Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
3 / 8
saboda shi ne na gwammace ba ka daina ba dan Mama, baki ya saki yana kallon fuskar Haj. Basira, ya ma rasa abinda zai ce mata, don 35 Бок 5 Sameera Mustapha: bala in mamaki, da ta bashi. Ajiyar zuciya ya yi tare da mikewa ya bar dakin, duk nacin kiransa da take'yi, ya yi tafiyarsa tare da Kara nadama akan abinda ya aikata, ya yi ma kansa alkawarin ba zai kara shan wiwi a rayuwarsa ba, insha Allahu. Tunda ya fita gidan Alh. Ashiru ya nufa ya ba shi hakuri akan abinda ya faru, Baban nasa ya ji dadin hakan, shi ya raka shi gidan da Alh. Mohd Shinkafi ya ba Mal. Sabi'u yana zaune duk ilahirin jikinsa a sanyaye ya rika ba da hakuri, Mal. Sabi'u ya ji dadin hakan fiye da yadda ake zato, nan dai ya yi masa nasiha mai ratsa jiki dama ya riga ya san matsalar sa da mahaifinsa, don haka ya ta ba da hakuri ai tuni komai ya wuce a nan yake cin abincin dare tare da Mal. Sabi'u kafin ya wuce Dubai. A nan Dubai ya hadu da wata yarinya mai suna Raliya, Raliya Muktar, yarinya ce da ta amshi suna gurin gasar kyau na kasar Dubai a dalilin haka sunan Mas'ud ya bazu a duniyar polo. Dama gashi tunda ya bar wiwi ya yi haske ya yi kiba a lokacin ne kamanninsa da Tahir ya baiyana, gashi dogo dashi ya yi kyau sosai Kasar Dubai ta karfe shi sosai. Duk in da zai je yana tare da Raliyan, bata taba yadda ya tafi ya barta ba, a dalilin kwarjininta shima nashi kwarjinin ya fito har ya yi yawa da 'yanmata ke mutuwa 36 Baki Biyu Sameera Mustapha: akansa, kun san dai yadda dan wasa yake da farin jini a rayuwar sa har dai in ya hadu. Raliya Mukhtar Balarabiya ce da tayi fito na fito wurin gasar kyau ta 'yanmata a London ta zama Queen har ta fara acting film din larabci a nan Dubai. Tana tashe a lokacin saboda kyaunta da iya kissa, iyayenta 'yan ainihin Jordan ne sai dai zamansu a Dubai ya kankama dan su koma 'yan Dubai. Raliya na bala'in son Mas'ud itama kanta ba zata iya fadar ainihin dalilin da yasa ba. Tunda ta dora ido akansa wata rana da suka je turniyal ta tseren Doki anan Dubai racing mehdon, ya cinye wannan gasar ta san duk yadda zata yi ta manne mashi. Shi kuwa kyaunta da iya shiga shi ya rinjaye shi ya zauna da ita sannan ya lura kasancewa da ita ya maida shi tauraron mujalar Dubai, kusan kullum sai ka gansu a gaban mujalar su biyu, ba yadda ba su fitowa ko a rungume ko a yaya ma gani zaka yi, a hankali har ya zama ana daukarsa yin talla na kayan kamfani. Nan da nan ya zama shahararre wurin iya zama da mata don ba shi ke neman su ba, su suke kawo kansu da kansu. A hankali ya sayi gida a nan Dubai har da motocin hawa, ko Nigeria bai cika zuwa ba, tunda ya tafi sai da ya yi wata shidda sannan ya koma shima a lokacin Alh. Mohd Shinkafi ya 37 Bak Biyu Sameera Mustapha: neme shi, to da ya Kara komawa bai ma yi tunanin dawowa ba don tsabar jin dadi da ya samu a Dubai, kyaun abin ya na bugawa kullum ya gaida iyayensa. A lokacin da ya samu shekaru biyu da fara kwallo a lokacin mahaifinsa ke gaya masa Tahir zai yi aure, Baba zai sake aure nc? Eh, kasan fa in lokacin abu ya yi, to sai anyi shi, haka ne to Allah yasa ayi lafiya. To kai fa yaushe zaka yi auren? Ni? Eh, kai, uhmm...zan yi Baba yana magana yana sosa keya kamar yana kallonsa. Ana sauran kwana biyu daurin auren Dayyiba ya shigo gari abunda ya daure masa kai shine, wai Tahir zai auri Dayyiba, yarinyar da yake shirin aure, ita kadai yake so, ita kaďai yake tunanin zai iya aure amma me yasa haka ta same shi? An ya zai iya aure kuwa? Tabbas ya sani a rayuwarsa yana son yara fiye da tunaninsa, sai dai a wannan lokacin auren ya fita ransa baki daya, don haka ma ranar da aka daura auren a ranar ya wuce ya koma Dubai. Suka ci gaba da zama da Raliya sai dai tunda Dayyiba tayi aure ya fara tunanin mafita, bai taba kawo tunanin auren Raliya ba, don sam ba su dace ba a cewarsa, ya sani itama kar ta tasan hakan don ita kuma bata ra'ayin yara ta ce ita ba za ta haihu ba. Dama shi bai taba ra'ayin ya aure ta ba, suna tare dai har ya dan ci gaba da zama 38 Baki Biyu Sameera Mustapha: London saboda wani club da ya samu yana musu wasa a can, a lokacin ne kuma wan sa Tahir ya soma son jawo shi jiki, so da yawa suna haduwa a London don idan Tahir ya je gun sa yake sauka, don haka ne ma in suna tare baya yadda ya aikata abinda yasan bai dace ba ta hanyar matan da yake tare da su, akwai lokacin da Tahir ya yi masa maganar aure, dariya kawai ya yi, yasan yadda ya yi aka bar maganar. Shakuwar da suka yi yasa Tahir ya daina zuwa London sai dai yasa Mas'ud ya wakilce shi, har ma a sanadin haka ya samar masa business a nan London, business din da ya dade yana nema bai samu ba. Sai gashi cikin wata guda ya samu, dawowan da ya yi dole ya sakar masa aikin ya ce, lallai shi ya kamata ya ci gaba. Sam bai so hakan ba, yana gudun kada ya samu matsala gun wasa polonsa, sai da Tahir ya gaya ma Alh. Mohd Shinkafi ya yi masa magana sannan ya amsa. Shi fa baya son ya takurawa kansa da yawa, kudın da yake samu a wurin wasan polo da talan da yake ya ishe shi zaman rayuwarsa. Ana cikin haka kuwa, Allah ya bashi sa'a sosai har ya gaya ma Tahir ya kamata su saya gida a London, da jin haka Tahir ya matsa ma mahaifinsa sai dai suje London su ga abinda Mas'ud ke yi, bai yi sa'a ba don zuwan ba zata 39 Bakı Biyu Sameera Mustapha: suka yi masa. Mata ne da maza cike а department din sa wai party ake yi na Valentine. Saukin abun shi baya shan giya baya shan komai, amma taba kam kamar akansa ta samo sunanta. Da suka kwankwasa kofar shi da kansa ya bude masu, take hankalinsa ya tashi, rudewa ya yi ya ma rasa ta inda zai fara, juyawa ya yi yạ koma ciki ya kashe radiyon da ke aika masu kida, ya bada hakuri akan mahaifinsa ne ya zo, dole party ya zo karshe duk yawancin su sun buge a zare suka firfito in sun fito sai su gaida su Tahir da ke tsaye cirko-cirko suna kallon ikon Allah. Da sauri ya rika kwashe kwalaben da aka yi amfani da su ya dan gyara falon, ya bude window don warin wiwi, sigari da giya ya fita, ya dauko room freshner yana fesawa, a lokacin suka shigo ya rasa abinda zai yi da kunyar da ya ji, sun sami wuri sun zauna suna kallon shi, a kasa kan carpet ya zauna yana gaida su, a sanyaye suka amsa masa, sun ma rasa ta inda za su fara. Tahir ne ya dan gyara zamansa ya ce, haba Amir, wannan ita ce rayuwar da ka daukar wa kanka? Alhaji ya amsa dama neman ta inda zai fara yake yi, fada yake yi sosai ta inda yake shiga ba nan yake fita ba, sai da ya zage shi tatas ya kuma ce dashi, to idan haka ne kuwa tunda ya 40 Baki Biyu Sameera Mustapha: koma baturen karfi da yaji, sai dai ya goge sunansa a matsayin mahaifinsa, ya nemi wani uban ba shi ba. Idanun Mas'ud sun yi jajir kamar garwashin wuta, kamar ya yi kuka ya marairaice murya, kayi hakuri Baba, ba zan hakura ba, Amir na gaji da fitinarka, ya ka ke son in yi da kai ne wai? Yanzu fa zuwa muka yi don mu baka labarin abinda ke damun dan uwanka don a raba aikin da yake yi a baka saboda a zatonmu ka daina halinka na shirme, shine ya matsa in zo mu fada maka abinda muka yanke a.....Baba don girman Allah kayi hakuri, na tuba. Dole Alhaji ya daina fadan saboda tashin hankalin da ya gani a kwayar idon Mas'ud. Ajiyar zuciya ya yi ya dube shi cikin ido ya ce, Amir dan uwanka Tahir ba ya da isasshen lafiya, shi ne yake son ka fara kula da dukiyarsa ta nan da Lagos, da sauri ya dubi Tahir ya ce, me ke damunka? Ciwon kirji ne ulcer ce ta cini ta cinye har ta taba min zuciya da hanji, na tashin hankali tausayin su baki dayan su ya kama shi ya ce, shine baka taba gaya min ba, nima ban san abun ya yi tsanani haka ba sai sati biyu da suka wuce don Allah Amir ina son in baka amana a hannunka, kai kadai na yadda da kai, don haka nake son in mallaka maka duk wata dukiya da nake juyawa, saboda ina tunanin abunda zai kasance nan gaba. Alhaji ya riko hannun Tahir 41 Baki Biyu Θ Sameera Mustapha: ya ce, zaka warke insha Allahu. Tahir wanda idansa ya cika da kwalla, ya ce ku yafe min ku gaya kowa ma ya yafe min in na mutu don a gaskiya.....Mas'ud ya katse shi ya ce, haba me yasa ka ke fadan irin wannan maganar an gaya maka ana rubuta ranar mutuwar ka a goshi ne? murmushi Tahir ya yi ya ce, to Allah yasa muji alheri, ya fito da takardu daga cikin jakar da ke gefensa, ya bude duk labarin dukiyarsa ne, ya mikawa Mas'ud gashi kayi signing, ya mika hannu zai karba sai Tahir ya hada da hannunsa ya rike gam, ya ce Amir ka rike wannan dukiyar amana saboda Allah ka ji, Mas'ud ya girgiza kansa, insha Allahu za ku yi alfahari da ni na gode, Allah ya bar zumunci, mahaifinsu kallon su kawai yake yi tausayinsu ya kama shi ji yake tamkar ya karbi ciwon da Tahir yake da shi yasa ma kansa, to amma ya zai yi kowa da nasa rai kuma kowa da nashi zai yi amfani. Cikin wata daya ya hađa shi da duk inda yake aiki har zuwa Thailand, har an fara bugawa a mujala cewa Mas'ud ya daina wasan polo saboda anyi wasa ya fi biyu da club dinsa ba ya ciki sakamakon haka kuma ana samun rashin sa'a. shi kuwa ba wai ya daina ba ne so yake ya yasan business din da Tahir ya bar masa shi yasa ya dauki hutu na shekara daya tal, don ya samu natsuwa. Raliya na ganin haka tasan mutumin Baki Biyu Θ Sameera Mustapha: nata ya zama milloniya don haka ta fara yi masa zancen aure, shi kuwa a lokacin a gaskiya ba wannan ne a gabansa ba, don bai da ra'ayin aure a wannan lokacin, gashi ko zama ma baya yi, sam basa samun isasshen lokaci tsakaninta dashi, rannan kawai sai ya yi tunanin ya yi weekend din sa a Dubai, ya shirya ya tafi cike da nishadi, abinda ya iske ne rabonsa da Raliya don maza take kai masa a gida, wannan lokacin ma turmi da tabarya ya kama su, sam ransa bai 6aci ba, don dama yana neman hanyar da za su rabu, gashi a saukake sun rabun. Aiki sosai ya ke yi sam baya da lokacin kansa, saukin sa abunda ya karanta kenan sannan yana da saurin fahimta ga ilimin iya sarafa aikin nan da nan abu ya bunkasa saboda ribar da ake samu ta ninku cikin wata shidda da ya soma aiki. A wannan lokacin ya hadu da wata yarinya 'yar Yobe bafulatana ce tana da kyaun gaske a Gombe suka hadu lokacin da yaje ziyarar abokinsa Sa'idu. A gaskiya ya sota sosai har yana tunanin aurenta, kuskure daya da suka yi shine da ya santa mace tun kafin suyi aure. Tabbas, yasan ya same ta a cikakiyar mace wadda bata san namiji ba shi ne namiji na farko da ya kwana da ita don haka nema ya yi mata alkawarin zai aure ta, bai taba zaton zai same ta a kintsattsiyar mace ba, don haka tare suke da ita Baki Bıyu a vanzu. Θ Sameera Mustapha: Jamila Abbas, iyayenta 'yan usulin Gombe ne, zama ne ya kai su Yobe, suna da arziki daidai gwargwado don sun ba 'ya'yansu ilimi na boko da Islama, suna da ilimi sosai don Jamila ta na 400 level a lokacin da suka hadu da Mas'ud ga shi zata gama kenan wannan abu ya shiga tsakaninsu da Mas'ud, ita kam sosai ta so ta kai budurcinta gidan mijinta, to amma a ganinta yadda maza sukai karanci a yau zata rasa Mas'ud in bata bashi hadin kai ba don ta lura don son harka me gashi da iya soyayya sam bai maida kiss bakin komai ba gashi in ya fara dole ne maki mace duniyar da ki ke ciki. A gaskiya rasa namiji irin Mas'ud asara ne a gunta don haka babu abunda zai nema a gunta ya rasa. Yana da wata goma da fara ciki ciwo Tahir ya tsananta, sai dai Tahir ya ce, kada a gaya mashi a wannan lokacin saboda aiki ya yi yawa sosai, har sai da aka dawo dashi Nigeria yana asibiti ciwo ba ji ba gani abun ya tsananta shi ne fa Alhaji ya buga masa waya, ai bai bari ya kwana ba ya diro Nigeria. A nan asibiti ya ci karo da Dayyiba tayi masa kyau sosai ta kara budewa ta cika cikakkiyar mace. Duk da yana tare da tashin hankali irin yadda yaga Tahir ya zama sai da ya yi mata kallon kurila saboda ba karamin haduwa tayi ba, zuwansa kuwa da kwana biyu Tahir ya Baki Biyu Sameera Mustapha: cika ya bar su da jimamin rashin sa. Da ya kama aiki a gaskiya babu ranar da zai kwana ya tashi bai yi tunanin Dayyiba ba, sai dai bai sani ba ko zata yadda ya aure ta ba, kafin ya ganta ya shirya son yin auren ya so kwarai ya aure Jamila, sai dai ganin Dayyiba komai ya juya. Tunaninsa duk ya koma gun Dayyiba, gashi ya kasa gaya ma kowa, ba lantana mahaifiyarsa da ya lura baya da makiya irin Dayyiba, sam bata san ta yanzu haka tun wata biyu da suka wuce take damunsa akan yasan yadda zai yi ya kwace dukiyar da Tahir ya mallaka masu ita da Gwaggo, mahaifiyarsa bata san a yanzu ma wanda ya ce zai takurawa Dayyiba sai inda karfinsa ya kare ba. Saukin ta daya ita ta haife shi shi yasa yake kyale ta yana biye mata da to. Jamila. Abbas kuwa abin ya fara damunta sosai gashi dai ta gama Makarantar da yake ta cewa ta gama, cikin dubara ya ce, da taje tayi bautar kasa ta gana kafin ayi aure so yake in dan ya aure ta ta zama secretary din sa, hakan ya yi mata dadi sai dai ita ba haka ta so ba, to amma ya zata yi dole ta yadda da shawararsa, ta tafi bautar kasa. Sai da Tahir ya sami shekara daya da rabi sannan Alh. Mohd Shinkafi ya soma damun Mas'ud akan zancen aure, shaida masa 45 ya Baki Biyu Θ Sameera Mustapha: yarinyar da zai aura tana makaranta ne da ta gama zai fada aje neman auren ta hakan yasa mahaifinsa ya kyale shi. Jamila kuwa tuni ta gama bautar kasar sai dai ta rasa abinda ke damun Mas'ud ya dauke kafa zuwa gurinta ma tun tana daurewa har ta kawo karansa gun abokinsa Sa'idu. Sa'idu ya riga yasan ba aurenta zai yi ba, don ko shekaran jiya nan da suka yi magana ya ce shi fa yarinyar da yake son aure tana nan, don haka ita yake son ya nema, dole ya fada mata abinda ake ciki, bakin ciki babu wanda bata yi ba, gashi ta riga ta sa son sa a ranta. Mas'ud ya yaudare ta ya ci amanar ta don haka ita kuma ta dauki alwashin zata shiga ta fita a halin ko kaka sai ta aure shi, a ganinsa ya cuce ta ya dauke budurcinta da take alfahari da shi sai rana tsaka zai aza mata gyada a hannu to ba zai zauna lafiya ba sai dai ya dawo ya aure ta. Shi kam yana nan yana tunanin yadda zai yi ya tunkari iyayensa da wannan zancen gashi wata shidda da mahaifinsa ya dibar masa ya cika ya ya zai yi? Yasan ba karamin aiki ya dauko wa kansa ba don kuwa Dayyiba ko kallo bai ishe ta ba ya lura duk ran da ya je Kaduna in ban da kallon raini da miskilanci babu abinda ke damunta, bata bari ma yayi mata magana ba ta bari ma su kasance su biyu a gu daya, mahaifiyarsa kuwa duk tabi ta dame shi akan ya 46 Sameera Mustapha: Baki Biyu zo ta sama masa mata, bai masa kan yaje ya ganta ba don ba wannan ne a gaban sa ba. Alhaji kuwa yasa masa ido har ya kara watanni huрп cur bai ce masa kanzil ba akan aure shi kansa Alhajin ya rasa abinda ke damun yaron nasa, namiji har namiji amma aure ya ki shi, abun sai addu'a don haka ya sa a fara addu'a don shi kam ya san babu mai shiryawa sai Allah (S.W.A). Lokacin da ya shigo Nigeria gidan Gwaggo ya sauka dama haka ya saba yi, ita din ya iske a falo maimakon Dayiba, don ya saba ita yake yawa gani a falon, bayan ta tarbe shi ne ta rika yi masa fada akan abunda yake sam bai da kyau. Tun can dama tana yi masa fadan to amma na ranar yafi tsanani, don haka ya daure ya cije ya fada masa ainihin abinda yake so, abin ya bala'in ba Gwaggo mamaki sai dai tayi kokarin maida shi ba komai ba har take ce mashi Amir, dama zaka iya auren Dayyiba? Bazawara ce fa murmushi ya yi ya ce Gwaggo ai ko Annabi Mohd (S.A.W) da bazawara ya fara gashi kuma ta girme shi ma ba ita ta karasa masa. Ta ce zan ba da hadin kai sosai a wannan al'amari sai dai ina so ka rike amana Amir, ya dauki alkawarin rike amanar Dayyiba ya ce, gobe zai wuce Gusau yasan Alhajinsa na fushi da shi, to ai sai ma in bika mu fadi komai, to Dayyiba fa Gwaggo? Ta ce, ka kyale ta ba sai mun fada 47 Baki Bivu Sameera Mustapha: mata ba, kasan ta da rigima kuwa? Kyale ta kawai sai mun fada can Gusau, don haka zan shirya gobe mu tafi tare ayi komai a idona. Yadda yake tunanin abin zai yi wahala amma cikin sauki kowa ya amshi maganar mahaifinsa ya sa masa albarka, sosai ya ji dadin hakan da ya yi su dai fatan alheri suka rika yi mahaifiyarsa kuwa har fushi tayi dashi duk da bai bari suka zauna ba, gudunta ya rika yi har ya koma. Bayan an sa ranar daurin aure sati daya. A gaskiya rayuwa wata rana tana da sauki, wata rana kuwa sai ta zama tarihi, abu kamar ba ayi ba. Bai dawo ba sai ana jibi daurin aure, abin mamaki ya hadu da Sa'idu, tare da Dayyiba, dama ita ce kanwarsa da yake ta bashi labari, ikon Allah. Ya lura bata son irin kallon da yake mata, shi kuma har a rana bai jin zai iya daina kallonta don a taurari ita ce zahra. Ranar sati aka daura aurensa da Dayyiba, abun haushi an hana shi ya yi mata magana dole ya wuce Dubai saboda akwai wasan da za su yi a can, har cewa ya yi ya fasa yin wasan, Alhajinsa ya ce, ai bai isa ba sai dai ya tafi daga baya za'a turo masa matarsa, akan dole ya wuce. Ranar Litinin, ya zamto a kullum sai ya buga ma Gwaggo don ya ji irin shirin da suke yi, tun bata son gaya mashi abunda ake ciki har dai ta kai ta 48 Baki Biyu Sameera Mustapha: fada masa rashin lafiyar Dayiba, hankalinsa ya tashi sosai amma ya ya iya, manya sun yi magana dole ya hakura har sai sun gaji sun turo mai matarsa. Tunda yake babu macen da ke dasa masa magana irin Dayyiba, ita kadai ce ke fada masa bakar magana da baya iya kwanciyar hankali ko dai bata san irin son da yake mata ba ne, ya sha alwashin duk yadda zai yi sai ya yi ta so shi, don shi a duniya babu wacce yake so sai ita. ** ** Ina cikin Jirgi ina tunanin wannan karfin hali da aka yi min, ko macen da bata aure wato budurwa an bata 'yancin ta zaba wa kanta mijin aure, ina nufin wadda ta balaga, sai gashi ni ban dauke ni bazawara ba amma kuma an danne min hakki. Ina tunanin wannan lamari bacci ya dauke ni. Shi kuwa Mas'ud yana racing na international world cup 2010, lokacin har sun gama kuma shi Allah ya ba sa'a, gobe ma za suyi da wani group din. Ya isa gida kenan, ya ga missed calls da yawa, ya kai missed calls hamsin, shine ma sanadin batery ya yi law. Da sauri ya bugawa Gwaggo don nata yafi yawa. Bayan sun gaisa take ce mashi, Dayyiba na kan hanya, ai bai jira ba ya buga ma direbansa ya ce, maza yaje airport 49 Bakı Bivu Θ Sameera Mustapha: ya sanar yana da bakuwa, sunanta Dayyiba Sabi'u. Haka kuwa aka yi, ya yi sallama da Gwaggo ya buga airport aka ce a haka ne ga ma jirginnan yanzu ya sauka, da saurinsa ya buga ma Kabir Al'amin, wato Embassy na Nigeria waya, ya сe, Eh, yana wurin don haka abun ya zama la sauki. A lokacin ya fara gyaran gidan da gidan a barka ce yake. Ni kam ban tashi ba sai da Jirgi ya sauka, sai da suka gama yi mana screening sannan mutumin da ya gabatar mana da shine wakilin Nigeria shi ya tambaya ko ni ce Dayyiba Sabi'u? Na amsa Eh, ni ce, ya ce maigidanki ne ya ce in sada ki da wanda zai kai ki masauki." Tabdijan, lallai ma wannan mutum, isa ta mai yawa. Da yake kyauta aka bashi ni bai da lokacin da zai zo ya tarbe ni, zan gani wane irin zama zamu yi. Na isa na shiga motar na wani hakimce a gefen owners corner na sha mur, sai ka ce ni ce mai motar, da muka isa gidan shi ya fito da sauri ya bude min kofa, da yake da a baya nake sai shigar ta yi daidai da ancen, shi ya riko trolly na ya shiga gaba ina binsa a baya. Ta lift muka bi sai da muka kai hawan karshe na uku, sannan muka fito muka isa kofar shiga, dama tuni ya dinga bugawa kamar zai fito waje, ya bude muka shiga, ya ce da turanci, oga ya ce dama idan mun 50 Baki Biyu Θ Sameera Mustapha: iso ki yi hakuri ki jira shi yana nan zuwa, ban amsa ba na samu wuri a daya daga kujerun da ke falon na nutse, kai kujerar ba dai laushi ba, na zare ido ina kallon falon don a gaskiya ba karamin haduwa ya yi ba, littafi na ciro na soma dubawa, wai da zummar in yi karatu sai dai sam na kasa bana da natsuwa a tare da ni. Ban fi minti ashirin ba, na ji ana kokarin bude kofa, gabana ya ci gaba da bugawa. Bude kofar ke da wuya mu kai ido hudu da Amir. Ban daina kallonsa ba, tambaya nake ma kaina, me kuma Amir yake yi a nan? Mece се dangantakarsu da mutumin.....?" Ya tsinka min tunani da ya ce, "Sorry, na bar ki kina ta jirana ko?" Maganarsa ta zo min wata iri, ba dai shí ne Mas'ud ba?" Kara matsowar da ya yi guna yasa na daina tunanin da nake yi, na hade rai duk hankalina a tashe yake. Kayan abinci naje siyowa su Gwaggo ba su fada min kina zuwa ba sai da na dawo daga racing, ya hanya? Irin kallon da na saba yi masa shi nayi masa yanzu ma ban amsa ba. Ba ki ji ina gaida ki ba ne? na turo bakina ina gunguni, ai sai na fashe da kuka, me ya same ki ya matso guna tare da son taba ni, kara na saki tare da ce masa, wallahi in ka taba ni za ka gane kuranka, kallona ya ci gaba da yi, ni kuma na ci gaba da kukana mai tsumar da rai, lallashi ya 51 Baki Biyu Θ Sameera Mustapha: soma, kiyi hakuri abinda Allah ya kaddara mana kenan, kai dai Allah ya kaddara mawa ba ni ba, na fada masa ina kokarin mikewa, kama hanya nayi na ja jakata zan bar falon, ya biyo ni, ina za ki? Ya yi tambayar a saukake, ban amsa ba na fara kokarin bude kofa, ji na yi kofar ta ki buduwa, nayi-nayi amma na kasa. Kaina na hada da kofar ina ci gaba da kuka, ya matso har inda nake ina za ki je? Ban sani ba, ni kawai ka bude min kofa in tafi, to shi kenan zan bude maki, amma sai kin gaya min inda za ki tukunna. Wuri zan nema in zauna inda ba zan rika ganinka ba, don ganinka illa ce a gare ni, ya ji zafin maganar, amma sai ya daure ya ce, kin ga dare ya yi, amma kiyi hakuri sai zuwa gobe...." Na katse shi, ni kam ba za ni yadda ba, wallahi an cuce ni, da aka yi min auren dole tsakanina da kai, to bari in gaya maka, tun wuri ka ba ni takarda ta don wallahi ba zan zauna da kai ba. Duk da ransa ya baci, haka ya daure yana lallashi akan in hakura da tafiyar nan har gobe. Jakar ya dauka ya yi ciki da ita, ni kuma na ki barin kofar, ina nan a gurin ya yi lallashin duniya na ki barin wurin har ya gaji ya kyale ni, ya yi wucewarsa, ina kallo ya bude ledojin da ya shigo da su, ya bude ya fito da abinci kala-kala ya saka wasu a fridge, sannan ya shiga daki ya dade a ciki ashe wanka ya yi ya saka jallabiya 52 Baki Biyu Θ Sameera Mustapha fara tas, ya shigo falon ya yi sallahr Isha'i, har ya idar ya dawo ya zauna ya sani a gaba yana kallona, komawa na yi kamar wata 'yar kankanuwar yarinya na tsugunna kaina a guiwa ina kuka, a hankali tare da ajiyar zuciya. Waya na ji yana yi da Alhajinsa, bayan sun gaisa na ji ya ce, "Eh, ta iso tuntuni, ok, gata ya mike ya nufo ni, ya dan rankafo ya ce gashi Alhaji na

Chapter 3 of 8