Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
5 / 8
akwatina ya dauko yana kwashen kayan yana zubawa. Me ka ke nufi ina Dayiban take? Tana magana tana zare ido kamar irin tana magana da danta. Banza ya yi da ita ya ci gaba da abinda yake yi, ta fusata ta isa gabansa ta hana shi ci gaba da aikin da ya sa kansa. Tana dubanshi cikin idonsa, na ce ina take ina ka kaita? Wani irin bangaje ta ya yi sai da ta fadi ta buge kanta a bango 'kwal' tuni kan ya kumbura, ta dake ta ki kuka duk da azabar da ta ji. Ta kara matsowa kusa dashi sai dai bata shige masa ba, sai dai ya ci gaba da kwansan kaya yana shirya su a akwatina, sai ta fara surutu, ni fa ba zan yadda ba dole ne ka dawo da ita gidan nan, so kake yi ka ci amanata, shi yasa ka dauke ta? To ba zan yarda ba, ya dube ta da jajayen idonsa ya ce, kin ga ki fita hanyata Suwaiba, kada ranki ya baci, ke ki ka ajiyeta a gidan nan ko ni da za ki rika yi min tambayar banza, to wallahi am warning you, kar kiyi zaton ina shakkar fata maki rai ne, ina kyale ki ne saboda darajar mahaifinki, if not da tuni na san yadda na yi da ke but let me Inform you, if am tired of your nonesense wallahi zan kore ki daga gidana, don ba ki da amfani a guna, baki da kunya Suwaiba, balle kuma tarbiya, wai ke kina ganin kina da wayau da za ki maida ni sakarai za ki san ni ba sakaran ba ne, wuri ki ka samu zan 69 Baki Bivu e Sameera Mustapha: nuna miki nima 'A' ne, ba wai ina.....mits tsaki ya ja, ban san ma me yasa nake bata lokaci na ina magana da ke ba, just be careful daga yau daga ni sai ke gidan nan, nayi kusan kaiwa bango da iskancin da ki ke takama dashi, ki san igiyar aurena biyu kacal ya rage kada ki sake ki bari in baki su a cikin ruwan sanyi kin ji na fada miki, yarinya ni na auro ta ba zaman ki take yi ba, don haka kada ki sake min magana akan ta, I have the right in yi abunda na ga dama da ita, babu ruwanki da ita, ki fita hanyata in zaman aure za ki yi to, in kuma ba za ki yi ba it should be over, I have no regret kin gane ko?" Duk maganar da yake yi harararsa take yi, tana tabe baki tasan ranshi ya baci sosai, amma don karfin hali da zai wuce ta yi saurin shan gabansa ta yi jaking din rigarsa wai sai ya fada mata inda Dayiba take, Suwaiba ki kiyaye ni I want to be honest with you ki daina wannan zancen don banga abinda ya shafe ki da ita ba, na barki nan you can do what ever you want, na kuma raba girki tunda na baki dama kun bani abuna zan rika kasancewa da kowaccen ko kwana biyu-biyu that all I concluded any kuestion? Ta fashe da kuka, wallahi ni ban yarda ba so ka ke yi ka cuce ni shi yasa ka raba mu naji ina son in cue kin sake min rigata kada ranki ya 6aci, wai ke mai wayo ko yaushe aka yi ki da zaki gwada da ni, sake min riga na ce maki kin san halina ni mai dukan mata 70 Baki Biyu Sameera Mustapha: ne don haka sai in nuna miki gaskiya, ki ka fada mata. Da taga da gaske yake yi ta sake shi, ta ce to na ji ina nema hakki na yanzu daga gare ka, bai san lokacin da dariya ta kuce masa ba, sosai yake dariyar ta mugunta ya ce ban gane hakkin da ki ke nufi ba, bayan kin ce kin yafe? Ba ki so. Don Allah kar ki bani kunya mana, jiyan nan ki ka fadi haka ko kin manta in tuna maki? Ta ce, ni wallahi yau dole ne ka kusance ni saboda ka riga da ka shirya hukuncin zama da mu haka, don haka daga yau za'a fara, wannan ne baki isa ba sai dai in ki bar gidan, nan cewa ki ka yi kin yafe don haka nima na yafe don Allah matsa min ina da abun yi. Ya wuce da akwati daya a hannunsa ya sa masu aiki suna kwasan sauran. Suwaiba ta shiga cikin wani yanayi na tashin hankali, dakinta ta wuce ta kule kanta a ciki me ta yi kenan sam bata bi abunda Jalli ya ce ta yi ba me yasa ta manta da shirin su? Ta tambayi kanta ya ya zata yi ta shiga uku duk abunda ta kafa ya rushe, sannan kuma ina ya kai Dayiba? To ya za ta yi ta bullowa wannan al'amari? Ta sake tambayar kanta, waya ta dauka ta kira Mama, ita ma kanta ta fara gajiya da matsalar surikar tata, yau a wahalce take saurarenta, ta ce, Mama shi kenan na gama na bat shirin da na fara, Mama na shiga uku na lalace, me zan yi in gyara? Mama ki taimake ni, wai Suwaiba ya za ayi bukatarki ta biya bayan ba ki ma kwantar da hankalinki gu daya ba, dadina dake garaje, sai 71 Baki Biyu e Sameera Mustapha: da Jalli ya ce kiyi kokarin su duka su sake jiki da ke, to gashi nan kin yi ma kanki, yarinyar 'yar matsiyata ne, kin san Karamin mutum kuwa? Duk yadda zata yi ta malake shi sai ta yi don ta gada daga iyaycnta. Nima da kyar suka rabu dani, balle ke da baki ma san ciwon kan.... katse wayar ta yi bata son fada, ita zata ciwa mutunci? Suwaiba ta jefar da wayar gefe tana takaicin dalilin da yasa ma ta amince da Mama, ta' ma manta ita uwar mijinta ce. Dama a ce mahaifiyarta ta halin su daya da Mama da ta fi kowa samun yadda take so, sam basu da kama da mahaifiyarta ko a fuska bale hali, kana haifa mutum amma ban da hali, ta sani mahaifiyarta mutum ce adila bata da hayaniya, to ko shine dalilin da yasa ta zauna da mijinta lafiya? Wayarta ta soma ringing a zatonta Mama ce, sai da ta yi tsaki sannan ta dauka, ta duba Augustina ne abokiyar ta ce da suka hadu a bar indan taje shan giyar ta ita da Jessica, ita ta ma manta da su ai nan kwadayinta ya motsa, ta dauki makulin mota ta kunna wayar ta ce, Augustina kina ina? Ina bar ne kwana biyu ban gan ki ba lafiya? Gani nan zuwa kada ki tafi don Allah, ok, ina jiran ki. Sun hadu suna nishadi da giyarsu, a haka ta kwashe komai da ke damunta ta fada mata, hatta muguntar da ta yi duk ta fada mata, Augustina ta ce, to ai wannan ba makirci ba ne, abinda ya kamata kawai mu nakasa ta kinga dole ne ya rabu da ita. Ta kyalkyale da dariya nima tunanina 72 Baki Biyu 0 Sameera Mustapha: kenan, bokan da nasa wannan aikin wasu sharadai ya shirya min ni kuma kishi ya hana ni aikata wannan sharuda nasa, ina fata wanda za ki kai ni gunsa ba ya da sharuda? A'a baya da shi, ni mace ce ma ba namiji ba. A ina take? Tana calaba, cross river za ki iya zuwa? Sosai ma me zai hana ni yaushe zamu je ni ko yau ne na shirya. Dama ai ni na fi son irin aikin 'yan wajajen ku kamar a aza wuka don haka da jirgi zamu ko? A'a da mota zamu, ai ba wani nisa, haba dai bayan an ce konan da Port Harcourt ana ten hours eh, ai ba ta nan take ba, ke dai muje in za ki je a yau ma sai mu dawo da yake ta buge take sai ta yadda da zancen Augustina a can kasan ranta tana zargin hakan, to amma ya zata yi tunda tana Bokatar aiki dole ne ta yadda da hakan sun shiga mota suka kama hanya gwagwala da sun yi tafiyar kusan minti sha biyar sannan ta ce su tsaya, mota ce parke a gun, sai ta ce su shiga wannan, ta dubi Augustina ta ce mu koma wancan? Ta ce, eh su za su karasa da mu ta fita tana waigen Augustina da ke kokarin shiga gefen tuki, waigo wan da zata yi sai ta ji an saka mata hankici a hancinta, ai bata kara sanin abunda ke faruwa ba. Da ta bude idonta ganinta ta yi cikin wani daki mai tsawo, tana kan gado kwance ta mike da sauri ai sai ta buge kanta da gadon sama, ta rike kanta ba ita kaďai ba ce a dakin sun kai su goma sha biyar, dalam, suma basu san inda suke ba, a 73 Baki Biyu e Sameera Mustapha: lokacin hankalinta ya tashi, tana kallc-kallen dakin, ta dubi mutumin da ke kusa da ita ta cс, "А ina nake? kallonta yake yi bai ce komai ba. Tuni ta fashe da kuka ai sai aka bude dakin wani katon mutum ne ya nufo ta, ta firgice don fuskarsa babu Imani a cikinsa. Tun kafin ya iso gunta ta yi gum ta tsuguna ta rufe bakinta da tafin hannunta tana girgiza kanta, ya tsaya cak a kanta yana huci ya yi mata magana amma a yare da bata ta ba ji ba, da alama gargadı yake bata. Shirun dole ta yi, ya kai hannunsa karkashin gadon ya fito da kwano ya bata tare da budewa, ai bata san lokacin da ta karfe tana ci ba, saboda tsabagen yunwa. Lafiyayyen abinci ne har da Juice, ta kwankwade sai a lokacin ta tuna abunda ya faru karshe tsakaninta da Augustina. To masu karatu wannan abu ya sami Suwaiba yana iya faruwa ga duk mai irin halinta, wannan labari da zan bada ya faru ne da gaske, matar take nemar wa 'yar uwarta nakasa wannan ba ma kishiya ba ce kawai adawa suke da junansu ta nemi hallakar da ita sai abun ya koma kanta, za aji irin hannun da ta fada za kuma aji yadda ta samu kanta sai a biyo a sha labari. ** Da Tahir ya dawo gidan bai damu yasan inda Suwaibar, ta shiga ba dan dama ya gaji da problem din ta bal ki ta ce ta tafi ba ai shi gaba ta kai shi. 74 Saki Biyu Bameer sadakar sun fado hannun a zalimai masu yankan kai labarin da take ji a waje a nesa yau gata ta zama l'ictim. Ta rasa ma tunanin da ya dace da ita, a yau tana zaunc duk wani bacci ya kaura a idonta, tunani a yau ta soma shi, ashc haka duniya take? Ta tuna lokacin da mahaifan ta suka nuna mata jin dadi a rayuwarta. Sun nuna mata gata don tafi sauran 'yan uwanta jin dadin har da lokacin da Baban ta ya yadda da bukatar ta na ta je America ta yi karatu mahaifiyarta ta yi bakin ciki sosai sam bata son tafiyar ta ba, amma haka ta hakura ta kalle ta. To a can ta kaga halaye na banza, bata da ra'ayin rayuwa irin na 'ya'yan Muslmai cikakkiyar sallah ma ta dai na kai tama manta rabon ta ta dauki hijab ko gyale tasa ta ce, zata yi sallah. Ta san yau ta mutu to tasan babu abunda zai rabata da wuta don an ce tun a duniya ake shaidar ka a yanzu ma da ta fado wannan wuri akan abunda ta so ta shirya shine ya dawo kanta, hawaye ne masu dunin suka zubo mata. A yau tana mai la'antar mai rayuwa irin ta ta, gun neman ki ba ka nemo rama, ita tasan hakan da Allah ya yi mata shinc daidai da ita a yanzu wata irin nadama da dana sani ya shiga zuciyarta, ita abun da yafi damunta shine iyayenta da bata nemi gafarar su ba. Ta san inda ta samu irin hali irin na mahaifan ta da bata wulakanta kanta ba...taba ta da aka yi shi ne yasa ta dawo hayaccinta, ta dubi wadda ta taba ta fuskar ta cike da hawaye, ta yi saurin goge fuskar ta da zanin ta 76 Baki Biyu 0 Sameera Mustapha: ta ci gaba da kallon matar. Tana yi mata kwanta c amma bata gane manufar ta ba, can dai sai ta lankwasa harshenta ta fara yi mata turanci a hankali suke magana, matar da sauri ta saki murmushi ta ce ita ma da turancin, tasan inda suke? A'a ta fada tana girgiza kanta, muna Cameroon ne! Ai tuni hankalin Suwaiba ya tashi ta firgita sosai sai da matar ta yi samin rike ta tana shafa mata bayan ta tana kuma bata magana don kada aji su, ai wani sabon kukan ta saki, tana sharbe majina sai dai a hankali take yi. Cikin kuka ta yi barci bata ma san lokacin ba, da asuba a ka zo aka ta dasu wai su kama hanya su tafi lokacin su ya yi, haka aka sa su suka yi tayi har zuwa wani dakin shima kule ya ke ko window babu, aka umarce su su zauna nan aka fara aske masu gashin kan su da aska da aka kawo kanta sai da ta canza kayan jikinta dama sauran ma haka suka yi, sannan ta zauna ana cikin yi kuwa sai a kawai kamar an ce juwa tana juyawa sai askar ta yanke ta, sosai kuwa ba kadan ba, ai sai jini ya soma zuba kamar a bakin kwarya tuni gardawan wurin bakin kofa suka iso suna yima mai askin masifa, ita dai bata jin abunda suke fadi amma da alama ya yi kuskure sosai ta san yadda aka yi ba sai ji ta yi an rufe mata fuskar ta da buhu aka rike, ta ita dai bata san ya aka yi aba aka tura ta cikin mota ba tana ji bata da ikon magana. Ta san anyi tafiyar kusan awa daya kafin aka tsaya aka jefar da ita waje ai kuwa 77 Baki Bivu Sameera Mustapha: sanadin haka kanta ya buga dutse ta sume. Da ta bude idon ta sai ta ganta a wani daki na kara an daure mata kanta da kyale da sauri ta rinke ta zauna, wata yarinya ta gani zaune gani zaune a gefenta zaka kai shekara tara da haihuwa, buzut ita ma ta mike ta fita daga dakin, suka shigo tare da wata mata da alama mahaifiyarta ce ta shigo rike da wata kwarya a hannunta, ta mike mata tasa hannu ta karba, nono ne a ciki ai tuni ta karba cikin lokaci kadan ta zuke ta shanye, suka karo mata, ta karfa ta shanye. Sai da daddare ta fito daga dakin ta iske duk gidan a waje a wasu na kwance wasu kuwa suna cin abinci, kai tsaye gun yarinyar nan taje ta zauna aka kawo mata abinci, tuwo ne da wata irin miya da ta kai baki kuwa da kyar ta hadiye ya zata yi, dole ne ta ci. Babu wanda yasan halin da Suwaiba ke ci don dama mai hali da ya saba fitina kuma gashi dama iyayenta ba su daure mata gindi ba don haka ma sai ayi wata bata yi magana da su ba tun suna damuwa har sun saba da shiru-shirun ta tun tana America. Shi kuwa Tahir tunda ya yanke hukuncin raba su ya fita hanyar ta. Mama kuwa dama ta gaji da biye mata don ta ci ka mika gashi bata da hakuri don haka itama a yau satin su biyu ba su yi magana, kowa ya gaji da hali irin na Suwaiba. Allah ya shirye ta amin. Sai da ya yi sati ya dawo ya wuce gidan 78 Baki Biyu 0 Sameera Mustapha: Suwaiba amma bata gida bai damu ya tambaya inda take ba don ya saba ganin haka don haka wanka kawai ya yi ya wuce gidan Gwaggo. Ya kuwa iske ta a falo tana gyaran gayen latis, ya yi sallama ya isa gunta ya zauna suna gaisuwa. Ni kam ina daki da nayi niyar fitowa ne, amma da naji muryar Tahir sai gabana ya fadi na koma na zauna. Ina jin su sama-sama hira suke yi, ai saina koma kan gado na zauna har na kusan minti goma sha biyar da dai na ga basu da alamar yanke hirar na dau waya na bugawa Aisha mun sha hira har take fada min zata je aikin Hajji wannan shekarar, na yi mata murna, da muka gama Amina na buga ma wa bayan mun gaisa take ce min da wa nake magana ne tun dazu sai nuna mata busy ake yi itama tana ne mana? Ashe mun shiga ran juna da Aisha, nake magana, to an yi calling schoolyau she za ki shigo wani irin murna ya shige ni da baya misaltuwa, dama na matsu in koma Makaranta, kai don Allah Amina amma nayi murna da yanzu ai mun gama suka bata mana lokaci, mun yi hutun watan hudu a gida gaskiya an cuce mu, ke dai bari Amina ta fada, ke wai har yanzu maigidan naki bai ce ki koma gida ba? Hum ke dai bari ya yi mirsisi ya ki cewa komai ke kina ganin zai ce in koma bayan har kwana ya raba? Hum haka ne fa, Amina sai anjima Gwaggo na kirana, bari in je in dawo kila in kara kiranki, muka yi sallama na dauki hijab na saka saboda wando ne a jikina da 'yar 79 Saki Bivu e Sameera Mustapha matsitsiya na saka. Na isa falo sai da na ji kamar in koma don Tahir ne zaune ya kuma tsura min ido, kamar a yau ya fara ganina. Gwaggo ya fada yana kallona, kin san 'yar kanwar nan taki bata da kirki? Tana fara'a ta ce, "me tayi maka? A take hankalina ya tashi ina kallonsa, kamar ya gane abunda nake ciki sai naji ya ce, taso ina nan amma ko ta fito ta yi min sannu da shigowa, oh lallai ba ta kyauta ba, kana tsamannin itama tirka ce? kunya ce ai dà ita. Ni dai naje gab da gwaggo na zauna ina kuma gaida shi, abun haushi bai ma amsa ba, to me yake nufi don ma ya samu na gaida shi? Ji nayi ya ce, tashi ki kawo min abinci, na yi kamar ba zan tashin ba sai da Gwaggo ta ce, baki abunda iya ce, ba ne? Shi dai idonsa a kaina sai ka ce zai cinye ni, kai Allah ya yi masa kallo gashi idanuwansa masu yaudara, a kwayar idonsa yana da wani abu na musamman da ban san ko mene ne ba. Na shiga na hado masa abincin akan tray na kawo na ajiye a gabansa, na mike zan tafi ya ce, ba ki yi serbing dina ba, na koma na tsuguna ina zubawa a flat dama fried rice ce da pepper chiken ga kuma salad da aka hada duk na zuba masa, da na mike zan wuce ji nayi ya riko hannuna, na yi saurin kallonsa na kuma kalli inda Gwaggo ke zaune ita kam hankalinta na kan T.V na dawo da dubana gunsa na ce, da zafi fa, baki kawo abin sha to zan kawo na fada saboda ya saki hannuna don rikon da ya yi min zafi ne dashi, ya sake ni ai gun ya yi 80 Baki Biyu Sameera Mustapha: jajir, kai wannan mutumin mugu ne, Allah ya shiga tsakanina da kai na fada a raina. Na koma kicin na shiryo masa abin sha, irin su ruwa da kayan lemo, amma abun haushi abincin ma kadan ya ci kayan sha kuwa ruwa kawai yasha, don haushi ban ma kara kallon inda yake ba. Ina zaune dab da Gwaggo na ce, Gwaggo an yi calling school yau Amina ke fada min, haba dai a'a ya yi kyau, ashe sai a fara shirin zuwa Makarantar, ina murmushi na ce, wallahi kuwa Gwaggo duk zaman ya ishe ni, dama....Tahir ya katse ni da ya ce, Gwaggo ban gane ta yi shirin makaranta ba, ai ba inda zata tunda ba ta san hakkina akanta ba, haba dai wane irin bata sani ba, sai dai idan akwai abunda take yi wanda ban sani ba, tuni idona na kallon tasa, ji nake kamar in yi kuka don wallahi tsakanina da Allah bana son Gwaggo ta san abinda muke ciki, da alama ya gano irin kallon da nake masa na rufa min asiri ne sai ya canza zancen ya ce, Gwaggo ni fa bana cin abincin 'yan aiki, so nake matata ta dafa min abinda zan ci da kanta. Duk da nasan akwai matsalar girki hankalina ya kwanta sam bana son abunda zai sa Gwaggo tasan abun da muke ciki. Mikewa ya yi ya bar gidan tare da jaddada shi fa bai amince da tafiyata ba, kuka na saka wa Gwaggo ta ce, dadi na dake baki da hakuri, don ya ce shine za ki damu to duk yadda aka yi abunda ki ke shukawa ba girki kadai ba ne matsalar, babu 81 Baki Biyu Sameera Mustapha: komai Gwaggo don Allah ki roke shi in tafi, nan fa da wata bakwai insha Allahu zamu gama. To Allah yasa ya amince kin san dai ba zan matsa masa ba. Sosai hankalina ya tashi na lura Gwaggo bata son ta matsa wa Tahir na riga na san duk abinda ya fada shi din za'ayi sai na fara tunanin abun yi, yạ zan yi? Na tambayi kaina Aisha na buga ma wa ina fada mata damuwata, abun takaici sai ta ce ai laifinki ne Dayiba, ko ni ce matakin da zan dauka kenan ta ya za'ayi aure tun watanni hudu da suka wuce amma baki san ki ba mijinki hakkinsa na kwanciya ba, kin manta irin fushin Allah da ki ke tare dashi ne? Ni fa na bugo ne don ki bani shawarar abunda zan yi in koma Makaranta ba wai ki sani gaba kina min fada kamar wadda ki ka ajiye ba, ai duk abunda na fada miki ba shawara ba cc? To shi kenan na ji Allah ba ki hakuri, bata jira abunda zan ce ba, ta kashe wayar, dama na san sai an yi hakan tun kafin in buga mata nake zulumi don na riga na san halin abu ta. Na sake buga mata sai da yai ta ringing kamar ba za ta dauka ba sai kuma ta daukan tana fadin, wallahi Dayiba kina da ban haushi, ai matakin da ya dauka wallahi ita ce daidai da ke, to Mama na gode...ko ba ki kira ni hakan ba na san matsayina a gun ki don haka ba zan baki gurguwar shawara ba. A haka dai na ajiye ina tunanin abinda zan yi amma shawarar ta bata ma yi tasiri a guna ba don ba yin hakan zan yi ba. Na ga washegari bai shigo ba, kai har muka 82 Baki Biyu Sameera Mustapha: kwana hudu ina jiran in ga shigowarsa amma shiru ka ke ji, na buga wa Amina ko an fara lecture ta ce ai tunda aka dawo ake ta lectures har da test wasu departments din suka yi namu dai ana shiga lectures sosai ranan Monday ma muna da test, ke wai ba za ki dauki laifin ki ba, ko ya bar ki ki dawo? Ni ban ma san ko yana nan ba, yau kwana hudu kenan ban gan shi ba da alama ya yi tafiya inda yana garin dole'ne ya shigo ya gaida Gwaggo safe da daddare, ikon Allah mutum da mijinshi amma bai san inda mijin yake ba, har na tsawon kwanaki. Lallai Allah ya ganar da ke, sai an jima zan je in tarbi mijina yau a hannuna yake, ai abun gori ne ma nima Allah zai bani wanda nake so tun kafin ta ce wani abu na ajiye wayar na zauna nayi shiru ina tunanin abun da ya dace in yi, naje na yi dabara na dauko wayar Gwaggo na kwashe duka numbobin sa baki daya naje maidawa na same ta tana neman wayar na mika mata ga wayar nan Gwaggo dama number ce na dauka, ta karba Tahir bai bugo ba? Na yi kamar ban ji abunda ta ce ba, sai kuwa aka fara kira ta dauka daga gani shine aisai na samu wuri na zauna. Jira nake in sun gama in duba number da ya kirata da shi, sun fi minti sha biyar suna maganar, can dai na ji tayi masa sallama na matso gunta na ce, Gwaggo ki roke shi don Allah in koma Makaranta, wallahi har an kusan fara jarabawa, me ya samu bakinki da ba za ki fada masa ba? Ai ina fada masa, amma ya ki 83 Baki Sivu Sameera Mustapha: kula ni, Gwaggo wata bakwai kadai ya rage tsakanina da Makarantar, don Allah ki taimaka, waya ta dauka ta kira shi, murna ce ta kama ni don nasan in ba ita ba tabbas yana iya hana in je Makarantar, haka kuwa tana fada masa ya bada hadin kai ya ce babu damuwa ina iya tafiya washegari, ai ban san lokacin da na kai dakina ba, ina murna ban tsaya 6ata lokaci ba na soma shirin tafiya washegari tun tara na safe na bar Abuja zuwa Kaduna. A Cameroon kuwa, Suwaiba ta samu kusan kwana biyar a gidan, sai dai duk ta fita hayyacinta, da yake gidan da suka taimaka mata gida ne na Musulmai kuma gidan Mallamai, a dole Suwaiba ta fara sallah, sannan da alama duk wani ji da kai da take fama dashi ya kau. Ta zama silent bata da aiki sai tunani da kuka, tana bakin cikin irin rayuwar da ta daukar wa kanta. A gidan Mal. Attahiru, mutumin Cameroon sai dai ba wai suna cikin birni ba ne, suna cikin daya daga cikin kauyukan garin ne. Tun usulin iyayen sa Malamai ne a nan garin, yana da matan aure biyu da 'ya'yansu su goma sha biyu, uwargidan na da takwas amaryar na da hudu, irin zaman da suke yi shi ya rika ba Suwaiba mamaki, matan biyu kansu a hade yake, suna bala'in shiri babu ruwansu da wani abu wai shi kishi, anya sun san kalmar ma? Ta kan yi wa kanta wannan tambayar, abinci ma tare suke ci a kwano daya, in ka ga dan dakin nan 84 Baki Biyu Θ Sameera Mustapha: ba za ka babanta shi da da na dayan dakin ba, ta lura duk inda ka zaba nan zaka kwanta, kai su ba su da matsala, ko 'ya'yansu ke fada ba su nuna bambanci, to ko dan suna auren Malami ne shi yasa suke hakuri? Ita dai

Chapter 5 of 8