Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
7 / 8
daure ina sha. Tausayin Tahir yasa na kasa sakewa, har na dan fada kwata-kwata share Mas'ud na yi, yau satinmu daya da kwana biyu ba mu yi magana ba, wayata kashe ta nayi idan suna magana da Gwaggo kuwa barin wurin nake yi in kuwa ta matsa min kuka nake sa mata dole ta kyale ni. Kwanan Tahir goma yana fama sai dai anyi dace don a gaskiya ya samu lafiya, har da wasa yake yi yanzu ya dan yi kumari. Ina daki ina sallah La'asar naji shigowar Mas'ud, yadda ya ga Tahir a hannun Gwaggo shima har sai da ya tsorata, tambaya ya rika jefa ma Gwaggo, me ya same shi Gwaggo? Ya aka yi ya zama haka? Rashin lafiya dama yake yi? Na ji ta ce masa, bai da lafiya Mas'ud, ya ma ji sauki ai, ya dade rike dashi ni dai ina daki jira nake yi ya shigo in balbale shi, har da haushin Gwaggo na ji da bata fada masa sanadin ciwon Tahir ba, ji nake kamar in je falon in yi masa.... Jin sallamarsa dakin yasa na daina tunani, na dube shi yana rungume da Tahir din, shi kuwa ya yi kwance a jikinsa kamar ya san shi ne mahaifinsa, ya ya dai sweet heart? Ban daga ido na kalle shi ba, kuma ban ma shirya tarbon sa ba, yana kallona har ya isa Baki Biyu Θ Sameera Mustapha: inda nake zaune. Tahir da na gani yasa na fara kwalla, me ya faru ne bab....na hana shi ida abunda ya yi niyar fadi, na ce menene ma bai faru ba, kasan ciki ne da ni? "Ban gane ba! Ciki?" "Eh mana, shi ne dalilin ciwon Tahir, don haka ne ma nake jiran ka dawo muje a cire, don cikin na affecting dinsa duba ka ga yadda jaririn nan ya koma kamar mai kwashoko, ciwo ya ci shi ya cinye." "Tashi دو mu tafi tun wuri kafin lokaci ya wuce." Zan mike na ji ya riko ni ya ce, "Haba darling, tsaya ki ji. "Ni ba abinda zan ji, sai amincewarka, in da ba don Gwaggo ba da tuni na fitar dashi." Yanzu kam shima fuskarsa ta yamutse, tsawa ya daka min wanda yasa na natsu. Tahir kuwa ya fashe da kuka don shima ya firgita. Ya miko min shi. "Bashi nono." Ya umarce ni. Dole na amshe shi nasa mai kan nono a baki ya amsa kuwa ya yi shiru, abin takaici ficewa ya yi ya bar ni nan, kuka na saki ina kara tausaya ma Tahir. Haka na ci kuka na na hakura, da na gama bashi nono na kai shi gun Gwaggo za ta yi masa wankan dauri. Kwanan Mas'ud uku amma babu abinda ke tsakaninmu sai gaisuwa, ya share ni, abun na 103 Baki Biyu Θ Sameera Mustapha: daure min kai, shin ni ke da laifi ko shi? Na lura in ban da hidima da dansa babu abinda yake yi, kullum yana tare da shi dalilin haka zaman daki na koma yi, don irin haushi da rashin son ganinsa da nake yi, nima nayi banza da sha'aninsa ko kallo bai ishe ni ba, Gwaggo ta same ni ta ce, ina jin duk yadda ku ka yi da Amir, nasan halin ki, da wauta, kadda ki zubar da cikin nan tunda gashi Tahir ya soma samun sauki sosai, ki rika kula da ci da shanki, ki saki ranki, ki yi hakuri, dibi yadda ki ka zama duk kin jeme, don Allah ki kwantar da hankalinki, insha Allahu babu abinda zai faru, Allah ya sauke ki lafiya." Kwallan idona na goge, tun daga lokacin kuwa na dage da cin abinci ba don komai ba sai don Tahir ya samu isasshan ruwan nonbo, Mas'ud kuwa har a lokacin ba ma ko magana. Haka ma ya yi shirinsa ya wuce Gusau daga can ya ce da Gwaggo zai wuce Dubai. A bakinta na ji tafiyarsa har da sakon kudi da ya bar min, abun na bani mamaki, wai me yake nufi shi bai dauki laifinsa ba ne? Har ya ke fushi dani? Ni ya kamata in yi fushi da shi ba karfin halinsa ya yi yawa wannan shi ne Hausawa ke cewa a duka ka a hana ka kuka. Cikin ikon Allah Tahir ya warware sosai har ya soma maida kibarsa, ciki kuwa ya ci gaba da 104 i Baki Biyu Sameera Mustapha: bunkasa ha rya kai wata biyu, ba mu waya da Mas'ud sai dai ya kira Gwaggo su sha hirarsu, sau da yawa muna tare da ita yake kira. Tun bana damuwa har na fara, da da hali da na ce taba ni in ji koda muryarsa, sai dai taurin kaina ya hana ni, watannnin Tahir uku da rabi gani da ciki wata biyu, ikon Allah. Ranar Alhamis na shirya zan fita gidan Umma na ke son zuwa, Gwaggo ta ce Mas'ud ya ce, kada in sake fita sai da saninsa, don haka in buga masa, na ce ki fada masa don Allah ba zan fada ba ai kina da abinda za ki neme shi ki buga ki tambaye shi, har raina abun ya bata min rai, na koma daki na dauki waya ta na bude na buga masa, ya dauka bai yi magana ba. Ni na fara gaida shi ya amsa da jin yadda yake maganar ya matsu in fadi uzirina ya ajiye, daurewa nayi na ce dama ina son in fita ne ban amince da fitar taki ba, yana gama fadin haka ya ajiye wayar, kallon wayar na dinga yi, a gaskiya na shiga wani hali na son Mas'ud. Sonsa nake yi a kullum, hana ni fitar da ya yi bai min ciwo ba sai ma dadin muryarsa da naji dama mun ci gaba da magana, bakar maganarsa bata ma 6ata min rai ba, kewarsa ta dame ni, gashi girman kaina ya hana ni in neme shi dole fitar ta ta fita raina baki daya. Hirar da suke yi da Gwaggo kadai ke sa in 105 Baki Biyu Sameera Mustapha: 1 zauna falon ko duk inda take zaune don a gaskiya ina bukatarsa kusa dani, ban da ikon kuma yin wani abu a kai. Tahir na da wata kusan biyar cikina kuwa na da watanni hudu har ya soma baiyana don in ka ganshi ka ce ya yi wata shidda, don sosai ya fito sauki na daya har a lokacin ba wanda ya sani ko su Aisha ban fada ma ba sai dai ya yi na su Anti Nafisa, suma Anti Badiya ta fada masu dan ta zo nan gida gaida Gwaggo ta gani, tsiya kuwa na sha ta har sai da na rika kwalla. Gwaggo ta roke ta ta kyale ni sannan ta bari, Anti Fiddausi kam kira na ta yi ta ce ke zarin na ki ma ko arba'in ba za ki bari kiyi ba? Ki ka dauki wani cikin, duk iyashegen da ki ke mana? Haka itama ta gama yi min tsiyarta ajiye waya yana iya dole na hakura tun ina kuke-kukena har na daina. A kalla sai da mukai wata biyu da rabi kafin Mas'ud ya shigo gari, muryarsa kawai na ji suna gaisawa da Gwaggo ya sa na ji wani irin farin ciki, sai ka ce dani yake hirar, ina daki amma ina lekensa ta kofa, ya yi kyau sosai ga saje da ya bari ya yi kwance a fuskarsa, kai Mas'ud dan iya ado ne, ya yi shigar sa a saukake, yadi ne mara nauyi a jikinsa, ya yi bala'in kyau a idona. Ban da halin zuwa falon don kunyarsa nake ji, ji da nayi ya ce, zai fita yasa naji bakin cikin hakan, wulakanta ni Mas'ud yake son yi, gashi sonsa ya 106 Baki Biyu 3 Sameera Mustapha: bunkasa ha rya kai wata biyu, ba mu waya da Mas'ud sai dai ya kira Gwaggo su sha hirarsu, sau da yawa muna tare da ita yake kira. Tun bana damuwa har na fara, da da hali da na ce taba ni in ji koda muryarsa, sai dai taurin kaina ya hana ni, watannnin Tahir uku da rabi gani da ciki wata biyu, ikon Allah. Ranar Alhamis na shirya zan fita gidan Umma na ke son zuwa, Gwaggo ta ce Mas'ud ya ce, kada in sake fita sai da saninsa, don haka in buga masa, na ce ki fada masa don Allah ba zan fada ba ai kina da abinda za ki neme shi ki buga ki tambaye shi, har raina abun ya 6ata min rai, na koma faki na dauki waya ta na bude na buga masa, ya dauka bai yi magana ba. Ni na fara gaida shi ya amsa da jin yadda yake maganar ya matsu in fadi uzirina ya ajiye, daurewa nayi na ce dama ina son in fita ne ban amince da fitar taki ba, yana gama fadin haka ya ajiye wayar, kallon wayar na dinga yi, a gaskiya na shiga wani hali na son Mas'ud. Sonsa nake yi a kullum, hana ni fitar da ya yi bai min ciwo ba sai ma dadin muryarsa da naji dama mun ci gaba da magana, bakar maganarsa bata ma 6ata min rai ba, kewarsa ta dame ni, gashi girman kaina ya hana ni in neme shi dole fitar ta ta fita raina baki daya. Hirar da suke yi da Gwaggo kadai ke sa in 105 Baki Biyu Sameera Mustapha: zauna falon ko duk inda take zaune don a gaskiya ina bukatarsa kusa dani, ban da ikon kuma yin wani abu a kai. Tahir na da wata kusan biyar cikina kuwa na da watanni hudu har ya soma baiyana don in ka ganshi ka ce ya yi wata shidda, don sosai ya fito sauki na daya har a lokacin ba wanda ya sani ko su Aisha ban fada ma ba sai dai ya yi na su Anti Nafisa, suma Anti Badiya ta fada masu dan ta zo nan gida gaida Gwaggo ta gani, tsiya kuwa na sha ta har sai da na rika kwalla. Gwaggo ta roke ta ta kyale ni sannan ta bari, Anti Fiddausi kam kira na ta yi ta ce ke zarin na ki ma ko arba'in ba za ki bari kiyi ba? Ki ka dauki wani cikin, duk iyashegen da ki ke mana? Haka itama ta gama yi min tsiyarta ajiye waya yana iya dole na hakura tun ina kuke-kukena har na daina. A kalla sai da mukai wata biyu da rabi kafin Mas'ud ya shigo gari, muryarsa kawai na ji suna gaisawa da Gwaggo ya sa na ji wani irin farin ciki, sai ka ce dani yake hirar, ina daki amma ina lekensa ta kofa, ya yi kyau sosai ga saje da ya bari ya yi kwance a fuskarsa, kai Mas'ud dan iya ado ne, ya yi shigar sa a saukake, yadi ne mara nauyi a jikinsa, ya yi bala'in kyau a idona. Ban da halin zuwa falon don kunyarsa nake ji, ji da nayi ya ce, zai fita yasa naji bakin cikin hakan, wulakanta ni Mas'ud yake son yi, gashi sonsa ya 106 Baki Biyu Sameera Mustapridя yi min yawa a zuciya ta, sha'awarsa ta min gyambo a ruhina, na shiga uku wannan wane irin so nake yi ma Mas'ud haka? Hawaye ne ya ciko min idona, tabbas dama sonsa na tun can asali yana tare da ni, ni nake yaudarar kaina. Bai shigo gidan ba sai bayan sallah Isha'i, dama tuni na idar ina jiran shigowarsa, Gwaggo tasa Asabe ta shirya masa abinci yana ci suna hira, kunne na kuwa na sauraren duk wani kalma da suke fadi can naji ya ce, Gwaggo aure zan yi a tunanina ban yi zaton na ji da kyau ba, na kara saurarawa gabana kuwa sai ya shiga faduwa da sauri-da-sauri, ya ci gaba, Gwaggo na gaji da halin kanwar ki bata son a na yi iyakacin kokarina Gwaggo kin san nayi kokari, da alama Gwaggo tausaya masa tayi, don a sanyaye take maganar, gaskiya ne Mas'ud nayi shaida haka wallahi har a raina ban ga laifin ka ba sai dai kasan ita Dayyiba kuruciya ce ke damunta, ka Kara hakuri da ita. Gwaggo dama akwai yarinyar da na nema nayi mata alkawarin zan aure ta, dalilin Dayyiba na fasa auren yarinyar, Gwaggo yarinyar taki aure ta ce, ni take so shine muka hadu da ita da naje Gusau gun Mama. To kin san dama Mama ta riga tasan da yarinyar, 'yar ina ce ina fata dai ba 'yar Dubai ba ce, a'a Gwaggo 'yar nan ce sunan ta Jamila 'yar usulin Gombe ce, to ai babu 107 Daki Biyu Θ Sameera Mustapha: laifi ko ba komai Allah ya baku daman auren mata hudu Mas'ud Allah ya yi maka albarka, na gode Gwaggo da irin fahimtar da ki ka min, haba dai Mas'ud ko ba don kana auren Dayyiba ba Allah fa ya baka dama, don haka ni zan baka hadin kai dari bisa dari, Allah ya hada kansu idan anyi amin ya fada, nan suka shiga wata sabuwar hirar, ni kuma na yi zaune ina kuka, bakin ciki ne? tashin hankali ne duk sun taru sun yi min yawa, tabbas ni na ja wa kaina, hakuri kam Mas'ud ya yi shi, to wai ya ya zanyi da raina ne? A duk lokacin da na dau mataki akan Mas'ud sai dai ni in ki nasara. To ni kuwa na yi niyar kwato matsayina gunsa, insha Allahu auren da zai yi ma sanadin na sai ya fasa shi, ba don komai ba ko don yadda ya ce yarinyar tana tare da Mama (Haj. Basira), zan zama sanadin hana wannan aure sai dai ban hana in dama ra'ayinsa son yin auran ba, to zan iya ba shi hadin kai ya nemi wata, dama ai ni bana jin tsoron zama da kishiya, don ba yau na fara ba, zama na da Suwaiba na iya zama da koda mace goma ne ba ma uku ba. Ranar haka na ta sake-saken yadda zan yi da hanyar da zan zame ma Mas'ud rai wada in ba ita babu, haka na tashi ina jero nafilfili saboda na kasa baccі. Washegari Amina na kira a waya da jin yadda 108 Baki Biyu Θ Sameera Mustapha: nake magana tasan babu lafiya, don haka ta ce, in yi hakuri ga ta nan zuwa don ko jin abinda nake fadi bata yi ba don yadda kuka ya ci karfina, tun a falo na tare ta da yake nasan Gwaggo bata nan, ko gaisuwa ba mu yi ba na fada mata abinda naji Mas'ud ya fada wa Gwaggo daren jiya, na kare da cewa, Amina ki taimake ni ki fada min abun da zan yi da zai sa ya janye auren da yake son yi, riko hannayena tayi ta ce Dayyiba ki natsu ki saurare ni, ki sani aure daga Allah ne, idan Allah ya riga ya shirya hakan ba yadda zamu yi, duk da Allah ya ce tashi in taimake ka, zamu bi ta hanya a saukake kuma insha Allahu za'a dace, idan dai dama zai yi don rashin son da yake ganin kina yi masa ne ai har da ke ciki Dayyiba, duk yadda za'a baki shawara baki dauka, yadda Mas'ud ke hidima da ke da kin hakura kin kwantar da hankalinki da kin gama mallake zuciyarsa, babu wacce zata ga Mas'ud bata kara kallonsa ba, ki duba ki ga ya aure ki a matsayin bazawara ki sani fa bai san ke budurwa ba ce, ya kamata kema ki sauko ko don gwaninta da ya nuna na yin hakan, hannunta ta kai kan cikina, nayi saurin kallonta, ta ce ba dai ciki ne da ke ba? Humm Dayyiba kenan, ashe rashin lafiya Tahir sanadi ne har muna ce miki hakori ne kai Allah ya yi miki zurfin ciki Dayyiba. Ni dai tagumi na maka ina saurarenta, 109 Baki Biyu Sameera Mustapha: wata nawa ne? hudu, na fada ina dubanta. Allah ya sauke ki lafiya, anya cikin nan bai fi wata hudu ba? Allah watanninsa kenan, mun dade muna tattauna ta inda zamu fara, bata tafi ba sai da Gwaggo ta dawo. Yau bai shigo gidan da rana ba sai lokacin da ya san zai ci abincin dare, dadin da naji shine da .ya yi wa Gwaggo a kwana lafiya, ina jin haka na tashi na saka wata irin nighty da iyakar ta cinyata, dama tuni Tahir ya yi bacci, har da turara jikina nayi da turaren wuta, ni kaina nasan ba karamin kyau nayi ba, abaya na saka na jе gun Asabe na tada ita don har tayi bacci na ce, taje daki na ta kwana da Tahir. Na isa bakin kofar dakin da nasan yake, ban jira bata lokaci ba na sa hannu na murda kubar kofar, sa'a nayi don kofar a bude take. Na shiga a hankali falon ba kowa kuma wutar a kashe, sai dai haske da ya dan fito daga cikin dakin bacci, a sanda na isa ina lekawa yana zaune kan table da laptop a gabansa yana latsawa, yana sanye da farar singilet da gajeran wando, gashinsa ya yi luf-luf a jikinsa, ya yi min kyau sosai. Da hanzari na bar wurin na cire abayar dake kan nighty na, na zare ribon din da ke daure a gashi na, dama nayi kitson kalaba gashi ya kwanta a bayana, ajiyar zuciya nayi kafin na yi karfin hali na kama hanyar dakin, 110 Baki Biyu Sameera Mustapha: cikin sa'a kuwa ya jiwo sanadin motsin da ya ji idonsa akaina, tabbas tarkona ya kamu don ya kasa dauke ido a kaina, biron da ke hannunsa ya fadi kasa, da alama rudewar ganina ne, ya sunkuya zai dauka nayi şaurin karasawa inda biron yake na dauka, kallona ya yi ya koma zaune, ni kuwa cike da kissa na zare rigar sama na rage da shimi, wadda komai nawa ya kasance a waje, na haye kan cinyarsa muna kallon juna. Duk wata kunya na kauda ita, na rika kallonsa cikin idonsa na ce, I miss u, na soma kissing din fuskarsa a hankali, na kai bakina kan kunnansa ina cewa, I love you, na kai hannuna kan kirjinsa cike da son tayar masa da hankali, na tube masa singiletin da ke jikin nasa, duk da ban taba yin hakan ba nasan nayi nasara don tuni yanayin idonsa suka sauya sun koma kamar mai jin bacci, ina ganin haka na mike so nake in ga ko ya kamu da sinadirin da na saukar masa, na yi kamar zan bar wurin da yake, riko hannuna ya yi, ya yi magana muryarsa a sarke, ina kuma za ki? Tuni na karanto abinda ke ransa, mikewa ya yi ya kai hannunsa ya sabule 'yar shimin da ke jikina a saukake, ya dauke ni cak ya aza tsakiyar gadon dakin, ko wutar daki bai kashe ba, ya soma aiwatar da wani irin soyayya, nima kuma ina maida martani, na bashi hadin kai fiye da yadda yake tunani, a ranar har da sumbatu 111 ya Baki Biyu Sameera Mustapha: rika yi, ni kaina na ji dadin yanayin da muke ciki, bamu natsu ba sai da muka murji juna son ranmu. Da Asuba na riga shi tashi, nayi wanka na wuce sashen mu, karfe tara saura na gama hada mashi breakfast, na dau waya na kira shi, ringing biyu tayi ya dauka. Na yi saurin cewa, Hello! Ya amsa da jin muryarsa a sake take, na ce dama abincin kari ne.....ya katse ni, ayya ai na riga nayi, ya yi shiru, ni kuwa wani irin abu-na ji da har na kasa magana, ya ci gaba, na gode ban amsa ba kuma ban kashe wayar ba, o.k to ba damuwa ban zan aiko a karba don ni har ma na bar gidan ina side na aikin da nake yi, a sanyaye na ce, a'a bar shi kawai na hada na rana. To shi kenan, karfe nawa zan turu?" Karfe daya ko bayan azahar, it's ok, sai Allah ya kai mu. Sai a lokacin nasan nayi sakaci da har ban san irin abunda Mas'ud yake ciki ba, dole in tashi in rungume mijina. Cikin kwana hudu na gama janye hankalinsa, tuni muka zama tamkar dama haka muke, ni kaina abun na ba ni mamaki, ashe abun haka yake da sauki dama ni ce na so in yi ma kaina sakiyar da ba ruwa? Abunda na yi shine abincin sa ni da kaina na ke hadawa, zan tabbatar da na yi abinda zai iya ci dadina dashi ba ya tadan abinci, komai ka ba shi yana ci, wanka ma tare muke yi, da baya zaman gida, amma tun ranar da na iske shi daki ya fara dawowa gida hatta break ya fito gida zai dawo. Da ya sami kwana takwas aka yi masa waya cewa Amina ta haihu, muna zaune tare dashi a falo 112 Baki Biyu Θ Sameera Mustapha: bayan ya gama cin abinci ya ce, in shirya gobe zamu Gusau, murna ta kama ni ko ba komai na dade ban ga su Babah Mairo ba, in ban da waya da muke yi. A daren nake ta shiri, da na fadawa Gwaggo ta се, Allah ya tsare ya kai lafiya. Washegari tun karfe bakwai saura muka kama hanya, don haka muka isa da wuri. Na yi murna nan ganin iyayena cikin koshin lafiya, sai da muka samu kebewa da Babah nake fada mata auren da-Mas'ud yake son yi, daga farko fada ta rika yi min, ashe Gwaggo ta riga ta fada mata komai daga baya kuwa lallashi ta rika yi har ta hada da nasiha. Da yamma ina zaune falo gab da Babah, ina cin tuwon masara da miyar kuka, nayi matukar kewar tuwan Babah, daga bakin kofa na tsinkayo sallamar Mas'ud ya shigo bayan Babah ta amsa masa yana rike da Tahir hannunsa, Tahir kiwya ne da shi, baya yadda da kowa daga ni sai mahaifinsa, da yake yana shan madara agun sa yake tunda muka shiga garin Gusau, ya sami wuri ya zauna kasa kan kafet yana gaida babba, na lura akwai suruku ta tsakanin Mas'ud da Baba, ai Tahir na kyalla ido kai na ya soma soma son zuwa wurina, Hassan ya shigo ya се, ana sallama da Baba waje. Tana fita ya matso kusa dani ya ce, honey me ki ke ci haka baki ma damu da shigowarmu ba? Na yi banza dashi, Tahir ya soma rigima na karfe shi na sa masa kan nono a baki, Mas'ud ya ci gaba da kallona, ki shirya muje gun Amina. To! Kawai na ce na ci gaba, da cin abincina. Bayan na gama na mike da kyar na mika masa 113 Baki Biyu Θ Sameera Mustapha: Tahir, kallo na ya yake yin yana dariya, haushi ya kama ni na wuce na shiga dakin Baba. Dressing na dauka sosai lace ne mai bala'in tashi, a Dubai Mas'ud ya sai min shi, kallon lace din green ne amma matured da ka gani kasan ba karami ba ne, ni kaina na san nayi bala'in kyau, duk da ramar da ke tare dani, amma nayi haske sosai ga shi fatar jikina ya yi mul-mul kamar 'yar morroco na saka flat slippers baka ke na fesa turare na fito na tarar ya fata na ce da Baba zamu gidan Haj. Basira. Da sauri ya bude min kofa na shiga, ya shigo ya miko min Tahir da ya soma son yin bacci, na rungume shi da muka fara tafiya ya rika duba na yana murmushi, da muka hada ido harara na galla masa, ya ce wai me nayi miki ne? Tun jiya da muka iso ko wayata an ki dauka, laifin me nayi? A fada min kada ciwo zuciya ya kama ni, na zumbure bakina, a shagwabe cike da kisisina na ce, babu komai, haba honey ta ki fada min ya za ayi in san laifina baki fada ba. Jiya kana tare da amaryar taka ne? Na ida zaman ina kallonsa, ajiyar zuciya ya yi ya ce, wace amarya kuma? Da yake maganar ta zo masa a baza ta sai duk yanayin fuskarsa ta canza. Ba au re zaka yi ba? Na fadi maganar babu jin komai a tare da ni bai amsar sa da nake son ji. Ya ci gaba da tukinsa a hankali kamar baya so, wa ya fada miki aure zan yi, a bakin ka naji murmushi ya yi sannan ya yi parking a gefen titi. Ya juwo sosai yana duba na, Dayyiba ban taba tunanin zan yi tunani in yi aure ba sai lokacin da ki 114 Baki Biyu Sameera Mustapha: ka murje ido ki ka nuna min kiyayya kiriri, ki ce ba ki son haihuwa da ni, in kin manta in tuna miki kin san cikin Tahir haka ki ka so zubar min da shi da na yi asararsa, yanzu kuma kina son ki zubar da wannan to don Allah me ki ke so in yi? Wallahi kin ji rantsuwar musulmi da kin zubar da cikin an da ba karamin abu zai taso ba, to daya ke Allah bai kaddara fitina tsakanina dake ba sai ya sauya miki shawara, sannan zance aure tabbas na nema kuma ina kai, hawaye ya zubo min jin hannunsa nayi a fuskata, baby don't cry kin san fa kina tare da condition, sannan bana son ki bata wannan kwalliyar taki kin yi kyau sosai. Aure za ka yi da gaske? Na tuba ka yi hakuri ba zan sake ba nasan nayi kuskure kayi hakuri, murmushi ya yi yana dai rike da fuskata tare da goge min hawaye, ya ce kada in yi auren kenan? Ban iya cewa komai ba na sunkuyar da kaina kasa. Fita ya yi daga motar ya zagayo guna ya karbi Tahir, ya bude baya ya kwantar dashi ya dauko tissue ya bani gyara fuskarki zamu yi magana an jima. Ban musa ba na karba na goge fuskata da yake da Foundation a fuskata bata wani lalace ba mun isa cikin gidan da gani gidan a cike yake, na fito da sauri na dauki Tahir, kawo shi in rike maki shi na ce a'a ni zan rike shi ina magana ina lullube cikina, dariya ya saki, kunya ki ke ji kada a gan ki da ciki? Na murtuke fuska ba tare da nayi magana ba, ki kawo shi, ni dai ka kyale ni, na kama hanyar shiga gidan don dama gida ba bakona ba ne, a raina kuwa ina tunani ırın badakalar da za'a yi. 115 Baki Biyu Θ Sameera Mustapha: Da na isa ciki da Amina muka fara haduwa, murmushi ta saki ta iso guna ta karbi Tahir budc ido ya yi ya fara kuka ta miko min shi tana min kallon tsab, hannunta ta kai kan cikina, ba dai ciki gare ki ba? Jina yi kamar in nutse da kunya, ikon Allah ta fada ta riko hannuna muka isa dakin Haj. Basira gashi Tahir ya soma rigima abun mamaki Haj. Basira ta iso ta karbe shi ta ce, kai yaron nan ka cika fitina, geshi Maman taka ba cikakkiyar lafiya ne da ita ba, jikina ya yi sanyi na sa kai na kasa, shin mafarki nake yi

Chapter 7 of 8