Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
2 / 8
garin nan ba ne, ya na iya, dole na hakura na rika fada masa hanyar da zai bi. Muna isa ban bari ya tsaya ba na bude kofa, ina kallonsa ta wutsiyar idona murmushi yake yi yana girgiza kansa, ban jira Gwaggo ba na fita kira na ta yi tana cewa kin ko dauko ledar kayan nan? Gabana ne ya fadi, kwarai naji haushin kaina, na kuwa manta dashi a gida, dubara ce ta fado min na rika yi mata magana ina sakin murmushi, Gwaggo mu bar ma kayan daga baya na kawo..." Amir ya katse min maganar da nake yi, ya ce ki zo muje mu dauko tun da na lura ba nisa da gida, haka kuwa maza ki je ku dauko ni na karasa ciki mu gaisa, uwar mantuwa. Tana maganar tana tafiya zuwa cikin gidan, wayancewa nayi na kauda bacin raina na shige bayan motar na zauna, dama an ce idan ka ga fada zai fi karfinka to sai ka maida shi wasa. Ina sauraron inga mun tafi, amma sai na ji 18 Baki Biyu shiru, na Sameera Mustapha: gano abinda yake nufi, bana son in yi masa magana gashi har lokacin sallar La'asar na gabatowa, don haka dole na fito na shiga gaban motar, a take ya tada muka fara tafiya, shin wai me ke damun mutumin nan? Tafiya yake a hankali sai ka ce yana jin tsoron hanyar, tsaki na buga na ce, aikin banza, magana naji ya yi a bazata da wa ki ke tsaki? Matse bakina nayi tare da bata fuska ban ce komai ba, ya ci gaba da tukin kamar dai yadda ya fara, ji nake kamar in bude motar in fita wallahi..... ya tsinka min tunani da ya ce, baby ni fa har yanzu ina kan bakana akan ina sonki! Ya dube ni, ni kuma na juya masa keya, ya ci gaba, kuma aurenki nake son yi...." Na yi saurin tsaida zancen da yake yi cike da tsiwa na ce, kada ka fara ba zan iya auren ka ba, saboda mene? Ya yi saurin fadan hakan, saboda bani sonka kuma baka kai matsayin da zan aure ka ba, nima nayi saurin bashi amsa, da alama maganar ta duke shi, sai dai bai kara cewa komai ba, sannan ya soma tafiya cikin gudugudu, har muka kai gida na dauko ya mai do ni bamu sake wani zancen ba, a raina kuwa wani irin dadi naji kamar in yi tsalle, zan fita na ji kofar a rufe, na sha jinin jikina ba tare da na dubi inda yake ba, na ce, zan fita. Kallona yake yi sosai na ji a jikina kuma ina kallon sa ta wutsiyar idona, ajiyar zuciya ya yi 19 Baki Bıyu Sameera Mustapha: ya ce. kina nufin ban kai matsayin da za ki so ni ba? Ya yı tambayar a kuntace da wata irin murya mai zati, dadi ne ya kama ni, da na ji irin bakin cikin da na sa shi, na amsa shi cike da isa na ce, "Eh haka ne, ni ka ganni nan bana burin auren irinka, ko zanyi auren da manya zan yi don kaga ko aure na na farko ai ba irin ka na aura ba, mai mata na aura, ni na fi son cikakken namiji da yasan hakkin aure, wanda ya kuma taba sanin daci da dadin zaman auren kai din nan kafi dacewa da macen da bata san zamantakewar aure ba, budurwa irin ka, dariya ya saki a tunanina ina zaton zan bata masa ne, ashe ni aikin banza nake yi, ya ce to idan Allah yasa na aure ki fa? Ya yi tambayar a kasaitance, nima murmushin na saki, don na lura idan ban yi masa hakan ba zai manna min karamin hauka, to wannan kuma hukunci ne na Allah babu mai ja dashi, kin fadi gaskiya yarinya, bari in barki sai anjima, idan na dawo daukar ku, da na ji ya bude motar ban wani tsaya na saurari karshen maganar tasa ba, na shigewata gidan Aisha. Na isa ciki na samu an taru sosai, nesa na samu wuri na zauna bayan na gaisa da jama'ar da na sani, sama-sama, nayi shiru ina tunani, yadda muka yi da Amir. Aisha ce ta karaso guna, ke me ya same ki haka ne, kin yi sanyi? Bayan ta kuma Amina ce, Halima na can na 20 Baki Biyu Θ Sameera Mustapha: neman ki ajiyar zuciya nayi na ce, himm, ku bari kawai menene bai faru ba ma, ku bari in baku labari, dama ni ba sallah nake yi ba, don haka na záuna in fada musu labarin tun farko irin soyayyar da muyka yi da shi sai dai ban fadı irin sonsa da burge ni da yake yi ba, a wancan lokacin bar wannan a raina. Na bar shi a matsayin sirrina, ni kadai. Amina ta jinjina kai lallai 'yar uwa kinyi advanture da yawa, dan tarihinki baki daya yadda ki ka san fim, to ke ki aure shi mana! Na shiga girgiza kaina ba zan taba iya aurensa ba, mutumin da ya daga hannu zai daki mahaifina? Allah ya tsare ni mahaifiyarsa kuwa bani da makiyiya irinta, don ta nuna sam bata kaunar jininmu. Yanzu haka fa ko ga mu ga maciji ba ma yi da ita, ajiyar zuciya Aisha tayi, Allah ya sauwake. A lokacin Anti Sakina ta iso gun mu ta ce, ana can fa ana neman mai jego mutane na son tafiya gashi ko hoto ba a yi ba, nan muka mike baki dayan mu muka shiga mutane. Sai bayan Isha'i Amir ya zo daukar mu. A gida ma haka ya takura min, ina zaune a daki yau ko hira ban yi ba na yi bacci. Washegari da karfe tara Gwaggo ke ce min zata Gusau tare da Amir, sai jibi za su dawo. Jikina ya yi sanyi sosai, na kasa tambayarta dalilin tafiyar tata. Dama ita bata jin nisan garin nan ta maida shi 21 Bakı Siyu Sameera Mustapha: kamar daga Kaduna zuwa Zaria, sam ban kawo wani abu na tsakanina da shi ba, ban ma ganshi ba suka wuce. Kwanan Gwaggo uku a Gusau ita da ta се kwana daya zata yi, kullum kuma muna waya sai dai ban tambayarta dalilin zamanta can. Sai da ta kwana biyar da daddare na buga mata waya, bata dauka ba, ban sa komai a raina ba, a tunanina kila tayi bacci tunda wajajen karfe tara ne na dare. Washegari na sake nemanta da safe na се, Gwaggo yaushe za ki dawo ne wai?" "Yar kanwata nima kaina ina kewarki, ko za ki sa direba ya kawo ki ne?" Na yi shiru ina tunani, ban jin zan iya zuwa Gusau a wannan lokacin ba, yadda a koda yaushe Baba maganarsa ba ta wuce ta in fitar da miji in yi aure, tun baba bata tanka min gashi itama ta soma takanas ta bugo min waya don haka na ce, ba sai ma na zo din ba zan hakura har ki dawo yaushe za ki dawo? Insha Allahu ranar sati zan shigo 'yar kanwata." Ba mu jima muna hira ba muka yi sallama, daga nan na shirya na je gidan su ya Saidu, nayi sa'a yana gida kuwa muka zauna sai hira muke yi cike da nishadi har na manta kewar da nake tare da ita, da na tashi tafiya Umma ta ce lallai 22 Baki Biyu Sameera Mustapha: sai dai in kwana tuna Gwaggo bata nan ban musa ba kuwa, ba abunda nake so in ga ranar da Umma da Baba za su hadu. Tare muka kwana a daki daya har take bani shawarar in fidda miji in yi aure, na ce da ita insha Allahu komai ya zo karshe zan fidda miki in yi aure. Da safe tare muka karya da ya Saidu yake fada wa Umma Baba ya kira shi jiya ya ce yaje gobe, ta saki fuska ta ce Allah ya kai mu goben. Bayan La'asar na ce zan koma gidan na ga Amir tsaye a gefen motarsa ya latsar wayarsa, ya Sa'idu kuwa sai da ya kai daidai gun sa sannan ya tsaya abun mamaki cike da murna suka rungume junansu suna dariya tare da tafa hannu, zare ido nayi ina kallonsu cike da tambaya a tattare da ni, menene dangantakar su? Ina suka san junansu? Dama sun san juna? Tambayar da na jerowa kaina kenan ikon Allah na fada a baiyane shi ya tunasar da su ina tsaye a kusa da su. Dama kasan mutan gidan nan? Amir ya yi tambayar, labarin da na baka wata uku da suka wuce ai wannan ita ce yarinyar da a sanadin ta na hadu da biological father na, ok, dama sune? Kana nufin Baba Sabi'u mahaifinka ne? of course ya fada, ya dube ni dama kuma kun hada dangantaka tsakaninku? Kwarai da gaske ai mahaifiyarta uwa ce a gun mahaifina saboda 23 Baki Biyu Sameera Mustapha: Inna yake kiranta, what a co-incidence this world is a very small place. Ni kam gajiya nąyi da saurarernsu nayi shigewata cikin gida duk da ina son jin labarin da suke wa junansu, ba su shigo ba sai bayan Isha'i ashe fita suka yi, Sa'idu shi ya fara cegowa a cewarsa Amir na waya a waje, kin san kuwa Amir shine babban abokina? Na ware ido ina kallonsa. Tun muna matasa muka hadu a America tare muka fara karatu, kuma tare aka kore mu saboda irin halaye na kuruciya da muka sa kanmu kin san halin kuruciya yana dariya yana bani labari, lokacin da taba bani labari soyayyar da kuka yi tsakanin ku har da rabuwar ku, kaina a kasa yake a wannan lokacin, ya ci gaba da cewa kin san yadda Amir ke son ki kuwa? Ya yi tambayar yana kallon fuskata, wallahi da na san ke ce da tuni na hada ku, hawayen da ya gani a fuskata yasa ya dakatar da abinda yake fadi na ce to ni bana son sa yaya don Allah mu dai na wannan maganar don bana bukatarta, sukut yake kallona to Allah ya sauwake, ya fada tare da mikewa, ni zan wuce dare na yi da sauri na goge fuska ta haba dai ya Sa'id karfe tara fa, sorry Sister akwai inda zamu ne da abokin nawa kila in shigo nan kafin in wuce Gusau saboda tare da abokina zamu wuce. Bayan na dawo daga rakiyar Sa'id na kulle ko 24 Baki Biyu Sameera ina tunanin wannan al'amari. Babu yadda Allah ba ya hukunta al'amari, gashi dai Ya Sa'id ya zama dan uwana, na jini ga kuma Amir ya zama shi ne babban aboki gun Ya Sa'idu. Da irc-iren tunanin da bacci ya dauke ni kenan. Ranar sati da karfe sha biyu saura, Gwaggo ta dawo daga Gusau, ni kam ban sani ba don barci nake yi. Sai da biyu saura na tashi na, shige bayi nayi wanka tare da alwala, tunda na tashi yau naji bana jin dadin jikina, duk a sanyaye nake ko baccin da nayi ne? na tambayi kaina, da na idar da Sallah na saka jallabiyanta baka ce mai duwatsu, shiga ta falo na lura da alamar baki a gidan kayan goro ne da su cigum, sweet, biscuit kwali-kwali sai a lokacin na lura da Gwaggo zaune a kan sallaya tana lazimi da gudu na isa gun ta ina murna itama rungumu ni tayi cike da kulawa, kai Gwaggo shi ne ki ka je ki ka yi zaman ki to ba gani na dawo da abun alheri ba, na dube ta cikin ido na ce kwarai da gaske dawowarki a waraka ce a gare ni a yau ban san dalili ba, duk jikina a mace na rasa me ke damun jikina, ba dai tyford dina zai tashi ba, ke ba wani tyford igiyar aure ce ta hau kanki 'yar kanwata! Aure na fada tare da zaro idanuna waye, gabana kuwa saboda tsananin bugawa da yake sai da na dafe shi da hannaye, na baki daya. Aure! Na 25 Bakı Biyu Sameera Mustapha: sake maimaita kalmar, Gwaggo ta ci gaba da cewa aure kuwa yau din nan aka daura shi da Mas'ud, Gwaggo ina fata ba zolaya ta kike yi ba, kin ga yanayin zolaya a tare da ni ne? ko na taba yi maki wasa irin wannan? Hawaye ne ke ambaliya a fuskata, na ci gaba da kallon fuskar Gwaggo ina son in gano in da zancen ta ke fuskanta, amma sai naga babu wasa a tare da ita, kai na na kwantar a kan cinyarta ina kuka wiwi, ina fadin kai Gwaggo ya zaku yi min haka? Me yasa ba za ku bani 'yancin da Allah (S.W.A) ya bani ba, an ki a baki 'yancin yanzu da aka daura sai ki dauri aniyar kwatarwa kanki wani 'yancin, ki nemi mijin da aka daura miki ki ce ya sake ki. Mikewa tayi tana ci gaba da fada, ta inda take shiga ba nan take fita ba, a nan na ci kuka har na gode Allah, a take kuma sanyin da nake ji ya dawo. Da kyar na koma dakina, bana son in yi ma Gwaggo taurin kai, na riga da nayi alkawarin bani kara bari in yi fushi da ita akan wani abu don haka bayan na idar da Sallah La'asar na fito falo ya Sa'idu na iske tare da Gwaggo suna hira, ya kallo ni ya na murmushi ya ce, amarya kenan kukan da na saki yasa ya daina zolayata, na isa gun Gwaggo nasa kaina a kafadarta ina rera kukana a hankali. Ya Sa'idu ya shiga yi min nasiha da ban hakuri, a raina na ce, ko ba ka fada ba hakuri ai ya zama dole, tun Gwaggo na share 26 Baki Biyu Θ Sameera ni har ta soma lallashi, haba 'yar kanwata ni fa dadi na da ke ba ki jin lallashi." Har dare abu daya nake yi akan dole Gwaggo ta matsa min nake cin abinci haka na daure nake taunawa. Bari jima ba kuwa na dawo da shi baki daya duk na amayar da abincin, Gwaggo bata damu ba sai dai zafin da taji jikina ya dauka. Washegari şai da muka je asibiti gashi duk tsawon daren amai nake yi, don haka Likitan ya ce za'a sa min ruwa ko da na wunin rannan ne, tuni bacci ya dauke ni a lokacin da aka sa min ruwan. Can cikin bacci na ji Gwaggo na waya, a'a Mas'ud da sauki, ta samu sauki bacci take yi yanzu sai da ta gama wayar sannan na bude idona, cikin yardar Allah kuwa na samu sauki aka sallame mu, an bani magunguna zan dawo allura na kwana uku, kai wannan wace irin rayuwa се. Cikin kwana biyu na zabge na rame, Gwaggo dai kullum in ban da lallashi babu abinda take yi. Washe gari tunda safe Baba da Babah suka zo Kaduna na tabbata, Gwaggo ce ta yi masu magana, suna zaune a falo Gwaggo ke kwala min kira, na fito gabana ke faduwa don fuskar Baba da na gani babu sassauci, naje dab da Gwaggo na zauna don gudun kada Baba ya duke ni, ya ce ke wai yarinyar nan me ki ka maida mu, 27 Baki Bıyu Θ Sameera Mustapha: matanen banza ko? To baki isa ba wallahi ba zan ja wata doguwar magana da ke ba zan bata miki idan har ki nemi bata min, saboda na lura ke so ki ke yi ki watsa mana kasa a ido....sallamar Haj. Maryam ta katse masa hanzarinsa. Ta iso ciki tana duban inda Baba yake, nan da nan shima Baba ya maida kallonsa akan ta ya furta a hankali Maryam! Ta amsa tana zama kusa da Gwaggo, falon ya yi tsit na lura Babah ta gano ta don haka sai ta tsinka shirun ta ce, Allah yau ya hada mu Maryam, ina kwana? Ta amsa da muryar nan ta ta, ta sanyi, suka kuma gaisa da Baba, Haj. Maryam ta ce, haba don Allah ya zaku rika yi mata fada haka bayan ba laifin ta ba ne, babba ta ce ya za ki ce ba laifinta ba a yau dinnan da muka lisafa shekarun ta kusan uku kenan rabon ta da aure, ta dube ni a'a baki kyauta ba 'yar nan duk da aure lokaci ne, nan fa Baba ya amshe maganar ya ci gaba da fada ta inda yake shiga ba nan yake fita ba, tun ina kuka har na daina don ya dawo nasiha kuma, haba Dayyiba ina so ki yarda da kaddara, ki dauka kaddarar aure ne ya same ki ki mika wuya gun Allah ya yi miki sakayya. Nasihar da Baba ya shige ni sosai, sai a lokacin na fara tunanin to, waye mijin? Dan wanne gari ne? menene sunansa tukunna? Duk kaina nake tambaya, kuma babu mai amsa min 28 Baki Biyu Sameera su sai na tambaya amma sai na yi gum da bakina. ina sauraren nasihar su. Baki dayan su suke magana kai yanzu ma lallashi aka koma daga haka kuma Haj. Maryam ta rika zaya ne min irin kuncin rayuwar da ta shiga, gashi kuma a yau ya wuce ya zama labari, Baba shima na shi ya dan fada har a karshe ya ce. Dayyiba don girman Allah kiyi hakuri ki rike auren ki ba don hali na ba don Allah na ce, tausayin mahaifina ya kama ni, haushin kaina na fara ji da gaske ne dai abinda suke cewa ni ce zakka a cikin 'ya'yansu. na shiga uku, astagfirullah na fara ambato a cikin zuciyata tare da neman gafarar su. Baki dayansu, abin dadi na shine duk sun yafe min, na kuma dauki alkawarin zaman aure. Wunin ranar Sallah nake ta yi ina neman gafarar Allah, ina neman sassauci daga gare shi. Tun daga ranar ban fasa ba, kwanansu Babah biyu har sai da ta leka gidan Haj. Maryam abun gwanin sha'awa, sun kulla kawance na aminci tsakaninsu. Na sami kusan sati biyu a gida ni ban ga mijin ba, ba kuma ban damu in san shi din ba, ni dai na daukar wa kaina alkawarin yin biyayya ga Iyayena da kuma yiwa mijin biyayya. Gwaggo ce ta tsinka min tunani ta ce, sai ki shirya gobe zaki wuce dubai gun mijinki, gaba na ne ya fadi ban ma san yadda aka yi na kasa amsa wa Bak Biyu Sameera Mustapha: Gwaggo ba sai da na ji ta ce, ba da ke nake ba ko ba ki ji ba, da sauri na ce na ji Gwaggo sai Allah ya kai mu goben. Ban tashi shiri ba sai da daddare, akwati daya tal na shirya sai kit da hand bag din da na rike. Washegari da karfe biyar muka wuce Abuja da yake ta can zamu tashi, ni an bar ni a duhu, ko a dan yi min bayanin waye shi, na lura mutumin zai yi girman kai, ace sati biyu da aure bai taba nemana ba balle ma in ce na taba jin muryarsa, da alama ikonsa zai yi yawa. Ni dai ina neman tsari da sharrin wannan aure. Sai karfe sha biyu na dare muka yi boarder a Egypt Air, karfe sha biyu da minti ashirin muka tashi. ** WANENE KUMA MAS'UD? Mas'ud Mohammad Shinkafi, wanda aka fi sani da Amir, sanadin an rada masa sunan mahaifin Haj. Basira shi yasa tayi masa lakani da Amir. Shi dai Mas'ud ya tashi yaro ne da baya jin magana da ya zama samari kuwa tantiri ya zama saboda da ya gama secondary sch. Ma da daurewar gindin mahaifiyarsa aka tura shi America. Haj. Basira tana bala'in ji da shi, kun san ana 20 Baki Biyu Sameera Mustapha: cewa tangararen yaro ko mutum ya fi shiga rai, don haka Haj. Basira bata taba yarda da duk wani abu na rashin ji da ake cewa yana da shi da ya ke duk a cikin 'ya'yanta sun fi shakuwa. An sha kawo kararsa gun ta na irin ta'asa da yake aikatawa, ga yaran gari sai ta auna shi da sharri ne aka kulla masa. Mahaifinsa kuwa ba su taba shiri ba saboda hali irin nasa, wani lokacin ma sai ya kwana uku ba a gida ba, akwai sanda ma aka taba daure shi saboda yawon dare da shi da abokansa, a cewar su party suka fito. Tafiyarsa America kuwa a nan ya hadu da Sa'idu Balarabe, shima din ba karami ba ne gun rashin ji. Dalilin korar su kuma da aka yi daga America shine sai da kwaya da wiwi da suka sa kansu, sai da suka sami sati biyu a prison sannan aka sa su jirgi aka dawo da su gida Nigeria. Mahaifin Mas'ud ransa ya 6aci sosai, saboda yadda ya maida kansa, hatta askin kansa dabanne, kan ya cika da gashi anyi kitso wani wurin kuwa an aske shi ga shan wiwi, shi saukin sa baya shan kwaya, don Alh. Muhammad sai da ya kai shi sicartrac aka kwada shi tas. Babu abinda yake sha sai wiwi sai dai inda abun yake da sauki ba wai ya cika sha ba ne, amma akwai shan sigari sosai a tare dashi. Daga karshe dai dole ya maida shi (A.B.U Zaria), nan ma shiriritar suka sa a gaba, don a 31 Bakı Biyu Θ Sameera Mustapha: nan suka Kara haduwa da Sa'idu aka ci gaba da shakiyanci. Ta bangaren mata kuwa, sai dai su bi Mas'ud don bai damu da su ba, har abokansa suka fara zargin ko shi dan ludu ne, abin kuwa ba haka ba ne, shi ne dai baya ra'ayin mace a wannan lokacin. Business admin yake karantawa, maimakon ya gama a shekara hudu a'a sai da ya shekara bakwai sannan ya gama, kai shiririta irin ta Mas'ud sai addu'a. A lokacin da zai gama ne ya soma son Dayyiba, ba don komai ba sai don idaniyarta, ya rasa abun da yasa yake son idanuwan Dayiba, suna yi masa kama da na 'yan Chainise, abu kamar wasa sonta ya yi masa yawa a ransa, sai dai bai iya fada mata ba saboda a lokacin 'yar Karamar yarinya ce dole ma ya daina tunanin ya fada mata don yasan 6ata lokacinsa yake yi, mahaifiyarsa yake tsoro bata taba son jin koda sunan mahaifin Dayyiba so da yawa idan ta zauna tana yi masa zancen su sai ya rasa laifin su. Ya kan biye mata ne don ya lura babu mai mara mata baya a 'ya'yanta sai shi, amma idan ta tura shi yi masu wani abu bai taba gwada yi ba. Ana cikin haka ne ya fara zuwa Kaduna yana buga polo ball, wasan nan ta hawa doki ana buga kwallo da sanda. Ga shi dama a nan Sa'idu yake, don haka bai da matsalar gun zama, ya kan dauki 32 Baki Biyu Sam lokaci mai tsawo a Kaduna wurin wasa a cewarsa lesson yake dauka, mahaifinsa kuwa ba yadda ya iya da shi, addu'a kawai yake masa, Allah ya shirya shi. Mas'ud bai taba damuwa da arzikin da yaba yayinsa, Idris shine mai kula da duk wani dawainiyar mahaifinsu, anan Zamfara zuwa Sokoto sai Tahir da shi kuma dama Allah ya yi maşa goshin arziki. Tunda kuma yake bai taba rokonsu abun hannunsu ba, duk da ba wai suna nuna masa halin komai ba ne shi dai ne halinsa yake haka. Abin su bai taba tsone masa ido ba, so da yawa mahaifinsu na yi masa kwatanci da su amma sai ya yi murmushi ya ce, Baba ai kowa da irin arzikinsa, nima zan samu ne idan nima ina da rabo, ya kan kira shi mara zuciya sai dai bai taba damunsa ba, shi dai ya fi son rayuwa mai sauki. A nan Kaduna ne aka fara tura shi Dubai, da yake suma suna son duk wani wasa da ya kasance da Doki ake yin sa. Da ya dawo hutun sati ne, ya samu Dayyiba na S.S.1 ta girma, kyanta ya karu, yana yi mata son zuciya daya ne, da ya furta mata kuma ta burge shi tayi saurin amince masa, duk da akwai rashin wayewa a tare da ita, amma tayi masa daidai sun fara soyayya a boye shi babu abinda ke damunsa idan mahaifiyarsa Haj. Basira ta gano akwai soyayya tsakaninsa da Dayyiba, sai kuma gashi a daidai 33 Bakı Biyu Sameera Mustapha: lokacin suka sami matsala da ita, ya lura tana da rashin kunya, ya kuma aikata abinda bai taba tunanin aikata shi a rayuwarsa ba, da ya daga hannu zai duki Mal. Sabi'u, tabbas yasan yana da rashin kunya da tsokana da shiga abinda bai shafe shi ba, sai dai a gaskiya tsakaninsa da sa'an sa yake wannan baya yi da manya, amma a lokacin da yake bacin zuciya da rufewar ido gashi dama sai da ya sha wiwi sannan hakan ta faru, sai da ya aikata wannan abu ne da hankalinsa ya dawo jikinsa ya yi bakin cikin abinda ya aikata, har ta kai Haj. Basira ta kore su sanadin sa, sam wannan abu bai burge shi ba a ranar ma bai kwana a gidan ba, wiwi kuwa ya sha ta har ta tashi halaka shi. Washegari don hankalinsa ya dawo jikinsa ya koma gida, kai tsaye sashen Mal. Sabi'u ya wuce amma sai yaga sun tashi, gun Haj. Basira ya wuce yana yi mata tambaya, Mama ina su Mal. Sabi'u? ta saki fuskarta ta ce, meye ruwanka da su, da zaka zo kana min zancen su, ko sallama ba ka yi ba balle gaisuwa, ya sami guri ya zauna ya ce, Mama kina nufin kin kore su? Ta washe baki tana dariya, ai kayi min daidai yaro na kasan tun yaushe nake son su bar gidannan, gashi yanzu a sanadin rashin mutuncin da ka yi masu sun bar יי gidan a saukake, yaro ka biya Mamanka..." mikewar da ya yi tasa ta bar maganar da take yi, 34 Baki Biyu Sameera Mustapha: ransa ya yi baki ya rasa abinda ke yi masa dadi, kai! Ta fada a tsorace, me ke damunka ne wai? Idanunsa jajir kamar gauta ya kai hannunsa biyu kansa ya koma ya zauna. Shin me ke damunka ne ina tambayarka dan Mama, (haka take kiransa wata rana saboda irin shakuwar da ke tsakaninsu har dai idan ya dadada mata rai). Huci yake yi kamar zaki, nan da nan ta shiga taitayinta batą taba ganinshi cikin yanayi irin wannan ba, ta matsa dab dashi ta ce, shin kana da lafiya kuwa? Ta kai hannunta kan goshinsa, babu alamun zafi sai zufa. Shiru tayi tana karantar halin da yake ciki, Mama ya fada ta dube shi, ina shan wiwi ta zaro ido, ban gane ba ta fada muryarta na rawa, kana shan wiwi haba dan Mama yaushe ka fara?" Yana girgiza kansa ban sani ba I can tell na dade ina sha Mama, ya riko hannayenta duka biyun Mama ina son in bari ya ya zan yi? Tausayinsa ya kama ta, itama ta rike shi kam ta ce, kayi niyya dan Mama a zuciyarka za ka daina da yardar Allah, Mama saboda ita na aikata wannan mugun abu ga Mal. Sabi'u, ba da son raina ba, mikewa tayi tana harararsa, ai dama kana da na sanin abinda kayi wa Mal. Sabi'u ne? idan

Chapter 2 of 8