irin rayuwar da suka
daukar wa kansu suna burge ta, ina ma ace itama
zuciyarta ta zama irin ta su. Idan ta koma gida tayi
kwantacin abunda suke yi ita da kişhiyarta Dayiba,
ita tasan ba wanda zai damu da dacewar ta don
sam bata da kirki, kai a Nigeria bata da wanda take
shiri da shi 'yan uwanta ma bata damu da su ba ko
waya ba su yi, iyayenta ma sai suyi wata bata yi
magana da su ba, haka zata zauna tana kuka tana
tuna irin halayen ta na banza da tayi a baya. Cikin
kwana ki nan bata da sukuni ko kadan a
rayuwarta, in ta tuna da abun son ta kuwa Tahir sai
ta kara bakin cikin halin da ta shiga, bata samun
bacci da daddare saboda tunani da ya yi mata
yawa. Da yake dakin amaryar aka ajiye ta saboda
duk 'ya'yanta ba mai kwana gunta suna dakin
uwargidan dama gefen Baban su dabanne, ita ta
lura da yanayin halin da Suwaiba ke ciki, don haka
a wannan daren da ta ji Suwaiban ta suma kuka
shine ta matso kusa da ita ta dafa ta, Suwaiba tasan
haka sai ya faru saboda bata iya 6oye damuwarta,
ai sai ta saki kukan baki daya a daren kukan
tausaya ma kanta tayi, ita kam belly bata iya cewa
komai ba, itama hawaye ne ke zubar mata a ido,
duk wanda ya kalli Suwaiba ya san tana cike da
85
Baki Biyu Samcera Mustapha:
damuwa, to amma ya zata yi sai hakuri tana
rungume da ita har sai da ta sassauta don kanta,
sannan ta dago suna kallon juna, idonta dai bai
daina fitar da kwalla ba, ta ce ki taimake ni don
Allah Belly ta riko hannunta, ta ce zan taimaka
daidai gwargwado, ki fada min abunda ke damun
ki, ki sani ba zamu ta6a sanin abunda ki ke ji ba
sai in ke ki ka fada mana, tunda ki ka zo gidan nan
muke tambayar ki duk da ba laifinki ba ne da farko
kina tare da firgita da har ba ki iya cewa komai, ki
godewa Allah na ki yazo da sauki, saboda karfin
halinki."
Ta rike hannunta da karfi wanda yasa Suwaiba
ta kalle ta, "ki fada min daga inda ki ke zamu
taimaka maki insha Allahu, ki koma in da ki ka
fito."
Suwaiba ba ta san lokacin da ta soma bata
labarin rayuwarta ba, tun tana karamar ta har
lokacin da ta kai kanta mahalaka. Belly ta ce,
"kada ki damu ke ki gode wa Allah, ya baki ikon
ci gaba da rayuwarki, don haka ki shirya gyara
kanki ki natsu ki roki Allah gafara, Allah maji
rokon bayinsa ne, haka kuma Allah gafururrahimu
ne, insha Allah zamu taimaka maki ni da 'yar
uwata, kafin ki koma...."
Ta katse ta "Ni ba zan koma ba, sai na ga
abunda na zamar da rayuwa ta, ina son in san
adinina don haka in zaku bani dama in zauna da ku
in kowa to da kun kyauta min."
86
Baki Biyu Ο Sameera Mustapha:
"Haba, ai mu abun farin ciki ne a gare mu, don
haka Allah ki kwantar da hankalinki, insha Allahu
gobe zan samu 'yar uwata in fada mata sannan mu
fada wa maigidanmu. Tun da ta bace bata taba
samun bacci irin na yau ba, har ta so ta makara.
Haka aka yi kuwa, washegari Belly ta fada wa
Binta abunda ake ciki, sosai tayi farin ciki da
wannan abu ai ba su jira wani abu ba suka sami
mijinsu da wannan zance, shima ya bada goyan
baya dari bisa dari.
Tun daga lokacin Suwaiba ta shiga Makarantar
Mal. Attahiru, da kanshi yake koyar da ita suna
karanta Alkur'ani mai girma a kullum, sai sauran
littattafai irin su fikihu, sira, Hadisi, da dai
sauransu. Aka raba kwanakin da za'a rika
karantawa, ai cikin ikon Allah kuwa Suwaiba tana
ganewa, da yake kun san an ce 'sa kai wanda ya fi
bauta ciwo' in ji 'yan iya magana.
Ta kuwa kwantar da hankalinta, duk wani aiki
na gidan tare suke yi, hatta daka da bata taba ko
taba tabarya a rayuwar ta ba, sai gashi a yau har
ma da girki tana yi, ba ma akan murhu ba, a'a akan
dutse da aka jera sannan ba da itace ake girkin ba,
da kara ake yi. Kai rayuwa kenan, babu inda bata
kai mutum, a rayuwar Suwaiba bata taba sanin
akwai wahala a cikinta ba sai yau gata tsamotsamo a cikinta, Allah yasa mu dace, amin.
A Nigeria kuwa, ni kam abun sai hamdala,
87
Baki Biyu Sameera Mustapha:
gashi na kama karatu sosai, babu wasa a cikinta
don muna shekarar karshe a yau sati na uku kcnan
a Kaduna, amma ba mu yi magana da Tahir ba, sai
dai kuma abun ya fara damuna, tabbas nasan Tahir
yana da kwatancin halayen da Gwaggo ke fadi, to
amma abunda ban gane ba shi ne, irin halayen da
Anti Suwaiba ta fada min har yau ban ga ko daya
daga cikin su daga gare shi ba, na tabbata idan
wani namijin ne to ba yadda za'ayi yasa min idon
yana kallona, a wannan zamani idan zan tuna yau
kusan wata goma sha daya kenan da aurenmu sai
dai babu abinda ya faru tsakaninmu, kuma sam bai
taba nuna damuwarsa. To ai dama shima ba sona
yake yi ba kamar yadda nima bana sonsa, don
haka baya da laifi. To menene dalilin wannan aure
da ba so a cikinsa saboda Allah! Su iyaye ba za su
tsaya su kwantar da hankalinsu gu daya ba, su yi
tunanin abunda ya dace da mutum ba, wani
lokaci..." wayata ta tsinka min tunanina, da na
duba number Tahir ce, a raina na ce, dan halak
kamar yasan tunaninsa nake yi.
Sai da tayi ta ringing kafin na dauka.
"Hello!" Ya ce, "Assalamu alaikum." Na amsa
masa, sannan na yi saurin fara gaida shi.
"To ya karatun?" Na amsa a dakile. "Lafiya."
"Ni ban gane ba Dayiba, anya kina da number
wayata?"
"A'a ban da shi." Na yi saurin ba shi amsa, ya
dan yi shiru kadan ya ce, "Dayiba ni nasan na aure
88
Baki Biyu Sameera Mustapha:
ki ne da zuciya daya, amma da alama ke har yanzu
ba ki gano hakan ba." Shiru nayi ban ce komai ba,
sai ya ci gaba. "A yau kusan watanni biyu bamu
tare, amma ko ki bugo ki ji ya nake, ko gaisawa
muka yi ai ba laifi ba ne ko, tun ina sa maki ido
har na gaji shin me ki ke so in yi ne? Duk na ma
rasa ta inda zan fara 'yar kanwar Gwaggo me ki ke
so in yi miki ne? Ina daga miki kafa ne don bana
śon in takura ki, ba na son in fiye son kai da yawa
amma ke na lura ba ki ma gano hakan ba. Ina lura
dake kayan lefe ma ba ki taba sawa ba to a nan na
gano ba karamin kiyayya ce tsakanina da ke ba,
shi yasa na yi kokarin kauda idona akan
al'amuranki, sai dai ke ba abunda ya dame ki,
saboda tsabar rashin son da ki ke min."
Jikina ya yi sanyi da bayanin Tahir, tunda na
daina son da namiji a rayuwata, wallahi ban taba
tausaya masa ba sai yanzu, ni nasan ina yin abunda
ba daidai ba, to amma ko na so in daure in hakura
da kaddarar da ta same ni, sai in kasa. To menene
abin yi? Tambayar da na jeho wa kaina kenan.
Ya tsinka min tunanina da ya ce, "Hello! Kina
jina kuwa?" Da sauri na amsa na ce, "Eh, ina jin
ka me ki ke so in yi wanda zai ba ki ikon ki sauko
muyi zaman aure tsakaninmu?"
Hawaye ne ya taru a fuskata, amma ban yadda
sun gangaro ba, na kasa cewa komai sai dai a raina
ina tausayawa kaina, ina kuma tausayawa Tahir
don a gaskiya duk da ban san shi sosai ba, yana da
89
Baki Biyu Sameera Mustapha:
hakuri, a da na dauke shi daya da sauran maza, a
gaskiya yanzu na gano ba kowa ke da halin wane
ba, to me zan ce masa? Ban san lokacin da na
motsa baki na ce "kayi hakuri ba, nima kaina abun
ya bani mamaki, da alama shima abunda ya ji
kenan, don da sauri na ji ya ce, "Babu komai ai
hakuri ya zama dole, ko in dawo ne mu hadu?"
"Ba aiki ka ke yi ba?" Na tambaye shi.
"Gaskiya aiki ne sosai a tare da ni, nan
Thailand, amma ban sani ba ko idan nasa aka yi
maki visa za ki zo ba."
Shiru nayi ina tunani, anya ayi haka? Ka daure
dai har ka dawo nan kaga saura 'yan watanni in
gama karatuna."
"Haka ne, ai ni na ma manta da karatun
Dayiba, wallahi bukatarki kawai nake yi."
Murmushi na yi, na ce, "To ka bari in gama
karatun sai ayi zaman da hujja."
"To shi kenan, Allah ya nuna mana, sai dai ina
יי
son in nemi alfarma daya daga gare ki."
"Ina saurarenka, Allah yasa zan iya." יי
"Insha Allahu ma za ki iya, ai ba wahala."
יי
"To shi kenan, fadi abinda ka ke son."
Sai da ya yi ajiyar zuciya sannan ya ce, "Don
Allah ki rika bugo min waya muna gaisawa, ki
sani ko muryarki na ji hankalina zai kwanta."
"Ai kuwa insha Allahu zan fara, kada ka samu
damuwa." Ya ci gaba da cewa, "To shi kenan,
Allah yasa, kila ma in shigo nan da sati biyu masu
90
Baki Biyu
zuwa insha Allahu."
"To Allah ya yadda."
Θ Sameera Mustapha:
Nan dai muka yi sallama. Tabbas da alama
Tahir daban ne a cikin 'ya'yan Hajiya Basira, kila
ya dauki hali mai sauki irin na mahaifinsa ne, mahaifinsa yana da saukin kai sai dai ba za ka
gane hakan ba sai idan kana kusa da shi, a da shima ina yi masa kallon irin Attajiran nan masu wulakanta Jama'a, ashe ba hakan ba ne ni na dauka haka, saboda tsabar Kuruciya. Na daukar wa kaina alkawarin zan rika buga masa kamar yadda ya bukata a kalla sau biyu a wuni.
Haka din aka yi, ina buga masa wayar kuwa
sau biyu a wuni, safe da yamma. Shi kuwa da rana da daddare tun bana sakewa muyi hira har na fara. Sai muyi kusan minti talatin muna hira da daddare duk da shi ne ke yawanci hirar kuma bai wuce
hirar aikinsa, a gaskiya suna aiki, kai kama samu dadin dukiyar da ka tara wahala ce, a gaskiya rayuwar dan Adam baki daya wahala ce, kamar yadda Allah (S.W.T) ya fada, talaka bai huta ba, mai arzikin shima bai huta ba, a kowane sati zai sa
a sa min kudi a account yanzu haka cewa nake yi
ya bari haka nan har in kashe wadannan ya ki, ina ganin a jiya alarm dina ya shigo an turo min kudi a
account da na duba sai naga ina da kusan million daya da rabi, na shiga uku ina zani da wannan
kudi haka? Shin shi ba ya jin zafin su ne a
rayuwata ta duniya ban taba tunanin zan rike kudi
91
Baki Biyu Sameera Mustapha:
masu yawa irin wadannan ba, duk da kyautar da
nake yi don a kowane sati dole ne in aikawa Baba
a kalla dubu hamsin, Baba kuwa dubu talatin
shima kansa Baba yana min gargadin in yi a
hankali kada fa in zama irin matan nan masu
daukar wa kansu in da ba su kai ba, nakan fada
masa ba ni nake yi ba wallahi haka Tahir yake min
ni bana ma sanin zai turo sai dai in ji alert kawai.
Na tashi ina da kwadayin son kudi, amma wallahi
yanzu tsoron kudin ma nake yi, don ban taba
tunanin zan samu hakan ba. Allah kenan, babu
abinda ba ya iya yi cikin lokaci kankani.
Suwaiba kam an zama 'yan Daji, har da fulanci
ta soma yi, duk da ya banbanta sosai da na nan
kasar, gashi sallah, ibada baki daya ta dauka ta
rungume abun gwanin sha'awa. Cikin watanni
biyu da kusan rabi Suwaiba ta canza rayuwarta,
ikon Allah, gashi a yau ta zama mace mai kamun
kai, wadda tasan hakki da darajar addininta, tun
tana kyamar abincin gidan har ta soma son
abincin, gashi ta koya ta iya zama garin kamar
dama da haka ta tashi, duk da tana tunanin gida a
ranta haka ta daure tana ci gaba da zama so take yi
ko izifi talatin ne ta kai kafin tayi tunanin tafiya,
da yake tasa kai ta maida hankali sosai gashi nan
har ta kai goma.
Ni dai ina Makaranta ina zaune gidan amina da
yake mijinta ba zama yake yi ba, kuma gidan da
92
Baki Biyu 2 Sameera Mustapha:
dakuna sosai, sannan sashen sa daban nc. Gwaggo ta kira ni take bani labarin Suwaiba ta
bace tun wata uku da suka wuce, hankalina ya tashi sosai don rabo na da ita kenan watanni kusan
hudu kenan yanzu, ba shiri na wuce Abuja. Ai
kuwa haka din ne Suwaiba bata gida maigadi ya ce
tun da ta fita da daddare bata sake dawowa gida ba, abun da yasa bai yi magana ba shi ya zata da
sanin maigidan, wayoyinta baki daya a kashe suke. Tahir shima sai da abun ya kai wata biyu shine
ya soma damuwa da rashin sanin inda take, ya san halinta kowane irin tashin hankali su kai, bata
wuce kwana uku zata neme shi, don bata iya gaba ba, to shi kuma da ya ji shiru shi a zatonsa ta
amince da sharudan da ya zayyana mata ne akan
ba za ta zauna ba shi yasa ma bai neme ta ba.
Mama ce take ta neman wayanta, ita kuma ta
zata fushi take yi da ita shi yasa bata nemanta a
waya, don bata manta ranar da take mata fada
akan natsuwa ta kashe mata waya shi yasa ta fita batun ta. Ana cikin haka ne Mama dai ta shirya ta je Abuja, yadda Suwaiba ta bar gidan haka ta iske shi a lokacin kuwa ana kusan wata biyu kenan da
ta bar gidan.
Yadda dakin yake a yamutse duk yawancin
kayan alatun dakin a fashe suke ga shi dakin ya yi kura, shi ya tabbatar mata da Suwaiba bata gida,
shi ne fa ta kira Tahir ya fada mata abunda ya sani
ta yi mamaki da Suwaiba ta tsallake ta ta wuce
93
Baki Biyu Sameera Mustapha:
gida mahaifanta, to fa Mama sai ta dauki zafi da
'yar uwarta, ita a cewarta ya za'ayi irin haka ta
faru har yarinya ta tashi taje gida amma a kasa
kiran ta a fada mata, shi ne da ta fito ta ke
tambayar maigadi kwananta nawa rabonta da
gidan? Ya ce, wata biyu kenan ita kuma sai kawai
ta wuce Gusau ta yi banza da 'yar uwar tata, shi ne
lokaci ya ta tafiya, Mama dai abun ya daure mata
kai, ta kasa hakura ta buga wa mahaifiyar Suwaiba
tana nuna fushinta akan abunda ke faruwa, Hajiyar
Suwaiba ta ce, wa Suwaiba ai bata Lagos, rabon su
da ita tun lokacin daurin auren Dayiba, haba dai
Mama ta fada hankali a tashe, ka dai ki ce bata
tare da ke? Humm, in dai Suwaiba ce waya ma sai
taga dama muke yi, tabbas kwanan baya na neme
ta waya shiru, har sau biyar duk da ba a lokaci
daya ba da yake kin san halin ta da rigima zato na
ko miskilancinta ne ya motsa don sai tayi wata ni
ba mu yi magana ba, ba akan komai ba sai don ina
mata fada akan irin rayuwar da ta daukar wa
kanta.
Mama na jin haka, ta sake neman Tahir ta fada
masa abinda ake ciki, nan fa aka fara nemanta
gidajen 'yan uwa da abokanta da aka santa tare da
su. Abu kamar wasa, yau kusan sati biyu kenan
shiru, sam mahaifanta ba su damu sosai ba, a
cewar su kila ta gudu ta koma America ne in tai
tsami ta dawo, Allah ya shirye ta.
To akan haka ma aka bar shi kenan ta gudu ne
94
Baki Biyu Ο
Sameera Mustapha:
saboda anyi mata kishiya, wasu kuma su ce fadan
da suka yi ne da Tahir yasa tayi fushi ta buya, don
ta daga ma mutane hankali. Humm hali kenan da
yake kowa yasan halin Suwaiba da fitina shi yasa
kowa bai yi mamakin 6acewar ta ba, 'yan uwan ta
ma sam basu damu ba, saboda dama sun san zata
iya kwantacen abunda ya fi ma hakan, a gaskiya
na yadda da ake cewa yanzu dabba ake kiyo ba
mutum ba ne, shi yasa ma aka ce a lahira ana
amfani da irin shaidar da aka yi ma mutum, Allah
ya shirye mu yasa mu gama lafiya (ameen).
Kwanana biyu a Abuja na koma Kaduna don
kowa ma harkar gabansa kawai yake yi.
Suwaiba fa? Tana nan a Cameroon rayuwa
gaba ki daya ya juya, ita kanta tana mamakin
kanta, ashe mutum na canza hali akan tashin
hankali? Ita kam ta gani a kanta, iyayenta babu
abunda ba su yi ba akan ta natsu ta zama
mutuniyar kwarai amma ta ki gashi don kanta ta
natsun dama ai Allah ne ke shiyarwa sai dai mu
muyi kwatankwacin namu tarbiyan ga 'ya'yanmu,
saboda shiryuwa na gurin Allah, Allah yasa mu
dace (Amin). Gashi yanzu Suwaiba ta zama
mutum, sallah bata wuce ta ga yawan nafilfili da
kuma Istigifari ga Allah, haka cikin dare zata rika
sallah tana addu'a tana kuka ita ta san tayi ba
daidai ba a da, babu abinda take godiya ga Allah
akai sai yanda ya nuna mata yadda rayuwa take
95
C
Bakı Biyu e Sameera Mustapha:
gashi a yau ta samu ta kuma dandani rashi ta kuma
gano matsalar ta, kuma ta dauki aniyar ceto
rayuwarta daga halaka. Allah ya ganar da wadanda
ba su ganc ba (amin). Ya kara shiryar damu baki
daya.
Sai da Tahir ya sami kamar wata uku rabonsa
da gida, ni kuma a lokacin na sami hutu, duk da ba
wani hutu ba ne na sati daya ne, a ranar da muka
yi hutun a ranar na koma Abuja, don Gwaggo ta
turo mota ta ce in zo gida. Abun mamaki Tahir na
nan, sai dai wai bai jin dadi, a gaskiya ya dan fada
ashe wai tun a can baya da lafiya, karfin hali ne
yasa ya zauna don ya karasa aikin da ya kai shi.
Ulcer ce gare shi, sosai ta kama shi, a yanzu haka
ko abinci baya iya ci sai dai abu ruwa-ruwa, ba
karamin tausaya masa nake yi ba, ko magana bai
cika yi ba, a dalilin haka ne nake cusa kaina a
al'amuransa, gashi sam baya son zancen asibiti sai
dai Doctor ya zo gida ya duba shi.
Ina da kwana hudu a Abuja, ciwon Tahir ya
tsananta, har sai da aka kwantar dashi National
Hospital a nan Abuja. Abu ba na wasa ba ne, don
ba a bari ma aje gunsa, ai tuni hankalin family ya
tashi, mahaifansa da 'yan uwansa sai tururuwa ake
yi ana duba shi, duk da ana hana ganin nasa. Ni
kam abun ya soma bani tsoro, don da aka tambayi
Doctor abinda ke damunsa cewa sukai jininsa ne
ya hau sosai, ga kuma ulcer tayi masa yawa don
gyambon har ya kai hanjinsa, suna so suyi masa
96
Baki Biyu Sameera Mustapha:
aiki ne to amma kuma ba za su iya yin aikin ba har
sai jininsa ya sauka.
Jikina ya yi sanyi sosai, nan da nan kuma na
rame don ina tunanin abunda nayi masa, yana
matsayin mijina idan ya mutu bai yafe min ba ya
zanyi in ban da rike hannuna da ya yi sau biyu bai
taba ko runguma ta ba, na shiga uku, duk wanda
ya kalle ni yasan ina tare da damuwa ba kadan ba,
ko abinci ba na ci kwata-kwata, wallahi ba
Karamin tausaya wa kaina nake yi ba, a wannan
lokacin. Sai da ya kwana uku bai san inda yake ba
kafin jininsa ya sauka aka shiga da shi tiyata.
Na lura ciwonsa ya yi tsanani da yawa, saboda
Doctors shidda ke kansa, ai ban san lokacin da na
fara kuka ba, Gwaggo ce ta rike ni tana lallashina
ta ce, ke ba a haka ai ba kuka za ki yi ba, kiyi masa
addu'a, ji na yi Gwaggo ta bani tausayi don idan ta
rasa Tahir nasan ba ni ce mai rashin ba ita ce.
Mikewa na yi naje nayi alwala na soma sallah,
nafila da yake karfe uku ne na rana. An dauki
kusan awa uku suna tiyata kafin suka fito, Doctors
sun nuna za'ayi nasara akan aikin da suka yi shi ne
dalilin da yasa kowa hankalinsa ya dan kwanta
kenan.
Sai da muka yi sallah La'asar kafin ya farfado,
zo kaga yadda kowa ya rika hamdala tuni asibiti ta
cika da 'yan uwa da abokan arziki, na ga Mama
tare da 'yar uwarta sun fita, sai dai ko kallo ban
ishe ta ba, da na gaida ta ma ko kallon inda nake
97
Saki Biyu e Sameera Mustapha:
bata yi ba, dama inda ba don Jama'ar da ke wurin
ba ni me ruwana da ita. Bana son in yi rashin
kunya ko rashin hankali shi yasa ban damu da
abunda tayi min ba.
A daren ranar Baba da Baba Mairo suka iso,
Tahir har yana dan kokari ya yi magana. Tunda ya
farfado ban samu ganinsa ba, saboda manyan
mutane da ke dakin gashi na matsu in je gunsa in
ga saukin da ake cewa ya' samu. Sai bayan
magariba lokacin mazan sun tafi Masallaci nayi
saurin kutsa kaina dakin, abun haushi bacci ya
dauke shi, dole na hakura na fito ina lekensa ta
glass din da ke kofan dakin, a raina na ji sanyi na
kuma ga fuskarsa tayi min kyau kamar ba mai jin
jiki ba. Daga inda nake ina kallon yadda fuskar
tasa ke sheki tayi sumul-sumul, Allah ya baka
lafiya na fada a fili, sai da na samu kusan minti
ashirin a tsaye.
Kafin na je don in yi sallah magariba, na rasa
gane abunda zuciyata ke nufi ba dai na fara son
Tahir ba? Na ji a cikin jikina akwai wani al'amari
da yake son samuna akan Tahir, na furta a waje,
Allah ya baka lafiya Tahir. Addu'a sosai nayi a
wannan daren don har lokacin bai tashi ba yana
barci.
Washegari bayan munyi sallah Asuba, ni dai
yanda naga dare haka naga safe, ni jira nake yi ya
tashi in ganshi ko hankalina zai kwanta, ina zaune
a gefan gadonsa na jingina tare da yin tagumi,
08
sunana ya kira a hankali da sauri na mikc ina
kallon fuskarsa, tayi kyau sosai, murmushi ya saki
wanda yasa na ji wani irin abu a jikina, ban san
lokacin da na samu wuri gab dashi ba na zauna,
ina yi masa sannu. Yana amsawa a hankali, ina
tausaya masa sosai a raina ban san lokacin da
hawaye ya soma zubo min ba, riko hannuna ya yi
na dube shi, girgiza kansa yake yi a hankali.
"Kada kiyi kuka, kiyi min addu'a, na dan yi
shiru kafin na ce, kayi hakuri da abunda nayi
maka ai sai na saki kukan baki daya, nasa kaina
akan gefen hannunsa a kalla nayi kusan minti
talatin a haka kafin na hakura na dago kaina.
Shima fuskarsa cike da kwalla ya rike hannuna
gam, kada kiyi kuka na yafe miki har a zuciyata.
Ai tun daga lokacin na sami sanyi a zuciyata tare
da daukar wa kaina alkawarin insha Allahu zan
zama mai biyayya da bin dokar auren Tahir dake
kaina, tausayinsa ya kama ni na rasa ta ina zan
fara taimaka masa.
Karfe takwas saura na safe Doctor ya shigo
ya duba shi ya ce a fara bashi ruwan lipton da
cokali, abun ba wuya, yanzu kam komai ya zo da
sauki da da ne sai ya kwana uku amma gashi
yanzu kwanansa daya har zai soma shan wani
abu. Daga lokacin kuma 'yan uwa akai ta zuwa
gaida shi, sai bayan azahar naje gida nayi wanka
na saka doguwar riga baka cean yi mata kwalliya
99
Bakı Bıyu 2 Sameera Mustapha:
da dutsina a wuyan rigar da kasan hannun, duk
da fadawan da nayi rigar ta yi min kyau ba kuma
komai na saka a fuskata ba. Fararen slipers na
saka, dawo asibiti abun mamaki asibitin ya cika
dam da mutane, ban kawo komai a raina ba,
saboda tunda aka kwantar da Tahir mutane ke
zuwa gaishe shi, sai dai na yau yafi samun
mutane.......tunanina ne ya katse da na lura
fuskokin kowa babu annuri, gabana bugawa yake
yi kamar zai fito...daga gefe Gwaggo ce kwance
Baba ce akanta, tana yi mata fitara meke faruwa
ne? na tambayi kaina sannan gaba ki daya na
tsinke na karasa gun su na tsuguna. Anti Badiya
ce ta riko hannuna kuka take yi sam babu
sassauci, can daga nesa Mama ce itama kukan
take yi, 'ya'yanta kuma zagaye da ita. Ba dai
Tahir ne ya rasu ba? Na fada hakan a raina kuma
hawaye na zuban min kamar ruwa. Na rike
hannunta nima na Anti meye ya faru? Ta ce tana
dubana na ciwon Tahir ne ya tashi, kin fita kenan
sai ya fara fizge-fizge sai da aka sama sa
oxygen, na shiga uku na fada ina hawaye.
Da kyar aka ciwo kan abunda ya taso ma
Tahir, suma kan su Likitocin ba su yi tsamanin
yana da rai ba, ba don nishinsa da yake fita daidai ba, sai da muka kwashe kusan awa uku kafin
Likitocin suka fito daga dakin suka ce basa son a
shiga ciki sai washegari.
100
Baki Biyu.
Suwaiba a can Cameroon ta rasa abunda ke yi
mata dadi, yau kusan kwana hudu kenan tana
fama da faduwar gaba ga kuma mafarkin da take
yi marasa kyau, duk hankalinta ya koma gida, ta
so ta yi shekara a nan har ta sauke, a yanzu ba ta
da buri da ya wuci ta sauke Alkur'ani mai girma,
sai dai da alama ba za ta iya ba don duk ilahirin
jikinta ya yi sanyi, yau ma haka ta wuni bata jin
dadin jikinta. Ba wai ciwo take yi ba, a'a jikinta
ne kawai yake a mace, tana tare da kasala. Da ta
fita gun karatu, Mal. Attahiru ke ce mata anya
lafiya ki ke Suwaiba? Ba ta 6ata lokaci ba ta
fada masa abinda ke damunta, ya numfasa ya
mike tsaye ya ce, ina zuwa. Dakinsa ya shiga ya
rufe. Tana nan zaune na kusan minti sha biyar
kafin ya fito ya zauna ya ce, Suwaiba ina so gobe
ki shirya muje garinku, naga da abunda ke
faruwa kuma abun ya shafe ki.
A sanyaye ta yi masa godiya ta ce, "To Allah
ya kai mu." Da ta isa