Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
4 / 8
Mama har ta so ta manta ba Dayiba kadai ake so ta jawo hankalinta ba, har da Tahir. Tabdijam, ashe akwai aiki ja a gabanta! Mama ta katse ta, ta ce kina jina ko kin san fa aikin da yake son yi ba zai yi ba sai kin 52 Baki Biyu Sameera Mustapha: tabbatar sun saki jiki dake, eh, na sani ta fada a ranta kam tasan tana da aiki. Na yi wanka na yi shiga cikin wani yellow lace mai bala'in kyau na yi kyau sosai, na wuce dakin Suwaiba itama ta yi shiri cikin super holland tare muka yi breakfast, ni dai nasa nayi dacen abokiyar zama na lura ba ta son ta ga bacin raina. Na sami kwana shidda a gidan amma babu ruwana da Tahir, bamma ganinsa kila sai dai in hange shi da nesa saboda muna jin horn din sa ko karan gate za mu shige dakunanmu, ni da Antin tawa mu kulle yadda kasan mun ga dodo. Ita kam Suwaiba in tà shiga daki in ban da dariya da jin dadin abunda ke faruwa babu abinda take yi, tasan ta riga da ta tsoratar da Dayiba, da alama burinta na son cika don ta ga alamun Dayiba sosai ta yarda da ita, ta fada a fili sakaryar yarinya da hankali bai ishe ta ba, kowa ta taba ganin ya yadda da kishiya oho! Ta kara kyalkyacewa da dariya sai kin bar gidannan kin koma gidan ubanki. Har na cika wata daya a gidan Tahir ba abinda ke hada ni da shi, sai dai in je gun Suwaiba mu sha hirarmu muyi kallon films din mu babu ruwanmu, mu ci mu sha shine aikin mu, na kara jin dadi da Makarantarmu taje strika dan haka hankalina a kwance ni har mantawa ma 53 Baki Biyu e Sameera Mustapha: nake yi wai ina da aure ko kuma aure ne ya kawo ni gidan nan. Gashi cook din gidan ya iya abinci sosai, bamu aikin fari balle na baki, 'yan aiki ne birjik a gidan, musamman ta bani 'yan aiki biyu suyi min hidima, a dakin na, abin mamaki na yi kiba nayi kyau duk wata rama da duhun da nayi ya washe, ni kaina nasan na sami lafiya, a gaşkiya ina jin dadin zama da Anti Suwaiba, ba kadan ba, sam ba za ka ce mu kishiyoyi ba ne don mun yadda da junanmu. A wannan lokacin ne, Gwaggo ta dawo zama Abuja, dadi a guna kamar in yi me, gidanta babba ne sosai, zaka iya kiran gidan 'garden house' don itace ne da furanni zagaye da gidan, a gaskiya gidan ya yi min bala'in kyau mijinta ya bata halak malak ko ya mutu babu wannan gida a gado, gashi bene ne mai hawa daya, dakuna kuwa birjit a gidan, ita da kanta tazo ta dauke ni ashe wai Tahir ya yi tafiya zuwa Thailand har ma ya yi sati biyu a can ni kam bam ma sani ba, na so kwarai in maida gidan Gwaggo wurin zuwa amma ta ki bani fuska don haka dole na hakura na daina zuwa, duk da akwai nisa tsakaninmu. Sosai Gwaggo ta ji dadin ganin yadda na kwantar da hankalina, kamar ta hadiye ni, ita a ganinta na hakura bata san dan nata mugun mutum ba ne. 54 Baki Biyu Θ Sameera Mustapha Tahir ya sami kamar wata daya da rabi da tafiya Thailand, Suwaiba kuwa a koyaushe tana bani labarin irin zaman da suke yi da Tahir har bata jin kunyar gaya min ko kusantar ta baya yi sai dai duka da take sha shima din don ta fada masa gaskiya akan zaman da yake yi da matan waje kila ba ya sha'awarta ne don a kullum yana tare da su saboda in ki ka ji irin matan da yake fita da su irin masu class din nan ne to ke kuwa irin matannan menene baza suyi maka ba don su ma ake ka, shi yasa wasu matan masu son auren namiji mai kudi sun shiga uku don basu san abunda zasu aura ba. Na ce, ni kam Anti baya tsoron cutar da ake dauka yanzu sanadin haka? Ta tabe baki uhm ke dai bari kawai Allah ya kare mu. A raina kuwa cewa nayi Allah ya kyauta ma in bada kai har nima in samu ai nesanesa dai. Shakuwa sosai maka yi da Anty Suwaiba saboda komai tare muka yi fita kadai ne bana yi, bana binta sai dai taje ta dawo. Ana cikin haka kuwa aka yi wa su Anti Badiya transfer Abuja, sai dai ita a yan ya take, washe garin da ta tare gidan ta naje nayi mata wuni ta ce, lallai yarinyar fa kin ji dadin aure kin ga yadda ki ka zama kuwa? Kamar iya Balarabiya na ce kai Anti kin cika tsokana ke dai zancen haka kin ga ki ban da ki kayi kuwa? Ke cikin da nake dauke da shine shi yasa na yi ki 55 Baki BiyU e Sameera Mustapha ban nan Anti ina shi ke nan dai duk mun bar Kaduna? Ke dai bari dama Tahir Allah sai ya saka masa kin san fa shi ya nema masa aikin a MTN shine aka bashi manager a dai marketing deptement a nan Abuja, Allah ki rike mijin ki yana da mutunci sosai, a raina cewa na yi a fuska ba da mutanen waje....ta tsinka min tunanin kin ji abunda nake fada kuwa? Na ce eh, ina jin ki, haka dai mukai ta hira, tana bani labarin irin abun alherin da Tahir ke yi masu. Haka muke ta zaman mu cike da nishadi, haka kuma ina kiran Baba da Baba a waya, Gwaggo kuwa ai babu ranar da bana kiranta. Ina kicin in dan dafa abinda zan ci, ranar in kwadayin indomie kuma yadda nake dafa ta tun a gidan Gwaggo haka nake sha'awarta, tun wadda Asabe ta koya min ita nake yi kuma ita kadai dama na iya dafawa. Na gama dafawa na juwo kenan muka yi ido hudu da Tahir a bakin kofar kicin din ya saka hannayensa a wandonsa ban san lokacin da plate din hannuna ya sullube ya fadi kasa ba, tas ka ke ji, ina kyarma na gaida shi, sam ban san lokacin da jikina ya fara rawa ba, shi kuwa sakin fuskarsa ya yi ya amsa ya ce, kiyi hakuri, ban san zan baki tsoro ba, amma kuma nayi sallama ashe ke baki ji ba, yay ina 'yar uwarki? Ya tambaye ni yana kallona, na dan motsa bakina kamar bakin na min ciwo 56 na ce, Baki Biyu Θ Sameera Mustapha: uhm-uhm ta fita ne? tambayar da ya jeho min kenan na sa ido na kasa na ce, ni ma ban sani ba, ya dan shigo cikin kicin din ya ce, idan ta dawo ki ce ina son ganin ku a falona, bayan sallah isha'i. Ba tare da ya jira amsa ta ba ya wuce, a raina na c,e kaji mutum sai zuciya kamar shi kadai ne mai ita, ina cikin sake-sake na na ji sallama Anti Suwaiba na yi saurin isa gunta kafin in ce wani abu ta ce, tana kallona Tahir ya dawo ko? Na ce eh, tun dazun amma Anty kin dade har ma ya tambaye ni in da ki ka je. Rabu dashi da Allah, ina yake ne? wallahi ban sani ba, ya dai ce in kin dawo in gaya miki yana son ganinmu a falonsa bayan Sallah Isha'I. Ta tabe baki ta ce, to Allah yasa dai lafiya, don abinda mamaki neman me yake mana? Na yi ajiyar zuciya da ta baiyana na ce amin. Bayan mun gama cin abinci na shiga bayi nayi wanka, nayi sallah magariba ina zaune dai akan sallaya ban tashi ba na dauko Alkur'ani mai girma ina karantawa, har aka kira Sallah Isha'i, sannan na tashi na yi na idar har da shafa'I da wutiri. Na yi abina, na yi shafa na fesa turare na dauko engilish wears dina riga ce bodyhug saboda ta dan matse ni pick cetana da taushi rigar sai na saka sket jeas dina yakai min har kasa, na saka slippers fari tas, na fauko irin 57 Baki Biyu e Sameera Mustapha: dan hijab dinnan da bai sauka sosai ba saka, na kulle daki na na wuce dakin Anti. Itama kanta sai da ta kyasa kwalliyata duk da bata fada ba amma na gani a idonta. Mun same shi zaune a falonsa yana kallon MBC 4 ana wani programme din na oprah sai muka sami wuri can nesa dashi muka zauna kujera daya muka tsura maşa ido. Ya dauki remote ya rage volume na TV, sannan ya ajiye remote din a gefensa, ya dube mu, ni dai nasa kaina kasa saboda bana ma son mu hada ido. Ya gyara zamansa shima yana fuskantarmu sannan ya ce mu bade wannan meeting din da addu'a a karanta kula'uzai har da Fatiha, sannan sai Ayatul Kursiyu. Haka din muka yi cikin minti uku muka shafa ya ci gaba. Suwaiba ya kira sunanta ke ce babba don haka da zan fara, na san tunda aka kawo Dayiba gidannan ya kamata in tara ku muyi magana, amma hakan bai samu ba shi ne a yau nake son in san wane shiri ko shawara za ki bamu akan yadda zamu zauna? Ina nufin ki zaba mana yadda zamanmu zai kasance na baki dama. Ta bata fuska sosai ta ce, wane zama kuma ka ke so muyi bayan wanda mu ke yi? Ka ga mu dai muna zamanmu lafiya da Dayiba kar ka zo ka canza mana tsarin da...." Ya katse ta, ba wai ina son in 6ata maku zamantakewar ku ba ne, a'a 58 Baki Biyu Sameera Mustapha: amma kin san ina da hakki a kanku ba wai na auro ku ba ne don in yi decourating din gida na ba ne sai don da ni da ku muyi rayuwar aure mai kunshe da nishadin rayuwa. Suwaiba ta mike tsaye ta ce, kai da Allah can, kai har wata nishadin aure ka sani a rayuwar aure? Bayan muzguna mana da ka ke baka gani ba don yanzu kana bukatar wani abu a gunmu shi ne zaka zo mana da dadin baki da dai ba mu san halin naka ba, mu ka barmu yadda muke ba ma son wani canji. Hakkin da ka ke ikirarin kana da shi a kan mu kuwa mun yafe bama so...." To ni ban yafe nawa hakkin ba, ya za ayi kenan? Wannan kuma kai ya shafa, uhum ni kaga tafiya ta saboda ban ga amfanin wannan meeting ba na rashin gaskiya." Tana kama hanya nima na tashi buzut na bi bayanta, sai ka ce ya biyo ni muka bar shi nan zaune. Ni kam Anti tayi min daidai, don na gani a fuskarsa ransa ya yi bala'in басі. Tahir yana nan zaune a inda yake na tsawon minti ashirin yana tunanin abun yi, don ya lura Dayiba ta amince da Suwaiba sosai, ta riga da ta bata shi gare ta, to yasan matakin da zai dauka. Ya mike ya shiga dakinsa, a zaton Suwaiba tana da wayo ta manta ita tana da nata shima yana da nashi ko don taga yana biye mata? Ya canza kayan da ke jikinsa ya saka T-shirt fara sol, an rubuta (Tommy hilfiger) da jan kala sai wando 59 Sakı Siyu Sameera Mustapha: Jeans sky bluc, ya gyara gashin kansa kace bai aje mata biyu ba, tamkar fan saurayi duk da yana da dan jiki sai dai na ce maku "He is not fat but he is huge" da ya ke yana da wadataccen tsawo shi yasa ba a ganin hakan ya wuce sashen Suwaiba kai tsaye ya san suna can. Ina zaune na kwabe hijabi na na lankwashe Kafafuwana kan kujerar da nake zaune akaі muna ta hirarmu da Anti Suwaiba cike da nishadi sai jin sallamar Tahir muka yi daga sama, kallonsa a kaina ya tsaya na yi maza na saka hijab dina ya yi kamar bai ga abinda nake yi ba. Ya sami wuri ya zauna ya ce, Suwaiba ina son ki bani aron kanwarki zamu fita ne. ta kawar da fuskarta da tsabar bakin ciki ta ce, ni me ruwana da fitarku, in ta ga dama ta bika ni bai shafe ni ba, don dama ai zamanka take yi. Ya mike ya nufi inda nake zaune, ke tashi mu tafi, hankalina tuni ya tashi na ma kasa mikewa gabana kuwa kamar zai fita don tsabar harbawa da yake yi, ya iso inda nake, ji na yi ya kamo hannuna ya mikar da ni, sai dai hankalina na kan Suwaiba, ji nake yi kamar in yi fitsari don tsabar tsoro, ji nayi ina cewa Anti bishi? Ta dan washe baki kadan ta ce, bismillah ni kar ki tambaye ni ai shi ya ajiye ki bani ba ni babu ruwana. Na dubi shi tuni har ya fara jana min fara tafiya, wallahi hawaye ne kawai bai fito min ba, amma kuka ma na kusan yin shi. 60 Baki Biyu Mictanha: Sameera Mustapha: Sai da muka kai bakin kofa sannan ya juya ya kalli Suwaiba ya ce, sai mun dawo. Haba wa, Suwaiba ihu ta rika yi tana kuka kan bakin ciki, ta rasa abunda ke mata dadi a rayuwarta, ai saboda tsabar takaici 6ata masa lokacin da ta rika football da kayan dakin ta ba, ta gano Dayibą tana bala'in tsoron Tahir ya zata yi ta sa Dayiba ta rika kai Tahir dole ne ta nemi wani hanyar don ta cimma burinta. Tafiya muke yi ba mai cewa dan uwansa wani abun, da yake ni ba 'yar gari ba ce, sam ban san in da zamu ba. Gabana ne ke faduwa ina kuma addu'ar Allah ya tsare ni daga sharrin wannan mugum mutumin, sai da muka yi kusan isa na gano gidan su Anti Badiya za mu, a raina na rika godewa Allah, tare da ajiyar zuciya. Mun shiga gidan ita da maigidanta suna ta hirarsu, gwanin ban sha'awa, kafafunta na kan cinyarsa yana matsa mata, duk sun kumbure. Sahabi ya mike yana mana iso, kuyi hakuri fa kofar a bude take, in ji Tahir, haba ba komai a same muka bar kofar bude. Na isa gun Anti ina gaida ta, sannan na gaida Sahabi, ya amsa ya ce, ya amarci? Murmushi na yi ban ce komai ba, na wuce cikin dakin Anti, biyo ni tayi dakin. Bari in kai masu abun sawa a baki sai in zo. Muryar Tahir na ji yana cewa, Dayiba nemo min abunda zan ci yunwa nake ji, tuni na bata fuskata, me wannan mutumin yake nufi? Sam ban san Anti na dakin 61 Sameera Mustapha: Sakı Bıyu ba, na yi tamkar ban ji shi ba, sai da ta dan matso kusa da ni sai ta cc, ke ba ki ji abinda Tahir ya fada ba ne? Na mike ina turo bakina, Anti kam kallona take yi kamar a ranar ta taba ganina, ni wallahi wannan mutumin so yake ya dame ni, to kada ki kai masa, anya kin san abinda ki ke yi kuwa? Da sauri na wuce kicin na iske tuwo da miyar taushe ga kuma farfesun kaji da fruit salad, uhum su Anti iya abinci kalla-kalla ni kam ina zan iya tuka tuwo balle kuma hada miyar. 'Na ma rasa ta inda zan fara, don a gaskiya komai ban iya ba, hatta serving na abinci ban iya ba, tsayawa na yi ina kallon kololin da na bude, muryar Anti na jiwo na tsinke don firgita nayi, a'a wai ke lafiyanki Dayiba? Mits, tsaki ta yi ke kam kin shiga uku, komai ba ki iya ba, ban ga amfaninki ba wallahi kina mace amma common serving baki iya ba, to balle girkin abinci, to ya ku ke yi ne? Na ce ai muna da cook ne shi ke yin komai ya shirya a table ah lallai kun hadu, tana magana tana hadawa tray naga ta dauko da plates guda biyu ta saka tuwon a daya miya a dayan sai ta dauko wani mai zurfi ta zuba farfesun sannan ta dauki abun sa fruit salad shima ta zuba ta jera akan tray ita ce to 'yar hutu dauka ki kai, murmushi na yi na ce, kai Anti ni tafi ki kai masa kada ya biyo mu kicin, na dauka ina tafiya a hankali, gudun kada in zubar, gashi tray ya yi min nauyi a hankali na iso na ajiye a can nesa da shi maimakon in kai gabansa, har a zuciyata 62 Baki Biyu Sameera Mustapha: ban dauka na yi wani abu ba ne, daga bayana naji Anti ta ce, yauwa sai ki dauki dan karamin table din can ki kai kusa dashi ki dauki abincin ki aza akai, na yi yadda ta ce, na san kallona yake yi, sai dai ni na ki in daga ido in kalle shi, haka kuwa na bar falon ba mu hada ido ba, na koma daki zan zauna anti ta ce ba ki fa gama ba, saura ruwan sha da juice, anya Dayiba kin san aikinki kuwa? Na mike ina gunguni ita kam kallona take yi tana mamaki. Da na dawo ta ce, don Allah dan matsa min kafafuna, wallahi ciwo suke min. Na zauna ina yi mata, ta ce 'yar uwa na lura kina tare da damuwa, me ke faruwa ne? Ai ji nayi idona ya kawo ruwa, sai hawaye zarrr, da sauri ta sauke kafafunta ta dafa min kafadata, fada min abinda ke damunki insha Allahu zan baki shawara da ya yi daidai da ke." Na dube ta da jajayen idona, na ce, Anti ni dai ban san me yasa ba na tsani namiji, haushi sukc bani ki sani ba tun yanzu ba, a'ah tun farkon so da na fara zan fada miki abinda kowa bai sani ba, firts love dina a rayuwa shi ne 'Ya Amir', na ga alamun mamaki a fuskarta, saboda babu wanda ya san haka. Na ci gaba da fada mata, ban taba son namiji a rayuwata ba kamar yadda na so Amir. Tun bai sani ba har ya fahimci hakan, ana wa tunanin shi ne yaso ya yaudare ni ya furta shima yana sona, a lokacin ina aji uku na secondary da 63 Saki Bivu e Sameera Mustapha: Mustapha muna tare da kawaycna Zainab kawata ce a nan (F.G.G.C) Zaria, take gaya mana labarin wata Kawarta da ta yauydari kanta ta mika wa saurayinta kanta, saboda irin tsabar yadda da tayi dashi duk da shine ya nuna mata kada ta damu da komai in dai tana tsoron wani abu ne to shi ai aurenta zai yi, wallahi anti ya maida ita tamkar matarsa, da kanshi ya samo mata pills take sha wai don kada ta yi ciki, daga Karshe bace mata ya yi Anti kin san yadda Baba itama tana tsoratar da mu. akan samari to shi ne fa na daukar wa kaina alkawarin kame kaina daga da namiji, kai da ireiren wadannan labaran na zama ina bala'in tsoron da namiji shi ne fa Ya Amir da na kwallafa wa raina shi, shi yaso ya yaudare ni shine fa na sa wa kaina kin su... "Me ya yi miki da ki ka yankewa kanki wannan hukuncin?" Miyau na hadiye ina kallon ta, na ce a gaskiya na farko mahaifiyarsa sai kuma shi da yake nema shige min, ni kuma a gaskiya tunanina iskanci kan fara daga shafan juna ne, shi ne na yanke shawarar rabuwa da shi. Tun kafin abun ya yi nisa gashi duk da shi kaďai raina ke so. Anti ta ce, sa'id fa? Ai shima kin so shi, sosai kuwa Anti amma kin san bai kai yadda naso Ya Amir ba, gani nake ba zan taba son kowa yadda na so ya Amir a rayuwata ba, Tahir fa shi da yake matsayin mijinki a yanzu? Tambayar ta yi min wani iri, don na lura Anti tana son duk wani abu da ya shafi Tahir, na lura suna shiri sosai, ban 64 Baki Biyu Θ Sameera Mustapha: iya cewa komai a kansa, na yi shiru ina kallon kasa, baki daya nayi shiru kuma na kasa ci gaba, can na tuno da abinda Anti Suwaiba ta fada min akan sa, don ban san komai akansa ba, ni na san dai mugu ne. Anti fa manemin mata ne." Murmushi ta yi ta ce, 'yar uwa kina nan fa lokacin da Anti Nafisa ke fada mana abinda zamu yi idan muka fuskanci irin wannan matsalar, hakuri za ki yi ki yiwa Allah Ibada, ni dai a yảu Alhamdulillahi zan ce, an a gaskiya Sahabi ya yi sauki akan farkon aurenmu, ba komai ba ne kuma sai addu'a da kuma kauda ido daga al'amuransa. Ni dai ina saurarenta amma a gaskiya ban dauki shawararta ko daya ba, don inda ta san waye shi da ta bani shawarar rabuwa dashi......ta tsinka min tunanina da ta ce kina jin abinda nake fada kuwa? Na girgiza kaina alamun "Eh, ta ce tashi muje falo kada suga mun kyale su. Suna zaune sai hira suke yi, Tahir sai dariya yake yi yana cike da nishadi, ka ganshi sai ka ce da gaske a waje zaka ganshi lamai-lamai, cike da saukin kai, muna shiga gida zai fara nuna halinsa na rashin mutunci. Bayan munyi sallama da su mun bar gidan sai muka kama hanya. Tafiya muke yi naga ya wuce hanyar gida, na dan dube shi ta gefen idona, tukinsa yake yi hankali kwance, na kalli agogon da ke makale a motar, karfe goma saura, ina zai kai ni cikin daren nan? Ai tuni hankalina ya tashi, gabana 65 Baki Biyu Sameera Mustapha: kuwa sai faduwa yake yi. Ban dai yi masa magana ba don bana son komai ya hada mu. Sai can ya tsaya gaban gate a lokacin na lura da gidan Gwaggo ne, ai sai hankalina ya kara tashi wallahi duk sai na tsinke, fargaba na ya karu. Ina tunanin abunda ya kawo shi gidan Gwaggo yanzu. Ya yi parking ya fita, a sanyaye nima na bude na fita. Bа dai karata ya kawo ba? Duk sai na ji babu dadi, ban san lokacin da na ce dashi, "Don kada ka gaya ma Gwaggo abunda ke faruwa." Jin maganar ya yi daga sama, hannunsa na kan kubar kofar ya dube ni nasa kaina kasa, kasa-kasa yake magana. To naji ba zan fada ba, ai ban san lokacin da na yi ajiyar zuciya ba. Sai da aka bude mana kofar, Gwaggo na zuane a kan kafet tana shan kayan itace, tana kallon wani Hausa film, mamaki ne a fuskarta, amma sai ta share tana yi mana sannu da zuwa. Naje dab da ita na zauna ina gaida ta. Bayan mun zauna sosai Tahir kam shima shan kayan itacan yake yi, yana fadin, Gwaggo film ake kallo haka? Uhm, kai dai na kasa bacci shi ne na fito na kunna, lafiya na ganku da daddare haka? Daga idon da zan yi muka yi ido hudu da shi, ya saki murmushi 'yar kanwar ki na kawo miki ku dan zauna. Gwaggo ta dube shi ta ce, ban gane ba, wani abun ya faru da ka yanke hakan? Babu komai Gwaggo, sai a hankali za ki gane, amma ko yau da muka yi magana da kai Tahir na ce maka akwai abunda ke damunka, 66 Baki Biyu 52 Sameera Mustapha: koda yake dama halinka ne, kai ba ka fadin damuwarka sai randa ta yi wari don haka Allah yasa haka ya fi zama alheri da sauri ya ce (Amin). Gwaggo na raba masu girki kwana biyu-biyu, Haj. Hauwa bata son ta takura wa Tahir tasan yana da babban dalilin yin hakan, ko ba komai tasan Tahir na da bala'in hakuri, yana iya hakurin fiye da shekaru goma akan abu, don haka ta ki ta kara yi masa wata tambaya don dama tun ba yau ba ta gano yana cikin damuwa. A sarari fara'a tayi ta ce, to madalla, Allah ba mu hakurin zama tare, amin ya fada yana mikewa. Ni zan wuce sai da safe. Gwaggo ta dube ni na dan kwantar da kaina a gefen ta. To 'yar shagwaba, an dawo ma fara zaman lallashi kenan na yi murmushi kai Gwaggo ni wallahi ba ki ji dadin da na ji ba, kamar ya san abunda nafi so kenan zama da ke a rayuwata, baya gun sa ta Gwaggo ina fa zai dame ki tunda baki da matsala sai ta shagwaba. A raina kuwa tunani nake yi meye dalilin yanke wannan hukuncin ni ban taba ganin anyi haka ba, ai wannan ba gidansa ba ne har zai shirya kwana mutumin nan akwai ikon banza. Ban hakura ba na dubi Gwaggo na ce, "Gwaggo hala ana yin haka nan ai ba gidansa ba ne da ya shirya hakan, wa ya fada miki? Gwaggo ke ki ka ce Baba ya yi maki gida fa da fa a nan, in ji ni ko ko dai ki ka dauka hakan dan ni ban san mun yi wannan maganar da ke ba, in ce an ce kayan ciki ne ya zuba maki? Hum ta fada tana 67 Baki Biyu Sameera Mustapha: murmushi, wannan gidana ne, ni na sayi abuna da taimakon Tahir, shi ya biya kashi saba'in cikin dari ya kuma mallaka min gidan halak-malak, tabdijam wannan wane irin kudi yake da shi? Na fada a zuciya ta, ta ci gaba ai ba karamar rigima aka yi ba da Baban Usman (Alh. Shehu Magaji take nufi) shi sai dai in zauna tare da iyalansa ni kuma dama Kaduna nake son zama, saboda bana son tashin hankali tsakanina da matarsa, na fi son nesa-nesa bana son takura, ana cikin haka sai aka yi masa transfer Lagos dama yana da gida a can amma ba girma sosai, shi ne fa abun ya lafa ya amince 'ya'yansu na nan a nan saboda Makaranta da shi da matarsa suke zama Lagos duk ranar Juma'a sukan dawo suyi week end a nan, to ni me ya dame ni, Allah ya ba ni in ce bana so, so kin ji yadda aka yi Allah ya kawo saukin saboda shi dama ba azalimin kowa ba ne, sannan yana aiki ne da niyar mutum. Ajiyar zuciya na yi ina kara so da kaunar Gwaggo, ita dai Allah ya yi ta mai tawakkali da duk abinda ya same ta, ta kan yi hakuri sai ya zo ya wuce. Muna nan muna hira har sha biyu ta wuce tare muka kwana dakin Gwaggo a ranar wallahi na sake na yi bacci sosai, ranar har da miyaun bacci, na dade bana bacci hankalina a kwance tunda na shiga gidan Tahir. Suwaiba sam ta kasa bacci damuwarta ita ce ina ya kai Dayiba, ga shi shima ya ki ya shigo gida balle ta tambaye shi, kwata-kwata bata rintsa ba 68 Baki Biyu Sameera Mustapha: saboda ta fitini kanta. Da Asuba ta ji motsi da saurinta ta fito falon ta ganshi zai shiga dakin Dayiba, ta yi saurin bin bayan sa zuwa ciki,

Chapter 4 of 8