Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
1 / 8
An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels BAKI NIYU HNL by samira mustapha HAUSAВООК.COM 2 BAKI BIYT SAMIRA MUSTAРНА Baki Biyu e Sameera Mustapha HAKKIN MALLAКА (М) Sameera Mustapha GODIYA Ga Allah (S.A.W), da ya bani fasaha da ilimin rubuta wannan littafin, sannan ga Maigidana Alh. Aliyu Sulaiman da ya ba ni goyon bayan rubuta shi, sai ga Iyayena Alh. Mustapha Haliru Bulasa da kuma mahaifiyata Haj. Fatima Yahaya, Allah ya Kara daukaka ku, amin. TALLAFI Ina godiya gare ki, Halima K/Mashi, da ki ka tallafa min, ki ka ba ni karfin guiwar rubuta wannan littafi, Allah ya kara budi, Allah kuma ya barmu tare, amin summa amin. TUKUICI NE GA Nusaiba Sa'id Moh'd, Najib Sa'id Moh'd, Anisa Sa'id Moh'd, Abduljalil Sa'id Moh'd, Arif Sa'id Moh'd INA KAUNARKU Anti Murja Bande Sokoto, Mama Sa'a O.P.U Hauwa'u Iya (lya mai kosai), Baba Abu BUGAWA A NA'URAR COMPUTER: NAFI'U SALISU 08038981211-07028573535 2 Baki Biyu ه N a farko ina so..." Ya dauki waya ya mika mata, "ki buga wa Gwaggota ki bata hakuri akan wulakancin da ki ka yi mata." Ta ce a ranta, “shi wai wannan ba ya da mantuwa ne, abunda ya faru wata biyar da suka wuce sai ya dawo dashi." Ta karba ba tare da son ranta ba, ta buga don dama number Gwaggo ce akan wayar, bugu biyu ta dauka, hakuri ta rika ba Gwaggo wanda ya dauki tsawon minti goma tana magana, bayan sun ajiye ya ce, sai sharadi na biyu ina son ki rika yi min abinci da kanki don bana son abincin dan aiki, ta dube shi ban iya ba, zan koya miki a hankali za ki ioya, ni na ke yiwa kaina abincin da zan ci, ko a office in kin lura ina da kitchen a ciki ni nake yiwa kaina, na kuma fi cin vegetable kin gane, da sauri ta ce eh, ina ganewa, ina son duk in za ki fita in sani, sannan ina son sai kin yi sannan sai mu daurawa kanmu sabon aure ba tare da kowa ya sani ba, in kuwa za ki tonawa kan ki asiri shi kenan ni dai ba zan yadda in kusance ki ba in ba Istibiradi ki ka yi ba, kin yadda da sharuda na? ta dan kauda idonta gefe ta me ka ke nufi da Istibiradi? Hmmn ba ki san abinda ake nufi ba? Ta girgiza kanta, ban sani ba, to ina so ki fada min gaskiya tsakaninki da Allah ba ki taba having sex ba? Gaban ta ya fadi sosai, ta ce No!no! tana girgiza kanta ban taba ba 3 Baki Biyu Sameera Mustapha: cike da mamaki ya ce, za ki rantse min? eh, kwarai zan rantse maka don wallahi ban taba kwana da da namiji ba a rayuwata, ta shigo sosai cikin jikinsa, abinda ta fada shi yasa jikinsa ya yi sanyi har ya biye mata. A nan falon ya murje ta ta murje shi son kasance cikin jin dadi sai da suka natsu sannan ya dube ta ya ce shekarun ki nawa? Ta amsa çike da jin dadita ce, ashirin da tara ya tsora mata ido tabbas gaskiya ta fada, a ransa ya ce, to ko shi yasa bai same ta cikakkiyar mace ba, bai sani ba ta talafo habarsa ta ce, Dolly kai fa shekarunka nawa? Ya yi dan murmushi, ya ce talatin da uku, don't tell me shekaru hudu kawai kaba ni yes! Shekaru na kenan, tun daga ranar suka sami junansu, shi dai yana biye mata ne ba don komai ba sai don tayi masa rantsuwa, sannan shekarun ta sun yi nisa. Kwanciyar hankali sun samu, don a kullum suna tare a kicin suna girki, har ta soma iyawa kuwa soyayya sosai suke yi, a kullum kuma suna tare ita tasan Tahir namiji ne dole ne kowace mace ta so shi don yana da komai da mace ke bukatar namiji ya samu, gashi kyakkyawa ga halitta sannan gashi gentleman babu ruwan shi da matar da bata shi ba, ita ta san tayi dacen miji wani gefe na zuciyarta kuma sai ta tuna da Jessica kawarta kuma aminiyarta, da sauri takan kauda tunanin Jessica, koda yaushe tana cikin 4 Baki Biyu Sameera Mustapha: koyon girki sai dai shi ya rasa dalilin ta na rashin iyawa, a haka dai yakan faure ya ciko ya dan yi kuskwarima sannan ya ci. Sun sami kamar shekaru uku suna soyayyar su a cikin shekarun ne suka haifi Nana Asma'u, a haka dai suke sai dai ita a wannan lokacin ta daina girki don ko ta girka baya ci, to meye amfanin girka masa, sannan bata son Gwaggon sa, shi yasa suke samun matsala, ita kuma a ganin ta tunda ta samu Asma'u me ruwanta dama ta riga da ta sa wa ranta, da ko diya daya tal zata haifa, ta bata tarbiya da ilimi da zai amfani yaron, tun da ta haife ta, take allurar planing sam bata wasa, duk bayan wata uku tana zuwa ta yi sai dai bata fada mishi ba, kai kowa ma bata fada ma ba. Suna da shekaru biyar da aure, Jessica Jojo wato abokiyarta ta America, wadda aka fi sani da JJ ta dawo cikinr ayuwarta, suna ganin juna suka rungume junansu, suna shafan junansu sai kace tare da namiji suke, ai basu tsaya ko'ina ba sai bedroom din Suwaiba, sa'ar su daya ba kowa a gidan, maigidan ya yi tafi. Asma'u kuwa tana Makaranta. A nan suka murje junansu ka ce miji da mata, ashe dama Suwaiba lezbiyan ce? Hmn ikon Allah dole ne ta rasa virginity din ta ko ba da dan namiji ba, kai wannan rayuwa ta yanzu sai a hankali. Ko me suke sha'awa da junansu 5 Saki Biyu Sameera Mustapha: oho! Tana mace kina mace, Ubangiji Allah ya yi mana sassauci, ya shirye mu ya kuma kare zuri'armu daga sharrin zina da luwadi, amin summa amin. Sai da suka natsu sai kuma Jassica ta janye jikinta tana shan taba, tsab Suwaiba ta gano laifin ta ta matso sosai cikin jikinta ta ce haba sweeti am sorry, ban san yadda nima nayi saurin canjawa ba kawai abun is a dream, domin ke kin san ina ki, harara Jassica ta wurga mata ta ce, dalla can bayan tun a America da ki ka hadu da dan iskan mutumin nan ki ka share ni, ni na gani a idonki a tun lokacin ki ka daina sona ni ce kadai nake hauka a kanki gashi yanzu ma ai ni na biwo ki, haba sweety kiyi hakuri har yanzu ina son ki a kullum ina tunanin ki sai dai na san ba zan samu halin komawa America ba ina dawowa iyayena suka matsa min in yi aure. Тo ba a can mun shirya yin aure ba ko kin manta? Sai a lokacin ta tuna fa, lallai sun shirya yin aure, to ya ya zata yi tunda namiji ya shigo rayuwarta? Ita dadi ma ta ji da Jessica ta zo don yanzu za ta sami wadda zata debe mata kewar namiji, don dama ita ba gwanar bin maza ba ce. J.J kiyi hakuri tunda yanzu kin zo, I will be with you all my life I promise you. Jessica tana bala'in son Suwaiba ya zata yi dole ta hakura ta rungume ta, suka ci gaba da shashancinsu. 6 Baki Biyu Sameera Mustapha: Tun daga lokacin Suwaiba babu ruwanta da harkar Tahir, don boys quarters ta sa aka gyarawa Jessica, a can suke haduwa su sha dadin su, shi dama maigidan tund aya ga Jessica ya san ba karama ba ce, dole yasa ya barta gidan don kada shi bai da kirki sai dai ko in kallan da Suwaiba keyi masa ya soma damunsa, dole ne ya shiga damuwa tunda shi mai bukata ne, sannan shi ba mai neman matan banza ba ne; tun tana wulakanta shi ahr ya hakura ya daina biye mata tun da dama 'yar buturiyarsa shima tana garin don haka kowa ma ya ci tsinkensa babu babbaka. Da abun ya yi yawa, sai ya kori abokiyar tata daga gidan, akan dole ta bar gidan ba karamin tashin hankali aka yi ba, don nacin Jessica ta се, ba inda zata sai da ta kama mata gida nan kusa da su, cike da sa'a kuwa suka samu, don haka a kodayaushe suna tare. Asma'u tana da shekaru bakwai a duniya ta ce ga garin ku nan, ba wani ciwo ta yi mai jinkiri ba, sai dai duk taimakon da Likitoci suka yi ba su iya ceto rayuwar ta ba, a lokacin ne Christina budurwar Tahir da Jessica suka hadu, ashe 'yan uwa ne, kuma dukkansu abu daya suke so, wato ita JJ tana tare da Suwai ita kuma Christina tana tare da Tahir, abun ya basu al'ajabi, dama ita Christina a London take da yake iyayenta anan 7 Baki Biyu Ο Sameera Mustapha: suke, amma abun mamaki ba wanda ya fada wa 'yar uwarta sirrin ta. kannan su kan su basu yadda da junansu ba don dama kowa ya san matsayin kowa. Suwaiba ta shiga damuwa sosai a wannan lokacin diyar ta daya tal tilo da take ji da ita, ita kaďai ce kwanta a wannan lokacin, shima Tahir abun ya dame shi amma da yake shi namiji ne dole ya fita dauriya, sun je asibiti har kala hudu amma babu bayani, duk da ita kadai take zuwa aka ce mata lafiya lau take, shi kan shi Tahir abun na bashi mamaki, yadda za'ayi ace 'ya daya ya haifa a rayuwarsa bai san matarsa ce bata so ba. Ana cikin haka zaman dai babu dadi a tsakaninsu a koyaushe ya je da maganar gun Gwaggo shi take ba laifin, ta kuma ba shi hakuri shi ne fa ana cikin haka rannan ya dawo gida, ya iske gidan a kulle da ya tambayi maigadin gidan shima ya ce bai ma san fitar su ba, shi dai yasan a kullum suna fita ita da wannan kawar tata JJ, kenan yake nufi, dirshan ya zauna kan benchin baba maigadi, tuni zuciyarsa ta rika harbawa don tsabar bakin ciki, idanunsa suka juye zuwa ja, ya yi kokarin danne damuwarsa amma ina, ya ce Baba dama haka take fitan Baba ya dan yi shiru ka fada min Baba, ka sani fa amanar gidannan na baka, idan ba ka faďa min ba wa zai gaya min in 8 Baki Biyu Jance dan san da fitar ta ko abunda take yi da ban tambaye ka ba, dama aikin ka ka kula min da amanar dukiyata da iyalina, ko ba haka ba? Ajiyar zuciya Baba maigadi'ya yi, bai taба son ya hada Alhajin da iyalansa ba amma shi kanshi ya san tun ran gini tun ran zane, tun da tun auren su ma matar bata da natsuwa to ya isa ya fada ya bata aure. Tahir ya san abunda Suwaiba ke yi ya yi nisa tunda har Baba maigadi baya son ya fadi laifinta, inda ita matar kwarai ce da tuni ya soma bayani, ya karanci baba, tsoro yake ji ya fada masifa ta tashi a gidan, ya sassauta muryarsa ya ce, Baba don Allah ka fada mini tsakanin ka da Allah me Suwaiba take ciki? Ba wai ka hada ni da ita ba ne, gyara nake son yi don haka nake son jin abunda ke faruwa. Eh! To a gaskiya iyalan ka ba wai ba su da kirki ba ne sai dai matsalar su daya ce, irin kwashe-kwashen abokai da suke yi, to irin abokanne ke juyar wa da iyalan naka hankali. Baba kayi min bayani da kyau ban gane ba...." Hon suka ji anyo kuma an sa sauti sosai a motar, sai ka ce irin gayunnan 'yan shekaru sha biyar da suka fara balaga. Baba ya mike zai bude kofar gate, Tahir ya dakatar dashi, shi ya fita ta karamar kofa ya jiyo muryar Suwaiba tana cewa kai dan tsoho ka bude min gate mana me ka ke nufi? Da yake dare ya yi sosai, don karfe sha biyu saura a wannan lokacin 9 Baki Biyu e Sameera Mustapha: ta lura ba ya da niyar budewa, don haka ta haska masa wutar mota ful light kuwa, ji ta yi kamar ta saki zawo ba ta taba tsammanin Tahir ba ne, a take ta kashe wutar baki daya ta ma rasa me zata yi, da saurin ta ta kashe sautin da ke tashi jikin ta tuni ya fara rawa, Jessica ta ce, meye haka? Ya za ki kashe min waka, da jin yadda take magana a buge take shi bai iso gun su ba, shi bai bude masu gate din ba, to me yake nufi ne? Suwaiba ta fada a fili, JJ ta ce, ke wai na lura tsoron dan iskannan ki ke yi, da ni ce ke da tuni na kashe shi na huta, mutumin nan ya cika takura, haka kawai zai rika maltreating din ki kamar 'yarsa, shin ba ki san rights din ki ba ne? macen aure tana da 'yanci kema ya kamata ki nuna masa matsayinki, its your life ba nashi ba da zai rika juya ki kamar yadda ake soya kwai, ko da yake na ga fa a Africa mace ba ta da ikon kanta sai abunda aka ce da ita, shi zata yi, sai a lokacin Suwaiba ta tuno fa da gaske ne abunda Jessica ke fadi, shin me yasa mace ba ta da 'yanci anan, sai abinda aka kayyade mata shi zata yi? Ta tuna a can America abunda ta ga dama shi take yi, babu mai takura mata, so nawa ma suna haduwa da matan aure a club amma babu ruwan mazajensu, to don me ita zata bayar da kanta, don kawai yana mijinta humm miji? Ta sake fada tana 6ata fuskar ta, ai ina wurin ta ne da shi da babu duk 10 G Baki Biyu 2 Sameera Mustapha: daya, don baya bata hakkinta a matsayin sa na mijin aurenta.....Tahir ya katse mata tunani da ta ga ya koma cikin gidan ya kuma rufe karamar kofar a tunaninta ya hakura, sai kuma suka ji shiru sun sami tsawon minti sha biyar suna hon amma ya yi banza da su. Su koma inda suka fito, ya fada a zuciyarsa yasan matakin da zai dauka, zai yi maganin wannan masifar, dama abunda ya so ya kauce wa kansa kenan tun lokacin da Mama ta ce ya auri Suwaiba, na daya baya sonta, na biyu ba ta da tarbiya, na uku bata da addini, tun da suka yi aure bai taba ganin tayi sallah ba. Sau da yawa yakan yi mata dubara suyi sallah tare randa bai ce su tare ba to fa shi kenan rannan ba za ta yi sallar ba, daga karshe kulle gate din ya yi da kwado ya shige gida abunsa. Sun kai minti talatin a gun suna buga kofar gidan, kafin dai daga karshe suka hakura suka tafi. Washegari da safe ma Suwaiba ta zo gidan a kulle ta kasa karasawa ma cikin gidan. Ana cikin haka sai ta wuce gidansu, tana kukan munafurci, kai mace-mace sai Allah. Karya da gaskiya ta shirya ta fada, shi mahaifin nata har ya soma gajiya da matsalar aurensu, ya dai saurara amma bai ce komai ba, daga karshe dai ta matsawa mahaifiyarta ta buga mashi waya ya zo aji dalilin sa na kulle gida ya 11 Baki Biyu Sameera Mustapha: barta. Haka kuwa aka yi, da ta nemi wayar a kashe take duka wayoyinsa a kashe. Ta rasa inda zata sa kanta don tashiga uku idan iyayenta suka gano matsalar da ake ciki, gashi ita dai zuciyarta bata sha'awar rabuwa da shi, don a gaskiya duk macen da ta sami miji irin Tahir ta gama jin. dadi, duk da ba ta kyautata mishi tasan yana iya hakuri da ita, abunda ya fi bata haushi shi ne, yadda yake nuna mata rashin so kiri-kiri, shi sam bata gabansa, ko suna tare sai dole ya zamaninshi ba don yana ra'ayi ba. To amma duk da haka bata taba kawo tunani rabuwa dashi ba don tasan mutuncin ta a idon iyayen ta shine zama da miji, don haka Jessica ma kauda mata sha'awa, amma ko kusa bata kai matsayin Tahir a gunta ba shi yasa ba yadda Jessica bata yi su gudu wata kasa da ba za a taba zaton zata ba ta ki. Ta sami kusan kwana hudu a gida amma babu labarin Tahir, hatta Mama nemansa suke yi ruwa jallo amma ba su samu ganin sa ba, abun mamaki ashe Tahir na Kaduna gun Gwaggo, yana yi mata rigima akan zai yi aure kuma ita yake son ta sama masa mata. Wani tunani ne ya fado wa Suwaiba, akan bari ta je Kaduna ta gani ko yana nan a can, karya ta yi wa mahaifinta akan Gusau zata je Mama ta ce ta je can, dama shi ido yasa mata 12 Baki Biyu 2 Cmnra Miictanha: Sameera Mustapha: don ya gaji da shari'ar, ba Gusau ta je ba Kaduna ta wuce cike da sa'a kuwa ta sami Gwaggon gida, kuka ta fashe mata dashi ta rika ba Gwaggo labarin gaskiya da karya, ana cikin haka ne Tahir shima ya shigo har ya juya zai fita, Gwaggo ta bashi umarnin shima ya sami wuri ya zauna a yi ta ta kare, duk da abun ya dagawa Suwaiba hankali sai ta dake ta kara maimaita abinda ta fada wa Gwaggo, shi kam Tahir kansa yasa a kasa yana sauraren wannan shiri na Suwaiba, sai bayan ta gama Gwaggo ta dubi Tahir ta ce, "tsakaninka da Allah haka labarinnan yake?" sai da ya dubi kwayar idon Suwaiba, ya ce Gwaggo a dauko Alkur'ani mai girma kowa ya yi rantsuwa." Gwaggo tayi ajiyar zuciya tana yi masu magana a hankali, itama kanta abun ya ishe ta daga karshe dai ta ce, tana son ta ji matakin da Tahir ya yanke don bata son su tafi su kara dawowa, don haka don Allah su yi hakuri da junansu, a lokacin Tahir ya ce Gwaggo ni aure zan yi buzut! Suwaiba ta mike kamar kazar da ta taka wuta, tana wani gintse fuska tare da girgiza kanta cike da mamakin furucinsa, mene ka ce? Ta fada a kasaitance, aure! Uhmm ana shirin yin abin tashin hankali kuwa, kara maimaita kalmar ka in ji, bai tanka mata ba, to ka kiyaye ni, kana ji na ka kiyaye ni don ni fa da ka ke gani ba kanwar lasa ba ce, ina fata da wasa ka ke yi? 13 Baki Biyu 0 Sameera Mustapha: Gwaggo sake baki tayi tana kallonta, a ranta kuwa mamaki ne, menene oho ma ta rasa me take ciki, Suwaiba ta tsinka mata tunani da ta ci gaba da cewa, wallahi ba zan yadda kayi aure ba, don ni bana iya shearing din namiji da wata don da za a halicce ni ma ni kadai aka halitta ka sani, ta nuna kanta, ko a gun iyayena bana da 'yar uwa ni kadai ce mace. Tahir ya katse ta a'ah ina ce ke kadai aka haifa ashe baki kai ba, ke bari in fada miki baki isa ba, kin yi kadan ke nama sake ki saki daya, ki je in kin samu miji ma kiyi aure, ba zan zauna da ke ba..." Haba Tahir, Gwaggo ta mike tana salati, ranta ya 6aci sosai a gabana a gaskiya ban ji dadin abinda kayi ba, ke!ke!!ke!! Suwaiba ta katse ta, munafuka ai ke ce sanadin komai..." maganar da bata karasa ba kenan ta ji ajiyar mari a fuskarta, tas!tas!tas! ka ke ji, sai da ta fadi kasa, zai kara dukanta, Gwaggo ta tare shi to shi ne fa ta bar wurin a guje ta banke kofar falon ta fice daga gidan. Gwaggo fada sosai ta yi ma Tahir, sam bata saurari abunda ya ke so ta fahimta ba, sai bayan sati daya da ya yi tafiya ya dawo ne, Gwaggo ta saurare shi da yake ta sauko, Gwaggo ya kamata ki bani dama in fadi abunda ke damuna, at least na yi hakuri na kusan shekaru tara amma ban samu nasara ba, don Allah Gwaggo ki tausaya min ki taimake ni in samu farin cikin da nake 14 Baki Biyu 2 Sameera Mustapna: nema nima fa mutum ne ina da feelings, ajiyar zuciya Gwaggo ta yi, tunda yake magana ji take kamar ta zubar masa da hawaye don sosai ya bata tausayi, tabbas yana bukatar canji ko zai samu sassauci daga lokacin da suka rabu har ya yi rama sosai, don haka ta saki fuskar ta da fara'a ta ce, haba dana sai ka ce ba namiji ba, to shi kenan naji kaje kayi auren Allah ya sanya alheri, bai san lokacin da ya dawo kusa da ita ba, farin ciki kuwa tamkar ya zuba ruwa a kasa ya sha, hakika kana neman sauki Tahir, amma ina so ka maida Suwaiba dakinta kafin kayi aure. Zan maida ta Gwaggo na gode da hadin kan da ki ka bani, na gode, amma fa ke za ki zaba min matar, ayi haka kuwa dannan? Eh, mana Gwaggo kinsan za6in Mama ce Suwaiba, yanzu kuma zabinki nake so. To shi kenan dan albarka, zan nema maka da sharadin in har na nemo ta babu fashi, da ita din dai za'ayi, babu fashi Gwaggo ko ya ya take na amince. To shi kenan ka bani lokaci. A ranar ya bude ciki ya ci abinci sosai. Tun da ya auri Suwaiba jin dadinsa ya kau, ya ma manta shi yasan zabin Gwaggo shi ne daidai da shi, ba za ta yi masa zabin tumun dare ba, ya bala'in yadda da ita, ya tabbata ba za ta zabo masa 'yar marasa tarbiya ba. Allah sa a dace (amin summa amin). 15 Baki Biyu 2 Sameera Mustapha: Bayan ya samu natsuwa, Gwaggo ta ce, su shirya su tafi Gusau don Suwaiba na can gara ayi komai akan idon su, komai ma ya kare, hakan ya yi masa dadi kuwa. A babban falon Alh. Mohd Sani Shinkafi aka taru har da mahaifin Dayiba Mal. Sabi'u, tunda aka yi auren Tahir baban falo bai taba shiga harkar auren ba, sai a wannan lokacin. Sai da ya ba wa kowa damar magana, a karshe dai ya dubi Tahir ya ce, Tahir na san ka da hakuri, då gudun zuciya. Ni dai shawara ta gare ka ka kara hakuri, idan kuma auren zaka yi ka yi adalci.....ihun Suwaiba ya katse ma falon Baba maganar da yake yi ta fashe da kuka, tana magiyar ita baza ta yadda ba. Tuni ita ma Mama ranta ya baci ta lallabi hannun 'yarta ta suka bar falon. Baban falo dama yana tur da irin tarbiyar Suwaiba tunda ya ganta yasan ba 'A' ba ce ta kai 'Z' a lokacin ya cewa Gwaggo to ke fa Tahir ya ce ke ya bar wa zabin mata, ina fata kin samar masa? Ta yi murmushi tana duban Mal. Sabi’u, ta ce ai ni auren gida ma nake son dan nawa ya yi, ba kuma kowa na zabar masa ba sai 'yar kanwata Dayyiba!" Ba Tahir kadai ya saki baki ba har da mahaifinta, don abun ya zo masa a ba zata, Tahir yana dubanta ya ce, dama Gwaggo akwai aure tsakaninmu? Sosai ma, ka mance cousin dinmu ce? Ba mu haďa komai da ita ba mahaifiyarta ce 16 Baki Biyu Sameera Mustapha: 'yar uwarmu, itama cousin din mahaifinmu сe, ikon Allah zuciyarsa tayi fari tas, bai san mi yasa ba wani irin farin ciki ke shigar sa ta ko ina a jikinsa, a idonsa kuwa ya ma manta yadda Dayyiba take, don sau biyu kadai ya ganta. Sai dai ya lura yarinyar akwai ji da kai, to amma sai ya samu natsuwa da kwanciyar hankali da zabin Gwaggo, Allah ya sa haka ya fi zama alheri. Haj. Hauwa ta lura Mal. Sabi'u ya shiga damuwa, ta gyara murya ta ce, Baban Nafi'u (haka take kiransa) anya shirin nan ya yi maka? Ajiyar zuciya ya yi sannan ya ce, a'a wane ni, in ce bai yi min ba, babu abunda zan ce sai fatan alheri, a rayuwa ta ban ga abunda zaku bukata in ki yi muku ba, bana fatan in taba kin duk wani abunda za ku nema a guna, don ni ban ga

Chapter 1 of 8