Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
8 / 8
koko dai almara ce. Haj. Basira tayi bala'in bani mamaki ta canza ko dan idon jama'ar da ke gurin ne? da kyar na daga kafa na isa cikin dakin na durkusa har kasa ina gaishe ta, ta amsa cike da sake fuska. Na san ba zan iya mikewa ba don haka sai na yi zama na a wurin, wai ina Baban shi ne ai da kin bar masa shi, da rigimar sa za ki ji koda kan ki daga gefen ta ashe mahaifiyarsa Suwaiba sam ban lura da ita ba, na soma gaishe ta, waya na ji Mama ke yi da Mas'ud ka zo ka dauki yaron nan mai rigimar tsiya ta kashe wayar, ta dube ni ta shiga kun Aminar ki ga baby. Na mike zan wuce, ta kira sunana na juwo na dube ta, ta ce na ga kafafunki duk son kubura kin dan rika zagawa don su sake, Mas'ud ne ya shigo yana cewa Mama zaman mota ne åi jiya ma sun fi haka kumburi, ni kam wucewa nayi, na isa dakin da Amina take na dauki baby, ta ce anya wannan cikin naki bai fi yadda Mas'ud ya fada ba? Kaina a kasa ban yi magana ba, ta yi dariya kunya ta ke ji wai? Ai ina ga tun cikin nan na wata biyu 116 Baki Biyu Sameera Mustapha: Mas'ud ya fada, na shiga uku, da mene? Ta tambayc ni, ai ba komai ba ne Dayyiba idan Allah ya kaddaro maka sai ka gode masa, ka rike shi. Haka na zauna ina kallon abun mamaki, sosai Mama ta sake da ni, ta sa a kawo wannan a kawo wancan har akan dole na saki jiki, sai dai nauyi da nake ji na mutanen da ke shigowa ganin nakc duk sun san halin da nake ciki don yawancin su 'yan uwan Mama ne. Bayan Isha'i Mas'ud ya ce, in fito mu tafi. Da muka isa gida sai na ki fita daga motar, ya ce mun iso fa ina son fita ne, kai tsaye na ce, tare zamu in ga amaryar taka, dariya ya saki ashe haka ki ke? Dama kina da kishi. Haba Baban Tahir, kasan dole ne in yi kishinka, ko ka manta kai ne first love dina? Ni na sani ina sonka har in mutu ba zan daina sonka ba, sai dai zargin da nake maka na yi murna baki biyu da ni da mahaifiyarka why! Ba za ka fada mana gaskiya ba sai.... Hannunsa ya kai kan la66ana dole nayi shiru, wannan dan bakin naki ya cika da surutu ba comma ba fulstop, tabbas nasan kin fadi gaskiya akan baki biyun da nake yi tsakaninki da Mama, amma tsakanina da Allah ba ina yin hakan ba ne don wata manufa, sai don in ina neman hanya mai sauki da zan fahimtar da ke da ita dukan ku kuna da mahimmanci a rayuwata. Ajiyar zuciya nayi, na ce to ya aka yi ta sauko har ta tarbe ni, ban taba zaton haka daga gare ta ba. Murmushi ya saki da har hakoransa suka baiyana, Allah ne ya kawo karshen fitinar da nima kaina ina tsoron ta. cikc da nasara Allah ya bani 7 Baki Biyu Sameera Mustapha: damar warware matsala abu na farko biyc mata da na rika yi sannan da Suwaiba da na smau ta same ta tayi mata magana, ni kaina nayi mamakin irin ilimin da Suwaiba ta samu, tana da ilimin addini fiyc da yadda ki ke tsammani, ina Dubai Mama ta bugo min waya ta ce, auren da nake cewa ina nema in fasa shi, ta bani labarin irin asirin da Jamila ke nema, itama din baki biyu tayi saboda idan tana tare da Mama zata nuna mata tana sonta, sai ta fita ta rika zagin Mama, har ma daga karshe ta kai sunan Mama gun wani Malami akan tana son a kashe ta don ba za ta aure ni ba Mama na kishi da ita a kaina. To ashe Malamin na Mama ne, shi da kansa ya kira ta ya fada mata, sannan a cewar ta ya fada mata irin matar da nake aure, ke kenan ya ke nufi, to in fada miki yanzu haka kullum gargadin da take yi min shine in rike ki amana. Jikina ya kara sanyi, hawaye cike da idona na ce shi kenan yanzu zancen auren babu? Hannuna ya rike in har ki ka zama mai biyayya a gare ni Dayyiba ina sha Allahu daga ke ba wata! Tuni na saki dariya, sirinya na ce, zan yi sweet love, I love only you. Zan yi maka biyayya zan yi maka duk abinda ka ke so, rungumi ni ya yi I love you too, Dayyiba there is no one but you. Na yi alkawarin rike ki amana, sannan babu baki biyu tsakanina da ke sai gaskiya da ya ke ma ina son ki zama mai gaskiya tsakanina da ke Dayyiba, na zama wallahi na zama ina fada ina matse ido na da yake zubar da hawayen farin ciki. Baki Biyu Sameera Mustapnа: ** Rayuwa kenan, yau gani da Amir Mas'ud din da nake mafarkin samu, tun ina karama, ban taba tunanin zan kara son da namiji ba a irin matsalolin da na samu a can baya gashi ya zame min alheri, da ake cewa mafarki na iya zama gaskiya tabbas na yarda don kuwa nawa ta zama gaskiyar shekarar mu, shidda da aure tsakanina da Mas'ud mun tara zuri'a da shi, muna da yara biyar haihuwa uku 'yan biyu sau biyu nayi gashi muna jin dadin rayuwarmu, muna zaune a Dubai, har a wannan lokacin bai dai na polo game din sa ba, tsakanina da Mama kuwa abin ba a cewa komai. Watan da ma mutum kan canza lokaci daya, a kullum idan na tuna irin rigimar da tsana da Mama ta dora a kanmu, sai in ta mamakin irin yadda ta canza farat daya in ban da ganin mutunci da zumunci mai karfi da ya shiga tsakaninmu abun dai ba a cewa komai hatta Gwaggo da ba su ga maciji tsakaninsu in ka gansu a yau kace wani abu bai taba shiga tsakanin su ba. A koda yaushe sai godiya nike yi ga Allah (S.W.A) da ya juya mana rayuwarmu. Ina zaune kasa kan kafet a tsakar falo na ina tsotson kashin rago, ga ciki kuma da nake dauke dashi na kusan wata biyar, muryar Mas'ud na jiyo ta baya na honey me ki ke ci haka ko a kira ni muci tare, ni dai ban gane ba, wannan cikin ya cika ruwa na lura tunda ki ka same shi solo ne tsakaninmu, idan na zo ci ma ba a son ba mu, daga bayan shi Fauziya ce da Tahir, suna biye da shi da gudu 119 DOI DIyu Θ Sameera Mustapha: Fauziya ta karaso ta rungume ni da yake ita kadai cc ma su ne kuma sukc bi ma Tahir da ita da Mohd sunan mahaifinsu Mas'ud muna kiransa Imam shima din yana biyc da su yana ta kokawar bude marfin Icc-Crcam. Kai Fauziya don Allah kiyi min a hankali mana, Mumy ina su Abdulkahar da Abdulhafiz suke? Zaman da Mas'ud ya yi a gabana yasa hankalina ya dawo gunsa, kashin da ke cikin flate dina ne bana son ya dauka, da sauri na daukc na rike a hannuna, dariya ya yi ya ce, kwantar da hankalinki 'yanmata ba dauka zan yi ba. Harara na jefa masa ina yogot dina? Na yi maganar a shagwabc, shima tambaya ya jefo min ina 'yan biyu na? suna daki suna bacci ba dai maganin bacci ki ka ba su ba? A'a wallahi bari ba su maganin bacci ba, tun da ikilishi ta lallashe su bayan rigimar da suke ta yi shine suka yi bacin maganin da ka daukc? Kada kira basu maganin bacci, na daina Baban 'yan biyu. Na fadi hakan cike da jan hankali. Karshe. Taku; Mrs Samecra Mustapha 120 COONSHO N665022|KatisinaGetrtaaMaakket Tae1008002998600, Bittattafan marubucivar BAKI BIYU SILA LADABI FITINAR MULKI YADDA ALLAH YA SO KAIDIN MACE BAKI BIYU KAIDIN MACE SIRALUSTTPНА SAMIRA MUSTARHA CCovefGrrpphies AGF Computers Fagge 07030319787 An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels

Chapter 8 of 8