Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
3 / 8
biyu daya ford ce dayan kuma landguriser, 34 Baki Biyu. Sameera Mustapha: sam ban sa komai a raina ba don nasan kila bakin Alhajin gida ne don idan yana gari dama yakan yi baki irin wadannan. Kai tsaye na shiga falo, kaya ne aka baje ana ta kallo, Anti Badiya ta ce 'yar halak tun dazun ake neman ki ina ki ka shiga ne, ga kayan lehen ki nan an kawo, harara na wurga mata tare da 6ata fuskata, ban ce komai ba na juya fuskata, ai sai muka yi ido hudu da Suwaiba, irin kallon da tayi min ya ba ni mamaki, sakin fuskar ta yasa faduwar gabana ya lafa, anya ita ce ko dai ban lura ba? Na tambayi kaina, dole nima na saki fuska ta nayi mai da mata martani na gaida ta, sosai ta yi fara'a tana amsawa, wato bani kadai abun ya ba mamaki ba, duk wanda yake falon kallonta ake yi don ina zaton ba a taba zaton haka daga gare ta ba, ni dai na karasa dakina ina tunani, anya abunda Tahir ke fadi akan baiwar Allah nan gaskiya ne? kai namiji namiji sai shi, dama na sha jin labarin idan namiji na son aure ko saki ga matarsa to yana iya shirya abunda matar bata ma taba kuskuren yi ba, bandaki na shiga sai da na watsa ruwa na fara alwala abun mamaki sai na ji hawaye na fitar min daga idona, ba ji ba gani, dole na daina alwalar na zauna kan water system ina kuka, a kalla na samu minti talatin sai naji ana kwan-kwasa kofar bayin muryar Mama Hadiza naji (yar babba ce a zaria 35 Baki Siyu Sameera Mustapha: take aure) tana cewa ke Dayyiba za ki fito daga bayin na bakinki tun dazun suke jiran ki, da sauri na mike na fara sabon alwala cikin minti biyu na fito tana nan dai tsaye a wurin wai ke wace irin yarinya ce, ba ki ko tsoron abunda ke bayin, wucewa na yi na fara sallah, hadawa nayi da Isha'l sannan na saka jallabiya ta, babu abunda na shafa ina zaune bakin gado sai ga Anti Badiya ta shigo, tashi muje uwargidanki ta ce ki zo kuyi sallama tana so su wuce masauki. Gyalena na dauka na yi saurin rike hannun Anti, ta gano abinda ke damuna, don haka sai ta biye min. Muna isa falin gun Gwaggo na je na zauna a kasa kan kafet kamar daga sama sia na ji Suwaiba ta ce, amaryarmu tun yau muka fara sayen baki ne, baki daya aka yi dariya, ni kuwa sai naji na fara jin kunyarta, mikewa tayi ta zo ta zauna kan kujerar da ke kusa da Gwaggo ta dan rankwafo don in ji abunda take cewa, kwali ta azamin akan cinyata ta ce, amarya ga sako mai mahimmanci, ango ne ya ce in baki, kuma ki bude ki saurara zai neme ki, dama a dalilin wannan sakon naki tafiya har sai na isar da sakon ango zuwa gare ki, ni dai kaina na kasa gabana kuwa kamar zai fito, ni dai sai na ji ta kwanta min, tausayin ta kuma ya kama ni, kai anya zan iya wannan.....Suwaiba ta katse min, tunanin da nake yi ta ce, to asha hira ce, to amarya 36 C Baki Biyu Sameera Mustapha: lafiya, mu dai bari mu tafi Gwaggo tayi saurin cewa, to Allah ya sanya alheri, ya baku ikon hakuri da junanku, baki daya falon aka amsa (amin). Gwaggo ta dube ni, haba 'yar kanwata dubi yadda ki ka maida kanki duk kin rame sai ka ce mai cewo, dubi idonki yadda suka kumbura sun yi dara-dara kamar tsokar nama, wai me yasa baki ji abunda ake fada miki ne, sabon kuka na saki na aza kaina a cinyarta, kuka nake yi sosai, haba Dayibba ba tun yau ake lallashinki ba, shin ba ki san aure shi haka yake kamar haßо ba? Lokaci ne dashi, in Tahir ba mijinki ba ne za ki ga ranar ko ta daurin aure ce a fasa don ba mai auren matar wani haka ma mace bata auren mijin da ba nata ba, don haka ki kwantar da hankalinki Dayyiba, ni dai ban ce komai ba, kuma ban daina kukan ba, Mama Hadiza ta ce, ke Hauwa kin manta yarinyar nan mai shegen taurin kai duk maganar da za ki yi mata ba ji zata yi gara ma ki kyale ta in ta gaji da kan ta zata daina. Anti Badiya ta jeho min atamfa, karamar super English a gabana, gashi nan ki nuna ma kawayen ki in za su yi, anko din ranar yinin biki ne, mikewa nayi na har wurin ina kara gunjin kukan da nake yi, ina ji Mama Hadiza na kyalkyatar dariya, tana yi min tsiya. Ni dai dakin Gwaggo na shige na ci gaba da koke-koken da 37 Baki Bivu 2 Sameera Mustapha: nake yi, ada ban dauki abin serious ba, amma abun sai Kara zama gaskiya yake yi na ma ace ni ba matarsa ba ce sai ranar daurin auren in mutu ko a fasa. Tun daga wannan ranar na kara figewa sai kace kazar da ake cire gashin jikinta, na kara ta da hankali na sosai, kayan lehen a washegari su Amina da Aisha suka zo suka gani, Gwaggo kuwa har da basu katin daura aure wai su gayyato 'yan makarantarmu, ba yadda bata yi da ni in diba in kai makaranta ba na ki. Kwana biyu da kawo lehe sai ga Tahir ya zo, abun haushi na shirya zan je Makaranta ina so in fita da wuri ko da karatu in yi, sam bana iya karatu sosai a gida saboda tunanin da nasa ma kaina. Ina jin su suna falo da Gwaggo sai hira suke yi na rasa yadda zna yi in fito saboda dakina a cikin ta falon ya ke, na kai minti ashirin ina shawarar yadda zan shiga falon wata zuciyar ta ce, ki wuce kawai, wata zuciyar tana bani shawarar in hakura har sai ya tafi tukunna, daga sama na ji budewar daki na sai da gabana ya tsinke saboda tsabar fargaba, Gwaggo ce ba tare da ta ce min komai ba ta riko hannuna, ya ya zan yi dole ne in bita, sai da muka kai gun zama sannan ta ce ku gaisa ina zuwa. Kaina yana kasa amma ina ji a jikina kallona yake yi, muryarsa na ji yana cewa, 'yanmata 38 Baki Biyu 6 Sameera Mustapha: babu gaisuwa ne ko ko kin dauki dayan side dinne in fara gaida ki, haushine, takaici ne ban sani ba, turo baki nayi ina kuma wasa da gyalen da ke kaina, kai wannan mutumin akwai kallo, na tabbata ina daga ido za mu yi ido hudu dashi, shi yasa na dake naki dago idon nawa, wallahi ban san sadda ya dawo kusa dani ba, maganar sa na ji akaina, sai da na firgita daya ke muryar sa irin mai girman nan ce sosai, dama ai shima ba karami ba ne yana da jiki ba laifi. Ban san lokacin da na daga idona muka yi ido hudu da shi ba, da sauri na maida idona kasa, na kuma ce ina kwana? Bai amsa ba in ban da aikin kallo babu abinda yake yi, kai wannan wane irin mutum ne dama haka yake? Na tambayi kaina, to kurwa ta kur in kai maye ne, sai dai ka ci kanka, don ni na fi karfin ka, jin nayi ya ce, dauko min wayar da na aiko miki, tsam na mike wani irin dadi naji dama ina tunanin yadda zan rabu da ita, don duk abinda ya fito hannunsa bana so. Shi kuwa a ransa burge shi take yi don ya lura farar kura ce ta cika tsoro, ashe ba karamin aiki zai yi ba ya lura da yanayin ta ko in ce ya karanci bata ra'ayinsa, kallon da ta yi mai yasa ya gano wani abu a kwayar idonta, murmushi ya saki ya ce, Allah dai ya kawo ki hannuna za ki so ni ne. 39 e Sameera Mustapha: BaN Biyu Ina zuwa na ajiye a gefensa, na koma can kujerar Karshe na zauna, bai ce komai ba ya dauka ya bude wayar yana hadawa, lebel nawa ki ke? Ban tanka masa ba na yi shiru, ya ci gaba da gyaran wayar sa shima ya yi shiru, sai da ya gama na ji ya mike duk hankalina ya tashi don naga alamar guna ya nufo, a take na soma jin fitsari don tsabar fargaba, wayar ya ajiye a gefena, ya ce amarya rowar murya ake min ba za ayi min magana ba, ba komai akwai lokacin da za ki yi ne, ta shi in ajiye ki Makaranta, Gwaggo ta ce min za ki je Makaranta, duk da murya ta na rawa na ce kai tafiyarka amma ni ba zan shiga motarka ba, a kan me? Ya yi tambayar cike da kasaita, Eyee! Mutumin nan da gaske yake yi, to ban zan shiga ba....muryar Gwaggo ce ta tsinka min tunanina, ki tashi ya rage miki hanya mana, ni bana son Gwaggo na yi min haka, sai ka ce ta san ba zan iya musa mata duk abunda ta bukaci in yi ba, to ko ta gane ne, na ji yana cewa Gwaggo bari in ajiye ta in dawo, Gwaggo ta ce, to Allah ya kiyaye. Dakina na shiga, sai da na shiga toilet na yi fitsari sai kuma na fito na rasa ma abunda zanyi da zai ba mutumin nan haushi, sai da na yi kamar minti goma sha biyar sannan na fito shima din don naga lokacin paper na karatowa ne. 40 Baki Biyu Sameera Mustapha: Na fita yana zaune a cikin mota, ko ina a kule yake. B.M.W ce baka sai sheki take yi, gashi ansa tinted glasses sai dai ba mai duhu ba, da gangan na bude kofar baya na shiga na zauna ni kaina naga kokarina. Na dake kuma sai kace motata, muryar nan dai tasa na jiwo sai da na yi shock kai muryarsa ta cika girma da yawa, ya ce, ki dawo gaba mana 'yanmata, ina jin sa amma nayi banza da shi, bai bata lokaci ba ya bude motar ya fita, na daga kai ina kallon abunda yake niyyar yi, kofar baya ya bude ya ce, kin san Allah zan fasa kai ki kuma zan hana ki zuwa Makarantar nan, wa ya yi losen? Ke! Don haka kiyi abinda na ce ko hakan ya faru da ke ai ba san lokacin da na fita ba kafin in shiga ya tambaye ni ina wayar da na baki? Ba so magana ba amma kuma na yi tunanin kada ya hana ni zuwa Makaranta, na san idan ya furta hakan to ko Makarantar zai hana in je ta baki daya. Tana falo na fada ina gintse fuskata, ya tsaya kawai yana kallona, ni kam juya masa bayana nayi ma ina shafa littafin da na rike, zagayowa ya yi ya ce, ki je ki dauko wayar nan, ko in yi abinda na yi niyya. A gaskiya tun kafin ya yi magana kwarjininsa da girmansa sun takura ni, da sauri na bar wurin na koma na dauko wayar, ina shiga ya ja motar, ba wanda ya yi magana na tambaye kaina haka 41 Baki Biyu @ Sameera Mustapha: yasan makarantar, na cije nayi shiru sai tafiya yake yi da abun ya ishe ni shine na ce Kaduna University fa nake, ya juya kan mota muka kama hanyar Makarantar, a raina na ce lallai mutumin nan yana so ya ce wani abu, muna isa cikin Makarantar da saurina zan bude kofa, amma ta ki ta bude, ya ce babu ma godiya za ki fita? Na gode na fada da sauri. Batun wayar da na baki ki sani idan na nema naji ta a kashe ko ki ki dauka zan yi sanadin da za ki daina zuwa Makarantar nan don dama ni ba son ta nake yi ba. Harararsa na yi, ki harara da kyau na dai fada miki. Har na fita daga motar ban kara kallonsa ba, zan wuce ya ce, karfe nawa za ki gama lectures din? Na so in yi banza dashi amma sai na tuna da maganar Makaranta da ya yi min, don haka ba tare da na kalle shi ba na ce, ai za'a zo daukata, ji nayi kawai ya wuce da motarsa, na ce a fili kamar yana ji na, wai shi wannan mutum me yake nufi so yake yi ya takura min, to wallahi ba zan dauka ba, yau dole ne ma in yi wa Gwaggo maganar Makaranta ta ai samu na ya yi ina yi zai zo da kakalensa na iya yi ya ce ba zan zo Makaran....Amina ta taba ni a bayana, lafiya? Da ke da wa ki ke magana? Mtsss na ja wani irin tsaki mai tsawo na ce bari ke dai wai wancan mutumin da aka hada ni aure da shi bakin cikin 42 Baki Biyu Sameera Mustapha: ci gabana a rayuwa yake yi, to wallahi zan yi maganinsa danni ba zan yadda ba, wane irin ci gaba ne ya hana ki samu wani illimin da nake nema yake ikirarin zai iya hanani in ya ga dama, to ta Allah ba ta shi ba, Amira ta lura, raina ya baci da yawa, jan hannuna tayi zo mu je kinga har kowa ya shiga class kin san fa wannan ita ce paper karshe, sai da gabana ya fadi, na dai daure na matse muka shiga aji. A ranar muka yi paper karshe ina tunanin a gaskiya jarabawar karshen nan sai Allah, don sai na zama confuse baki daya na fita hayyacina, da na isa gida ma rigima na rika yi wa Gwaggo, tun tana kula ni har na bata haushi, kayan da na ga ana shigowa da su shi ya kara sa na yarda lallai ba karamin shiri suka dauka ba, duk wani tunani ma ban san irin wanda zan yi ba. Dole na koma 'yar daki, da yake anan Kaduna za'ayi komai tun ana saura kwana uku daurin aure 'yan biki suka fara isowa ni dai ina daki na kule kaina a ciki, babu kuma wanda ya bi ta kaina. Daya ke ba wani event za'a yi ba da yawa ranar sa lale ne ma aka shirya shi tamkar dinner, wannan aiki Anti Badiya ne da Anti Fiddausi a ranar sai da Gwaggo ta nuna min bacin ranta sannan na yarda naje gyaran kai, Amina da Aisha suka raka ni, Aisha ta dube ni tana min dariya, ban tanka taba daina lura so take yi, in yi magana. Har aka 43 Baki Biyu e Sameera Mustapha: gama mun gyaran kan nawa a kumbure nake jira kawai nake yi in fashe. Tahir ya neme, ni a waya yakai so talatin amma na ki dagawa, na kuma saka ta a silent don haka ma wani kiran bana ji bana gani kai tunda ma ya bani wayar bana daukar wayarsa. Da daddare bayan anyi sallar Isha'i, zo ku ga yadda gida ya cika fam da mata. Ni kuwa cikin milk and chocolate colour na wani hadadden material mai kyalli, aka shirya ni, a wurin shirin ban da ikon in ki dan Gwaggo tsaye tayi a kaina, Anti Nafisa ita ke yi min make up. A gaskiya nima kaina ban gana ni din ba ce don na yi kyau sosai tamfar ba ni ba. A gaskiya an shirya shi sosai an kira mata masu kidan kwarya aka cashe, ni abunda ya fi daga mun hankali na shi ne, yadda Anti Suwaiba tasha rawa, kowa ma na mamakin wannan al'amari, ikon Allah, ta lika min kudi 'yan naira dubu-dubu da dari biyar babu iyaka, kowa kuwa sai san barka suke yi min akan nayi dacen kishiya, ni kam a raina tausayin ta nake ji. Hotuna munyi-munyi har na gaji, haka aka ci aka sha aka raba alherin da aka yi na auren aka watse. Washegari ne akai yi min kunshi mai dan karan kyau har da stones aka sa min da yake dama ina period. A ranar tare da abokaina muka wuni. 44 Washegari kuwa karfe goma da rabi na safe aka daura aurena da Tahir, anyi haka ne don a ranar ake son a wuce da ni Abuja. Ai kuwa karfe hudu da rabi na yamma muka isa, nan ma wani taron Anti Suwaiba ta hada min na musamman, kayan sawa ma iri daya muka sa, sai da dan ni na saka ashoke ne a kaina da kuma kuguna. Kowa na yaba hali irin na Anti Suwaiba, da yake baza ayi dinner ba, kafin takwas na dare an watse sai ni da abokaina, Aisha da Amina kam mazajen su suka dauke su, tare da abokaina muka kwana. Washegari breakfast sai da muka tsalake babu abunda ba ayi ba, da yake su Anti Badiya a guest house din mijin Anti Fiddausi suka sauka, sai da aka yi sallar Azahar tukunna suka shigo gidan, sun ja min kunne kamar yadda iyayena suka yi min nasiha, na dube su ina kuka na ce, Anti in fa akwai abunda ke damuna, meke damunki? Sun tambaya duk a lokaci daya, Baba fa ba ta zo bikin nan ba don ban ganta ba, na kara fashewa da kuka, anti Nafisa ta ce, gaskiya bata samu zuwa ba sai a ranar daurin auren suka zo tare da Baba, hala ba ku hadu ba da aka kai ki gun Baba lokacin. da za'a taho nan Abuja? A'a, ni ban ganta ba, to hala Baba na bari a ganta ne aka gaya miki? Ai ko mu ma bamu gantan ba ko irin nasihar nan da ake ba dawa sai dai su Gwaggo suyi, amma ita kam gudu take yi na tsayar da 45 Baki Biyu Sameera Mustapha: nan, na tsuguna gabanta ina lallashinta. nima hawaye ya zubo min, daga sama Tahir ya shigo dakin amma yana daga bakin kofar dakin, Anti Suwaiba na ganinsa ta hau zaginsa, Allah ya isa tsakanina da kai mugu azalimi, kai wane irin mutum ne wai? Iye ina tambayar ya za'ayi ana kawo yarinya za ka nuna halin ka gare ta, to sai Allah ya saka min, bai jira ta gama ba ya wuce abunsa, ta dube ni tana cewa, sam ban so ki ji abun da ke faruwa ba Dayiba, amıma ya zanyi zafi ya yi zafi dama haka yake Anti? Na fadi hakan muryata na rawa don a gaskiya hankalina ya tashi, ni na san bai da halin kirki, saboda mahaifiyarsu haka take da mugun hali....Anti ta tsinka min tunani, ta ce kada ki damu 'yar uwa, wata rana sai labari zai daina ne, amma Anty shekararku nawa da auren bai daina ba? Ai kuwa sai ta soma shekarar mu ta takwas kenan amma kullum dukan safe daban na dare daban, ni na ma manta yaushe na ga dariyarsa, yana da mugun hali da baki zato in kin ganshi a hili za ki ce gentleman, amma wallahi mugun mutum ne, baya da imani ko kadan, gashi da 'yanmata waje ba ya iya kula da iyalansa amma su 'yanmatan sai su ci mai isarsu, ko kinsan wani lokacin har gidannan yake kawo su? In kuwa nayi magana a gaban su zai ci min mutunci har da duka ma. 47 Baki Biyu Sameera Mustapha Mun sami kusan awa biyu tana bani labarin Tahir, ji nayi ina bala'in tsoron sa, ni na sani namiji namiji ne, to wai auren dole ne? ni dai a rayuwa ta ba zan taba dacen miji ba, ga tsoron sa ga tsanarsa duk a tare dani, ni dama bana kaunar namiji mai duka, to dole ne in kama kaina, zan san yadda zan yi insha Allahu sai ya rabu da ni ba zan iya ba. Da ta lura na shiga damuwa sosai, sai ta dafa ni ta ce, kada ki damu ba zai kasance a kanki ba, amma iyayenki a gaskiya basu yi zaben kwarai ba, sai dai kila ya daina. Ranar sukuku na wuni kamar wadda kwai ya fashewa a ciki, da wuri na nemi duk abunda nake bukata na shige daki, na kulle da makuli. Suwaiba kam tasan ta kulla mugun abu, don haka sai ta rika kyalkyatar dariya, tana tafa hannunta a can cikin dakin ta. Ta san ta gama tsoratar da Dayiba, wayiwa! Ta fada a fili sai naga karshenki, ta tuna a jiya da yamma sako taje karba a tashan Abuja daga gun Mama, ita fa so take yi ta nakasa Dayiba wajajen bayan magariba ta zuba magani a bakin kofar dakin wai idan ta taka to ta takan amma tsab ta ganta ta shigo falonta, dalilin kukan ta kuwa shine, Tahir na shigowa gidan ta bishi dakinsa, da ya ganta ya gani a fuskarta, masifa ce tafe da ita don haka sai ya share ta ya ci gaba da abunda yake yi. Ta 48 Baki Biyu Sameera Mustapha: sami wuri kan lazyman cushion dinsa ta zauna tana kallonsa, can dai ta ce, ango kasha kamshi, hala saurin me ka ke yi ne naga kamar zaka tashi sama? Ta yi mai tambayar da alamar ta zo da magana, ya dube ta yana murmushi, a'ah ke kuma mutum ya yi aure ai dole ya yi sauri ya sami ni'imar amaryarsa, ta kai hannunta kan kirjinta don ji tayi kamar zai fito waje don tsabar bakin ciki, me kake nufi? Ya sake dubanta ban gane me nake nufi ba, amarya ke jira na fa ba kema kin kira ni baka kusance ni ba sai da na kusan shekara gidanka? Cewa fa kayi na riga da na gama yawon gantali, itama ai haka ne don haka ba zan yadda ba itama haka zaka yi mata don da alama mata fini yawon iskancin don na lura gogaggiya ce gata dama fara ce to ai fararen mata yawancin su....ya katse ta, ke bana son zancen banza, kina jina ko tun shigowar ki na lura kin shigo da shirin ci min mutunci, to ba zan dauka ba, kin gane ko, na fada miki tun farko auren nan ba na yi ba ne don in wulakanta ki ba, Suwaiba insha Allahu zan kwatanta adalci tsakaninku, dariya na fitar hankali ta saki, adalci? Ta tambaye shi kai din ne zaka yi adalci? Ta sake tambayarsa, tare da girgiza kanta ai ni bana yadda da duk shirin ka in fada maka, ni fa na fada maka tun farko bana shearing din da namiji, saboda ni haka har ya hana ta ci gaba da 49 Baki Biy Sameera Mustapha: magana, ashe za mu gani dani dake wa zai fadi gaskiya, kuma waye mai ikon gidannan ina zaton ni ne? to bari ki ji in fada miki duk iya yin ki kiyi amma ni kuma ni ne mai yin abunda na yi niyar yi in kin ga dama ki zauna in kin ga dama ki tafi duk abunda ki ka shirya ma kanki ki aiwatar ke ki ka sani. Ni kake fadawa haka? To ni kuwa zaka gani sai ka san ko ni wacece, sai ka san ni mace mace mai 'yanci a rayuwarta, abunda na zaba shi zan aikata. Ta wuce fuu tana gunguni ya bita da kallo, anya yarinyar nan tana da hankali kuwa? Ya fada a ransa, ko da ya ke laifinsa ne da ya ki daukar mataki akan ta tun farkon yana gama tunanin shine ya wuce dakin Dayiba yana murda dakin ya ji shi gam har sau biyu yana gwadawa, ya san ayi haka don ya lura itama yarinyar 'yar tsiwa ce. A sanyaye ya bar gun ya fice daga gidan baki daya don tsabar takaici gun Christiana ya wuce. Bai shigo gidan ba sai da asuba har ya shiga dakinsa ya yi wanka ya yi sallah ya ji ihun da Suwaiba ke yi har a ransa ya san shiri ne shi yasa bai bi takanta ba sai da ya gama shirinsa tsab sannan ya fito dauke da suit case dinsa da ka ganshi da kaga ya yi shirin fita office. Yana isa kuwa ya ganta tare da Dayiba, ya karanci tsana daga idon Dayiba, yasan Suwaiba ta riga da ta 50 Baki Biyu e Sameera Mustapha: hada boom da. haka ne ma bai nemi sanin komai ba, ya yi ficewarsa, yana tunanin ta inda zai bullowa wannan al'amari. Washegari ma ina kwance da asuba kamar jiya naji ihu, yau kamar abun yafi na jiya don cewa take yi, na shiga uku jama'a a taimake ni na shiga uku na lalace zai kashe ni...." Ai ban san lokacin da na kara shigewą cikin bargona ba, gabana kuwa kamar zai fito don tsoro, kuka na saki ina tausaya wa kaina, can na ji an yi shiru don haka na yi tunanin ya fice na bude kofa a hankali ina leke, babu kowa na fita na kulle dakina da hanzari na isa dakin Suwaiba, yau ma a kasa na ganta zaune duk ta fita hayyacinta, na karaso gunta ina yi mata sannu, sabon kuka ta saki, nima sai na bita mukai ta kuka sai da ya ishe mu, ta riko hannuna ta ce, Dayiba kina bani tausayi tun ba akai ko ina ba Tahir ya fara nuna miki halinsa yau kwananki hudu a gidannan amma kin fahimci abunda maigidanmu yake yi na kara sakin sabon kuka ni nasan haka rayuwa ta zata kasance ba zan taba kaunar da namiji ba har in mutu, ban gane ba Dayiba ai a take ban boye mata komai ba akan mazajen da na so a rayuwata suka ci amanata, ta dan rungume ni ta ce, kada ki damu sai dai ina yi mana jajen auren mutum irin Tahir, saboda dai a gaskiya ke yarinya ce karama bai kamata ki fado irin 51 Baki Biyu e Sameera Mustapha: hannun namiji irin wannan ba, saboda sam jikinki bai saba da wahala ba, tabbas hankalina ya yi bala'in tashi, tsanar Tahir kuwa karuwa take yi a zuciyata, sai ka ganshi ka ce mutumin kirki ne, amma ashe mugu ne, oh! Allah ni kam na shiga uku ko sati ban yi ba amma bakin ciki ya karu a rayuwata, a gaskiya Gwaggo ta cuce ni ba kadan ba, ko da yake ba laifinta ba ne, bata san ya canza ba a zaton ta yana nan yadda yake da yana gunta to amma ai dama mutum kan canza halinsa me yasa ba za ta fahimci haka ba? Anti na ji ta tabo ni ta ce, kada fa ki sa wannan abun a ranki tashi ki je kiyi wanka kin san har yau ba a daina zuwa ganin daki ba, kada a shigo a same ki haka. Na mike jikina duk ya yi sanyi, na wuce dakina. Suwaiba yau kam rawa take yi har da juyi, ta gano Dayiba ta tsani Tahir tsab ta gani a kwayar idonta, to sai kin bar gidan nan, waya ta dauka ta bugawa Mama tana bata labarin yadda suka yi, Mama dai ta tunasar da ita sharudan da Jilli ya basu, na su shawo hankalin su baki daya ne, ta yi shiru tana sauraren

Chapter 3 of 8