diyarsu anan ba" Mamy tafada tana kallon Abba, "kenan Mamy abuja za ai daurin aure" Jawad yatambaya "eh a acan za ai" ita dai Ilham batace komai ba, seda suka kammala Mamy taraka Abba yatafi, itakuma Ilham tanufi bedroom dinta danta shirya tafuce, tanata shirye shiryen biki, dayake gobe zatayi bridal shower, Friday kuma a daura aure,
bayan Ahmad yagama shirinsa tsaf, yafuto su Mamy ne da Hajiya a falour, "Hajiya Mamy zan wuce nashirya" "ok Ahmad Allah yatsare ka gaidamun da yaya na sakuna mom dinka" "okay Mamy zataji" "to Ahmad Allah yatsare semunzo, shi wancan yanacan yana bacci bemsan zaka tafi ba ko" "Hajiya yasani ai" "to shikenan ka gaishe su sosai semunzo" daga haka yafuto, Ilham ce tafuto itama cikin shirinta nafuta, Hajiya ce takalleta tace "ah amarya futa zakiyi" "eh Hajiya gurin kwaliya zanje nayi booking" "ok gobe ne ko, yatura miki kudinne" "eh Mamy yaturamun" "ok to sekin dawo" daga haka tafuce, bayan Ahmad yafuta yaga Jummai tadawo daga kaiwa me gadi karin kumallo, tareta yayi yanafadin "yawwa dama zan baki sako ki bawa Zuhura" yafada yana bude jakar hannunsa, farar takarda yadauko yamika mata, tadan rusuna ta karba yace "ki tabbata kin bata" "insha Allahu yallabai" daga haka yanufi motarsa, Ilham ce tace "am yaya Ahmad" juyowa yayi yana kallon ta, lokacin datake karasowa gurin "yaya Ahmad wai dan Allah baka rabu da wannan matsiyaciyar yarinyar" wata tsawa yadaka mata yace "kada ki kara ce mata matsiyaciya idan ba haka ba wlh ranki seya ɓaci" shiru tayi bata kara cewa komai ba, shikuma yashige mota, me gadi yabude mai gate yafuce, itama motarta tashige itama ta fuce,
"auntyn yara" kallonshi Inna tayi tace "na'am Alhaji" "ranar juma'a fa bikin Ammar, kuma a abuja za ai daurin auren, dan haka zamuje tare" "oh bikin har yazo kenan" "eh yazo Alhaji usman ke gayamun jiya" "to Allah yakaimu dai" "ameen daukomun kaya nasa kinga yau kinsa na makara office" murmushi tayi tanufi Waldrop din tabude tadauko mai kaya ta ajiye mai, "bara naje falour naga me yarannan suke" daga haka tafuce shikuma yashiga kimtsawa, Halifa ne yafado jikin Yasmeen yana fadin "yaya Yasmeen ki mata magana wai seta dakeni" kallon Amira Yasmeen tayi tace "haba Mira saboda me zaki dake shi" "yaya Yasmeen kayana ya hargitsa mun nagaam ninkewa" "haba Halifa meyasa ka hargitsa mata" "bansaniba yaya Yasmeen" "ok toke kiyi hakuri be saniba" "zakazo kasame nine" daga haka tawuce, Inna ce tafuto tana fadin "to me kuma akeyi" "aunty wasa sukeyi" "ai nasan haline yanzu se suyi fada" "yawwa aunty anata kiran wayarki tun dazu" mikamata tayi ta karba, "yaya Yasmeen ki kaimana cartoon" "ok miko remote din" tashi yayi yadauko yamikamata takarba, cartoon din takai, "Yasmeen kiramun Mamy naga itake kirana" amsa Yasmeen tayi tana fadin "kai aunty wai yaushe zaki koyi wayarnan" "ni wannan wayar ina zan iya, shi yasa nace yasiyamun me madannai yaki yasiyamun wannan yar shafen" dariya Yasmeen tayi tana mika mata wayar, amsa tayi tare da yin sallama "maman Zuhura ina kikai wayar ne inata kira" "ina daki nabar wayar a falour ne" "ok zancen bikin Ammar zanmiki ranar Friday ne daurin auren fa, a abuja za a daura sedai ku tawo keda abban su Yasmeen" "eh dazu yake fadamun" "gobe kuma Ilham zatai nata shine nace Amira da Yasmeen suzo nan gida sesu hadu da Zuhura su tafi" "to ba matsala sena fadawa daddyn su" daga haka sukai sallama, kallon Yasmeen Inna tayi tace "Yasmeen kinji gobe zakuje gidan maman Nadra zaku tafi biki tare dasu Zuhura" "aunty zamu hadu da zuhura" "eh tare ma zaku tafi ai" Halifa ne yakalli Inna yace "aunty hardani ko" dayake yanzu gaba dayansu aunty suke cemata jin Yasmeen nafada, kallonshi Inna tayi tace "banda kai autana banda yara, party din na yan mata ne ai" bata rai yayi yaci gaba da kallonsa, abban Yasmeen ne yafuto yana fadin "zan wuce ni" "yawwa yanzu Mamy takirani take cemun gobe yarannan zasuje party din Ilham gobe" "to ba komai suje" daga haka yanufi kofa itama ta bishi,
bayan yatashi a bacci yashiga toilet yayi wanka yafuto yashirya cikin kananan kaya, sumai kyau, izzar shi takara futowa, falour yafuto, yatarar dasu Mamy da Hajiya zaune, gaishe su yayi suka amsa Hajiya tace "ango me bacci" "Hajiya nagaji ne" "me kayi kai kuwa haka" "Ahmad yawuce fa kanacan kana bacci" Mamy tafada tana kallonsa "oh harya wuce to ai shikenan" "bara nasa Jummai takawo ma breakfast" kiranta tayi nanda nan sega ta, tafadamata tahadawa Ammar breakfast, amsawa tayi tana wucewa, kallonshi Mamy tayi tace, "Please kamun wani taimako mana" "Mamy taimako kuma" "eh kaje shop na sarkoki da dan kunnaye kasiyama Zuhura saboda naga bata da wanda zatasa a biki, ni bana da lokaci, zamuje kunshi da gyaran kai, kuma zanbiya nakarbo mana dinkinanmu dana bayar" shiru kawai yayi bece komai ba "idan bazakaje ba nasa Jawad" "no Mamy zanje mana sena tashi aiki" "shikenan ai" Jummai ce takawo mai abincin tana dorawa saman table, abincin yafara ci, be wani ci dayawa ba, yace yakoshi , mikewa yayi yana cemusu seya dawo, daga haka yafuce.
yana isa airport, yatarar da Nafeesa harta je, rungume shi tayi, shikuma ya manna mata kiss a kumatu, "beb nayi ta jiranka" "to yanzy ai nazo muje lokacin tashi yakusa" daga haka suka wuce, koda suka shiga jirgin gurin zamansu daya, tana manne ajikinsa, bayan jirginsu yatashi ne takalle shi tace "beb senaji dama mu aurata ne" "yi yayi kamar be jitaba "
tayi mamaki yau Fahad be takura mata ba, koda aka futa break tabayar zezo inda suke kamar yacce yasaba, kusan karfe 2:00pm Bala driver yazo yadaukar su, suna futowa tayima kawayenta sallama suka shiga mota, bayan sun isa gida, suna shiga falour suka tarar da Hajiya zaune a falour ita kadai, "Hajiya mun dawo" suka fada gaba dayansu, "to sannunku, kuje kucire uniform kuzo kuci abincu" amsawa sukai suna wucewa, tana shiga tawatsa ruwa kana tayi alwala , tafuto tayi sallah, doguwar riga tadauka ta atamfa tasa, kana tafuto dining ta nufa Jummai tafara zuba musu, bayan sun gama , Mamy tafuto cikin shirinta, doguwar riga tasa tayi rolling da mayafin rigar, "au kundawo ashe dama ku nake jira" "eh Mamy mundawo" "kunyi lunch ko" "eh munyi" "to kutashi mutafi dama zamu futa dake Zuhura da Nadra, kai kuma Muhsin kawuce islamiyya, seka bada excuse din baza su zoba" "Mamy ni kadai zanje kenan" *to meye ba namiji bane kai" "to Mamy ni senaje nikadai" "Zuhura tashi kidauko mayafi mutafi" "tom Mamy" daga haka tamike, ranufi dakinta, mayafi tadauka tafuto, "yawwa to muje hajiya semun dawo" daga haka suka fuce ,
koda suka sauka a airport din abuja, hotel yanema musu suka sauka, seda suka gama sheke ayar su, kana yashirya yatafi gida, yace mata da daddare ze dawo, gida yanufa, yana zuwa yatarar da mom na zaune, kan kujera tana danna waya, karasawa yayi ya zauna kusa da ita, kallon shi tayi a tsorace , tana fadin "son baka da mutunci meye haka zaka tsorata ni" "kai mom be kamata ki tsorata ba ai" "yanzu ba wannan ba kaje ka watsa ruwa kazo kaci abinci" "ok mom dad be dawo ba ko" "ai se dare kasani" tashi yayi yashiga dakinshi, yana shiga yafada saman bed, ya kwanta, komai na dakin fes yake, tashi yayi ya bude wadrope yadau kaya ya canja, saboda yayi wanka a hotel, bayan yafuto ya wuce dining, me aikinta mom takira ladidi rati serving dinshi, seda yaci abincin yagama, yadawo yazauna kusa da ita, "mom ya shirye-shiryen biki" " gashinan bama mu fara ba, sedai gobe za aimun kunshi, saboda Friday bayan daurin aure zamuyi dinner tamu ta iyaye" "Mamy dinner kuma to ai mu bamu sani ba" "au haka zamuyi bikin salam ba nishadi" "to ai Ammar shine yace baza suyi dinner ba" "rabu dashi ai bamu fadamai ba, nida Mamynsa mun hada dinner bayan daurin aure" "hakan ma yayi kinga shima ai dole zezo daurin aure" "to wai kai son yaushe zakayi auren ne" "ai mom nama samu ni, jira nake agama na Ammar" "wow my son yar gidan waye kasamo mana" yasan dama tambayar dazata fara mai kenan, "am am mom dama agidan Abba take" "gidan su Ammar to wace kenan, ni nasan Hajiya khadija bata da kanwa kuma nasan Abban shima kanwarsa dayace kuma tana london tana aure, to wace kenan" a nitse yafara bata labarin rayuwar Zuhura yadda zata fahimta, kura mai ido tayi , seda yagama ta ce "ban taba sanin baka da hankali ba se yau, kana nufin yar matsiya zaka kawo mun matsayin suruka, to ka canza tunanin dan baze taba yiwuwaba" "wlh mom dandai biki ganta bane tanada hankali da nutsuwa wlh mom idan kika ganta zaki sota" "rufemun baki na lura har yanzu kuruciya bata gama sakin kaba" "mom please ina sonta sosai" tsaki taja tana tashi tawuce, dafa kanshi yayi yasan dama dole wannan ranar zatazo.
💞 SOYAYYA DA IZZA 💞
Story and writing by Hadizatu✍️✍️
Mrs (KD)
Yar amanar jajirtattu💪💪
https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v
💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
(J.W.A)
_Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️
page 38
_________________Se yamma su Mamy suka dawo , suna shigowa ana kiran sallar magariba' hakan yasa Mamy tace suje suyi wanka suyi sallah, se su futo suci abinci, itama bedroom dinta tawuce, Zuhura nashiga, tafada toilet tayi wanka tayi alwala tafuto tayi sallah, bayan ta idar tadau kaya tasa, gaban mudubi ta tsaya tana kallon kanta a mirror, ita kanta tasan Mamy ta gyara ta, ga kanta nata sheki, bakikikirin, an tufke mata shi a keyar ta, yazuba kafadunta, dan tanada gashi, ga kunshi baki da ja, jinta take cikin nishadi, bayan tashirya tafuto, kitchen tanufa, ta tarar da Jummai nata hada kayan abinci zata kai dining, "aunty Jummai sannu da aiki" "yawwa Zuhura sannu kun dawo" "eh aunty Jummai mundawo" kallonta tayi tace "kinga yadda kikai kyau kika zama yan mata" dariya Zuhura tayi tace "kai aunty Jummai bara natayaki nakai wannan" tayi maganar tana daukan, dayan daga cikin kulolin, "yawwa Zuhura anbani sako na baki fa" "wanne sako kuma" "yama yake da suna, Ahmad yace nabaki" tafada tana mikamata, "oh yaya Ahmad yatafi ko" "eh yatafi" kayan tadauka tafuce itama Jummai ta debi sauran tafuce, kayan suka jera saman dining, seda suka gama, dukkansu suka hadu dining din, Jawad Mamy takalla dake ta kallon Zuhura tace "Jawad yayanku yadawo ne" saurin kallon Mamy yayi yace "eh Mamy yadawo naga yaje sallar magariba" "okay Zuhura yimai magana yazo yayi dinner" amsawa tayi tana nufar part dinsa , tana zuwa tayi knocking, izinin shiga yabayar , ta tura kofar ta shiga, kallonta yayi, seyaga yau tamai kyau sosai, katse shi tayi da cewa "Mamy ce tace nama magana kazo kayi dinner" "am ki kawomun nan banajin zan iya futa" to kawai tace tana fucewa, bayan taje ta sanarwa da Mamy abunda yace, sawa Mamy tayi Jummai tahada mata komai kan tire, tabata karba tayi tawuce, bayan takoma tashige da sallama, mikewa yayi daga kwanciyar dayake, kan centre tables ta ajiye mai, tadau plate tafara zuba mai, hannunta yake ta kallo dayasha kunshi, jiyake kamar yakai hannu yataba, harta gama besani ba, seda tamika mai, kana yadawo hayyacinsa, karba yayi yafara ci a hankali cikin nutsuwa, seda ya kusa cinyewa ya kalle ta yace "ke bakya zamane, karki samun ciwon kai mana" yayi maganar ba tare daya kalleta ba, zama tayi tana kallon TV din datake a kunne, "zoki bani ruwa" tashi tayi tadauko ruwa a fridge tazubamai a cup glass, tamikamai, seda yasha ya ajiye cup din yace "zuba kici nasan baki ciba" "ah ah inna koma zanci" daga kafada yayi alamar ko ajikinsa, diban kayan tayi tana fucewa
koda ta futa ta tarar duk sun gama harsun shige, Jummai na tattare gurin tana kwashe kayan, kallon Zuhura tayi tace "Zuhura kinci abincin kuwa" "aunty Jummai bacci ba sedai yanzu" "to muje kitchen seki zuba ko" daga haka suka wuce, suna shiga Jummai tazuba mata, tana ci suna hira,
daddare yafuto ze futa, Mom dinshi yatarar a falour, sannu yamata, ta amsa kasa kasa, kana yace "zanje gurin wani abokina" "seka dawo" tafada ba tare data kalle shi ba, fucewa yayi, daya daga cikin motocin gidan yadauka ya fice, hotel din daya ajiye nafeesa yanufa, yana zuwa kuwa, yayi knocking, jimawa tazo tabude tare da rungume shi tana fadin "beb dama nagaji da zama ni kadai" batare dayace komai ba yajata suka shige, yamayar da kofar yarufe, kallonshi take, kwata kwata baya walwala, ba kamar yadda yatafi ba, gefen fuskarsa ta shafa, tana fadin "beb yadai kamar baka yanayi me kyau" kwantar da ita yayi saman bed din ya hade bakinsu gu daya, yana kissing dinta, itama mayar mai take,
"aunty Jummai ina wayarki"? "kin gantanan saman drower" "aunty Jummai bara nayi kira kinda kati" "eh akwai ragowar kati" dauka tayi kana tadau takardar tasa number Ahmad a wayar ta danna kira,
wayarsa ce keta kara, amma yakasa kai hannu yadauka, saboda nafeesa ta kamkamaeshi tsam ajikinta, wayar ce takara shigowa a karo na biyu, seda takusan katsewa ya kai hannu yajanyo wayar yana dagawa, karawa yayi a kunnensa, shiru tayi se daga baya tayi sallama, amsawa yayi kana tace "yaya Ahmad Zuhura ce" saurin mikewa yayi yana ture nafeesa daga jikinsa, kana yadai dai ta nutsuwar sa yace "my queen kina lafiya" "lafiya na kalau yaya Ahmad ina fata kaima haka" "haba my queen ko bani da lafiya ai jin muryarki yasa na warke" "dariya tayi daga cikin wayar tace "kai yaya Ahmad" "kina mamaki ne" shiru tayi kana yakara cewa "amma ranar Friday dake za a tawo ko" "ni ai bansaniba" "inasan nahadaki da Mommy na taganki" "ah ah yaya Ahmad nidai kunya nakeji" "kunya kuma to ai ina tare dake karkiji wata kunya" "yaya Ahmad dare yayi zanje na kwanta" "kai my queen kinamun rowar muryarki ko" "bahaka bane inason na kwanta gobe da school" "to shikenan queen sena kara jinki, ku kula dakanki kinji, kyi bacci me dadi kiyi mafarki na" "to yaya Ahmad seda safe" daga haka takashe wayar, shima kashewa yayi yana murmushi, dan yanzu yaji zuciyarsa tayi fes, tabbas yanasan yarinyar, baze iya rabuwa da ita ba, dole ne mom dinsa tayi hakuri ta karbe ta aduk halin datake, Nafeesa ce takatse mai tunani tana fadin "beb wacece kuma queen" "wacce zan aura mana" "aure kuma? "to baby haka zan ta zama banyi aure ba" "nikumafa to" "nafadamiki gaskiya bazan iya aurenkiba, harkarmu dai zamu iya yi amma kicire batun aure" "wlh Ahmad baka isaba, harna fadawa Daddy na kai zan aura kazo ka anja magana no baze yiwuba" mikewa yayi yana fadin "to seki koma kifadamai kin fasa danni bazan aureki ba" "haka kace" "yes" yafada yana fucewa" da ido kawai tabishi harya fuce,
gida yanufa, yana zuwa yayi parking, kana yashga falourn, dad ne da mom dinsa suke zaune, dad nacin abinci, karasawa yayi yana zama, "Daddy sannu da dawowa" "yawwa Ahmad kadawo kenan" "eh Daddy nadawo" "to sannu yaka barosu" "kowa yana lafiya" "to masha Allah" "bara na shiga ciki" mom ce tace "basakaci abinci ba" "no mom nakoshi" daga haka yashige bedroom dinsa , girgiza kai tayi kawai tana kallon shi har ya shige, yana zuwa yafada toilet yayi wanka ya canja kaya ya kwanta, yana tunanin Zuhura, da tunaninta bacci yadauke shi,
tana gama wayar tamika ma Jummai wayar, karba Jummai tayi tana fadin "nagane dalilin dayasa yace na tabbata nabaki" murmushi kawai tayi kana tace "bara naje na kwanta naga dare yayi" daga haka tafuce, bayan taje dakin ta canja kaya tasa na bacci, gadon tahau ta kwanta, taja abun blanket ta rufa, kin kashe wutar dakin tayi, saboda tsoro batasan duhu, dahaka bacci yadauketa,
tunda ta tashi da asuba bata komaba, tadau qur'ani tana bita, san sunfara screening din sauka, be fi saura sati guda suyi sauka, bayan tagama tadau azkar tayi, seda gari yafara haske ta mike tashiga toilet tayi wanka tazo ta shirya tsaf cikin uniform, daya daga cikin turarurrukan da Mamy tasiya mata taduka ta fesa, kana tafuto rataye da jakar ta, tarar dasu tayi a dining suna breakfast, itama zama tayi, Jummai tazuba mata, bayan sun kammala, suka mike suka fuce, Bala driver yaja su suka tafi
yau dawuri yafuto, dan haka suka hadu gaba daya sukai breakfast tare, bayan sungama, ya mike, yana musu seya dawo, ba jinawa Abba Jawad suka tashi suma, Mamy taraka Abba, shikuma Jawad yashiga motarsa yatafi, itama Ilham bayan tagama, tamike takoma daki, wanka tayi ta shirya, kana tafuto, "Mamy na tafi" "ina kuma"? "Mamy kunshin mana kuma tau friend dina zasuzo na abuja zankaisu hotel din da zasu sauka" "hotel kuma a hotel kawayen naki zasu sauka su kuma" "eh Hajiya sunce sunfi son hotel din" "to shikenan sekin dawo" Mamy tafada tana kallon ta, daga haka tafuce,
bayan ya isa office, duk inda yawuce, ma aikatan suna gaishe shi tare da yimai Allah ya sanya alkhairi, mamaki ne yakamashi jin abunda suke fada, seda ya isa office yazauna kana yafara tunanin akan me suke mai, seda ya zurfafa tunani kana ya tuna gobe daurin aurensa, danshi sam yama manta dazeyi wani aure, to amma waya fadamusu, abunda yashiga tambayar kansa kenan, wata zuciyar ce tace 'to meyesa bazasu sani ba kainefa kawai bakasan auren amma kowa naso, dole za a dora shafukan sada zumunta' wayarsa ce takatse mai tunani, dauka yayi, wani doctor ne ke kiransa, dagawa yayi, tare da dayin sallama, amsawa yayi wancan yana fadin "doctor Ammar kana asibitin ka ne"? "eh ina nan" "so dan Allah zamu kawo wani mara lafiya, abun ya gagare mu ne" "ok ba damuwa" "daga haka yakashe wayar" Ammar nada kwarewa a harkar likitanci, ko wanne irin yanayi mara lafiya ke ciki yana kokarin sama masa lafiya taeda da goyon bayan Allah (S.W.A) shi yasa duk manyan likitoci sun sanshi kuma suna yabawa kwarewarsa,
se 12:00pm Ahmad yafuto daga daki, Mom ce takalle shi yayin da ake zana mata kunshi tace "wato son se yanzu ko" karasowa yayi yazauna yana fadin "nagajini sosai, mom me ake miki" kallonshi tayi tace "kunshi mana" "kamtayayi a hannun Zuhura ake kunshinan" "wata uwar harara ta galla mai tace "karna kara jin kafadi sunan yarinyar nan anan gidan" "ni wai mom narasa me ta miki haka" "yar matsiyata ce " takaici ne ya ishe shi yabar gurin jin ana ciwa masoyiyar sa mutunci, kan dining yanufa, be jira kowa yazi yayi serving dinshi ba yayi dakansa yafara ci
cikin kuka take fadin "Mommy wlh dagaske yafadamun wai aure zeyi" "kwantar da hankalinki my daughter be isaba seya aureki, ki gama bashi jikinki yace ze auri wata bayan ke" "Mommy yaushe zaki dawo to" "ki kwantar da hankalinki kwanannan zandawo daga dubai din akwai wanda nake jira ya sallame ni" "to Mommy dan allah kidawo da wuri" "zandawo fa, amma kinsan me, karki nuna mai kin damu, kidinga janshi ajiki kuci gaba da harkarku har na dawo musan mafita" "to Mommy hakan zanyi" daga haka sukai sallama takashe wayar, duk cikin turanci suke maganar, kasancewar maman ta tana jin turanci sosai, dan ba kasar da bata zauna ba, haka kuma mahaifin Nafeesa daya rasu dan Lagos ne acan suka hadu ta aureshi, har zaman saudiyya tayi, dan acan ma Nafeesa ta girma,
karfe 2:30pm Bala driver yazo yadauke su, suka wuce, bayan sun isa gida, su Mamy na zaune falour, ita da Hajiya, shigowa sukai da sallama, Nadra tafada jikin Mamy, tana fadin " Mamy mundawo" "to autata sannunku da dawowa" Zuhura da Muhsin ma abunda suka ce kenan , suma Mamy tamusu sannu, kana suka wuce ciki, bayan taje tayi wanka, tadau kaya tasa, tayi sallar azahar, kana tanufi kitchen, Jummai ce keta aikin girki, "aunty Jummai mundawo" "sannunku Zuhura" "aunty bara natayaki" "kai Zuhura keda kika dawo yanzu" "ah ah aunty bara natayki" daga haka suka shiga aikin, bayan sun kammala suka jera a dining, seda suka kammala lunch, kana suka tattare gurin suna kwashe kayan suka kai kichen.
💞 SOYAYYA DA IZZA 💞
Story and writing by Hadizatu✍️✍️
Mrs (KD)
Yar amanar jajirtattu💪💪
https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v
💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
(J.W.A)
_Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️
page 39
_________________Jummai ce ke wanke-wanken itakuma Zuhura tana mayar dasu mazauninsu, Nadra ce tashigo kitchen din tana fadin "yaya Zuhura kizo inji Mamy" "to kicd ina zuwa" daga haka Nadra tafuce, "aunty Jummai bara naje Mamy tana kirana" fura tayi tanufi falour, bayan taje ta duka gaban Mamy tace "Mamy gani" "dama maamn kice takira waya tace nabaki" tafada tana mikamata wayar, amsa tayi, Mamy tace kije da wayar idan takira kika gama seki kawo mun, amsawa tayi da to tana shigewa, dakinsu tanufa, kafun takarasa kiran Inna yashigo wayar, dasauri ta dauka, tana fadin "hello Inna" "na'am Zuhura kina jina" "eh Inna ina wuni" "lafiya lau ya mutan gidan" "kowa lafiya Inna , yaushe Inna zakizo dan allah" "kinga ba wannan nake magana ba, inason fadamiki yau su Yasmeen da Amira zasu zo, dan Allah ki kula da ita, tana taso ku hadu" "toke Inna
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 14 Chapter of 19