Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
2 / 8
abinda zan biya ku dashi ba sai addu'a, amma wani hanzari ba gudu ba, ina so a tambayi Tahir ko yana sonta..." Gwaggo ta katse shi kada ka damu Baban Nafi'u, Tahir da ne mai biyayya yana da karamci ga sanin darajar iyayensa, shi ya bani zabi ni kuma nayi tunanin hada shi da 'yar kanwata mu dai hadin kan ka muke so. Nima wallahi ban da matsala, na bada hadin kai fari-bisa-dari, Allah yasa a dace, a kuma yi a sa'a, gaba ki daya aka amsa (amin). 17 Saki Biyu. Θ Sameera Mustapha: Tahir tunda ya bar garin Gusau Lagos ya wuce ya rasa gane kansa, wani irin nishadi da farin ciki ke shigarsa, da alama ya fara son Dayiba to why her, ya tambayi kansa, ya yi soyayya sau da yawa a rayuwarsa, tunda ta rasu jin dadinsa ya kare, to amma a wannan lokacin farin cikinsa na so ya dawo, menene amfanin mutum na da kudi amma ba ya da wadda ke bashi farin ciki? Duk kudin ka idan ba ka da wadda zata maida maka martanin so to gaskiya kana da babban gibi a rayuwarka yana ji a jikinsa lallai Gwaggo ta yi masa zabe daidai da shi, tuni duk bakin cikinsa da raunin da yake fuskanta ya kau, sai farin ciki a tare da shi. Nan da nan ya soma maida kamanninsa cikin Kankanin lokaci. Tunda Mama da Suwaiba suka bar falon nan suke tunanin shirin da ya dace ayi don kada wannan aure ayi shi, hankalin Mama ya gama tashi, baki daya ta tsani iyalan Mal. Sabi'u shi kađai ne asirinta bai ci akan sa ba, duk da wani lokacin zata ga kamar ya yi sai kuma daga baya ya barkace, don haka ta yanke shawarar zuwa gun Boka Jilli da bata da wanda ya fishi duk a cikin bokayenta, ita ta rasa dalilin da yasa Mal. Sabi'u yake son shiga harkar ta, don me ne zai hada jininta da zuri'arsa, shi ne abu na karshe da tayi tunani akansa, gashi tunda maiyar nan (haj 18 Baki Biyu 2 Sameera Mustapha: Hauwa kenan) ta sa baki tasan kamar anyi an gama. To amma ba za ta yarda hakan ta faru ba, don sam layin Tahir ya fi karfin na Dayyiba, su da ke matsiyata mene za a ci da su, kananan mutane ai sai irin su idan ana maganar manya kuma manyan ne dai dai da kansu amma zata yi maganin su. Bayan kwana uku, jira take yi taga ko Tahir zai shigo amma shiru, abun ya kara kona mata rai, wai me Tahir ya maida ita ne, bai taba nuna kishinta, kuma a matsayinta, ta mahaifiyarsa duk a cikin 'ya'yanta shi ne zakka a gare ta, shi kadai ne bata iya juyawa. Ta yi ajiyar zuciya da ta tuna wansa Idris shi baya iya aiwatar da komai sai ta ce ayi, duk abinda zai yi sai ya sanar da ita gashi da gudun zuciyar ta wani lokacin da gangan take takura masa, sai Amir shi a daya so ya fi karfin ta saboda shaye-shaye da yake yi, amma daga baya kamar an yi ruwa an dauke shima juya shi take yi, har gara Amina bata cika sa ta cikin jerin 'ya'yanta ba, don ma tausayi take bata, karamin yaro ta aura da bai da komai don haka me zata ci da shi su je can su karata, dan autanta ne ma ya biyo ta sak shi yasa take ji dashi. Duk wani asiri da za'a binne a wuri da koma karbowa shi ke yi, babu abinda bai sani ba a game da ita, dukkan Malamanta ya san su. 19 Saki Siyu e Sameera Mustapha: To me yasa Tahir shi daban ne, komai ta shirya a kansa sai ya lalace, ku duba ku ga dai duk aikin da aka yi akan aurensa da Suwaiba, ba Karamin kudi suka kashe ba, amma abun ya ki dadi a son ranta Suwaiba ta mallake shi ko ba komai ta raba shi da Haj. Hauwa, amma abun ya gagara, a kullum ma soyayyarsu karuwa take yi. Amma ba komai, zata shawo kan Tahir zata yi duk abun da ya dace, ko menene shi zata yi har sai ta cimma burinta. Boka Jilli da ta maida shi tamkar mahaliccinta nan zata dole ne ya yi wani abu da zai hana ayi auren nan, dole ne a fasa shi za su yi shiri ne sosai. Suwaiba kuwa ta fitini kanta da kuma tayar da hankalinta sosai, ita ya zata yi ne? Ba ta taba tunanin zata hada namiji da wata ba, dole ne tasa Mama gaba ta hana wannan aure dama gata da shegen kwadayi, tun lokacin da suka yi aure tasa ta ta bude mata account duk dukiyar nan da mijinta yake da shi bata gode ba, babu abinda ya fi daure mata kai idan ka ganta kamar ba ta rike kudin, a kulluyumin tana nan kamar bata cikin hayyacinta, to zata cika ta da kudin don dama Tahir ba ya rabuwa da sa mata kudi a account din ta ko da ba su shiri, da zuciyar ta ta tuno mata da Jessica kuwa, wani irin dogon tsaki taja, ita ta ja mata duk wata masifa da take ciki, yanzu 20 Baki Biyu 2 Sameera Mustapha: ta gaji ma da daukar nauyin ta kurar ta zata yi, ita fa yanzu Tahir take so, ba za ta iya rabuwa da shi ba, zama da shi yanzu ta fara, don haka zata yi komai akan ta same shi. Ta kudiri niyar raba shi da yarinyar da aka bashi ko ta halin ka-ka. Karo suka ci a kofar falo ita da Mama, yauwa dama ke nake nema, ina ki ka shiga ne? mama ta fada tana dubanta. Nima ai ke nake nema Mama, ina so ki dauki mataki akan auren Tahir, ki sani fa ni ba zan zayna da kishiya ba, don ban ga ke da Mummy kůna da ita ba (kishiyar), don haka nima ba zan zauna da kishiyar ba, haba kwantar da hankalinki, ki ke dai je ki shirya muje gun Jilli, komai zai canza kada ki damu, buzut ta mike ai ni a shirye nake babu wani shiri da zanyi, Mama ta dube ta daga samanta har kasa, night gown ce da ta kwana uku a jikinta bata cire ba, anya ma ta yi wanka? Ta tambayi kanta, sannan ta ce, ina nufin kije kiyi wanka..." ta katse ta cike da fushi, ni ba zan yi wanka ba ki tashi mu tafi bana son yin wankan ai ba dole ba ne wanka ni fa abunda ya zama dole gare ni shi ne warware auren nan da wannan munafukan suka kulla. Mama ta lura yarinyar ta fita hayyacinta sam bata tare da jikinta, dole ta kyale ta. wani dan Raramin gyale ta saka akai suka wuce. 21 Bakı Siyu Sameera Mustapha: Boka Jalli sai da ya saurari abunda suka zo da shi ita Suwaibar cewa ma ta yi a nakasa Dayiba, ko ma a kashe ta kawai kowa ma ya huta, Bokan ya yi dariya tabbas mu masu iya kisa ne amma ki bari mu nuna musu, irin mu mu nuna musu wulakanci a rayuwarsu, yana magana yana kyalkyatar dariya sai kuma ya bar dariyar ya bata fuskasa, ya cę, wani hanzari ba gudu ba, an nuna min akwai auren nan Tahir zai yi aure! Kuma kema za ku zauna, sannan idan muka ce zamu kashe ta to tare zaku mutu." Suwaiba ta zaro ido tsoro ya shige ta, a'a a bar na kisan a dai nakasa ta Boka, a nakasa ta.' To sai dai wannan zamu nakasa ta zata zama bata da wani amfani, ba a gun mijinta kadai ba har da iyayenta sai sun gaji da lalurar ta, ta washe baki tana taya Bokan dariyar da yake yi, ke ya fada cike da daga murya, ya isa haka, а tsorace ta kama kanta. Sai dai akwai wasu sharuda da zan gindiya miki, dole ne ki bi shi idan ba haka ba ba zai yiwu mu kama mijinki ba, yana da karfi sosai saboda yana da ibada bai hada komai da ibadarsa ba, don haka ina so ki kula ki natsu in fada miki abinda za ki yi, ta yi saurin gyara zamanta, ta ce ina jin ka Boka. Tuni bakin Mama ya mutu, ta bar abun tsakanin Suwaiba da Bokan don a gaskiya duk rashin imaninta bata taba kawo tunanin ta yi kisa 22 Baki Biyu Θ Sameera Mustapha: ba, ta raba mutum da duniya ba, ashe komai ka ke yi akwai wanda ya fika, don haka ta maida su hoto ta kali Suwaiba ta kalli Boka suna ta bayanin su tsakaninsu. To ina son ki shirya zama na fahimta tsakaninki da mijinki, ban gane ba, za ki gane ne, ina nufin ki ba mijinki hadin kai kuyi zaman lafiya, ki bi shi da duk abinda yake so ko ki ka san zai sa, ku zama kusa da shi kiyi shi saboda ya saki jiki da ke, don a yanzu din nan da nake baki labari digon sonki ba ya tare da shi, ya nuna mata wani dutse da ke gabansa an diga masa paint baki wannan zuciyarsa ne, idan dutsen nan bai koma ja ba to ina fada miki ke dinnan baki a zuciyar sa baki daya. Ta fashe da kuka, na shiga uku ni Suwaiba ya zanyi da raina? A'a bana son kuka hadin kanki nake so idan kina son wannan aikin ya yi, a dole ta sassauta kukan ta don a tsawace yake mata magana. Muryarta na rawa ta ce, ya ya zanyi boka me zan yi ya so ni? To ki bude kunnuwanki da kyau ki saurara, ina son idan kin koma gidansa, ki zama mai biyayya a gare shi, ki zama mai son abunda yake so, idan kika yi haka dole ne ya sauko, ya saki jiki da ke, anan zan rika gani, don dutsennan da na nuna miki zai rikida ya koma ja, idan ma baki yi ba to ba zan gani, don idan dutsen nan bai koma ja 40 23 Bakı Biyu e Sameera Mustapha: baki dayansa, aikin da zan yi maki ba zai yiwu ba. Da sauri ta ce, don wannan ai kadan ne, zan bishi ko don bukata ta biya, ya yi kyau to ina so ki bashi hadin kai dari-bisa-dari akan auren da yake son yi, don na ga duhu a auren kila ma ba za ta fi wata ba ta bar gidan, wai amma na ji dadi, ai ban gama ba ya fada yana fitar da wasu kullin magani sun kai ashirin, kala-kala kuwa. Hajiya matso kusa kema ki ji ke kin san ka'idojin aikina, idan aka kauce dole ne a sake daga farki, eh gaskiya ne na sani. A cikin kankanin lokaci ya zayyane masu komai yadda za su yi amfani da shi, ita dai Suwaiba saurare take yi, amma kila kwara uku ta rike suma din don kalar ledar maganin daban ne. Bayan an kwana biyu, Mama ta bugawa Tahir ta ce tana son ganinsa, bai bata lokaci ba ya je Gusau, ya yi mamakin irin tarbar da suka yi masa su dukansu, Mama ba ba Suwaibar ba. Haka aka yi masa girki kala-kala, duk da ya bayyana mamakinsa a fili, ba su nuna masa wani abu ba, Mama sai jan shi da hira take, yi can ta ce ga abinci can da Suwaiba ta shirya masa, а zuciyarsa ji ya yi ba zai iya cin abincin ba, duk da yana jin yunwa ya mike kuwa ya je ya bude kololin yana dubawa, sakwara ce da miya ugu tasha egusi, sai farfesun kayan ciki da kuma 24 Baki Biyu Sameera Mustapha: papper chicken sosai abincin ya shiga ranshi, sai dai bai yadda da shi ba, don haka ya dauki ruwa yana sha ya ce Mama gashi shigowa ta kuwa sai da na ci abinci gun Hassan, amma babu damuwa zan ci anjima ajiye min, kallon kallo suke yi da Mama da Suwaiba, ya gani a fuskokinsu, basu ji dadin hakan ba, sai ya share kawai ya ci gaba da cewa, Suwaiba na maida aurenmu, tunda baki wuce iddar da ke kanki ba, sai ki shirya mu wuce tare, dadi ne menene? Itama ba ta sani ba ya tsinka mata tunani da ya ce, bari in fita zan dawo da daddare akwai wani member na house of reps, da nake son gani, Mama ta ce haba dai ko hutawa ba za ka yi ba? Mama dole ne mu je neman na abinci, ko tayi mana addu'a kawai. To shi kenan Allah ya tsare ya bada sa'a. Tabdijam ya fada a ransa yau za ayi ruwa ya shigo gari basu sa in sa da Mama ba, anya wannan abu gaskiya ne? Ya tambayi kansa, to zai bi su yadda suka shirya kansu, sun jira shi har dare amma bai dawo ba, takaici kamar Mama ta fashe, amma ya zata yi an ce dole ne su lallashe shi ya saki jiki da su, sai wajajen karfe sha dayan dare ya bugowa Suwaiba waya yana fada mata meeting ne ya tsayar da su yanzu haka basu tashi ba suna nan suna tayi don haka sai ta shirya gobe su wuce, ta shagwabe masa kai Dolly tun da ka shigo garin nan nake son ganin ko fa abincin da 25 Baki Bivu. e Sameera Mustapha: na yi wahalar yi ma ya zama a banza kenan, shi ma sai ya biye mata ya ce, oh suith a ba wai da gangan ba ne ki san fa dole mu nemi kudi saboda ku, ta yi dariya na jin dadi, to shi kenan Dolly babu komai Allah ya kai mu goben suka yi sallama. Lallai maganar Boka Jalli ya soma zama gaskiya, to amma anya ita zata iya sharing din namiji da wata kuwa? Gashi da alama gida daya zamu zauna, duk dai da kanta take magana. Тo shi kenan za'a gani ya zaman zai kasance don ta san zafin kishi ta yana iya birkice komai. Tare suka koma da Tahir sai da suka biya Kaduna gun Gwaggo sannan suka wuce Abuja, sai dai ba su sami Dayyiba gidan ba. Washegari suna karyawa ta dube shi tana yi masa barkwanci, ango, ango kasha mai, ya ce ke kuma uwargida sarautar mata. Yo kai amaryar a ina za ta zauna? Sai da ya hadiye dankalin da ke bakinsa, sannan ya ce, a can side, ya nuna da hannunsa. Ta dubi inda hannunsa ke nuni, gefen shima kusan irin nata ne dakuna biyu da toilet a ciki sai dressing rooт. Ajiyar zuciya ta yi, to Allah ya sa muyi zaman lafiya kai kuma ka kwatanta adalci tsakaninmu, har a ransa ya ji dadin furucinta, sai dai ba ya son ya nuna mata hakan don dai ya lura wannan zaman da alama tana son suyi zaman 26 Baki Biyu Sameera Mustapha: lafiya, ya yi gyaran murya da yasa ta dube shi amma idanunta sun kankance don tsabar kishi, ya gano hakan shi yasa ya ke son ya kwantar mata da hankalinta, don haka ya rike hannunta ya ce kada ki zarge ni wallahi nima ban taba sa ran zan auri mata biyu ba, kaddara ce na sani kin sani a baya muna zaune cikin kunci amma nayi miki alkawari in har ki ka dage aka yi zaman lafiya a gidannan, to za ki same ni mai sauki da adalci insha Allahu." Duk da hawayen da suka taru a idonta, haka ta daure ta hadiye su ta na cewa, to Allah ya baka ikon yi. Ta karasa cin abincin nata, shi dai ya yi saurin barin gidan kada shirin da suka fara ya barkacе. Yana tafiya ta shige daki ta kwalla ihu tana kuka tare da magiyar ta shiga uku anya zata iya bada hadin kai kamar yadda Boka Jalli ya bukata? A wannan ranar ta sha kuka, akan dole ta hakura don ita kanta kukan ya ishe ta. Wannan karon kam ta ga canji sosai a tare da zaman su, ko dawowar da yake yi cikin dare ya daina, a Masallacin da ke hade da gidansa ma yake sallah magriba, ita ta san da zata daure a zauna lafiya to da ba karamin dadi zata ji ba, amma sam bata ma taba kawo batun hakuri a zuciyarta ba, don ganin take yi an cuce ta, ita ba zata iya ba zama da kishiya, tana ita din ce za ta 27 Baki Biyu Sameera Mustapha: zauna da wata aba wai kishiya, tana hakuri ne kawai don su cimma nasarar su. Babu ranar da ba a barbada mishi magani cikin abincinsa, kuskuranta daya bata tatance kwantancin da aka ce ta zuba, sai dai ta auka, a ganinta idan an zuba da yawa zai fi aiki da sauri kila ma ya ki auren. Amma ba ta san tana 6ata shirin Boka Jalli ba ne. Tare suka hada lehe, babu abinda aka saya guda daya, duka biyu ne yadda ya yi wa Amarya haka ya yi wa uwargidansa, set biyu na akwati ya yi masu, ta zabi nata har da mota ya canza mata sannan baki daya ya canza yanayin gidan, a kala falon gidan ya kai guda uku, sai dakin shi da yake dauke da waiting room sannan kuma a ciki akwai dressin room. Shi dai Tahir bai taba zuwa tadi ba, a tunaninsa sai Gwaggo ta ba shi izini, amma ya ji shiru. Tun da aka bashi mata yake jiran ya ji anyi masa iso don su gana da Amaryar tasa. Ana saura sati uku daurin aure ya je Kaduna, amma bai samu ganin Dayyiba ba, daga gidan Gwaggo sai ya wuce gidan abokinsa, ya tarar ma Badiya ba lafiya, amma taji sauki. Bayan sun gaisa yake bata labarin abunda ya kawo shi Kaduna, ko tana da masaniya akan abunda ke faruwa ko yarinyar (Dayyiba) bata sonsa ne? 28 Baki Biyu Sameera Mustapha: Ita dai Badiya ta san Dayyiba ba karamin dace tayi ba, gashi sam ta ki ta kwantar da hankalinta duk ta lalace ta fita hayyacinta..." Ya katse mata tunaninta, Mamana wai me ke faruwa ne? Ya za'a bari ya hadu da matar ba, ballantana su gana, shiru ta kara yi don bata san abunda zata fada masa ba, ta ma rasa ta inda zata fara, sai ta wayance tayi fara'a, ta ce kai kuma mene ne na sauri, hala ba ka santa ba ne? "kin san Allah zan iya cewa ban san ta din ba, don ina ga sau biyu na taba ganinta a gidan Gwaggo, shima din ba kallon kurilla nake mata ba, don na lura bata son in yi mata magana." Ta yi dariya ta ce, kai Tahir baka da dama. To kila Gwaggon taka ita tasan dalilin rashin baku damar zantawa da juna, don haka sai ka same ta don kun fi kusa, ai nayi kusan aikatawa, ke dai Mama next zuwa da zan yi dole ne in ganta, kin san fa tunda Gwaggo ta kulla wannan al'amari sai na ji dadinsa, na samu kwanciyar hankali, gani nake yi duk matsalata ta kau, na samu natsuwa kuma da Dayyibar, wani irin bala'in tausayi Tahir ya ba Badiya, in ya san irin tashin hankalin da ake yi da ita akan auren sa da ya tsinka mata tunanin da take yi, Mamana bari in wuce sai na kara shigowa,Allah kara sauki. Ta mike ta raka shi. 29 Saki Biyu e Sameera Mustapha: ** Ina school mun gama jarabawar ranar muna tare da Amina, sam bana sha'awar komwa gida don a ranar aka ce Tahir zai zo gidan, sai na bi Amina gidanta. Ina zaune a falonta nayi shiru ashe Amina tana ta yi min zance ni kuwa ban san ma tana yi ba, don na yi nisa a tunani. Ta zauna gab da ni ta ce, "habna 'yar uwa, ki sani aure fa ba mutuwa ba ce, ki sassauta ma kanki mana, kada fa wani ciwo ya kama ki, na ce dama na mutu Amina da na huta, wallahi bana son sa bana kaunarsa, gashi bana son in ki yi wa Gwaggo biyayya, na daukar wa kaina alkawarin ba zan taba kin abunda ta nuna sha'awar in yi ba, hawaye ne duk ya bata min fuskata, ya ya zan yi da rayuwata? Na tsani family din su baki dayan su. To ai ke Dayyiba ba ki so ne ki gane, don Allah ya halicce shi a gidan ba shi zai sa ya zama daya da su ba, ba fa mahaifiyarsa ta rene shi ba, ni kuwa ina kyautata zaton shi halinsa daban ne, idan shi halinsa daban ne da na familinsa to ki sani shima ai namiji ne ni fa babu abunda bana so a rayuwata, irin namiji na tsane su, basu da amana, mayaudara ne in ban da burin su su maida mata bayin su ba su da komai a akan ta, don haka ne a kullum nake kara nisanta kaina daga gare su. 30 Baki Biyu Sameera Mustapha: Amina sosai ta zauna ta ce, "haba Dayyiba, ana baki kina roko, ki sani sa duk wannan hali na maza da ki ka zayyana duka mata ma na dashi, a karshe ma in fada miki mace ita shaidan ce, duk da ba a taru an zama daya ba dole shaidancin wata ya fi na wata. Tabbas maza a yau sun zama abunda suka zama, amma ki sani mata ma hakan suke shi yasa a gun Allah zunubanmu daya ne, a kan aiyukan mu, shi Allah bai bambanta ba, dukanmu bayinsa ne babu wanda ya fi wani face wanda ya fi tsoronsa, abunda nake nufi anan shi ne, kiyi wannan aure saboda Allah kiyi auren nan saboda bauta masa da biyayya a gare shi, tunda shi ya umarce mu da muyi aure mu raya Sunnar Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi. Bari in dan baki labari, ko in ce tarihi akan wani lokaci da Annabinmu (S.A.W) yana zaune shi da taron mata a ciki har da Nana Aisha (Allah ya kara yarda da ita) kin gane taron an yi shi ne musamman dan a fadi halayar maza ma'aurata wato ina nufin zamantakewar da mata ke yi da mazajen su, kin san duk watà damuwa da mata ke ciki a wannan lokacin tare da mazajen su suka zayyana? Amma to make the story short, ta mike ta bude dorowar da take ajiye "disc" din ta ta zaro guda biyu ta kawo min ta ce, gasu ina so don Allah idan kin samu dama ki saurari wadannan "CD disc din 31 Baki Biyu e Sameera Mustapha: ki ji abinda ya kunsa, na karba ina kallon rubutun da aka yi wa'azin marigayi Sheikh Ja'afar Mahmud Adam ne, zaбаbбun loссосі bakwai akan aure da tarbiyya (1) Mata a Alkur'ani mai girma (2) Siffar mace mumina (3) wacece mijinta yafi? (4) Bita-zai-zai (5) Tarbiyar yara a Musulunci (6) Hakkin 'ya'ya a kan iyayensu. Ta ci gaba, "Ba ke kadai ba ya kamata duk wadda ta ji sanarwar nan ta nemi kaset ko disc itama ta saurara ta ji ma kunnanta abinda ya Kunsa. Ke kin san mace kuwa Dayyiba? Ina so ki sauko ki lura, wallahi mu ma mayaudara ne, mu ma muna son mu maida namiji bawa in dan mun samu dama, sannan mu ma ai maciya amana ne, na dakatar da ita na ce, na sani mu ma muna da namu amma maza sun fi, him bari in fada miki wallahi kowa kansa ya sani, amma in an zo fadin gaskiya a fade ta, bari kiji wani dan misali, akwai wani mutum mai arziki yana da dukiya sosai, bai cika zama ba yana da mata uku, kowace yana tafiya da ita wata shidda-shidda kamar yadda suke tsarawa, matarsa ta biyu ita се shaidan a gidan, don ita za a ce kamar yafi dasawa da ita, saboda barikancinta ne oho! Tana fita zina sannan ya dauki dansa na fari ya bata amanarsa, taje tana kwana da yaron suna aikata 32 Baki Biyu Sameera Mustapha: aikin assha! A uzubillahi mina shaidanin rajin, na yi saurin fada, ta ce eh kwarai haka ya faru, don Allah mi za ki kira wannan cin amana ce yaudara ce shin me za ki kira wannan labari da na baki? Ajiyar zuciya nayi, labarin ya sa jikina ya yi sanyi, lallai ana abubuwa a duniya, Allah shi kadai yasan irin zunuban da muke daukar wa kanmu, Allah ya shirye mu, Allah ya shirye mu abunda nake iya fada kenan, ban iya cewa komai ba ta ci gaba don Allah 'yar uwa ki kwantar da hankalinki guda daya ki karbi kowacce kadara ce ta zo maki, na turo baki ni fa Amina bana son wannan mutumin ne, ta mike cike da jin haushi, to kada Allah yasa ki so shi, na gaji da baki shawarar....haba kawata, wallahi na yadda da duk abunda ki ka fada, ni dai kawai bai min ba me yasa ba za su bani dama ba, in zabi wanda nake so? shiru tayi ba ta ce min komai ba, na san takaici ne ya ishe ta, na san hakan, haka muke da Gwaggo ma a kullum har ta gaji tasa min ido, sai dai in in ta koke-koke na amma bata ce min kala. Nayi saurin canza hirar, Anty Amina ina Abdulkadir din ki da sauki ko? Yau na zama Anty, to tunda na fada miki gaskiya, a'ah wallahi ba haka ba ne na dai ji an gidan ku haka suke kiranki, ke dai ki ka sani, Abdulkadir kuwa a gaskiya da sauki, ban dai san waje ba, kin san 33 Saki Biyu Sameera Mustapha: fa shi gyara a hankali yake shiga, a gaskiya saukin da na gani shine irin daren da yake yi a da ya daina, don yanzu haka anan abincinsa yake da Krafe goma tayi zai shigo ya ci muyi hira, sannan nayi masa tambaya akan shaye-shaye ya yi min rantsuwa ba shi ne da shaye-shayen ba Dahiru ne dan yar mahaifiyarsa, lokacin da ya yi hutu a gidanne yake sha, dalilin barin gidan ma kenan da ya gano ya yi masa magana ya yi fushi ya tafi abunsa. To Allah ya shirya, na mike tsaye ina dubedube, ta kalle ni ba dai tafiya ba? Tafiya kuwa zan yi don na san wannan mutumin ya tafi, na fada ina kallon agogo, kin ga har karfe shida tayi, sai Allah ya kaimu gobe, hum ke fa saura mana papper uku next week, zamu gama ke dai bari yadda ki ka san ana jan kwanakin sai sauri suke yi ban san me yasa ba, kenan dai nan da sati biyu za'a fara biki gashi kin ki fitar da anko, mits nayi tsaki na ce, ke da Allah rabu da ni ankon me? Zan fitar sai ka ce dama auren so zan yi, ke fa ki ka dauka aure zan yi, amma ni a guna da auren da babu duk daya. Amina kallona take yi bata ma san abunda zata ce ba, Allah ya ganar da ke amma kin fi karfina. Da sauri na bar gidan naje gida amma abun mamaki gidan namu akwai baki, motoci ne har

Chapter 2 of 8