karama tayi diri irin wanan maza dayawa sunsha biyota har gida amma bata sauraronsu saboda babanta yace yarinyace ita Mu koma ainahin labarin Yau suke graduation dinsu na kammala makaranta dan haka dawuri yafuta makaranta yana zuwa kayanshi yasa se alokacin yatuna da Ahmad wayarshi yadauka yana kiranshi dagawa yayi sorry abokina na makara ina hanya tokai sauri ka karaso ok wayar yakashe Ahmad be jimaba ya karaso anan ne akafara gudanar da bikin graduation din, seda aka kammala binkin, Ammar yagaji sosai garden din school din ya tafi dan ya huta wata budurwce take takowa gurinsa tanazuwa ruwan roba ta mikamai karba yayi batare daya dago yaga wayeba idanshi nakan wayarshi bude ruwan yayi yana kafawa abakinshi dama kishi yakeji seda yagama sha yace kazauna mana kodai dan sanda zakaine budurwarce tazauna tana facing dinshi kallonta yayi yace yadai bakomai sunana humaira ni yar nigeria ce inba damuwa zamu iya zama abokai, ah ah yafada yana mikewa baki tasaki tana kallonshi inda tace ko tayaya Ammar sena sameka, Ahmad yashiga nema dan su wuce gida ya dubashi ko ina be ganshiba dan haka kawai yanufu parking space hango motar ahmad din yayi da alama akunne take karasawa yayi daf da motar bakin tintek ne a glass din dan haka ya kwankwasa glass din motar zugewa akai Ahmad ne manne da wata yarinya yana kissing dinta ya kwantar da kujerar da take kai, ganin haka yasa Ammar juyawa yabar gurin motarsa yanufa yayimata key yabar makarantar gida yanufa yanazuwa yashiga wanka sedaya gama shiryawa tsaf, yunwa yakeji dan haka yashiga kitchen ya hada copee yazauna afalon yana kallo wayarshi ya dauka yayi dialing number mamynshi Zaune take afalo ta mike kafarta anamata tausa wayarta taji tayi kara dauka tayi tana fadin my son ykk lpy lau mamy gobefa nake Shirin dawowa Nigeria to gobe kuma bazaka kara hutawaba ah ah mamy nagaji da kasarnan to shikenan Allah yadawo dakai lpy ammeen yace mamy abba yadawone daga dubai din, be dawoba tukun ok to zankirashi yanzu bayan sungama wayarne ya kira abba, abba ina yini lpy lau Ammar ya karatu kun kammala ko yaushe zaka koma gida eh dama abba sonake gobema nakoma to gobe kuma eh abba to shikenan nasadai akarasa aikin hospital din naka me bi ko sun gama amma zantambayi mamynka to abba ngd Allah yakara arziki ameen ya amsa sukai sallama Ahmad ne yashigo yana fadin abokina ashe kadawo ko kallonshi Ammar beyiba yadai ko patreshia tazone yafada yana dariya au namanta ban gayamakaba tace ta gaji da wulakacinka ta hakura, yafimata sauki to dawasa nake sonake dama kayi magana kasan dai bazata taba rabuwa dakai ba sedai idan Nigeria kakoma to ai gobema zankoma ni, gobe kuma haba kabari se jibi mana, naga da kaine kake tacewa ka matsu ka koma Nigeria yanzu kuma kace se jibi abokina bazaka gane bane akwai yarinyar da mukai ciniki da ita ne kuma gobe 10 na dare zamu hadu wannan kuma kaita shafa nidai gobe zanbi jirgi natafi kai kazauna se jibin taya zanai nazauna ace kuma ina ina kaji dashi yamike yabar falon Babane yashigo yana sallama amsawa sukai su duka karasowa yayi yayinda zuhura ta daukomai tabarma zama yayi yana fadin samun ruwan wanka bazaka fara cin abincinba faradai samun ruwan saboda na gaji sosai yau ogonmu yasamu aiki da yawa mikewa tayi tahadamai ruwan wankar yayi, seda yagama shiryawa sannan ya futo zama yayi ya jawo kwanan abincin ci yafara y,i zuhura ce ta mike tashiga daki tafuta da kayan da sir mansir yabata, baba kaga anbani kyauta a makaranta to kyauta kuma me kikayi baba tambaya yayi shine nabashi amsa shikenan se ya dau wannan kayan yabaki harda kudi wlh baba babu wani abu daga wannan to yayi kudin tabashi tace gashi baba kayi amfani dashi to ngd to jeki kwanta daki tanufa dan tayi bacci bata jima da kwanciyaba tayi bacci baba ne ya kalli inna yace yarinyarnan tanada kokari naga alama kyanta makaranatar masu hali tab lallai malam dawani kudin yace Allah ze kawo to Allah yakawomana ammen yace yana tashi hannu ya wanke yanufu daki inna ma kayan ta ta tattara takai dakin girki ️ 💞💞Soyayya da izza💞💞 Story and Writing by hadeexatu (Mrs KD) yar amanar jajirtattu💪💪 Page 4 Mamy ce sukete shirye shiryen dawowar su Ammar saboda yakirata yace mata karfe 2:00pm na rana zasu sauka dan haka tun karfe 11 suka fara aikace aikace, girki sukai kalala Zuhura ce tafuto daga daki zama tayi kusa da inna yajikin naki dasauki inna ai kan yadena ciwo, tunsafe take fama da ciwon kai hakanne yasa bataje makarantaba, ina baba? yafuta gun aiki tun dazu inna barana watsa ruwa amira daukomun bokiti a bandaki to tace tamike wai ina halifa yana kofar gida yaronnan yakoyi yawo wlh tafada yayinda amira takawo mata bokitin tana fadin yaya zuhura gashi yawwa yar kanwata tashi tayi tanufi bandaki dan tayi wanka amira zoki karbomun mai shogon isah to ta amsa tana futa Babane kwance zazabi yarufeshi yanata nishi ko tashi baya iya yi ogansune ya nufo wurin yana fadin haba malam haruna yazakazo ka kwanta bayan kasan aikinka dakyar yake magana yace wlh jikina ne ba dadi to waye yakejin dadi yanzu inbazaka iyaba sena nemo wani mikewa yayi dakyar yazauna ah ah barana tashi da dai yafi yafada yana yin gaba 2:30pm su Ammar suka iso gida inda dama ankai bala driver yadaukosu, bayan ya saukesune suka shiga falon, da gudu nadra tazo ta rungume Ammar tana fadin oyoyo yaya Ammar jin an anbaci Ammar yasa mamy futowa daga kitchen tana fadin well come my son Ahmad sannunku da dawowa yawwa mamy yagida lpy mamy nayi kewarku sosai nima haka nadra ce tace ya Ahmad oyoyo aini fushi nake dake ni bikimin oyoyoba kika tafi gurin yaya Ammar ko to munbata rungumeshi tayi tanafadin kayi hakuri yaya Ahmad kaifa abokinane kamanta dariya yayi yana daukanta yace to na hakura kiss ta mannamai a kumatu tanafadin yawwa yaya Ahmad, ina muhsin da jawad mamy ce tace muhsin yafuta jawad kuma yana school ok Ahmad ku shiga ku watsa ruwa seku futo nahada muku abinci to suka fada nadra yasauke suna nufar part din Ammar, nadra ce tabisu abaya ke dawo mana karki bisu mamy gurin yaya Ahmad zanifa ai yanzu ze dawo zoki jirashi anan Bayan sunshigane mamy tashiga hadamusu abinci wanka sukai suka futo dining suka nufa dan suci abinci mamy tayimusu abinci kala kala da juice kala kala saving dinsu tayi suka faraci mamy ce tace Ahmad munyi waya da momynka tana abuja eh mamy nasani amma seka huta kaje ko eh se gobe bazaka bari next week ba mamy gobendai ai zandawo to ai shikenan, tunda sukafara maganarsu be samusu bakiba abincinshi kawai yakeci Ammar sekuje tare da Ahmad abuja inba hakaba baze dawoba mamy sena dan huta yabari se jibi mana to Ahmad kaji kabari se jibin ko tom shikenan nadra ce tace yaya ahmad nima zanbika tom shikenan zan tafi dake dagaske gyada mata kai yayi. Seda suka gama cin abincin Ahmad yacewa da Ammar yazo yarakashi gurin wani friend dinsa ba inda zani, ba inda zaka? eh ok tom yanafadin haka yafuce motarshi yadauka ya futa. Ammar kwanciya yayi kanshi na kallon siling da haka har bacci me dadi ya daukeshi Baradai natashi na shirya islamiyya karna makara au makarantar zakije eh inna ai naji sauki to Allah ya kiyaye daki tanufa tashirya tsaf tafito inna nagama to sekin dawo bara najira maryam tazo zamatayi, yaya zuhura ki tsayamu mutafi tare toki sauri ki shirya mutafi yaya zuhura nima zanje wlh bazani dakaiba bazama kakeba sedai ka hanani karatu dan haka ba inda zakaje kazauna a gida. autah na tawonan kaji idan yaya maryam tazo zaka bita, itama taki zuwa amira futo mutafi na biyamata gidansu tom muje inna sukaiwa sallama suka nufi kofa. halifa muje namaka wanka unguwa zamuje inna ba unguwar dazamu je shikenan se za a unguwa ake wanka muje ni suka wuce bandaki Gidan su maryam tanufa sallama tayi aka amsa mata shiga tayi dakin su. umma inayini lpy lau zuhura ya ummanki tana gida umma ina maryam bangantaba maryam sun tafi unguwa bata fada mikiba amma shine bata fadamunba ai dayake batasan harda itaba mikewa tayi tana fadin to umma semun dawo to Allah yabada sa a ammeen ta amsa hanun amira takama suka wuce makarantar Se kusan karfe 5 yatashi yayi wanka yayi sallar la'asar seda yagama shiryawa sannan yafuta falour mamy ce kadai a falourn. mamy ina yini anyini lpy ina Ahmad din yafuta, tundazu ai, ok muhsin ne yashigo sanye da headphone akunnenshi ganin Ammar zaune yasashi saurin cire headphone din karasowa yayi yanafadin yaya Ammar yaushe kadawo, yau sannu da zuwa yawwa ina yaya Ahmad yaje unguwa daga ina kake dama yasan dole se yayimai wannan tambayar yaya dama ball naje to yayi dayawan ai gara aje ball din bara naje nayi wanka azuciyarshi kuma yace to yanzu mun banu tsauri yadawo, wucewa yayi, Ammar ne yakalli mamy yace mamy ya maganar hospital dinane eh munyi magana da abbanku harma angama, kai kawai yake jira yawwa dan wlh nafusan nafara aiki dawuri da canaiwa da abbanku yabudema Ahmad ma tunda kaga komai tare kukeyi to mamy ai zamu iya yi da wananan duka ko da dai shima yabudemai daya fi. to kaga ka girma yanzu ka gama karatu gashi har zaka fara aiki yakamata ka nemo mata kayi aure mamy bayanzuba se dan nan gaba inane gaban bakai yanzuba se gaba kazama tsoho kaki auruwa dan ba budurwar dazata auri tsoho tafada tana dariya kai mamy tsoho kuma habadai kasan me nida zakajema gurin ilham ka daidaita danaji dadi ilham kuma mamy to meyeda ilham din kyakyawa da itah mamy bance tanada aibuba kawaidai ni bayanzu zanyiba, kai tokodai sena kaika amma rukiyane dariya yayi yana mikewa mamy barana dauko wayata nakira Ahmad yayi hakan ne kawai danya kauda zancen.part dinshi yanufa wayarsa yadauka gaban mirror yakira Ahmad waikai yaushe zaka dawone yanzu zan tawo kaffa ka shirgani asibiti zamuje ok ganinan katse wayar yayi yakoma yazauna tunanin maganar mamy yake wai ilham wata yarinya da ita kozanyi auren ma se in auri yarinya Antashi daga islamiyya hanun amira tarike suka nufi hanyar gida tafe suke sunata hira amira nabawa zuhura labarin yan ajinsu tanata dariya . tafiya yake yana gudu dan yasan halin Ammar baya jira hangota yayi tanata dariya, dariya take sosai, wow yafada yana kallonta, saitinsu yayi parking tare da zuge glass yana fadin sannufa bata bashi amsaba, amira ya kalla yace kanwata yayarki bata magana ne? tanayi tafada tana kallon zuhura dake tafiya shikuma yana binsu kadan kadan amota to ai ni takimun magana yan mata ki dan kalleni mana in fada miki wani abu gaskiya kinada kyau saurin kallonshi tayi wow Masha Allah beautiful girl kinga bara na nafito hannun amira taja tafara sauri kokarin futowa yake wayarsa tayi ringing dauka yayi, kaifa nake jira ok ganinan Ammar kabatamun shirina amma duk yacce zanyi sena nemoki akwai kaya bana wasaba ga kyau gaskiya yarinyarnan tayimun kala tace, daga haka yaja motar yatafi 💞💞Soyayya da izza💞💞 Story and Writing by hadeexatu✍️✍️ (Mrs KD) yar amanar jajirtattu💪💪 Typing Page 5 Shigowa tayi da sallama innace ta amsa tanacewa harkun dawo mundawo inna sannu da aiki yawwa, autah daukomun abincinna to ya amsa ke yanzu bazakije kicire uniform dinba zaki zauna cin abinci inna yunwa nakeji aike kullum dama yunwa ga kanwarkican batace yunwaba se ke nifa inna ina bawa cikina mahimmanci ah to lallai sekicigaba Ahmad na shiga gida part din Ammar yanufa samunshi yayi yana shiryawa cikin shadda sky blue ta karbeshi sosai hula yadauka yasaka Ammar ne yace ah lallai abokina na yarda mundawo Nigeria meka gani shigarka wayarshi yadauka yana fadin muje ko ok muje futa sukai atare dakin mamy suka nufa dan su sanar da itah, suntafi samunta sukai kan sallaya tana lazimi karasawa dakin sukai suka zauna bakin gado Ahmad ne yace mamy zamuje asibiti, to to adawo lafiya, ameen suka fada suna fucewa harabar gidan suka futa Ahmad ne yace bara nai driving dinmu ko, ok to kama hutashe dani dariya Ahmad yayi suka shiga mota, hanyar asibiti suka nufa Ahmad ne yace abokina kasan yau nayi babban gamo namefa wata yarinya nagani, tsaki Ammar yayi, kai wannan yarinyar ta dabance gata kyakykyawa ga diri ga shape gata chocolate beauty kai bazaka taba ganewaba seka ganta naso na karbi number ta kada meni da kira to ai seka koma ka karba ko, aibansan a ina takeba to seka hakura, bazan hakuraba sena nemota daga ganni zatai gardi au da iskanci kake sonta kenan kai ba iya iskanciba da zata aureni ma zan aureta ammafa sena moreta tukun semunji dadin juna dan yarinyarnan ba karamin dadi zataiba wani kallo Ammar ya watsa mai yamaida kanshi kan screen din phone dinshi Baba ne yashigo gidan a daddafe kana ganinshi kasan yana jin jiki inna ce takaraso dasauri tana rikeshi zuhura daukomun tabarma to tace daga daki tabarma taduko tafuto ganin baba a ririke yasata sakin tabarmar tanufi gunshi baba meya sameka baka da lpy sannu duk ta rikice shimfidamun tabarmar komawa tayi ta shifuda tabarmar tashiga dauko fulo kwantar dashi inna tayi tanamai sannu malam wai meke damunka ne wlh habiba nima bansaniba kawai tafarar daya ya rufeni ciwon to sannu, sannu sukaita zubamai duk hankalinsu ya tashi AMMAR CLINIC HOSPITAL abunda akasa kenan a saman asibitin kana ganinshi kasan yasha kudi, ciki suka shiga duddubawa suka hauyi ko ina da ko ina yayi bawata matsala bayan sungamane suka wuce gida mamy ce zaune a falo tana waya da hajiya rukayya mahaifiyar Ahmad , daga cikin wayar naji ana fadin, oh to ai hadin yayi bawata matsala nima naji dadin hadin sosai wlh saura kuma musanar da iyayensu ko eh su Ammar ne suka shigo kingansuma sun dawo anjima mayi waya kashe wayar tayi tana fadin harkun dawo eh mamy mundawo ok kunganiko yayi, yayi sosai to kuje kuyi dinner gashican a dining tom suka amsa suka wuce dining abincin suka fara ci, jawad ne yashigo su Ammar ya hango kan dining dan haka yasaita kanshi sallama yayi amsawa sukai su duka yaya Ammar kundawo ashe batare daya kalleshiba yace eh mundawo yaya Ahmad sannu da zuwa yawwa jawad sannu wucewa yayi azuciyarsa yanafadin yaya Ammar beyi maganaba naci sa'a maganar Ammar ce ta katseshi inda yake cewa amma dai ba school kajeba nan naje yaya shine kuma se 9:00pm zaka dawo ah dama dayake munje escoution wani gari kuma garin yanada nisa ok kasandai banasan yawon dare ko gyadamai kai yayi yace eh nasani good to daga yanzu duk inda kake katabbata 8:00 agida tayima tom ya amsa yana wucewa, duk abunda suke mamy najinsu tana sane taki sa baki saboda tasan halin jawad yasaba kaiwa fiye da hakama amma yanzu tunda Ammar yadawo ze dena, mikewa Ammar yayi yana fadin mamy inajin bacci sosai kuma gobe nakeson fara aiki gobe kuma eh to ai shikenan ok good night yafada yana shigewa ciki, Ammar yamatsu yafara aiki ko dan hutawa bazeba Ahmad yafada to yariga yanace dawuri zeyi tom ai shikenan jawad ne yafuto, dining yanufa mamy ina iya lami ne mezatai maka saving dina gaskiya baza a kirataba yau tayi aiki dayawa ta gaji tana bukatar hutu mamy yakamatafa kisamo yar aiki budurwa wanna tsohuwar ta tsufa fa kaga inzakai saving din kanka kayi Ahmad ne yayi dariya yace ko dai yau bakajin yunwa ne yaya Ahmad yunwa kai amma kakejira azo ai saving dinka rabudashi dai Ahmad abincin yazuba yafara ci Kwanasukai basuyi bacci ba saboda jikin baba yarikice numfashima dakyar yakeyi safiya nayi inna tace zuhura kawai mukaishi asibiti tana kuka tace eh inna mukaishi dan Allah shiga kidauko hijabi kikai yarannan gidansu maryam tom shigatai tadaukosu suka nufi hanyar gidansu maryam tanufa kana ganinta kasan arikice take gidan tashiga tayi sallama ta gaisheda ummansu

Chapter 2 of 19