Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
1 / 8
An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels BAKI NIYU HNL 3 by samira mustapha HAUSABООK.СOM BAKI BIYU Baki Biyu Sameera Mustapha: HAKKIN MALLAKА (M) Sameera Mastapha GODIYA Ga Allah (S.A.W), da ya bani fasaha da ilimin rubuta wannan littafin, sannan ga Maigidana Alh. Aliyu Sulaiman da ya ba ni goyon bayan rubuta shi, sai ga Iyayena Alh. Mustapha !Haliru Bulasa da kuma mahaifiyata Haj. Fatima Yahaya, Allah ya Kara daukaka ku, amin. TALLAFI Ina godiya gare ki, Halima K/Mashi, da ki ka tallafa min, ki ka ba ni karfin guiwar rubuta wannan littafi, Allah ya kara budi, Allab kuma ya barmu tare, amin summa amin. TUKUICI NE GA Nusaiba Sa'id Moh'd, Najib Sa'id Moh'd, Anisa Sa'id Moh'd, Abduljalil Sa'id Moh'd, Arif Sa'id Moh'd INA KAUNARKU Anti Murja Bande Sokoto, Mama Sa'a O.P.U Hauwa'u Iya (lya mai kosai), Baba Abu BUGAWA A NA'URAR COMPUTER: NAFI'U SALISU 08038981211-07028573535 2 Baki Biyu Sameera Mustapha: ar Sa'id ya mike zai wuce sai na ji HiBaba ya ce, "Sa'id Balarabe Ruma." Ba Sa'id kadai ya saki baki yana kallon Baba ba, har da mu da muke zaune a wurin. Ya aka yi Baba yasan cikakken sunansa? Baba ya ci gaba, "kai dan Asiya ne 'yar gidan Dalhatu?" Da sauri Sa'id ya koma zaune yana duban Baba ya ce, "haka ne, ni ne danta na fari sai dai Alh. Balarabe ba shi ne mahaifina ba, mahaifina ya rasu ban ma san shi ba, don kafin יי Mamanmu ta haife ni ya rasu.' Nan da nan idanun Baba suka juye suka zama jajir, kamar garwashin wuta. Da alama hankalinsa ba ya tare da mu, dukan mu kallonsa muke yi mun kasa cewa komai, Gwaggo ce tayi karfin hali ta ce, hala Baba Nafisa kasan iyayensa? Ajiyar zuciya Baba ya yi kafin ya dago ya dubi Gwaggo ya ce, ba za ki gane ba Hauwa, wadannan sune usulina, ina ga rabona da su tun ina dan shekaru ashirin da haihuwa a duniya. Cike da son jin dalinsa Gwaggo ta ce, ashirin fa ka ce, to menene hujjarka, na yake ma kanka wannan hukuncin? Murmushi ya yi na bata kai zuci ba, ya ce, Baba komai za ku ji komai insha Allahu amma ina son sai na koma Gusau gun babba sannan zan fadı ainihin labari na ya dubi Sa'id ya ce, yaro kana iya tafiya sai mun ne me ka, Sa'id cike da tashin hankali a 3 Baki Biyu Sameera Mustapha: idonsa, ya ce, Baba don girman Allah ina son jin aini irın dagantakar mu tsakaninmu don haka ina neman alfarma nima ina son bin ko rannan da zaka je Gusau sororo baba yake kallonsa, jin bai yi magana ba Gwaggo ta ce, babu damuwa kana iya zuwa amma fa shi gobe zai koma, don haka ma tare za mu wuce a goben, ba damuwa zan iyà bin ku zuwa can sai dai ina son don Allah kuyi min uzuri sai na tashi daga ofis sannan zan kama hanya don Allah kada a fara zacen sai na iso ina so kwarai in san danganta kar mu da ko. Baba ya ce, kada ka damu ba zan fada ba insha Allahu sai ka isa tukunna. A sanyaye kowa ya bar falon don abun akwai daure kai gashi yadda yanayin Baba ya canza fiye da yadda ku ke tsammani, ransa a bace yake sosai duk wani annuri da sakin fuskarsa ya kau lallai da alama babu sauki sai gurin Allah, Allah yasa muji alheri, ashe muna da alaka da su Sa'id shi yasa ake cewa muna kama tabbas nima ina ganin kamar tamu har dai yau dinnan sai na ga sun mafi kama da Baba, ikon Allah wannan abu akwai daure kai. Duk yadda aka yi akwai dangantaka mai karfi tsakanin mu don ban taba zaton zan yi yi saurin sauka da abinda Sa'idu ya yi min ba, amma lokaci daya na ji bana iya ci masa fuska, nan da nan na ji duk na kasa ma ci masa mutuncin da nayi kudurin yi masa, can 4 Baki Biyu 3 Sameera Mustapha: cikin zuciyata yana da wani kima da ba zan kira shi so ba, sai dai na rasa menene wannan abu, to ai koma menene zamu ji in Allah ya kai mu goben. Washegari kuwa tun goma na safe muka bar garin Kaduna zuwa Gusau, sha biyu da rabi muka isa, sai bayan La'asar Sa'id ya iso, sai da muka yi sallah sannan muka zauna falo, mutum biyu ne kadai ba sa nan don su suna da nisa Anti Fiddausi da kuma Anti Badiya, Baba ya fara bamu labarin rayuwarsa a Katsina. ASALIN MALAM Ni cikakken dan usulin Katsina ne, a nan cikin wani gari da ake kira Ruma, mahaifina Alh. Bashir Ruma, da mahaifiyata dukansu 'yan Ruman ne, to da yake ma su 'yan uwan juna ne, kun san Katsinawa da son yi auren gida. Duk da ba tare ake zama ba, sai dai kuma tushen mu daya. Mahaifin mu suna da yawa a gun iyayensu, don mahaifinsu mata hudu ne da shi bayan haka ma akwai wadanda ya aura suka rabu su biyu suna kuma da 'ya'ya da shi. A lokacin ni ina dan aji daya a Primary mahaifina ya rasu.. Ni kadai ke gare shi, gaba da baya sai dai mahaifiyata da ta sake aure a dutsenma, ba ta ma yi tunanin tafiya dani ba saboda tun rasuwar Babana kanina ya dauke ni. Ina nan tare da Baba 5 Baki Biyu Sameera Mustapha: Hassan sai dai sam bana jin dadin gidan saboda yadda matarsa ta gallaza wa rayuwata, saboda tsabar wahala sai da na taba guduwa zuwa gidan wan Babana, da kyar aka maido ni, gashi shi kuwa Baba Hassan ba ya iya hana ta duk abinda tayi shine daidai, ana cikin haka Baba ya bar Ruma ya koma Funtua, da yake shi Manomi ne sosai gashi sana'ar noma ta karbe shi sosai, don haka ne ta cire ni Makaranta baki daya ta ce, ai gara in rika taya Baba Hassan noma, wannan shi ne dalilin da yasa ban yi Makaranta ba, wulakanci da wahalar rayuwa ba wadda ban gani ba. Muna! Muna!! Allah shi ne zai yi min sakayya, amma ta gallazawa rayuwata ta duniya, haka zan ga 'ya'yanta na zuwa Makaranta amma ban da ni. Da na girma lokacin ina da shekaru sha takwas a gun noma babu abinda ban iya ba har na koya tuki da motar Baba Hassan sai dai ko shi bai san na iya ba. Wata rana naje sayen abincin rana da yake akwai gun saidawa a kusa da inda muke aiki, na hadu da Maryam, aiki take yi ma mai abincin Maryam ta shiga raina tunda na aza idona akanta. Ai ban jira wani abu ba nayi mata magana cikin ikon Allah kuwa muka fahimci juna, har na soma zuwa gunta hira, a saukake da na san 'yan uwanta baki daya kuma suka amince 6 Baki Biyu Sameera Mustapha: da ni, da ya ke da kun san muna aure da wuri, da kuma ba Makaranta ake yi ba, iyayenta suka soma yi min zancen aure, ban jira komai ba naje nayi wa Baba Hassan magana. A zahiri ya nuna min farin cikinsa, sai duk jikina ya mutu don na gani a kwayar idonsa kamar abinda bai masa dadi ba. Bayan kwana biyar da yi masa magana ne ina gun aiki Dalhatu dan Baba Hassan na uku ya zo nemana, Baba ne yake kirana a gida kuma ya ce mu zo maza-maza tare da Dalhatu, abun ya bani mamaki da ba za a bari in dawo gida ba, awa nawa ya rage in bar wurin aikin, na tambayi Dalhatu abinda ke faruwa, ya ce Baba Usman ne ya zo ai ban san lokacin da murna ta kama ni ba, duk a cikin su na fi sakewa da shi, don shi ke kwatar min 'yancina idan ma za'a danne. Cike da farin ciki na isa gunsa muna gaisawa, sai dai na lura ransa a bace yake kwarai, ga su muna da mijinta a gefe dukkan su fuskarsu ba kyau, Baba Usman ne ya fara magana, kai da gaske ne ka fitar da wadda ka ke so? na sa kai na kasa ina murmushi, na ce, eh gaskiya ne Baba, to Muna ta ce kun yi maganar Asma'u diyar kanwarta da ita, akan ita ce zaka aura! Kuma ka amince da hakan? Gabana ya na bugawa na daga ido na kalli Inna fuskarta babu kyaun gani ta wani bude 7 Baki Biyu Θ Sameera Mustapha: hanci tana rarraba ido kamar....Baba ya ce kana jin abunda na fada, haka maganar take? Kada ka cuci kanka don ba kowa zai zauna da matar ba sai kai, Baba a gaskiya ni Maryam nake so ba mu taba maganar Asma'u da Inna ba. Baba Usman ya yi murmushi na gamsuwa ya ce, da kyau shi kenan an gama kana iya tafiya, da zan bar wurin naji Inna ta soma ba har da cewa to sai ta ga yadda za'ayi ayi zaman auren, ita da renon. yaro shine don ka kai munzalin aci moriyarka zaka yi min butulci, to wallahi in kun san wata ba ku san wata ba, Baba Usman ya riko hannuna ya jani waje, rabu da ita ba abinda zai same ka sai alheri, butulci akan ka aka fara yarinyar fa bata da hankali ma, irin yarannan ne da ba a haife su da lafiya ba, masu zuwa duniya da matsalar ciwo irin ta shanyewar kafa, ko wani gefen jikinsu dai a nakasashe ne, shine ta zabar maka don kai ne baka son dadin rayuwa, tsana ce karara Inna take nuna min ta yaya zan auri mace irin Asma'u bayan ni nasan ina da komai da ake son cikakken namiji ya mallaka, ba wai na ce ita Asma'un ba mutum ba ce, a'a amma gaskiya ba zan iya zaman rayuwar aure da ita ba. Ba a maida sati ba, su Baba Usman suka dawo nema min auren Maryam, ai kuwa anyi shi cike da sauki, don har mahaifin Maryam ya ce a gama komai kafin a tashi. A take kuwa aka yi 8 Bakı Biyu Sameera Mustapra: komai don har da Sadaki aka yanka a lokacin aka kuma sa ranar aure, nan da wata daya da rabi albishir din da Baba Usman ya zo min dashi kenan, tun da aka sa ranar aure da Maryam abincin gidan Baba Hassan ma na daina ci, kirikiri zan ga alamun barbaden magani a ciki, cikin gidan ma na daina shiga saboda irin wulakancin da Inna Muna ke yi min, ita da yaranta. Ana saura kwana biyar daurin aure aka fara zuwa daga Ruma, aka kuma hado min sha uku ta arziki, daga gun 'yan uwa da abokan arziki na mahaifina, dama nima na dan tara nawa komatsai aka hada aka kai a matsayin lehe. An daura aure ranar Juma'a bayan anyi sallah Juma'a, a ranar kuma muka tàre da Maryam a gidan kawunta, da aka ara mana sai dai iyayena sun ce Ruma za mu koma don akwai gidan mahaifina da ya bari. An dai bar shi akan sai mun yi sati biyu anan sai mu wuce can. Bayan kwana uku da aure abin mamaki cikin tsakiyar dare na rika jin kamar ana buga mana kofa, Maryam na gefena tana barci, na mike na isa gun kofar ina leke, babu kowa a gurin don haka na bude kofar tare da dauko buta don in zaga, ina tsalake kofar dakin, ji nayi kawai na soma tafiya tunanina ya 6ace, ban san abinda nake ciki ba tafiya kawai nake yi, ni dai ban san abinda ke damuna ba har na smai tsawon kwan 9 Bakı Biyu Sameera Mustapha: ashirin da bakwai ni dai ban san yadda aka yi ba sai gani a kasar Zamfara, cikin ikon Allah a nan na soma sabuwar rayuwa, sam bana son a ambaci sunan garin. Katsina, a rayuwata cikin ikon Allah, Allah ya hada ni da mutumin kirki irin Alhaji Moh'd Shinkafi, wani lokacin zaka ga kamar ba a cikin hankali kaina nake ba đa yake idan lokacin wahala ya kare sai kaga abu ya wuce kamar ba ayi ba. Sai da na samu kusan shekaru goma sha uku sannan na soma samun natsuwa, can zaka ga na tuna da su Baba Usman wani lokacin kuwa sai in tuna da Maryam, sai dai ban taba fada ba, sai a wannan lokacin, bayan haka ma Mairo ta taimaka min a rayuwa don sanadinta na kara samun lafiya abinda yasa sauran matana suka fita kenan, da a gaskiya sai mai hakuri ke iya zama da ni, da yake ina da rabon 'ya'ya gashi kuma na haifa, bai fi ma shekara uku ba da na kara samun isasshen lafiya sanadin wani Malami da nake karbar magani a gunsa. A gaskiya Mairo Allah sai ya saka miki ko ba a nan duniya ba, to a lahira ina rokar miki aljanna fiddausi. Sharkaf nayi da hawaye da jin wannan labari na Babanmu, ashe rayuwa haka take? Kana nan baka damu da mutum ba shi nema yake yi yaga Karshenka, tabbas sammu aka yi wa Baba. 10 Baki Biyu Θ Sameera Mustapha: Muryar Sa'idu ce ta tsinka min tunanina, da ya ke maganar cikin kuka ya ce, anya ba kaine mahaifina ba! Furucinsa yasa kowa ya maida hankali gunsa. A gaskiya sai a lokacin naga kamanni tsantsa da mahaifinmu ne Sa'idu yake kama shi yasa ake ganin kamarmu dashi ashe photocopy din Baba ne, ikon Allah wani abun sai Allah, baki daya falon ya yi tsit ana kallonkallo mu kalli Baba mu kalli Sa'id, da ya ci gaba da cewa, mahaifiyata, sunanta Hajiya Maryam Balarabe sannan ta bani labarin mahaifina ya rasu tun kafin a haife ni, sannan wani lokacin kuma takan ce min ita bata san yadda aka yi suka rabu da ita dai ta wayi gari bata ganshi ba, kukan da Baba yake yi shi ya dakatar da Sa'idu, ya се Allah ya isa tsakanina da Inna Muna, idan ita ce sanadin abinda ya same ni, Sa'idu kam shima kukan yake yi, ya isa gun Baba, ya sa kansa kan cinyar mahaifina yana kuka wiwi, dole Baba yа daina kukan yana lallashin Sa'id. Abu kamar a fim, Sa'id ya kuma zama wa а gare ni, wannan abun al'ajabi ne a gare mu, baki daya. Ga kuma murnar ganin dan uwanmu, Allah shine abun godiya da ya nuna wannan al'amari cikin sauki. Sai da aka natsu sosai duk wani hawaye ya bushe sannan ne Sa'id ya ce, mahaifiyarsa na nan a Kaduna tana aure. A gaskiya wannan al'amari ya yi mana dadi, Baki Biyu Sameera Mustapha: Gwaggo ta ce, ah wani abun sai Allah, Sa'id ya zo neman aure gashi abu ya juya to Allah ya kare mu daga sharrin dan adam, amin muka amsa baki daya. Mun kwana biyu a Gusau ranar Lahadi Sa'id ya ce, zai koma Kaduna don zuwa office, Gwaggo ta ce, to ai gara mu ma mu koma tunda abun ya zama haka, Allah ya ba kowa rabonsa amin. Mun kama hanyar zuwa Kaduna, abinda na lura dashi shi ne, yadda Sa'id ke jin kunyata, ni kam wallahi ko a jikina dadi ne ya yi min yawa. Washegari Sa'id ya zo ya dauke mu zuwa gun mahaifiyarsa, saboda na matsa ina son ganinta, Gwaggo ta ce, ai har sai kin gaji da ganin nata tunda yanzu an zama daya. Gida ne babba sosai bayan an bude gate mun shiga, motoci ne cike da gidan, ga tsarin gida irin ginnan na da amma har a yau bata wuce lokacin ta ba. Har mun isa falo wanda a cike yake da kayan alatu irin na zamani, Sa'id ya ce, mu zauna bari ya yi mata magana, bayan minti biyu sai gasu sun fito, wai a gaskiya mahaifiyarsa ba a bar ta a baya ba gun kyau, fara ce ba ka taba cewa ita ta haifi Sa'id saboda tana da jiki mai kyaun gaske. Jikinta a sanyaye ta rika fara'a tana gaisawa da mu cikin natsuwa, kusa da Gwaggo ta zauna, 12 Baki Biyu Θ Samecra Mustapha: muka hada ido da ita, ta fadada murmushinta, ta ce ke ce Dayyiba? Nima na sakı murmushin na ce, eh! Ni ce ai ga kamanni nan sak dai da mahaifinku, shi kuwa jininsa ya cika karfi, baki daya aka yi dariya. Cikin kankanin lokaci aka cika mu da kayan abinci sannan ta saki jiki sai hira suke yi da Gwaggo nan da nan suka shiga hira kamar da can sun san juna da aka kira azahar 'ya'yan ta suka rika shigowa suna gaida mu, ikon Allah Halima dama ke kanwar Sa'id ce? Eh, wałlahi ta fada ta iso inda nake zaune dama ku ne 'yan uwan Ya Sa'id da ya bamu labari jiya? Mune Halima, Umma haka suke kiran Hajiya Maryam ai tare muka yi state University (Kasu) kai haba dama ashe kun san junanku, Allah ne bai yi ba kuwa da mun hadu don a cewar yaya sai mun je mun gaisa, to gashi ai a saukake mun haďun. Ta ja ni zuwa cikin dakin su, muka shiga sabon hira. 'Ya'yan Haj. Maryam uku da ya Sa'id hudu kenan Hálima ita ce 'yar ta ta uku, saboda-akwai adama ita ee babba sai autan ta Sagir, Babansu Soja ne, belgeria balarabe ruma, babba ya san shi tun a funtua shi ne saurayin Haj. Maryam na farko kafin Baba ya santa, dama ai an ce matar mutum kabarinsa. Wai har yanzu baki yi aure ba Halima? Haba dai nayi muna gama school, Sai dai har yanzu Baki Biyu Θ Sameera Mustapha: ban haihu ba, aiya! Allah ya kawo, ke fa ba ki haihu ba? Humm! Ban haihu ba kin san naigidana ya rasu! A ya yi hakuri wallahi ya Sa'id ya fada mana, Allah ya jikansa amma ai kamar ya yi shekara da rasuwa ko? Eh! Shekarunsa biyu da wata shidda, yaushe za kiyi aure? Ta yi tambayar tana murmushi, ajiyar zuciya nayi kafin na ce to sai Allah ya kawo mijin to kunna, kai dai 'yar uwar a yadda ki ke din nan kice ba ki da manema gaskiya ban yadda ba, haka ne to ko in ce gwanin ne ban samu ba, na fada ina dariya. Hira sosai muke yi da Halima. Karfe biyar saura Gwaggo ta ce, in fito mu tafi, a gaskiya sam ban ji komai a tare dani ba sai godewa Allah da nayi akan yadda ya shirya abun. Da muka isa gida muka zauna ni da Gwaggo muna tattaunawa akan family din mu, da na Sa'id, take bani labarin Haj. Maryam har da karamin hauka tayi da Baba mu ya bace, cikin Sa'id kuma da ta samu sai da ya kai wata hudu sannan aka sani. Bayan ta haihu bacewar Baba ya zama mata sabo saboda karamin Sa'id. Bayan sati daya da faruwar haka sai ga Baba Usman da Baba Salihu sun zo gidan Gwaggo, sun dade sosai kafin suka ce za su wuce Gusau, ranar Asabar gun Baba mu. Ni kam da karambani sai da na kai su gidan Anti Badiya, Baki Biyu Sameera Mustapha: sun yi murna sosai da ganinta, da son samu ne da na kai su gun Anti Fiddausi a Abuja, amma da muka yi waya da ita sai ta ce, mu bar shi za ta 70 Kadunan dama ranar Laraba. Anti Fiddausi ta zo Kaduna da alama wani cikin gare ta, kai Anti ke dai kullum haihuwa? Harara ta Gwaggo tayi ta ce, tafi can ke kenan kullum mita akan yayin ki da kannanki, na haihuwa, Allah na roke ka ba ta, haihuwa ba sassauci in ga yadda zaki yi, kai Gwaggo ki daina min wannan fatan don ni so nake ko nayi aure sai na samu irin shekaru hudun nan kafin in haihu, to ai su ba kan su zabi ba don ga Maimuna nan ma itama da cikin, a'a lallai ni kam ai ko haihuwar farko nayi, sai yaran dan tasa kafin in kara haihuwar, ita dai Anti Fiddausi bata ce min komai ba sai dai murmushi da take yi. Zumunci sosai ya shiga tsakaninmu da mahaifiyar Sa'id yawanci muna zuwa gidan ta itama tana zuwa gidanmu, itama Halima a nan kusa da gida take aure, tana auren Soja ne itama, a karkashin mahaifinta yake Major Jibril maiwada, shima kuma mahaifinsa Sojan ne, aminin Baban Halima ne. Wata ranar Alhamis nayi shiri cikin lace ash ne da ratsin fulawa ja, dinkin fitted ne na dauko a baya sai dai ban riga na saka ba na isa gun 15 Bak Bry Θ Sameera Mustapha: Gwaggo na zauna muna dan taba hira, sai bayan sallah azahar zamu fita zamu suna Aisha cc ta Kara haihuwa, ke kin fauko ledar kayan kuwa? Na mike ina dariya lah! Kin ga har na manta ke dai kin cika mantuwa, wata rana ma nasan sai kin ce kin manta da kanki, na kara kwashewa da dariya kai Gwaggo na wuce dakinta, dawowan da zan yi na işke Amir ya shigo falon, kamshin turarensa ya biyo ko ina, ba tun yau nasan kamshin turarensa ba, don haka gabana ya shiga faduwa, na rasa kuma dalilin hakan. Babu abinda na ki jini da irin halinsa bacin irin kallon da yake min, na tsani haka sam bana kaunar wannan abu, abunda ya fi bani haushi da shi kuma babu ruwanshi da Gwaggona, nan kallo na zai ta yi magana na dainawa take, da zarar ta ga inda hankalinsa ya koma kaina abun haushi kuma abayar da zanyi amfani da itama akai ya zauna. Duk na bi na tsargu da irin kallon da yake min, ko gaishe shi na kasa. Kai tsaye kofar fita na kama, Gwaggo ta ce hada masa abinci Dayyiba, raina ya yi bala'in baci, sai dai ya na iya, dole ne in yi. Da na hada abincin ma Asabe na ce ta kai masa. Haushi ya karu a gare ni, saboda ya kusan awa daya da rabi suna hira da Gwaggo da abun ya ishe ni dole na koma falon na wuce dakina, a lokacin na ji Gwaggo na cc masa, babu damuwa, 16 Baki Biyu Θ Sameera Mustapha: zan yi mata magana, wata abayar na dauko, na yafa na isa falon kamar zan fashe, Gwaggo kam ko a jikinta na lura hirar nayi mata dadi, ringin din wayan hannuna tasa hankalinsu ya dawo kaina, sam bana yadda mu hada ido da shi, na kara wayar a kunnena. Amina ce ta rika yi min sababi na rashin zuwa, bata bari na ce komai ba ta kashe wayar. Na isa gun Gwaggo ina yi mata magana, cike da shagwaba, kai Gwaggo lokaci fa na tafiya, ai dama fita zaku yi ne? ko kallon inda yake ban yi ba na ci gaba da abinda nake yi, Gwaggo ce ta amsa masa, Eh, fita zamu yi, kawarta ce ta haihu." Ok, to muje in sauke ku mana, a'ah bar shi kawai, kada mu bata maka...." Ya katse Gwaggo kada ki damu Gwaggo ina garinnan har zuwa gobe saboda ina son zuwa Gusau. Idan ku ka gama sai ku kira ni in dauko ku, a take raina ya yi baki na bala'in tsukewa, amma babu yanda zan yi don haka na sha jinin jikina, sai da ya fita Gwaggo ta ce, min kin san Amir ke yake so? ji na yi kamar in yanka ihu, sai dai nayi kokari na kama kaina, kuma na yi kamar ban ji abunda take fadi ba, itama kyale ni tayi muka kama hanyar fita, da sauri na shiga gidan baya ina wani huci ina turo hanci na cika fam kamar ballon. Abun takaici kuma ashe na zauna inda zai 17 Baki Biyu Sameera Mustapha: rika ganina ta cikin mirror gaban motar, hada ido muka yi dashi ya sakar min murmushi, harara na sakar masa nayi saurin komawa dayan gefen, ina kallon gefe na da muka hau titi, ya ce Gwaggo ina zamu ne? ta ce, ai Dayyaba ta san gidan don haka sai ki rika fada masa hanyar da zamu bi, yanzu kam na kai karshen kulewa na tunzuro bakina, ina magana unguwar Dosa za mu je, ya dan jiwo da kansa sai fa kin nuna min ba wai nasan

Chapter 1 of 8