gabatar da sallah, sai ta
mike ta sulele ta cikin ciyayi ta bi ta wata
siririyar hanya. Ta nufi gurin da Yarima
Zaiyan ya sanar da ita, cikin rashin sani
kuwa tana barin gurin sai aka shafa
addu'a, daga nan sai Sarki ya yi umarni
akan a ci gaba da tafiya.
Ko yarima bai yi tsammanin hakan
ba amma da ya ji wannan sanarwa sai farin
ciki ya cika masa zuciya domin ya na
ganin lokacin da Lushmaira ta nausa da
gudu cikin dawa, ya tabbata koda ta dawO
ba zata taba samunsu a hanya ba dole ne ta
koma.
Shadilat kuwa sai hankalinta ya
dugunzuma ta shiga damuwa ainu cikin
rashin karfin haka take tafiyar duk ta
damuu.
Sai da Gim Gimbiya Lushmaira ta yi
tafiya mai nisa a sannan ta isa inda Yarima
zaiyan ya kwatanta mata sai tawyi tsaye
57
TURABAR GASKIYA-3 MADAKI
tana duban wajen, sai an fada da gani biri zai
ci mutum. Dajin ya zamo ma'abocin kwarjini
sannan shiru ya mamaye gurin bake daya,
dan haka sai ta fara waige waige cikin sanda.
Bata ji doriyar wata dabbar ba, dan
haka sai ta rasa abinda ya kamata ta yi, domin
ta samu ta gano inda Zakanyar take, tana
tsaye cikin dube dube sai kawai ta ji gurnani
daga can nesa kadan, ko da ta tabbatar da
wannan gurnani ba na komai bane face
gurnani zaki sai ta gyara tsayuwarta ta kuma
kurawa gurin idanu, tana tsaye sai ga wani
narkeke Zaki ya fito daga wani kogo na
bishiyar darbejiya.
Da fitowar wannan Zaki sai ya 'yi
girgiza wanda ya haddasar da korar jikinsa ta
tashi sama, ya saka kafarsa yana sosa kansa.
Da sauri Gimbiya Lushmaira ta koma
da baya ta 6oye domin ganin Zakin ya yi
mutukar ranata, tabbas ko da ita da Shadilat
da kuma Yarima Zaiyan za su hadu ba za su
iya da wannan Zakin ba.
Tana nan rabe tana son ganinya
kauce domin ta sulele ta koma can in
58
TURABAR GASKIYA-3 MADAKI
da ta fito domin ta san wutsiyar Rakumi ta yi
nesa da kasa, in ma ba rainin hankalin ba ta
yaya za gwada jarumtakar dan adam da Zaki
jrin wannan alhalin kuma baka rike da komai,
tabbas sai yau ta kara yarda Yarima Zaiyan
makiyinta ne kuma baya kaunarta....
Numfashinta ya dauke lokacin da ta
hango Zakin ya nufo inda take 6oye gadangadan ta yi sauri janye jikinta dan kada ya
lura da ita domin ta fuskanci ba ita ya gano
ba a kwai inda ya yi niyar nufa.
Tana makale a jikin bishiya ya zo ya
wuce, yana gurnani. Yana wucewa Gimbiya
Lushmaira ta yi ajiyar zuciya har ta dauki
hanya zata koma sai kuma ta tuna da cewa
waye mahaifinta ta tuno irin gwagwarmayar
da mahaifinta ya yi a duniya kafin ya rasa
rayuwarsa, ta tuna irin bajintar da take so ta
yi anan gaba na soke idanuwan Macijiya
Burukul Kursum.
Nan da nan wani irin karfin ya shigeta
ta koma da baya ta dubi Zakin da ya yi nesa
ya nufi wata fadama dake nesa.
Cikin sanda ya juya ta nufi inda
59
TURABAR GASKIYA-3 MADAKI
Zakin ya fito, koda karasawarta sai ta sunkuya ta leka cikin abin da bata zato ba shi
ya faru tana lekawa sai taga jariran zakuna
gudu biyu suna kwance, uwarsa tana nesa da
su tana sharar barci.
Koda gimbiya Lushmaira ta ga wannan
al'amari sai farin cikin ya cika mata zuciya
ainu nan take ta yi farin ciki ta tabbatar da
cewa zata yi abinda Yarima ya umarceta,
muddin kuwa ta samu nasara, to zata hada shi
da gagarumi aikin da ba zai iya ba. Domin ta
haka ne zata nuna duniya cewar ita jaruma ce,
kuma ta haka ne karfin da yake takama da shi, zai dusashe a cikin birninsu.
Koda yin wannan tunanin sai ta zura
hannu ta dauki daya daga cikin jariran
zakunan, a cikin sanda. Amma me ta na dago
kai ta hango Namjin Zakin nan ya na dawowa da cikin matsanancin gudu.
Ganin haka yasa Lushmaira yunkurin mikewa da sauri ta falfala da gudu tana rike
da wannan jaririn Zakin.
Zakin ya kurma wani uban ihu
mai tsananin firgici ya bi bayanta. Ita kanta
60
TURABAR GASKIYA 3 APМАDAKI
Gimbiya bata san tana da irin wannan gudun
da takeiyi ba, sai dai duk irin gudun da itake
Zakinınan ya ninka nata domin sau tari yaná
kamota saita zille ta sauya hanyal na нег
16 ms Warnan (alamari yariyin mutu kar tayar
da hankalire Lushmairagdomin Zakin namya
kuntäta inga i shiogajiyansta farassarkartasta
sedudustana ganin ba zatuliya samun hasara
ba. ilsy malaiseligist
nsasnKoda ta fara layrjuwa na dibarta sai ta
dake ta di igabal da gudun tañarrike da jaririn
Zakin, a hannuntasy sbug issdol nimob syset
smul Av hakahar tlisol indainsukanyada
sansaninnaslokaci hankulintasba Rararhinta
shìyal yi da ganin yanda gurin yasyi shira ba
kowa da alamar sun ji ma da yin gabastana
tsaye cikin tsoro da fargaba Zakin yakara so
fitinıgurin ayana gurmanins hiskansanyaugaji
likes su kø yi gaba da gabasdarita bab halin
gup sq kdub avea elim smuk st នigm
ainswOimbiyduLushmairaz tarcird dankwdlin
kantwdagd sauti faures Rarari jaririn Zakin
sannan ta yi zafinohamanpe daurerijshisrda
jikin swatatsiririyer sbashlyawol in2
TURABAR GASKIYA-3 MADAKI
Aikuwa kafin ta kara wani Yunkuri
Zakin nan ya yi sufa kanta da niyar ya
turmusheta, amma sai ta azama ta bar gun ta
sauka akan kasa, gurin ya'cika da kura.
Da ganin haka sai ta ja daga kamar
yanda shima ya dago yana fuskantarta da
Kara damara. A wannan lokaci sai ita ta
nufeshi cikin fushi zuciya suka kauri da
hargitsatsten yaki.
Gimbiya Lushmaira ta yi danasan
kaiwa wannan Zakin bara a karon farko kai
tsaye domin lokaci guda ya yagar mata fatar
bayanta gurin ya kwalane ya yi fari ya kuma
saka hakuransa akan kafarta yana neman ya
cisgeta, da kyar Lushmaira ta iya kwace
kanta.
Ba tare da ya jira ta samu sukuni ba
zakin nan ya kara nufarta da niyar ya
turmesheta amma sai ta yi ta 'yan maza ta
murgina ta kuma mike tsaye duk da jini na
zuba daga jikinsa sai ta dunkule hannuwanta
cikin karfin halin ta tsaya kan Kafafuwanta
tana jiran isowar Zakin.
Shi kuwa sai ya saka kafarsa a kasa
62
TURABAR GASKIYA-3 MADAKI
gami da tona kasa ya/yi kuka mai cikc da
amon ya yi kanta koda ya iso gare sai ta
daddage ta kai masa naushi a fuska
Ta yi kuwa sa'ar samunsa a idonsa nan
take sai ya kauri da wani hargitsantsan ihu
mara dadin ji. UCAH UM
Lokacin da ya kife kasa kafin ya kara
samun wani karfin halin ta sauri juya da niyar
daukar jaririn zakin nan da ta daure shi. KP
Abinda ta gani shi ya yi mutukar
razanata ta ji gabanta ya yanke ya fadi ba
komai ta gani face, uwar Zakin tana
shinshinar jikin dan.
Wani hargitsantsan kuka ta ji, a bayan
tana waigawa taga daya Zakin ya mike ya yo
kanta.
WANI IRIN GAGARUMIN YAКІ
ZA'A KWAFSA TSAKANIN GUNGIYAR
MUSULUNCI DA TA KAFURCI.
WANE IRIN GUMURZU SADAUKI
ZAIYAN ZA SU KWAFSA TSAKANINSU
DA MASU KIBIYO DA SUKA BOYE A
CIKIN CIYAYI
63
TURABAR GASKIYA-3 MADAKI
INA LABARIN MACIJIYA
BURUKUL KURSUM.
YAYA GIMBIYA LUSHMAIRA
ZATA KARE DA WADANNAN
ZAKUNAN.
MU HADU A CIKIN LITTAFI NA
HUDU GA MAI SON JIN CI GABAN
WANNAN LABARI NAKU HAR
KULLUM
ADBUL'AZIZ SANI MADAKIN
GINI
64
TURABAR GASKIYA-3 MADAKI
KADAN DAGA
BA TSIRA
A wani zamani can baya lokacin
jahiliya kimanin shkaru dubu biyu kafin
daukakar birnin Misra an yi wata babbar
daula da ta kunshi manya birane guda uku.
Birni na farko ana kiransa da suna
Darul Husuk, na biyu kuma Baitul Lazima
na ku kuwa shi ne Nurul Amsar.
Gaba daya wadannan birane uku
suna da girman kasa, arzikin noma da
kasuwanci amma kuma suna cikin wata
babbar masifa ta rashin zaman lafiya
saboda ko yaushe acikin yake-yake suke,
ga yawan kawo hari na 'yan fashin, an rasa
sarki guda daya wanda zai ia kare Kasarsa
da jama'arsa daga wannan masifa saboda
mutanen kowane birni basu da adalci da
tausayi, rayuwa ake yi kawai irin ta
dabbobi.
Wanda duk yafi karfin wani zai iya
kashe shi, ko ya yi masa fin karfi ya
65
TURABAR GASKIYA-3
kwace masa gida, mata da gona.
MADAKI
Bisa wannan dalili ne mutanen
wannan daula suka fara kokarin yin hijira
domin su gudu daga nahiyar gaba daya,
amma sai gudun nasu ya zamo na banza,
tunda basa samun tsira saboda a kokarin
guduwa ne kuma suka rinka haduwa da
masifu ta ajalinsu.
Asararar dukiyoyinsu da kuma
iyalansu. Nan fa rayuwa ta yi tsananin
mutuka a cikin wannan daula ga shi dare
da rana kasashen a cikin yake yake suke, a
koyaushe za'a iya kawo har, idan ma
mutum a cikin daji yake rayuwarsa kamar
ta kiyashi take.
Sarkin dake mulkin a birnin Nurul
Amsar shi ne mafi adalci a cikin sarakunan
ukun amma kuma ya tsufa ainun baya iya
yin komai kuma ciwo ya ci karfinsa, yana
da matar aure guda daya jal mai suna
Lahira sai kuma da guda daya wani
matashin saurayi dan shekara goma sha
€99
TURABAR GASKIYA-3 MADAKI
takwas ana kiransa da suna Huzainu.
Huzainu ya taso da gagarumar
jarumtaka ta iya yaki da kuma kwarewa
wajen iya farauta a daji, a rayuwar Hizanu
babu abin da yake so sama da ganin ya
kawo karshen rashin zaman lafiya a
wannan daula tasu, amma sai yaga abin
yafi karfinsa, domin a haka ake rayuwa a
nahiyar tun kafin ma a haife iyayensa.
Watarana da yammaci sai ciwo yai
itsananin ga Sarki Saiham wato mahaifin
Yarima Huzaini har ta kai cewa yana suma
a wannan lokaci Huzainu da mahafiyarsa
tare da dukkanin fadawan Sarki Saiham na
zaune a gabansa suna ta faman shara kuka.
Kwatsam sai aka ji Sarki Saiham ya
bude baki ya ce,
"Kowa ya fita ya barsu shi da
99 iyalinsa."
Nan take kuwa fadawa da duk
hadimai suka fice daga cikin dakin, aka
bar Huzuinu da mahaifiyarsa, su biyu
67
TURABAR GASKIYA-3 MADAKI
kacal, duk da haka sai Sarki ya dubi
Huzainu ya ce ya rufe tagogin da kofofin.
Cikin sauri Huzainu ya cika umarni
sannan ya zo ya zauna daf da Sarkin suka
kurawa juna idanu, suna masu zubar da
hawaye: Sarki ya bude baki da kyar ya ce,
"Ya kai dana ka yi sani cewa gaba dayan
kasashen nan uku dake cikin wannan daula
zasu rushe nan da cikar kwanaki kadan,
zała zubar da jini mai yawan gaske za'a yi
asarar miliyoyin rayuka da dukiya mai
yawan gaske.
Abinda nake so da kai shi ne ka
dauki mahaifiyarka da sauran amintattun
jama'ata ku sulale ku bar nahiyar nan gaba
daya in ba haka ba kuwa gaba dayanku
mutuwa za ku yi."
Kodaujin wannan batu sai hankalin
Yarima Huzainu da na mahaifiyarsa ya dugunzuma ainun Huzainu ya dbi Sarki
yace, "Ya kai Abbana ina amfanin mu yi
tagudun da babu tsira ka sani cewa
68
TURABAR GASKIYA-3 MADAKI
muna cikin mugun yanayi na gaba tsini
baya siyaki, muna gidan bamu tsira ba
haka ma muna dawa."
Sarki ya yi tari har da aman jini
sannan yace, "Ya kai dana na yarda da
jarumtakarka da kuma sa'arka, lallai kada
ka sare domin ina ji a jikina cewar zaka
iya kubotar da kanka da kuma dukkan
.masoyana י,
DAGA MADAKIN GINI YANA
NAN TAFE BA DA JIMAWA BA
eZINA MASU YIWA MAKARANTA
NA TUNI TA SABON LITTAFINA DA
YA FITA MAI SUNA WASIKAR JINI.
mTSARARREN LABARI NE DA
AKA KWAFSA GAGARUMAR
SOYAYY ALS DA HARGITSANTSEN
YAKIE? ewind s
CIN AMANA MUNAFURCI
GAGARUMAR BAJINTA YANA NAN
A KASUWA IN BAKA NEMA KA
69
TURABAR GASKIYA-3 MADAKI
NEMI SHI A KASUWA. YANA NAN A
KASUWA
Kadan daga KARAGAR MULKI
A wani zaman can baya mai tsawo
da ya shude a kasar Hindu an yi wani
gawurtaccen Sarki wanda ya shahara akan
karfin mulki da kuma karfin sihirin tsafi
wanda masana da masu bincike suka
tabbatar da cewa a wannan zamani babu
wani matsafi da ya kaishe karfin sihiri a
duk fadin duniya komai na jin dadin
duniya Allah ya baiwa wannan Sarki
wanda ake kira da suna Kanzal, face rashin
haihuwa.
A wajen mahaifinsu su tara ne kuma
gaba dayansu maza ne babu mace ko daya
Sarki Kanzal shi ne dan auta a gidan
sarautar kuma shi Allah ya baiwa Sarautar.
Lokacin da mahaifinsu ya kwanta
ciwo sai gaba dayansu su taran kowa ya
kwallafa ransa akan sarautar har ya
zamana cewa suna ta kaiwa junansu har
70
TURABAR GASKIYA-3 MADAKI
domin su hallaka junansu, bisa dole
kowannensu ya nemo hayar dakaru na
waje, domin tsare lafiyarsa, amma duk da
haka sai da kowannensu ya sha bakar
wahala ya kusan rasa rayuwarsa saboda
mugun tanadin da sukewa juna.
Wadannan 'yan uwa guda tara suna
yin tsananin gaba, babu wanda yake son
yaga wani a raye.
Babu wanda yafi shan wahala acikin
su sama da Sarki Kanzal domin awannan
lokaci shi ne mafi kankanta a cikinsu.
Sau uku ana sassarashi ayi masa
dukan kawo wuka ana zaton ya mutu, kai
akwai lokacin ma da aka daddaure shi
tamau da igiya aka sashi a cikin buhu aka
kulle buhun kuma aka jefashi a cikin teku
amma bayan sati biyu sai ga shi ya dawo
fada a raye duk jikinsa yasha dinki na
saran takobi.
Daga wannan rana ne Kanzal ya
hada nasa inasa yabar Rasar ya
71
KATSIRK BOSTNESS ON
TURABAR GASKIYA-3 MADAKI
bazama a duniya neman sihirin tsafi, ba'a
sake jin duriyar Kanzal ba sai bayan wata
shida.
A fada ya tarar da ana shirin yin gasa
kala takawai a tsakanin 'yan uwansa
domin a baiwa wanda ya lashe gasar
karagar mulki nan take Kanzal ya ce, ai sai
a kara gasar ta zama gudu tara tunda ga shi
ya dawo.
Nan fa mamaki ya turnuke gaba
dayan jama'ar dake fadar aka kurawa
Kanzala idanu bisa ganin kankambarsa da
kuma gangancin da yake shirin yi na shiga
wannan gasa.
DAGA MADAKIN GINI YANA
NAN TAFE.
TugiarCaakiya
ABDUL'AZIZ SANI
MADAKIN GINI
TURBAR GASKIYA --4 MADAKIN GINI
TURBAR GASKIYA 4
okacin da Gimbiya Lushmaira take duban
wadannan Zakuna miji da mata sun yi
mata kawanya sai nan take ta shiga cikin
tsananin ta shi hankali
Cikin 'yar sarsarfa suka dinga matsuwa
inda take, tana masu wani hargitsantsan gurnani mai zaranar da zukatan maʼabota saurare.
Nan ta tsaya ita ba abin ta zura da gudu ba, ba kuma abin ta yi yaki dasu ba domin ko ba
gwadaba linzami ya fi karfin bakin kaza, amma
lokacin da ta ga sun yo kanta cikin fushi sai ita
ma hankalinta ya dugunzuma domin ta aiyana a
ranta cewa, idan ta tsaya tabbas za su sami
nasara akanta idan kuma ta ta shi tsaye ta kare kanta, watakila ta samu ta yi nasara akanta.
Nan take tunanin irin jarumtakar da mahaifinta
ya yi a lokacin da macijiyar Burukul Kursum ta shi go birninsu ya fado mata a lokacin da mahaifiyarta take bata labarin irin namijin kokarin da ya yi har ya soke idon macijiya a
yanda aka siffanta mata macijiyar loma guda
4
TURBAR GASKIYA --4 MADAKIN GINI
zata yi wa wadannan Zakuna ta gama da su,
tabbas idan ta kasa karo da wadannan Zakuna
babu shakka ko inda ake yaki da Macijiya ba za
ta iya zuwa ba, in kuwa hakane kudirinta ba zai
taba cika ba.
Wannan tunanin shi ya yi tsananin karawa
Gimbiya Lushmaira Karfin ta ji wani sabon karfi
ya shigeta bata san lokacin da ta kwarara
Kabbara ba. Ta tunkari Zakunan kamar yanda
suke tunkarota.
A tare suka yi sufa kanta, ita ma sai ta
daka tsalle ta yi kansu a ka wata bahagoyar
haduwa a cikin sararin iska, su duka suka gauro,
wani taimako da Allah ya yi mata, a lokacin da
aka ta shi sama da niyar ta yi karo da wadannan
Zakuna sai suka fita ta shi sama, dan haka su
biyu suka gauro suka zube kasa bisa faduwar
rashin tsammanin domin dukkanin su basu fadi
akan kafafunsu ba kamar yanda ita ta fadi a kan
nata kafafun.
Kafin su yi yunkuri mikewa sai ta yi
azama ta yi kan Namijin Zakin da yake kokarin
mikewa a cikin tsananin fushi.
Tun daga inda take ta yi alkafira ta fada
5
TURBAR GASKIYA --4 MADAKIN GINI
kan Zakin ta mai da shi, ya kara wani yunkuri
zai mike ta saka kafa ta taka wuyansa iyaka
Karfinta.
Nan take ya kama kakarin mutuwa ita
kuwa sai ta kara dagewa tana cikin haka bata
ankara ba ta ji an sureta an doka ta da kasa.
Cikin rashin bazata ta dubi wannan
Zakanyar ce ta kara yunkuruwa cikin ta shin
hankali ta kara biyota zata kara turmesheta.
A wannan lokacin karfin Gimbiya ya
gama karewa amma ta ta kwala wata Kabbara
domin ta riga ta san idan wannan Zakanyar ta
turme sheta to sai dan Buzunta, ai kuwa yin
wannan kabbara sai ta yi sama tamkar wacce aka
saka kugiya aka shillata, koda ta ta shi fadowa
sai ta sauko a kan Kafafuwanta.
Ai kuwa tana faduwa Zakanyar nan ta
Kara yin kukan kura ta yo kanta. Irin mahaukacin
gudun da take yi yasa Gimbiya Lushmaira ta
fahinci idan ta sameta za su yi muguwar
ragwabza, ai kuwa sai ta falfala da gudu. Ita ma
Zakanyar ta bi bayanta suka kasa tsire cikin
tsananin gudu, wata dabara ta fadowa Gimbiya
Lushmaira lokacin da ta ga Zakanyar ta kara
6
TURBAR GASKIYA --4 MADAKIN GINI
tsananta, wajen ne man ranta, dabarar da ta fado
mata ita ce wata dogowar bishiya ta take
gabanta, suna cikin gudun sai kawai Gimbiya
Lushmaira ta kara azama dan ta nufi jikin
bishiya tana kuwa isa sai ta kama tattaka bishiyar
tamkar wata 'yar biri, sai da ta yi nisa a saman
bishiya a lokacin da Zakanyar ta dako tsalle da
niyar ta cafkota sai kawai Gimbiyar Lushmaira
ta wultsila da baya, Zakanyar ta dake bishiyar.
Saboda karfin da Zakanyar ta yi wajen
dokan bishiyar sai da Bishiyar ta karya biyu rabi
ya zubi kasan jijjigen bishiyar ya kuma ya
tumboko amma bai gama tumbukcwa ba, amma
rabin bishiyar ya cire sun yi tafiyar ruwa da
zakanyar, Zakanyar ta fadi kasa ko shuruwa bata
yi ba.
Aikuwa ganin wannan nasara da Gimbiya
Lushmaira ta yi sai ta yi sauri zuwa inda jaririn
Zakin nan yake ta dauke shi ta kara falfalawa da
gudu domin kuwa duk Zakunan ta lura basu
mutu ba, domin kuwa sai motsi suke.
Koda ta yi nisa sai ta fara tafiya a hankali
domin wata shu'umar gajiya ta sarketa haka nan
bata san lokacin da ta zube kasa ba amma saboda
7
TURBAR GASKIYA --4 MADAKIN GINI
tsananin naci irin na gimbiya Lushmaira bata
saki wannan jaririyar Zakin ba.
Al'amarin su Yarima Zaiyan da sauran
tawagar su Sarki kuwa lokacin da suka kara nisa
a cikin tafiyarsu, har ya zamana sun shigo cikin
dajin da 'yan sumamen daga 6angaren Su Sarki
Madham suka boye cikin ciyayi sukc. Koda
Suka shi go wannan gurin sai tafiyarsu ta koma
sassarfa kuma da yawa daga cikin mayakan da
suke kan gaba sun zare makamansu.
Ba komai ya sa haka face, kawai sun lura
cèwar akwai alamar wasu halitton a gun, ba dan
komai suka gane haka sai ganin da yawan
Tsunsayen dajin sun ta shi sama, sannan
kananun namun dawa sun komo wajen dajin
idanuwansu na kallon cikin korayen ganyayyarki
Lokacin da suka isa tsakiyar dajin basu
gushe ba suna kara falfalawa da gudu suna
kabbara tare da daga makamansu sama.
Haka nan suka wuce wannan dajin batare
da maboyan Dakarun sun yi illar komai a gare su
ba.
Lokacin da Ayarin Dakarun suka gama
wucewa sahu-sahu, su ka yi nisa sai Dakarun
8
TURBAR GASKIYA --4 MADAKIN GINI
suka firfito suka tsaya su ka yi cirko cirko suna
numfarfashi. Domin wani irin tsuro ne ya cika
musu zuciya har ya haifar musu da kasa aiwatar
da komai.
Su ka fito daga cikin maboyar Sadauki
Aksar ya tsaki gami da doka kafarsa a kasa, ya
cе.
"Tir da wannan jarumtakarmu da har kwarjinin wasu zai hanamu mu aiwatar da
abinda shugabanmu ya umarcemu, yanzu mai
kuke zaton za mu je mu sanar da Sarki. Wani mai bi masa da ake wa lakabi da
Kuffuru, ya numfasa ya cc, "Ya shugaba ni kaina abinda yake raina ke nan, kuma na tabbata idan har muka komawa Sarki da labarin wannan
ragwanta da mu kai ba mu da hukunci da ya
wuce harshensu ya karce kasa, ma'ana kaifin takobinsu ta datsa wuyanmu, sai dai ba za mu taba barin haka ta faru kuma aikata hakan ba ya
na nufin mun gama asarar aikinmu bane, yanzu
ma akwai dama tunda a yanzu muna bayan
wadannan Dakaru abu na farko da za mu yi
saurin yi yanzu shi ne mu bi bayansu tun kafin
su Isa Sansanin da za a yi wannan gumürzun mu
TURBAR GASKIYA --4 MADAKIN GINI
bi su da tsananin harbin kibiyoyi yanda za mu
rage yawansu idan ya so kafin su ankara damu
sai mu juya da baya mu gudo"
Koda Sadauki Askam ya ji wannan
shawara daga yaronsa Kuffura sai ya yi aminci
da wannan shawara nan take ya yi umarni da a ci
gaba da bin bayansu, sannan ya yi umarni kowa
ya fitar da masunsa.
Nan take dakarun suka bi umarninsa suka
aikata abinda ya umarce su da su yi.
Koda suka dunguma zasu fara tafiya sai
suka ga mutum a bayansu, su duka suka waiga.
Suna waigawa sai su ka yi ido biyu da gimbiya
Shadilat, suna ganinta suka ganeta kamar yanda
ita ma ta ganc su, ba komai yasa suka shaidata
sai ganin kamanin da su ka yi da Sarki Abu
Zaiyan, nan take sai Askam ya kyalkyale da
dariyar mugunta. Sakamakon dariyar da yake
yasa daukacin jama'arsa su ma suka kaurc da
wannan shu'aumar dariya.
Gimbiya Lushmaira tana tsaye da jaririn
Zakinta a hannunta tana binsu da kallo cikin
tsananin mamakinsu
Nan suka kuma daina dariya da kansa
10
TURBAR GASKIYA --4 MADAKIN GINI
Sadauki Askam ya yi kanta da niyar ya kamata,
amma kafin ya isa gareta sai kawai ya ji wani
irin ihu yana ta shi daga bayansa, kukan fitar rai
ko da ya waiga sai yaga ai tuni an ci karfin sama
da mutum duba a cikin dakarunsu.
Yana duban Dakarun nasa suna sulalewa
kasa suna faduwa, amma ya kasa ganin wanda
yakc musu wannan 6arnar saboda tsananin zafin
namar mai aikata kisan, bai ankara ba ya ga gaba
daya dakarun duk an karkashesu, ya zama dan
kauye sai waige yakc yana son ganin wani
mala'ikan daukar rai ne ya zo yake girbar masa
Dakaru.
Ba shi ba hatta Gimbiya Lushmaira kallon
mamaki take, cikin tsananin faduwar gaba
Yarima Zaiyan ya bayyana a daf da shi, wanda
saboda tsananin firgici Sadauki Askam sai da ya
saki fitsari a wandonsa.
Gimbiya Lushmaira tsananin mamaki ya
hana bakinta rufawa saboda irin jarumtakar da
Yarima zaiyan ya yi amfani da ita wacce bata
taba ganin ya yi irinta ba.
Sadauki Askam ya dubi Yarima yana
kirma ya zuba giwowinsa a kas, yana neman
11
TURBAR GASKIYA --4
yafewa.
MADAKIN GINI
Koda Yarima ya dube shi sai ya tsar ta
masa yawo a fuskarsa.
"Ahir dinka da a ke kiranka da gwarzon
Sadauki kuma har yake jagoranta wadansu
Dakaru dan aiwatar da wani shiri na karkashin
kasa, ina son ka sani duk kan shirin ku mun fara
saninsa daga fara shigowa cikin wannan dajin
haka zalika ko da aka fita daga cikin dajin nan ni
ban fita ba ina nan ina son na ga sabon shirin da zaku kulla.
Dajin wannan batu sai jikin Sadauki
Askam ya Rara rawa, yana makyakkyata, shi
kuwa sai Yarima Zaiyan ya dube shi cikin fushi
ya ce, ka dauki daya bayan daya ka dora dukkan
dakarun da na salwantar akan dokinsa ina nan
ina jiranka.
Aikuwa nan da nan Sadauki Askam ya
fara aikin cikin sauri-sauri gudu-gudu, kafin
wani lokaci har ya kwashe su duka, ya na gama
dora su a bisa dawakan kowannensu sai Yarima
Zaiyan ya dube shi ya ce..
Ya kai wannan sakaran jarumi kasan
abinda ya sa na sa ka aikata haka,?"
12
TURBAR GASKİYA --4 MADAKIN GINI
Cikin rawar jiki Sadauki Askam ya ce, "ya
shugabana ban da masaniya akan hakan.?"
Da jin haka sai Yarima Zaiyad ya yi
murmushi ya cc, "Abinda hakan ke nufi shi ne za
ka jagoranci gawarwakin izuwa sansaninku ka
labartawa sakaran Sarakanku yanda aka yi aka
salwantar da rayuwakan wadannan dakaru, ka
basu labari ni ne Yarima Zaiyan daya daga cikin
dakarun cikin birnin Baitul Haural ina so ka
sanar dasu cewa guguwar bala'i tana daf da
isarsu kuma duk irin shirin da suke tunanin za su
yi a kanmu mun riga mun gama da ku, fatanmu
mu hadu a fili daga mu gidaddabaku in har ba
zaku bi TURBAR GASKIYA BA.
Koda Yarima Zaiyan ya gaba sanar da
Sadauki Askam wannan sako sai ya juya da
niyar ya yi gaba ya barsu a nan da Gimbiya
Lushmaira.
Nan take gimbiya Lushmaira ita ma ta yi
gaba batare da damuwa da shi ba. Yana tafiya
kawai ya ga ta zo ta wuce shi ranta kuma a басе
bata ko kallonsa, ga jaririn Zakinta a hannu.
Koda Yarima Zaiyan ya dubeta sai ya yi
sauri ya ya sha kanta, ita ma ta tsaya su ka yi
13
TURBAR GASKIYA --4 MADAKIN GINI
cirko cirko suna kallon juna na tsawan lokaci a
farko kallon kurillar da sukewa junansu, basu
san a irin matsayin da suke ba, domin kuwa
kowannensu wani tunanin ya tafi na daban.
Yarima Zaiyan ya dawo haiyacinsa ya yi
saurin dubanta kamar bai shiga wani hali na
tsawon lokacin da ya yi yana dubanta ba, ya се
cikin kakkarfar murya kamar yana doka mata
tsawa.
Take ita ma ta dawo haiyacinta ta dube shi
da shakka, tana saurarensa.
"Yake wannan karamar yarinyar mai
shirin zama jaruma, hakika a yanzu na tabbatar
da cewar kin yi kokarin da idanuwanki za su iya
jure ganin irin gagarumin gumurzun da zamu
kwafsa tsakaninmu da makiyanmu, tabbas, bana
da haufi ba zaki tsorota ba a yayin da
idanuwanki suke kallon wannan gumurzu,
sakamakon wannan bajintar da kike na dauko
jariririyar dabba."
Yana zuwa nan a cikin zancensa sai ya
juya da niyar ya wuce gaba, da ganin haka sai
Gimbiya Lushmaira ta dakatar da shi da cewa.
"Kai kuma a yau ne na fara tunanin dinbin
14
TURBAR GASKIYA --4 MADAKIN GINI
shckaru da ka dauka kana kowan yaki, duka ka
yi su nc a banza, domin kuwa ka bani mamaki da
har kake fada na shammata, duk wani jarumi mai
ji da tumbatsarsa jarumtarsa, baya yaki da wanda
bai shirya ba, dan haka akwai saura rina a
gabanka."
Tana zuwa nan a jawabinta sai ta cilla
masa jaririn Zakin ta yi gaba cikin gudu kafin ya
dawo daga mamaki kalamanta tuni ta yi nisa.
Cikin sanyi jiki ya baro cikin dajin Shi
kuwa Askam tuni ya dauke hanya yabi wata
siririyar hanya wacce ta zagaya ce ya tura
dawakan da matattun dakarun da suke kai
Koda Gimbiya Lushmaira ta isa cikin
tawagarsu ta yi sauri karasa inda sahunsu yake ta
tarar da Shadilat a cikin sahu tana tafiya, koda
Shadilat ta ganta sai mamaki ya rufeta har ta
kasa yin hakuri ta kamo hannun gimbiya
Lushmaira ta ce.
"Ya ke 'yar uwata shin yaya a ka yi kika
kamo a cikin wannan tafiya, da tuni na cire rai
dake.?"
Da jin haka sai Gimbiya Lushmaira ta yi
murmushi tun daga lokacin da tafi kawo irin
15
TURBAR GASKIYA --4 MADAKIN GINI
gwaggwarmayar da ta yi da Zakunan zuwa
lokacin da Yarima Zaiyan ya iso ya yi yaki da
Dakaru sama da dubu goma da irin bajintar da ya
yi, ta kuma dora irin yanda Yariman ya
gwasalcta a cikin tafiyarta da kwazonta sannan ta
karc da ita ma irin gwasale shin da ta yi, duk ta
sanar da ita.
Da jin wannan bayani sai Shadilat ta ce,
"A gaskiya kin yi kokari kuma na yaba da irin
kwazonki domin kuwa ban yi tsammanin samun
nasararki ba, ni kuwa