Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
6 / 8
Basira da ba zata matsa min ba, shi ya tsinka min tunanina da naji ya riko hannuna da ke kan fuskata ya ce, come on Smiley, kukan ya isa haka, kina wahalar da kanki da yawa, sam mutum in nan bai da kunya, kunya dai bai santa ba, a gaban Gwaggo fa yake min haka, babu yadda zanyi ni kuma in hana shi abunda yake yi, don kada Gwaggo ta kara jin haushina, karshe ma rungumo ni ya yi yana lallashina kamar wata 'yar shekaru biyar, shafa bayana yake yi, ai ke ki ka ja me ya kai ki tunanin zubar da ciki? Gwaggo ta kama hanyar daki tana cewa, zan shiga ciki Mas'ud, Allah ya tsare, sai mun yi yawa." Ba ta jira jin abinda zai ce ba, tayi shigowarta daki, tana shigewa yana lalubo bakina ya soma aikin nasa, ban ga alamun yana son bari ba gashi idan yana kissing dina sai ya rika kara, a hankali na cije shi a harshe, da sauri ya dube ni cikin ido ya ce, lafiya? Idonsa sun yi jajir na marairaice a shagwabe na ce, amai zan yi, ki yi mana ya fada yana son ci gaba, na dan janye kaina, nan fa gidan Gwaggo ne don Allah kayi hakuri, zo muje sashen..." ban bari ya karasa ba na maida bakina cikin nasa na riga na san in dai ba minti goma zuwa sha biyar ya samu 87 Baki Biyu Θ Sameera Mustapha: ba ba zai kyale ni ba, ai kuwa sai da ya cika adadin lokacin sannan ya rabu dani, ashe baby kin fara sanin halina, that is good, zo muje gun mota ki karbo ma Gwaggo tsaraba."Mun isa gun motar yana rike da hannuna, ya ce da direba ya bude but, ni in rasa direba nawa ne da Mas'ud kullum sabuwar fuska zaka gani, kwalayen drinks ne da su kayan shayi na lura babyna na ciki drinks yake so ko? Ya yi tambayar yana kai hannunsa kan cikina, shi wai ba san nan ba irin Turai ba ne da ake baiyana sirrin ma'aurata? Gashi da nacin tsiya idan ya yi niyar yin abu sai ya yi shi kila idan bai yi ba mutuwa zai yi. Agogon hannunsa ya duba ya ce, it's time, zan wuce ki kula da kanki, ban san me ya kai ni ce masa ba za ka bari sai da safe ba? Murmushi ya saki, dole ne in tafi saboda gobe da karfe takwas na safen London ina da meeting kafin lokacin nake so in isa, Jirgin mu zai tashi da karfe dayan dare na yau, yanzu Abuja zan wuce insha Allahu." Ajiyar zuciya nayi na ce, "To Allah ya kai ka lafiya." Rungume ni ya yi, na gode da addu'arki, a zahiri kamar mutumin kwarai a badini kuwa Allah kadai ya sani, sai da ya wuce sannan na shiga cikin gida, tsoron hada ido nake yi da Gwaggo, don nasan fushi take yi da ni. Tana kwance a kan gado da alama ta fara bacci, na 88 Baki Biyu Sameera Mustapha: kashe wuta nima na hau gado har zan kwanta, na tuna ban yi sallah ba, saukowa nayi na shiga toilet nayi alwala na fito nayi sallah. Washegari na lura Gwaggo fa fushi take yi dani sosai, bata dauki abun da sauki ba, don haka na rika shisshige mata, sai dai ta ki sakin jiki dani. Na kira su Amina na sanar dasu na dawo, ihu sukai tayi suka ce suna nan zuwa. Kamar hadin baki, tare suka shigo gidan cike da murna, muka rungume juna, kowace da 'ya'yanta, muka shige daki bayan sun gaisa da Gwaggo mun shiga Aisha ta ce, Amina gaskiya ki ka fada, Dayyiba ta zama 'yar can, na harari Amina, me ki ka ce na yi kuma?" Ta yi fara'a ta ce, mene ma ban fada ba, Aisha fada mata mana ke ba komai ta ce ba illa irin sha'awar zaman da ku ke yi da maigidan naki, na ja tsaki, ni na zata wani abun ne ma, kin ga yadda ki ka zama kuwa 'yar uwa? Kin yi kyau kamar an canza miki halitta. Kai Aisha bana son sharri, wallahi ba karya na fada ba, Amina ta ce anya wannan kyaun da naga an kara babu bayani? Zan yi magana Asabe ta shigo da kayan ciye-ciye ta ajiye suka yi mata sannu, ita kuma ta gaida su ta fita, ai Aisha na bude kular abinci da yake jallof ce amai ya taso min, da gudu-gudu na isa bayi na amaye da juice din da ke cikina. Sai da suka taimaka min, irin kallon da suke min yasa na 89 Baki Biyu Θ Sameera Mustapha: fashe da kuka. Ikon Allah suka fada baki me akai maki kuma? Na zauna can nesa da abincin ina share kwalla, Amina guda ta saki tana Kyalkyalewa da wata irin dariya na keta, Allah ya kama ki yarinya, Aisha ta ce ciki ne da ke Dayyiba? Kema sai kin tambaya in ga idon wadda ta ce ita ko aure tayi sai ta shekara sannan zata yi ciki, dole na saki murmushi na tuna lokacin da na fadi hakan, Aisha ta yi dariya ta ce, kai na fa tuna haka ki ka ce, to ya aka yi ne? na galla mata harara na ce, ba zan fada ba, 'yan gulma kawai." Nan fa sukai ta tsokanata, share su nayi ban ce komai ba, don ban da bakin magana, tare muka wuni har sai bayan La'asar sannan suka fito za su wuce, yaran su sai wasa suke a tsakar gida, Gwaggo ta ce, mun gode da zumunci da bata nan ma kuna lekowa, Allah ya yi maku albarka, bayan sun wuce na shigo ciki na zauna dab da Gwaggo na ce, kai Gwaggo Allah ba zan kara ba, wauta ce ke damuna, Allah Sarki, wadda aka haifa yau. Ai ban san haka ba, je dai ki halaka kanki da rashin wayau, ke dinnan ke ki ka dauki halin 'yan fari don Nafisa kam ba haka take ba, duk a gidan ku ke ce mai hali haka, ni dai addu'a zan taya ki dashi, Allah ya shirye ki. Tun daga lokacin kuma ta sauka, waya ce ta yi ringing, Gwaggo ta dauka, ta ce, a'a Mas'udu, sannu Mas'udu, ya hanya? An isa 90 Baki Biyu Θ Sameera Mustapha: lafiya?" Da alama ansawa yake yi, ta yi shiru tana saurarensa, can naga ta dube ni, ta ce ban sani ba nima kila wayar bata yi ne, ai kana kira ka ce? Gabana ne ya fara faduwa, tabbas naga kiransa amma mirsisi na ki dauka, ta kara dubana tare da miko min wayar na ansa na sa.a kunnena muryata ciki-ciki na ce, "Hello!" Ya amsa "Kina lafiya?" "Lafiya lau." Na amsa a takaice, hala har yanzu jikinne? A'a yanzu babu abunda ke damunki? Ya tambaya Eh, na fada ya yi shiru ban san abinda ya yi tunani ba, sai kuma ya ce, to sai da safe. Na ce to na kashe, Gwaggo dai na ji na amma bata ce komai ba. Tun da na dawo Kaduna ba inda nake zuwa, ko nan da gidan Anti Badiya Gwaggo ta hana, sai da nayi kwana hudu tukun ta ce muje tare ko awa daya ba mu yi ba muka koma gida, ina ga tun ranar ban kara fita ba, Mas'ud kuwa a kullum sai ya neme ni a waya sau uku a rana wani lokacin da gangan sai in ki dauka. Haka dai rayuwar ta rinka tafiya sama-sama muke dashi, sai da ya sami wata daya da sati daya sannan ya zo. Ina zaune a tsakar gadon dakin da nake duk da ba a dakin nake kwana ba amma kayana na dakin, dakin Gwaggo nake zuwa in yi kwanciyata, jin an taa kofar yasa na kalli kofar in ga mai shigowa. Mas'ud ne ya shigo fuskarsa 91 Ο0 Baki Biyu Sameera Mustapha: cike da fara'a, kasa motsi nayi daga inda nake, naga ya kara kyau sosai yana sanye ne da Kananan kaya a jikinasa, sky blue jeans ne da Тshirt fara tas an yi zane da kalar blue da ja, tayi masa kyau sosai, matsowar da ya yi ya zauna dab da inda nake zaune yasa na dube shi ya ce "Ya ya dai baby?" Ya yi tambayar yana neman taba ni, ba yadda zan yi in hana shi, na rasa dalilin da yasa in dai Mas'ud ya matso jikina, sai jikina ya yi sanyi, duk da kin sa da nake yi a zahiri. Tabbas Mas'ud namiji ne cikakke da zai iya sace zuciyar mace cikin kankanin lokaci, bakinsa da yake kokarin sawa a nawa yasa na dawo daga duniyar tunanin da na shiga, kai mutumin nan akwai iya salo, ga iya wasanni na ma'aurata shi yasa bana shakkun in dan na sassautawa raina muyi zaman aure tsakanina dashi, zan ji dadin rayuwata. Haj. Basira ce ta fado min a raina, kuma tuno zancen da suka yi a kaina da Gwaggo da karfin gaske na janye kaina, me ya faru? Ya yi tambayar ta cikin makoshinsa, don ya riga da ya yi nisa, mikewa nayi niyar yi amma na kasa, saboda rike ni da ya yi, me ki ke nufi ina za ki? Ban yi magana ba amma ina kokarin kwace kaina daga gare shi, babyna nake son in taba, ya fada tare da mikewa tsaye. Haushi ya bani da har kwalla ya cika tab a fuskata, ya saki hannuna ya 92 Baki Biyu 3 Sameera Mustapha: ce wai Dayyiba ya ki ke son in yi ne? Am trying, kin sani kullum kuma ina fada maki how much I love you, ya ki ke so ne? ka rabu da ni, ka sake ni shine abinda nake so. idanunsa a lokacin sukai jajir ya tsaya yana kallona, da alama ya ma rasa abinda zai ce, wannan kalma da ki ka fada saki ba zai taba faruwa ba, don haka na ke baki shawarar ki ma daina wannan tunanin..." ni kuma ba hakan zai sa in so ka ba, fuskata ya tallabo da hannayensa biyu masu taushin gaske ya ce, Dayyiba me zan yi maki ki so ne? wallahi ke kadai nake so a rayuwata, me nayi maki da ba za ki iya yafe min ba? Duk abinda ki ke so Dayyiba ki fada min, I promise, I will do it for you, I love you." Ni kaina nasan hakan, to amma me yasa yake yi min baki biyu ne, idan ina tare dashi sai ya nuna nice abun sonsa, idan yana gun Haj. Basira kuwa sai ya nuna mata ita ce majibincin shi, baki biyun shi ke kashe ni yake hana ni sakewa da shi, ya tsinka min tunanina da ya soma kissing dina ta ko ina a fuskata, har ya koma kan bakina, dole na kyale shi har ya samu natsuwa. Kwankwasa kofar dakin yasa ya sassauta bai iya amsawa ba, ni ce naje gun kofar na bude, Asabe ce ta ce "Sa'idu ne ya zo yana falo." Na amsa to, jikinsa a sanyaye ya iso gun kofar ya се bari in je in ganshi, ya fice ban san lokacin da 93 Baki Biyu Θ Sameera Mustapha wani irin tausayinsa ya kama ni ba, ban san dalilin da yasa nake tausaya masa ba duk lokacin da nasan baya cikin farin ciki. Na tuno irin son da nake yi masa da sai dai wani lokacin idona na tuna irin zaman da muka yi a Dubai, ina jin dadi a raina to kodai har yanzu ina sonsa ne? a sanyaye na dauki abaya na fita da nufin in gaida Sa'idu. Kwana uku ya yi ya koma London, ya ce min wani business ne ya samu a can da 'yan shelf suma mai ne sana'ar su, bai takura min ba sai dai wasanni da ya kasance tsakaninmu sosai. Cikina na da wata biyar, duk wani ciwo na rabu dashi, ji na nake tamkar ba mai juna biyu ba, gashi har ya fito ga cin tsiya komai ci nake yi, a wuni sai in yi ci shidda ba abin mamaki ba ne. shi yasa nayi kiba sosai, muna kuma dasawa da Mas'ud tun ina kin sakewa dashi har takai ma na fara nemansa a waya, mu yi hira. Idan ya yi tafiya yakan dauki lokaci bai zo ba, idan ma zuwan ya yi bai wuce kwana uku zuwa biyar ya koma, idan kuwa ya yi sati to Gusau ya je. Kirikiri Gwaggo ta hana ni zuwa Gusau, ba ma Gusau ba ko nan cikin Kaduna ba ta bari in je ko'ina, don haka kullum ina gida in dai ba awo za ni asibiti ba. Haka rayuwa tai ta tafiya har ciki ya kai wata 94 Baki Biyu Sameera Mustapha: tara, da nakuda ta tashi kuwa cikin dare wajajen karfe goma sha biyu saura, dole muka shirya zuwa asibiti. Muna isa da minti talatin da shidda na haihu, wai na ji abunda mata ke ji, Allah ya raya mana 'ya'yanmu, yasa musu albarka, amin. An sami da namiji fari sol da shi. Washegari tun safe aka sallame ni don Alhamdulillahi da ni da baby lafiya lau, Gwaggo kuwa murna kamar zata yi me, dakin da nake aka maida dakin jegon, nan da nan Gwaggo ta rika kira tana sanar da mutane abin alherin da ya faru. Nan da nan 'yan barka aka fara tururuwa shi kuwa gogan nawa karfe goma na dare ya iso Abuja, ya bari sai da safe amma ya ki ya biyo dare ya iso sha biyu na daren, lokacin ina bacci ga baby gefe na, shima baccin yake yi. Kai na da na ji ana shafa min yasa na bude idona a hankali, sun yi jajir saboda bacci nake yi mai nauyi, ganinsa gabana yasa na saki fuska ta, ya mike ya zaga daya gefen ya dauki babin yana yi masa addu'a tare da sumbatarsa, kallon su kawai nake yi saboda sha'awar da suka bani, fuskar Mas'ud cike take da murna sosai, a lokacin wani irin sonsa ya murdo ni, har sai da na ji nauyi da muka hada ido da shi, na san ya gano hakan shi ne dalilin zuwa inda nake, rike da jaririn a hannunsa ya riko hannuna yana murzawa, ya ce cike da kulawa, ya jikin ki? Murmushi na saki na 95 Baki Biyu Sameera Mustapha: ce da sauki, sai dai na rasa dalili nauyinsa nake ji, ban san wannan abu ba. Mun dan jima yana nuna min farin cikinsa ya ce, na riga na zabar masa suna, Tahir za a sa masa, hawaye ne ya ciko idona, na ce, hakan ya yi daidai, Allah yasa mahaddacin Alkur'ani ne, wanda kuma zai amfane shi duniya da lahira. Kwanana uku da haihuwa gida ya kara cika da mutanen Gusau, kun san Gwaggo da jama'a, Mas'ud kuwa set na akwati ya yi min har seti biyu, sha biyu kenan baby kuwa set daya, abun dai sai wanda ya gani, zinari kuwa sai da ya saka set hudu har da daimond. Da na yi masa magana sai cewa ya yi ai ban yi maki lefe ba, ni sam na ma manta da lefen. Ranar suna an cika sosai, yaro dai ya ci suna Tahir. Haj. Basira ko kira bata yi ba balle ta zo suna, ban ma sarai ba. Wajajen karfe hudun yamma aka fara lunchen, abin mamaki sai ga Suwaiba, mun rungume junanmu don murna, har tana ce min bana da kirki, na bata hakuri muka yi canjen number waya. Suna kam ya yi armashi sosai, don sai bayan Isha'i aka watse, sai 'yan Gusau ne sukai saura, suma washe gari kowa ya kama gabansa. Mas'ud ya sami kwana uku bayan suna, ya fara shirin tafiya a cewarsa tare zamu tafi, ya sami Gwaggo yana zayyane mata irin tsarin da 96 Baki Biyu Sameera Mustapha: tara, da nakuda ta tashi kuwa cikin dare wajajen karfe goma sha biyu saura, dole muka shirya zuwa asibiti. Muna isa da minti talatin da shidda na haihu, wai na ji abunda mata ke ji, Allah ya raya mana 'ya'yanmu, yasa musu albarka, amin. An sami da namiji fari sol da shi. Washegari tun safe aka sallame ni don Alhamdulillahi da ni da baby lafiya lau, Gwaggo kuwa murna kamar zata yi me, dakin da nake aka maida dakin jegon, nan da nan Gwaggo ta rika kira tana sanar da mutane abin alherin da ya faru. Nan da nan 'yan barka aka fara tururuwa shi kuwa gogan nawa karfe goma na dare ya iso Abuja, ya bari sai da safe amma ya ki ya biyo dare ya iso sha biyu na daren, lokacin ina bacci ga baby gefe na, shima baccin yake yi. Kai na da na ji ana shafa min yasa na bude idona a hankali, sun yi jajir saboda bacci nake yi mai nauyi, ganinsa gabana yasa na saki fuska ta, ya mike ya zaga daya gefen ya dauki babin yana yi masa addu'a tare da sumbatarsa, kallon su kawai nake yi saboda sha'awar da suka bani, fuskar Mas'ud cike take da murna sosai, a lokacin wani irin sonsa ya murdo ni, har sai da na ji nauyi da muka hada ido da shi, na san ya gano hakan shi ne dalilin zuwa inda nake, rike da jaririn a hannunsa ya riko hannuna yana murzawa, ya ce cike da kulawa, ya jikin ki? Murmushi na saki na 95 Baki Biyu Sameera Mustapha: ce da sauki, sai dai na rasa dalili nauyinsa nake ji, ban san wannan abu ba. Mun dan jima yana nuna min farin cikinsa ya ce, na riga na zabar. masa suna, Tahir za a sa masa, hawaye ne ya ciko idona, na ce, hakan ya yi daidai, Allah yasa mahaddacin Alkur'ani ne, wanda kuma zai amfane shi duniya da lahira. Kwanana uku da haihuwa gida ya kara cika da mutanen Gusau, kun san Gwaggo da jama'a, Mas'ud kuwa set na akwati ya yi min har seti biyu, sha biyu kenan baby kuwa set daya, abun dai sai wanda ya gani, zinari kuwa sai da ya saka set hudu har da daimond. Da na yi masa magana sai cewa ya yi ai ban yi maki lefe ba, ni sam na ma manta da lefen. Ranar suna an cika sosai, yaro dai ya ci suna Tahir. Haj. Basira ko kira bata yi ba balle ta zo suna, ban ma sarai ba. Wajajen karfe hudun yamma aka fara lunchen, abin mamaki sai ga Suwaiba, mun rungume junanmu don murna, har tana ce min bana da kirki, na bata hakuri muka yi canjen number waya. Suna kam ya yi armashi sosai, don sai bayan Isha'i aka watse, sai 'yan Gusau ne sukai saura, suma washe gari kowa ya kama gabansa. Mas'ud ya sami kwana uku bayan suna, ya fara shirin tafiya a cewarsa tare zamu tafi, ya sami Gwaggo yana zayyane mata irin tsarin da 96 Baki Biyu Sameera Mustapha: シ ya yi ta ce, sam ba za ayi haka ba, sai dai koda sati hudu ne in samu a gurinta, rai bace ya bar garin ko sallama ba mu yi ba, har sai da ya isa Thailand ya bugo min, kullum muna waya shakuwa kuma na karuwa tsakaninmu. Cikin sati uku da haihuwa mun yi bul-6ul da ni da jariri mun yi kyau sosai, muna shan tattali gun Gwaggo, mun shiga sati na biyar ne Mas'ud ya zo Kaduna, ya tadda ba ma nan mun je asibiti don murna da ta kama ni, har da zazzabi na rika ji, sai karfe biyu saura muka dawo na wuce daki na yi sallah. Tahir na gun Gwaggo, wajajen hudu da minti goma Mas'ud ya shigo gidan. Muna zaune falo, muna hira da Gwaggo ya shigo ido ya kura min direct kuma guna ya nufo, ya zauna daf da ni, Gwaggo da ta ma rasa abinda zata ce, sai cewa ta yi a'a Mas'udu ashe kana gari? Ya amsa Eh, ina nan yau dinnan na shigo. Asabe ta ce, kun je asibiti lafiya waye bai jin dadi? Та се, gata nan mun ce tayi mata kamun karfi, ayya ya nuna tausayawarsa gare ni, tare da kai hannunsa kan goshina, ni dai nauyin Gwaggo yasa komai ma na kasa yi sannu ya fada a raunane, ina Tahir yake ne? Da sauri na mike, ya riko hannuna ina za ki? Kokarin fisge hannuna nake yi, ina kallon inda Gwaggo take, shi kuwa ko a jikinsa, a lokacin Asabe ta shigo falon rike da Tahir, ya saki hannuna ya je ya amshe shi yana washe 97 Sameera Mustapha: baki, inda Gwaggo take zaune nan naje na zauna, bai nuna min ya damu da hakan ba, Tahir har ya yi bacci na amshe shi na kwantar dashi a daki ina jin su suna ta hira da Gwaggo naji dadi da bai biyo ni ba. Bayan mun yi sallah Isha'i ne Gwaggo ta ce, na ga rawar kan mijin nan naki ya yi yawa, don haka ki yi kokarin kame kanki, don ba ki mayi arba'in ba...." Sallamar sa tasa ta daina maganar, mikewa nayi ina gaida shi naje na shirya masa abinci na wuce dakina, kula hira suka yi har Gwaggo ta gaji ta ce da shi zata kulle kofa, to da alama ya gano ta sai dai bai musa ba ya fita. Washegari haka nayi ta doje masa don na lura sosai Gwaggo ta sa mun ido, don haka ranar ma ba mu wani hadu sosai ba, sai lokacin da ya shigo muna sallah isha'i, na gaida na kawo masa abinci, kwanansa biyu kenan yau, ya ce jibi zai wuce bai ma yi maganar komawa ta ba, wannan lokacin. Da karfe sha daya saura na safe ina zaune gaban mirrow ina shafa mai, don a lokacin nayi wanka sai ganinsa nayi kamar wanda aka jeho, duk da na tsargu da irin kallon da yake min sai na dake na ci gaba da abinda nake yi, karasowa ya yi ya sance ribon din da na daure gashina da shi, da yake a kwance gashina yake sai ya zubo ya yi kwance a bayana, na kasa magana don 98 Baki Biyu Θ Sameera Mustapha: wani irin abu da na ji a jikina. Mikewa nayi gabana ya fara faduwa, nayi niyar barin wurin amma na kasa, ya ce kin san fa tunda na zo ba mu gaisa ba, mun gaisa mana, a ina? Ya tambaya, a takaice tare da riko hannuna, jikina tuni ya fara rawa, ni kaina abin na bani mamaki, to ko don yadda Gwaggo ke gaya min in nisance shi necoho! Tsoro na ake ji ne kuma Dayyiba? Na girgiza kaina, a'a ko ba kiyi missing dina ba? Na yi na fada da sauri, to shi ne ki ke guduna? Yana magana ya rungume ni yana shafa ta, ina son kamshin jikinki baby, cikin dubara ya kai bakinsa kan nawa, haba tuni na manta duniyar da nake ciki, sam ban taba sanin nayi missing dinsa ba. A takaice dai ban san lokacin da na bashi hadin kai 100% ba, muka more junanmu. Mun murji juna kamar ba zamu bari ba, sai dai da muka natsu na fara share kwalla, ya rungume ni, lafiya? Ya tambaye ni, Gwaggo ta ce kada in yadda in baka hadin kai, saboda me? Nima ban sani ba, to ke kin san dai ba wani abu ba ne kо? Ya fada yana kara bina da wasanninsa masu tsada. Ba mu gaji da junanmu ba, muka rabu don kiran Sallah azahar da aka yi, sai da na fito na tuna da Tahir, tuni na isa gun Asabe na dubo shi yana nan yana bacci, Gwaggo kuwa dama bata nan gidan Umma taje, mahaifiyar Sa'idu, dama Baki Biyu Sameera Mustapha: sukan yi wa junansu ziyara, Mas'ud kuwa bai wuce kwana hudun ba ya wuce. Kewarsa nake yi sosai, na tsińci kaina da so da Kaunar Mas'ud a raina, har ina manta zargin da nake masa, waya akai-akai muke yi yanzu, ga shakuwa a hankali ya soma shigar mu. Bayan sati biyar da tafiyarsa, ya gaya min zai je India daga nan zai wuce Chaina, akwai business din da yake son ya samu, na shigo da barkono zuwa Kasar London da yake su dama barkono ba nasu bane, basu da shi, na ce dashi zan taya ka addu'a. A wannan lokacin ne Tahir ya soma rashin lafiya, zawo yake yi babu sassauci, wuni daya tal yaro ya zube sai hanci da ya rage masa duk hankalina ya tashi na rasa abinda ke min dadi, muna asibiti gun Likita yana duba shi, na lura Gwaggo tafi ni damuwa, Doctor ya ce, yana son ya duba ruwan nonona, ban jira komai ba na bada aka shiga laboratory, don a duba. Mun samu kusan awa daya sai da aka sa mashi ruwa a gaskiya yana jin jiki sosai. Da Doctor ya shigo ya tambaye ni, Madam kinga period din ki kuwa tunda ki ka haihu? Gabana ne ke faduwa, saboda tsabar fargaban da ke tare dani, ban iya amsawa ba sai girgiza kai da na yi, yaushe ki ka gani? Ya tambaye ni, na kuma cewa a'ah ban gani ba, ya yi dan rubutu ya ce, ki zo office ina so muyi scanning mu gani da alama Baki Biyu Θ Sameera Mustapha: ciki ne da ke, na zaro ido na wanda tuni ya ciko da kwalla, bin Doctor nayi, ai kuwa haka din ne, ciki ne ya tabbata don har ma yana cikin sati na hudu, oh ni na shiga uku da wane ido zan kalli Gwaggo? Doctor kuwa sai da ya yi mata bayani ya kuma ba da shawarar in za abar cikin to a ci gaba da ba Tahir nono saboda ruwan nono na yana da kyau, idan ya bi jikinsa zai warware. Kunyar Gwaggo nake ji don haka na ki sakin jikina. Itama bata ce min komai ba, dole na ajiye kunya gefe guda na zo har inda take zaune na ce, murya ta a sarkake, "Allah ba laifina ba ne." ta dube ni fuskarta a sake, ai laifin nawa ne ko? A'a Gwaggo wallahi shi ne ya bi ya dame ni, ki tambaye shi, in ce masa me don me ya neme ki? To ai ga abinda nake gudu nan ya auku, Allah ya baku lafiya daga ke har dan naki. Gwaggo ai Doctor ya ce, za'a iya cirewa, harara ta dalla min ni wannan ba da bakina ba, sai ki fada ma uban rashin kunyar abinda ya faru, idan ya bada bakin ayi sai ayi, amma ni kam ba da miyaun bakina ba. Haka aka yi, kwananmu hudu a asibiti, Tahir ya dan ji sauki, Gwaggo ta nemi a sallame mu tun da kashinsa ya dan yi daidai, muna komawa gida muka shirya kasuwa zamu a hada masa maganin hausa (gargajiya kenan), an ko hadu 101 Baki Biyu Sameera Mustapha: masa don babu wanda ba a bashi ba, har da na shafawa aka hado masa. Tuni renon Tahir ya koma gun Gwaggo, nima an hada min na sha, duk da bana son maganin haka na

Chapter 6 of 8