Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
7 / 8
cikin gida ta fada wa Belly da Binta abinda ke faruwa, suma sun jinjina da abinda ke faruwa. Sun dai bata magana amma sam hankalinta bai kwanta ba, ba ta son ta rasa iyayenta ba tare da ta nemi gafararsu ba. Washegari bus suka shiga irin wannan doguwar babba ce sosai, tafiyan kwana daya da rabi suka yi suka isa Niger, da yake ta nan suka 101 Bakı Biyu biyo. A Kalla dai sai da suka kwana uku suna tafiya. Da suka shiga Katsina, da za su shiga mota ta Kaduna suka shiga. Tafiya suke yi kamar basa yi don Suwaiba ta gaji sosai, sai wajajen Karfe sha daya saura suka isa tashan kawo na Kaduna. Tashan mota suka yi suka wuce Abuja a cewar ta gara sun karasa don su huta baki daya. Karfe biyu da minti goma sha uku suka isa bakin Kofar gidan Tahir, dabara ta fado mata ta ce da direba tana zuwa, ta isa bakin kofar gidan tana kwankwasawa Baba Maigadi ya bude don abun nan na leke yana lekawa duk da duhun daren ya gane Suwaiba da sauri ya bude kofa ya cika da mamaki. "Hajiya ke ce? Shigo mana." Ya fada yana bata hanya, ajiyar zuciya tayi ta saki murmushi ta ce, "Ni ce Baba, ya bayan rabuwa?" Ya amsa "sai alheri." Ta dan dubi cikin gidan ta ce, "Tahir fa! Yana nan?" Baba ya ja dogon numfashi ya ce, a hankali yana asibiti an kwantar dashi yau kwanansa shidda kenan." Tuni hawaye ya soma fitowa a fuskarta. Ba ta iya tambayar Baba maigadi inda aka kwantar dashi ba, sai Mal. Attahiru ne ya tambaye shi, saukin abin mai taxi yasan asibitin, don haka kai tsaye suka wuce. Muna zaune cirko-cirko kowa da abinda yake 102 Baki Biyu Sameera Mustapha: tunani a zuciyarsa, yau kwanan Tahir biyu kenan bai san a inda yake ba, yana "comma" sai abinda Allah ya yi, kaina na hada da guiwa ta duk abin duniya ya ishe ni, na san na kamu da son Tahir, to ya...Mama ce ta tsinka min tunanina da ta ce Suwaiba! Tayi maganar a tsawace, wanda yasa. kowa ya kalli inda take kallo. Tabbas Suwaiba ce, naga ta jeme ta rame anya ita ce? Na mike nima na soma tafiya zuwa inda take, don tuni Mama ta isa gunta, tana kuka tare da rike ta itama Suwaiba kuka take yi, na ban tausayi. Ina tsaye daga gefe ina kallon yadda Suwaiba ta zama, anya lafiyarta kalau? Nan aka zagaye ta kowa da tambayar da yake mata, ita dai bata amsa ba. An sami kusan minti goma sha uku kafin mahaifanta suka shigo suka rungume ta baki daya, sai a lokacin ta soma fadin abinda ya same ta. sam bata ji nauyin fadin abinda ya kaita ga wannan mahalaka ba, ai ni tuni jikina ya soma rawa kamar mazari dama haka take? Idon da muka hada da ita yasa tayi saurin mikewa ta iso guna tana kuka, dakewa nayi na tsaya amma wallahi tuni na tsure. Riko hannuna tayi ta ce, don girman Allah Dayiba ki yafe min, guiwarta a kasa take neman gafarata, ai ban san lokacin da nima hawaye suka taru a idona ba, na ce na yafe miki duniya da lahira, ai ban san lokacin da na rungume ta ba ina hawaye. Daga bayan mu muka 103 Baki Biyu Sameera Mustapha: jiwo hayaniya, doctors ne su biyu suka shigo asibitin cikin gudu suka shiga dakin Tahir, na shiga uku ai tuni zuciyata ta buga, kowa dakin ya nufa, Tahir ne ke ta shure-shure wallahi nasan ina tausaya wa kaina idan na rasa Tahir, to amma sai naga kamar ban kai Suwaiba zama abun tausayi ba, don tafi ni saninsa. Irin yadda take ta surutai na ban tausayi yasa na bar wurin naje nayi alwala na soma jera nafilfili, cikin ikon Allah kuwa abun ya sassauta, ya farfado har yana amsa gaisuwan mutane. Na shiga dakin na iske Suwaiba rike da hannunsa sai sharfar kuka take yi, tana rokonsa gafara. Abun tausayi, duk an su sun bani bala'in tausayi, na isa gefen sa ina dai tsaye ina kallon fuskarta da tayi kamar ba shi ba, jini kuma na ga an rataye ana sa mishi. A lokacin muka jiwo sallama, muryar na san ta amma na manta ko a ina na san ta, na kuma kasa daga idona in dube shi, kaina a kasa ina ta son in tuno inda nasan muryar nan amma na kasa ganewa, har ma ya rika magana da Tahir a hankali, in ba ka saurara ba ba za ka ji abinda ya ke fadi ba. Gabana wani irin bugawa yake yi, na rasa dalili ai ban san lokacin da na bar wurin ba, don tuni marata ta cika da fitsari, don na so in gano mai ainihin muryar. Ya Amir ne, haka na fada a zuciyata, har na kai kofa na ji an ambaci sunana, 104 5 Baki Biyu Sameera Mustapha: waigowan da zanyi muka yi ido biyu da Amir, tas-tas-tas gabana yake yi, na yi saurin dauke idona daga nasa saboda a gaskiya gaba ki daya ya canza, yayi fari ya yi kiba ashe ba karamin kama yake yi da su Tahir ba, fuskarsa ta cika sosai, gashi ya bar saje ya kwanta luf a fuskar tasa, ya yi min kyau a idona...katse min tunanina Tahir ya yi da ya ce, in kin fita ki ce da Baban falo ya shigo. Na saki fuskata na ce, to. Tahir murmushi ya sakar min kafin na fita, na fita kenan sai na hadu da su za su shigo, sai a lokacin suka yi sallah Isha'I, na fada masa da sauri ya Karasa. Ina toilet tunani ne ya kama ni, mamakin canzawar Amir nake yi, ga baki, daya ya canza kamar ba shi ba ne, kai anya shi ne ko dai kallon tsoro nake masa? Kai ina jin dai idanuwana gezo suke min ban lura da shi ba da kyau, hayaniyar da na jiwo a waje shi yasa na yi saurin barin bayin saboda ihun Mama ne yafi firgitar dani, "Innalillahi wa inna ilaihir raji'un" Allah ya yi wa Tahir cikawa." Ai ban san lokacin da na koma zaune ba, kukan zuci nake yi, ba wai kuka nake yi na waje ba, hawaye ne kawai ke gangara daga idaniyata, kai a wannan rana ta zama ranar tarihi a zuri'armu baki daya. Dan a gaskiya munyi babban rashi, a raina tabbas nasan ina tausaya ma kaina don irin son Tahir da ya shige 105 Baki Biyu Ο Sameera Mustapha: ni lokaci daya amma gaskiya na fi tausaya wa Gwaggo don sai da tayi suma har biyu a lokaci daya, daga karshe ma gado aka bata. Allah Sarki! Rayuwa kenan, gashi muna ji muna gani Tahir ya tafi ya bar mu. Asibitinnan kan kice kwabo. Ta cika da jama'a har babu inda zaka zauna duk a matse ake. Da ya ke karfe biyar saura ya cika sai aka yanke shawarar a shirya shi ana idar da Sallah asuba sai ayi jana'izarsa, abun jin shi nake yi tamkar mafarki don na bala'in sawa raina Tahir zai tashi, ko rabuwa ta ta karshe da shi, ya bani kwarin guiwar zai tashi. To ta Allah ba taka ba, kana naka Allah na nashi, Allah yasa mu dace ya sa mu cika da kyau da Imani (Ameen). Da aka yi jana'izarsa gidan Gwaggo aka wuce baki daya, har da Gwaggo muka koma gida, ina zaune gabda ita duk fuskokinmu a kumbure yake har a lokacin kuma bamu daina kukan ba, sai dai kukan zuci yafi yawa. Zaman makoki muke yi, tuni na kara rama don dama tuni dama ramar ta so ta yi min yawa. Kwanan Tahir uku da rasuwa, aka kwasa muka wuce Gusau, shinkafi a kaje sai da muka kwana sannan muka wuce gidan Baban falo a nan cikin Gusau, har aka yi kwana bakwai Gwaggo bata da lafiya, a yanzu haka tana kwance a asibiti jininta ne ya hau, ni kam ina nan 106 Baki Biyu Sameera Mustapha: tare da ita. Sai da ta kwana shidda a asibitin sannan aka sallame ta. A gaskiya Gwaggo da Suwaiba sun ji jiki ba kadan ba, ni kam rama ce nayi kamar mai ciwon tyford dina ne ya tashi. A nan gidansa na Gusau aka ce muyi takaba, ni ce na koma ina rarrashin Suwaiba, baki daya ta fita hayyacinta, kai so cuta ne, da yake ni mai zurfin ciki ce, sai dai in ta kukan zuci. Kayan abinci babu abinda babu komai a adana mana. Haka aka yi sati hudu jama'a suna zuwa gaisuwa, a gaskiya Tahir ya yi jama'a sosai ga yabo da ya samu gun mutane. Kyakkyawar shaida kam ya same ta, Allah yasa mu ma in tamu tazo mu cika da kyau da imani amin summa amin. Da aka yi sadakan arba'in, a lokacin an taro gidan Baban falo aka yi ta addu'a. Bayan sallah Isha'i ne aka tara mu a babban falonsa na kasa, ni kam ina daga can nesa anan ina hango manyan iyayenmu da 'ya'yansu. Alh. Ashiru shine mai bi ma Baban falo, shine ya bude taron da addu'a sannan ya kara yi mana gaisuwar marigayi Tahir, daga nan dokiyar Tahir baki daya aka fada, ana son a raba gadon tun a yau. File ne Barrister Kasimu shine Lauyan Tahir, ya fara gabatar da tsarin da Tahir ya bada akan wasu dukiyoyinsa, wadanda ba za su kasance a cikin 107 Baki Biyu 0 Sameera Mustapha: rabon gado ba. Kamfaninsa da ke Thailand sunan Gwaggo Hauwa ya saka ya bar shi akan ita ce mai kamfanin halak malak, takardar aka fito da ita aka nuna sannan ya rubuta ya bar wa Amir amanar ya kula da kamfanin yana kuma son a ba Dayiba wani sashi na kamfanin, wato matsayi na board of directors. Yana da wani kamfanin a nan Nigeria yana son Amir ya zama mamallakin wannan kamfani nasa halak malak, wannan kamfani ita ce wanda yake juya kudinsa ta hanyar mai na petrol da yake Lagos. A nan Lauyan ya yi shiru, ya yi sallama ya zauna wani ne ya mike ya gabatar da duk wata kaddara da Tahir ya tara. Nan fa aka fiddawa Banki nasu aka kuma raba shi kamar yadda addinin Musulunci ya tanadar. Ni da Suwaiba a kalla sai da muka tashi da gidaje hudu-hudu, bacin kudin da aka ce ya kai million biyar, tabdijan, lallai ashe ba karamar dukiya Tahir ya tara ba. Nan dai aka ba kowa nashi aka watse. Ina Gusau dai ban koma Makaranta ba, da yake an ce duk da idda da nake yi ina iya zuwa Makarantar tunda anyi arba'in, wallahi ji nayi Makarantar baki daya ta fita raina, na rasa dalilin hakan, sam babu nutsuwa a tare dani, sai dai karfin hali da nake yi in shiga mutane don kada tunani ya yi min yawa. Tunda da Tahir ya rasu, ba kwanciyar da zan yi ban yi mafarkinsa ba, ni 108 Baki Biyu Sameera Mustapha: nasan na cuce kaina da na daukarwa kaina karfin halin da ban amincewa Tahir kaina ba, a raina ina tunanin irin hukuncin da Allah zai yi min idan muka hadu gobe, wani lokacin kuwa idan na tuna ya ce, ya yafe min sai in ji dan sassauci a tare da ni, an sami kusan wata biyu da rasuwar Tahir kafin na koma Kaduna, saboda nan da kwana goma za'a mu fara jarabawa. Dole na rika bin lecturers suna yi min make-up test saboda baki daya ban yi ba. Bayan na gama jarabawa, Abuja na wuce gun Gwaggo, ban ji dadin yadda na ganta ba, duk ta rame ai sai mutuwar Tahir ta zama min sabuwa, sai dai idan ina gaba Gwaggo ina iyakar kokarin yaki da damuwa ta saboda Gwaggo ta saki ranta. Cikin ikon Allah kuwa ta saki jikinta don abinci ma sosai take ci, ba karamin kula nayi da ita ba, nan da nan ta soma kumari. Har muna zama muna hira cike da nishadi, sai dai ni kam sam ba haka ba ne a guna, sai na shige faki zan ta kuka ina kuma neman gafara gun mahaliccinmu. Da yake lokacin nan kwana kin ba wuya sun zo sun wuce wata ya zama sati, shekara kuwa ta zama wata har nayi na gama idda ta. A lokacin kuma result dinmu ya fito, ikon Allah gashi na rike degree na a hannuna na fito da low-credit, ban da matsala. Service muke jira a kira mu. 109 Bakı Biyu e Sameera Mustapha: Har a lokacin ban maida jikina ba abun mamaki sai gashi na zama Ustaziya, haka su Amina ke kira na, saboda na koma wata shirushiru, sannan hijab din da nayi amfani dashi lokacin da nake Idda shi din na ci gaba da amfani dashi. Ashe mutum kan canza? Nima а koda yaushe ina mamakin kaina, duk wata ji da kai da iya yi na bar shi, nayi bala'in natsuwa babu ruwana da wata kwalliya, kai smiling da ake kira nama a da ba za a kira ni da wannan lakani ba duk ta dama tun da namiji ya gasa ni a rayuwa na rage, wasu abubuwan to a yanzu ma abun yafi muni, ganin nake yi, dama haka Allah ya shirya min rayuwata ba zan yi dacen zaman aure ba. Kowa ne namiji nake so to sai ya zama mini matsala gani da wata irin zuciya da in ta kamu da son namijin sai na wahala, ko daya ke Tahir son sa ya shige ni ne a ba zata ko don hakurinsa ne yasa hakan oho! Allah ya zaba mana abunda ya fi zama alheri a gare mu shi ne addu'armu a kodayaushe. A yanzu kam komai ya wuce daga Gwaggo har ni mun saduda mun bar wa Allah komai yana tafiya normal. Ina zaune a falo ina kallon Indian film a zee aflam, hankali na na gun kallo har aka shigo bar sani ba, da yake ina falon Gwaggo ne, zaman da aka gefe na yasa na tsorata na dube gunin wa zan gani! Amir ne! Da saurin gaske na 110 Baki Biyu dauke ido na Sameera Mustapha: daga kallonsa. Gashi mun hada ido da shi, ya aka yi ban ji shigowarsa ba, a gaskiya ya canza daya wa, ya yi kiba kamar yadda Tahir yake kai ashe ba karamar kama suke yi ba, abunda Tahir zai nuna masa haske, shi kuwa yafi Tahir gashi kai gashi yana da saje tun fil-azal, yanayin sa da kusan komai sa irin na Tahir, oh! Allah mai talita, sai dai Amir halinsa sai shi......ya katse min tunanin da nake yi, ke baki ga mutum ya shigo bane ba za kiyi gaisuwa ba? Maganarsa ta zo mu a baza ta, ban san lokacin da na murguda baki ba tare da tsuke su, na kuma wani bata rai kamar dawo, gero ina kallonsa dama ta gefen idona fuskarsa a sake take tun lokacin da ya shigo, na fada cike da kasaita, ai da zaka shigo baki yi sallama ba, ni kuwa a sani na an koyar damu wannan, na yi shiru, sai dai gabana kamar zai fado saboda yadda take bugawa, karfin hali ne nake yi zaman da nake yi agun da son samu ne da na gudu don ya maida hankalinsa baki daya a kaina. Kallo na yake yi kamar a yau ya taba ganina, gashi kayan da ke jiki na ba masu nauyi bane atamfa ce riga da sket, anyi masu dinki fitted kaina kuma babu don kwalli, gashi kitson twixin nayi, duk da ba kwaliya nayi ba amma nasan fuskata tayi kyau. Dama rabona da kwalliya tun rasuwar Tahir, ban san tunanin me ya yi ba ya mike tsaye, gabana ci 111 Baki Biyu e Sameera Mustapha: gaba ya yi da faduwan can daga bakin kofa a jiyo muryar Gwaggo ai sai na ji kamar an sauke min wani katon dutse. Na mike buzut na bar wurin, abun haushi bai daina kallona ba, kai gaskiya wannan mutumin 'A' ne sam baya jin nauyin abinda yake yi, Gwaggo har ta je ta zauna bai sani ba, har magana take yi masa amma sam hankalinsa ba ya tare dashi, sai da na shige daki na na kule sannan, na ji ya suma an sa Gwaggo ko a jikinsa kuma kai wannan mutumin kunya ma bata ishe shi ba, maganar dukiyar da Tahir ya bar wa Gwaggo yake yi dama kowane wata sai an kawo mata report, akan abunda ke faruwa. A yau ma shekara ce ta cika ya zo da kansa ya yi ma Gwaggo bayanin dala-dala abunda ake ciki, tun da Tahir ya rasu, ya kan leko gun Gwaggo ya gaida ta, sai dai ikon Allah bamu taba haduwa ba sai yau. Ya tabbatar mata da komai yana tafiya daidai, sannan akwai meeting da ake yi kowace' karshen shekara na board of directors na kamfanin don haka ana bukatar ta a Thailand don ita ce mai kusan kashi saba'in a dukiyar kamfaninta, ta ce haba dai Amir ni fa na fada ma tun farko kai zaka ci gaba da kula da wannan kamfanin, ni na baka dama na amince maka kaje kayi duk abinda ya dace, wallahi bani ta zargi ko zato akan ka, na san zaka rike amana. Sosai ta kashe masa jiki bai iya gardama da ita, 112 Baki Biyu Sameera Mustapha: ajiyar zuciya ya yi to na gode Gwaggo, insha Allahu za ki zama mai alfahari da ni...haba dai Amir nifa na san zaka iya na san zaka yi adalci sam bana da kwakwaton hakan. To Gwaggo, Allah ya bani ikon rikewa. Amin ta amsa da sauri, ji nayi ta kwala min kira ban so Gwaggo ta kira ni yana gidan nan ba, na dai tashi na fito sanye da hijab a jiki na, nayi kamar sallah nayi da yake sallah azahar ya yi sallah, za kiyi? Ta tambaye ni zan dai yi ne, kafin nan don Allah kawo ma wannan katon tazurun abinci, ta yi maganar cike da wasa na kama hanya naji yayi dariya, har da taba hannunsa biyu, kai Gwaggo lokaci ne bai yi ba amma zan yi ai, haba Amir shekarunka nawa yanzu, amma ace aure dai kа ki shi, ka tuna fa girma ka ke yi ba wai ragewa ka ke yi ba, a kullum shekarunka karuwa su ke yi ina mamakin rashin auren ka, shiru ya yi kamar baya gun. Na hadu abincin na ajiye a gabansa ba tare da na dube shi ba, da ina ji a jikina kallona yake yi sai dai na yi iya kokari na ban bari muka kara hada ido ba, da na wuce zuwa daki na ji yana ce mata, Gwaggo zan yi aure insha Allahu, nan ba dadewa ba. To Allah sa, daga nan na shige cikin daki na rufe na shiga toilet don in yi alwala bayan na idar da sallah na fito falon don da alama ya tafi. Gwaggo na zaune akan sallaya, tana tahiya, na 113 Bakı Biyu Ω Sameera Mustapha: samu guri na zauna, ban yi minti uku da zamanba Asabe mai aiki ta shigo falon wai nayi bako, abun ya bani mamaki saboda ni nasan ban ba wani appointment ba, to waye wannan? Na san ina da manema sosai don tunda na fita idda na fara samun masoya sai dai bana kula kowa ba dai Amir ba ne, wallahi in shi ne sai na bata masa don na lura shi mutumin banza.....ba za ki tashi ki ga mai kiran naki ba ne? na bata fuskata tare da zunburo bakina irin na shagwaba, kai Gwaggo ni fa ban ba kowa A.P ba, dama na ce an baki ne kin gan ki ko to zan bata maki rai, haka za ki zauna ba aure? Ki kiyaye ni kin ji ko, tun watan jiya Baban Nafisa ya fara min zancen ki, Suwaiba tana gidan miji wata hudu da suka wuce, amma ke kin yi mirsisi baki ko sauraren kowa, na san abunda ki ke bugun gaba dashi wai ke yanzu ba wanda zai matsa miki kinyi auren farko to za ki sha mamaki, don kin san kina karkashin iyaye ne dole ne ki amince da furucinsu. Ba za ki kama hanya ki wuce ba? Na kama hanya in buga kafata irin na shagwaba. Da na isa waje mota ce har mota Jeep na iske, na tsaya daga bakin kofa sai ka ce mai tsoron motar bude kofar motar aka yi aka fito wa zan gani! Sa'idu ne tsohon saurayina, wanda ko shekara dari muka yi ba mu hadu ba, zan gane shi, don ko ban ce shi ne first love dina ba, to 114 Baki Biyu 2 Sameera Mustapha: shima nayi sonsa, kuri na yi masa kamar zan cinye shi, sai kuma na kama kaina na yi kamar ban ji mamaki kafin ya iso har na fan jingina da bangon wurin ya isowa ya yi sallama na amsa cike da son sanin abinda ya kawo shi, shima ya lura da hakan sai ya sha jinin jikinsa, ya ce Dayyaba ina wuni? Na amsa, lafiya, ya muka ji da hakuri? Mun gode Allah, na fada kaina a kasa, ya yi shiru kafin ya ce, to-za a bani gun zama ba ne Dayyaba, sai da na sake duban sa daga kasa har saman sa sannan na kauda fuskata ina duban inda fararen kujeru suke na ce, bismillah. Bayan mun zauna ne ya ce, ashe maigidan ki Allah ya yi masa cikawa, wallahi tuntuni na so in zo in yi miki ta'aziya amma na kasa, saboda laifin da nayi miki, ina bakin cikin hakan kuma a kullum na tuna, sanadin haka bana samun isashen baci bana da kuzari, ina ta neman hanyar da zan zo in nemi gafarar ki Dayyiba, ni na san ban kyauta ba na ci amanar ki don na san ko ni aka yi ma ba zan ji dadi ba, don haka nake neman gafarar ki Dayyiba don Allah ki yafe min." A take naji jikina ya yi sanyi na tuno irin yanayin da na shiga lokacin da...ya katse min tunani na na dan dube shi na ce, ai ya wuce na kuma daďe da yafe maka don Rahma ta zo nan 115 Baki Biyu e Sameera Mustapha: bayan kun rabu to tun a lokacin kaima na yafe maka don na gano dama kai din nan ba mijin aure na ba ne, ya za ki ce haka Dayyiba ai kuwa ni mijin auren ki ne, saboda ni a shirye nake in aure ki, murmushi na saki wanda yasa hakura na suka bai yana, ni dai na ce maka na yafe maka amma a gaskiya babu aure tsakaninmu sai dai mutunci to ki bani izini mana in rika zuwa muna gaisawa, shiru na yi ina tunani, ban ma san abunda zance maka ba Sa'id, ni da zaka gane da mun hakura da duk wata hulda da zai hada mu, sai dai in mun hadu nayi maka alkawarin ko a ina ne zan tsaya mu gaisa. Saboda Allah Dayyiba na ke rokon ki ba don halina ba, a gaskiya Sa'id ya daure ni ban san dalili ba sai tausayin sa nake ji, ba dai har yanzu ina son saba nasan shima nayi son sa a da, daurewa dai nayi na ce to shi kenan babu laifi kana iya zuwa. Mun sha hira kuwa dashi kamar ba zamu rabu ba, sai da karfe shi da saura ya tafi, na shigo cikin gida fuska ta a sake, har na manta ranar da na saki jiki nayi hira ta nishadi, Gwaggo na iske a tsaye da alamar ni take jira. "Waye ya zo gun ki?" Ta yi tambayar fuskarta babu annuri. Jikina a sanyaye na ce, "Bakon da ya tafi?" "Eh, ai kin san dai tambayar kenan." Uhm, Sa..i...d ne, Sa'id! Sa'id!! Sa'id fa ki ka ce? Baki da hankali yarinyar nan, dama da 116 Baki Biyu Sameera Mustapha: Sa'id ki ke hirar ta kusan awa uku? Gwaggo gaisuwa yazo ya yi min, Eh, gaisuwa...wallahi abunda ya kawo shi kenan, ke dai ki ka sani ni abunda zan fada maki shine, kada ki bashi fuska har ya nemi shige miki, don na lura baki da wayau ke sakarai ce, duk irin wulakancin da ya yi maki a baya kin manta da ya hankali bai ishe ki ba, to in ma gaisuwar ce ayi bata wuce minti goma zuwa sha biyar, to ban yadda da hakan bà ki canza tunani, don in ki ka yadda da yaudararen yaron nan to ba a gidan nan ba sai dai ko can inda ba nan ba." Bata tsaya taji abinda zan ce ba, ta wuce dakin ta, a nan na zauna ina hawayen tashin hankali ya zanyi da rayuwata. Komai nasa a gaba sai raina ya baci, shi yasa nake cewa ba zan yi aure ba, don ina ji a jikina aure ba zai taba kwantar da hankalina ba. Bayan sati daya da zuwan Sa'id, ya zo har na kwana biyar amma haka zan ki fita bana sanin halin da yake shiga. Sam Gwaggo ta ki ta damu da al'amarina sai na yi ta fushi abincin ma sai in wuni ban ci ba, ita kuwa tasa min ido. Ranar Juma'a bayan Sallar Juma'a ne Baba ya zo daga Gusau, haka muka tarye shi, muna zaune a falo bayan sallar Isha'i Gwaggo ta ce, Baban Nafisa dalilin kiranka shi ne, don in fada maka Dayyiba ta fidda miji sai ayi abunda ya kamata, shi yasa na fi so ma ayi komai kana zuwa, gabana 117 Baki Biyu Θ Sameera Mustapha: faduwa yake yi kamar zai fadi don ban taba sanin Gwaggo ta shirya hakan ba, ta ci gaba. "Sa'id take so, don haka gata nan sai ka yi magana da ita a san lokacin da zai zo gaisuwa ya san mu mu ma musan shi." Ya dube ni ya soma sa min albarka, dama Dayyiba wallahi na damu kwarai da rashin aurenki, mamaki ya kama ni, Gwaggo ba ta fada mishi tsakaninmu ba, ai ban san lokacin da hawaye suka taru a idona ba, tausayin Gwaggo ne ya kama ni, tabbas ni butulu ce, Baba ya tsinka min tunani da ya ce, hala dan wane gari ne? na sunkuyar da kaina kasa na ce, bakatsine ne. To ya yi kyau, ki fada masa muna son ganinsa gobe." Mikewa nayi a sanyaye na ce, to. Dakina na wuce anya a rayuwata zan samu sukuni kuwa? Gwaggo fushi take yi dani ya ya zan yi da kaina. A ranar na kasa samun isasshen barci saboda bakin cikin da ke tare dani, a gani na na yi wa Gwaggo butulci. Washegari bayan na idar da sallah, na yi saurin isa dakin Gwaggo, na same ta kan sallaya tana karatun Alkur'ani mai girma, Suratul Yasin take karantawa a hankali da alama kuma tana cikin nishadi, tabbas Gwaggo tana bani sha'awa kwarai da gaske, tana da Ibada sam bata wasa gun addu'a da karatun littattafan addini, Allah ya bamu daushenta, don dai a gaskiya in ka samu rayuwa irin ta Gwaggo, to ina son ranka gama da duniya lafiya. 118 Baki Biyu Sameera Mustapha: Zama nayi dirshan a gefenta akan tayals ina sauraren ta, sai

Chapter 7 of 8