Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
10 / 11
wuka muka dauka muka dabawa kanmu ba ya ya kuke ganin zamu samu nasara alhalin a cikin 44 TURBAR GASKIYA --4 MADAKIN GINI majiya karfin talatin da muke ji da su, biyu sun tafi, ta hanyar Sarkinsu kadai. Kada ku manta a kwai Sarkin yaki Safwan mun san kwazonshi ba tun yau ba, ga kuma Yarima Zaiyan wanda labari ya zo mana cewar shima tsakwakurine." Koda ya kawo nan a cikin batunsa sai Sarki Husaka ya ce, "Haba ya kai Sarki Tarmas kada ka manta, da waye Sarki abu Zaiyan ai ku da za a samu lagonsa ba yanzu ba, kai da ka zuba ido akwai ribar a nan gaba. Kafin su ankara sai suka ji ihu wani Barden ya fito ganin wannan katon da ake Kira Rislalu sai hankalinsu ya kwanta domin kuwa shi kuma bai da wani lokaci da aka taba nasara akansa, duk irin yaki da ya yi a duniya wanda a kalla ya yi yakukuwa dari biyar, ba'a taba samun lokacin da aka lakuci koda yatsansa ba, saboda tsananin masifarsa a filin daga ko 45 TURBAR GASKIYA --4 MADAKIN GINI jinin makiya bai taba wanke masa fuska, saboda zafin namansa kuwa sai ya kashe mutum biyar a sa'ili daya Dan haka ko da ya fito sai suka kara mai da hankali a fili, bai Kai Jaura tsaho ba amma dai ya fi Jaura kauri shi a cure yake guri gudu, ya kware wajen raba hanta da jini, sannan ya kware wajen sarrafa masana iya yaki, takobi ce guda biyu a hannunsa dukkaninsu basu fi kamu uku uku ba, yana tafiya yana jijjiga kwanjinsa yana motsa ga66ansa dan karamin bante ne a jikinsa kawai dan haka surorin jikinsa duka a waje. Sarki Abu Zaiyan ya na rike da mashin da Ya hallakar da Jaura, sai ya wullar da shi gefe, a wannan karon sai ya tsaya yana murmushi, shi kuwa Risalu sai ya tsaya yana hararar Sarki. Wannan al'amarin ne ya fusata Sarki Abu Zaiyan ya kukan kura ya yi kan Risalu, aikuwa 46 TURBAR GASKIYA --4 MADAKIN GINI yana isa gare shi sai Risalu ya daga kafarsa cikin a zaba ya doki Sarki a kirji, Sarki ya tafi da baya ya fadi kasa. Cikin fushi Sarki ya mike tsaye ya fursa da yawu, ya kara yin kan Risalu da gudun koda ya isa kan Risalu sai Risalu ya soke Takobin ta shi guda biyu a jikin bantansa ya kama Sarki ya daga shi yasa ya wujijjiga shi ya cilla shi can gefe daya. Abin da Sarki ya fara lura da shi ga wannan Sadauki ba a yi masa shigar burgo domin a kasa yake, yana iya fahintar duk da irin yunkurin da ka zo masa da shi, dan haka sai ya daina binsa, shi kuwa sokon sai yake tsammanin Sarki tsoro ya ji dan haka sai ya nufo Sarki yana mai kiran Sarki da hannu wato yazo Sai Sarki yake ja da baya har ya zamana Ya takure Sarki Abu Zaiyan ya kai shi karshen inda jama'a su ka yi musu da'ira, Sarki na ja da baya shi kuma na kusanto Sarki, ai kuwa sai ya 47 TURBAR GASKIYA --4 MADAKIN GINI yi sufa ya kamo Sarki da hannu daya ya daga shi sama, koda Ya daga Sarki sama ya kama jijjiga shi yana kokarin ganin ya runtuma shi da kasa, shi kuwa Sarki a she ya dauke takobi daya daga jikin bantai din Risalu aikuwa nan take Sarki ya shammace ya soka masa takobin a cikin hammatarsa. Wani abin mamaki sai Risalu ya yi cilli da Sarki ya kuma kama kotar Takobin ya cirota daga hammatarsa ya kurma wani uban ihu na fusata yabi Sarki da niyar ya danne Sarki ya ja daga ya daina ja da baya lokacin da ya iso gaban Sarki sai Sarki ya kama kai masa duka da hannu da kafa aikuwa sai salon fadan ya sauya nan suka shiga kaiwa junansa duka da hannun da Kafa suna karewa a wannan lokacin ne kowa ya samu naushi a baki har sau uku. A sannane suka ja da baya, kamar wasu Zakaru, wannan al'amarin ba 48 TURBAR GASKIYA --4 MADAKIN GINI karamin yiwa Sarakan uku dadi ya yi ba domin ganin yanda Risalu kawai ke walar da Sarki. Shi kansa Sarki ya yi mamakin yanda Risalu yake fahintar dukka irin abinda ya yi niya, amma sai ya sauya dabara, cikin zafin nama Sarki Abu Zaiyan ya yi kansa, shi kuma Risalu sai ya tsaya yana tunanin ya tare shi, amma me a lokacin da Sarki ya isa gare shi sai ya zabe daga waftar da ya kawo masa ya kuma sace wukar ta daya kubin ya soka masa a dokin wuya. Lokaci guda Su Sarki suka ga Sarki ya wuce salin alan shi kuma Risalu ya yi tsaye, ya kuma daina motsi, suna tunanin wani karfin shifin yake sai kawai suka ga Risalu ya fadi riga ji a kasa ku shurawa bai yi ba sai a sannnne suka ga ashe soka masa wuka Sarki ya yi ta dokin wuya. Wannan al'amarin ne ya jawo 49 TURBAR GASKIYA --4 MADAKIN GINI hankulan Sarakan domin a tsai da fadan haka kowa ya kuma ya kara shirin. Nan da nan suka bukaci haka Sarki ya yi farin ciki da haka domin dama lokacin Sallah ya yi, dan haka kowanenesu sai suka koma nasu sansanin. Lokacin da Sarki Tarmas da kuma Sarki Husaka da Madhman suka kebance sai Sarki Madham ya dubi Sarki Husaka ya ce, "Hakikanin gaskiya akwai gyara a cikin wannan yaki, saboda haka ku saura shawara, ni dai ina da ita in ma baku da ita abin nan dole a samu a bi ta karkashin kasa, ba komai nake nufi ba face, a cikin Sadaukin da zasu kara da Sarki Abu zaiyan akaro na hudu ya kamata a ce, An samu wata guba da za'a yi amfani da ita a shakawa Sarki, idan ya so shi Sadaukin sai ya yi farat daya ya kashc shi, ka ga dai ku dai fili ya hautsine mun samu babbar nasara. 50 TURBAR GASKIYA--4 MADAKIN GINI Koda jin wannan shawara ta Sarki madham Sarki Husaka da Sarki Tarmas sai suka hada baki suka ce, "Kai da kana da wannan dabara amma baka yi sauri zuwan mana da ita ba. Da jin haka sai Sarki Madham ya yi murmushi ya ce, "Hakika a baya bani da wannan dabara amma a yanzu da wahala ta kai wahala (sai ta fado min dan haka yanzu abinda za ayi shi ne mi yi umarni da ahada huda da gumar da zai shaka, ya mutu.ua LHAikuwa nan take su Sarki suka yi umarni da aka hada wannan abu, Sadaukin da Za'a yi wannan fafatawa da shi, aka ba shi aka kumà sanar da shi yanda zai yi aiki da ita, nan take sai suka ci abinci suka samu hutu, sannan suka komafili пто0 wwed Avcan kuwa 6angaren Su Sarki Abu Zaiyan an yi sallah an ci abinci, dan haka Sarki ya karayin bayanit dan Karawa 251 TURBAR GASKIYA --4 WMADAKIN GINI jama'ar imani da tsoron Allah sannan ya Kara yin shirin yaki, aka fito filin daga Koda fitowarsu sai suka ga ashe tuni Sadaukin da za a yi karawar da shi ya fito yana tsaye a filin daga yaña ta dage dagen hannu ana tafa masa.ie aled ni Д ab ing Shi kuwa Sarki sai yayi sallama da jama'arsa ya shiga tsakiyar filin batare da shakka ba, Yarima zaiyan a wannan lokacin suna zaune da Shadilat suna hira mai dadi ita kuma Lushmaira tana can bayansu kishi duk ya hanata sukuni, banda harara babu abinda take aiko musu da ita. Amma lokacin da aka fara kwafsawa sai hankalin. kowaya koma kanfilin fafatawar. busy ide eb tausz sok eks ida sduAna shiga fili sai aka fara fafatawa domin kuwa kowa a huce yake, lokacin da suka fara artabu sai fadan ya fara bawa kowa mamaki domin yanda suka kasance cikin kaiwa juna bara hannu da kafa suna 1252 TURBAR GASKIYA --4 MADAKIN GINI shillo tare da kaucewa dukan juna, tun da aka fara wannan karafkiya babu wanda aka taba Sarki shi kansa wannan fadan yafi burgeshi da yakin da su ka yi a baya domin kuwa a wannan yakin yafi zagin damtse a dirji juna abinda ya fahinta da sabon Sadauki shi ne masani ne wajen iya yaki da hannu ga takubba a hannunsa amma bai damu da ya kai suka da ita ba, a na cikin haka Sarki ya yi sa'ar naushinsa a fuska. Ya tafi daga taga zai fadi sai ta tirje ya gyara rikon Banjo din da aka ba shi a hannunsa ya kusanto Sarki Sarki ya yi alkafira ya doke shi a kirji sadauki ya kara yin baya, amma saboda naci ya kara dawowa nan suka kara kaurewa da sabon yaki, domin ya sanja salon fadan ganin Sarki ya fahinci inda ya dosa anan ne ya samu lagun Sarki har ya naushi a fuska sau biyu kuma a cikin naushin ne ya yi sa'ar 53 TURBAR GASKIYA --4 shaka masa wannan Banjo din. MADAKIN GINI Aka ci gaba da yakin kamar Sarki bai ji komai ba, suna cikin yaki Sarki ya shammace Sadauki ya karya masa wuya 6aras. Ai kuwa kafin ya sake shi wani Sadauki da ake kira Hirnanu ya fusato ya fito da karfi ya taka Sarki, Sarki Abu Zaiyan ya mirgina kasa ya mike cikin dauriya, kafin ya kara yin wani yunkuri Hirnanu ya kara yin dirango a bayan Sarki ya kirbawa Sarki naushi a mukamuke ya kuma zare takobi da niyar ya sare masa kai amma sai Sarki ya baje a kasa ya kuma kwashe kafafuwan Hirnanu. Nan take Hirnanu ya zube kasa, Sarki ya ya kama kansa ya danna a cikin kasa, aduk girman Hirananu sai ga shi ya kasa kwacewa ga shi kuma sai tirjjiya yake saboda tsananin walaha babu damar shakkar numfashi sai dai kasa da yake 54 TURBAR GASKIYA --4 MADAKIN GINI shaka Sarki Bai daga shi ba sai da ya ga ya daina motsi. Nan ma Sarki bai daga Mataccen ba wani sadauki ya kara yo sufa ya dake shi ta baya Sarki Abu zaiyan sai ya fadi kasa kuma ya kasa ta shi. A wannan yakin da (aka yi su Sarki tarmas suna ganin cewar gubar bata samu shiga Sarki ba amma ganin ya kasa ta shi sai suka kama murna domin sun san aikinta ne. Koda Wannan Sadauki ya kara yo tsalle sai ya kama Sarki da niyar ya jashi a kasa, amma sai Sarki ya cije, yaki ya jawo shi kuwa Sadauki sai kokarin janshi yake a cikin wannan lokaci ne aka ga jikin Sarki ya saki nan take ya fara yin amai, aikuwa nan Sarki Yaki Safwan da kuma Yarima Yazid suka kamo da tsananin firgici har ya zama sun yi rige rigen tasowa amma Sarki na ankarewa da su sai ya daka musu tsawa da su dakata, shi kuwa wannan Sadaukin 55 TURBAR GASKIYA --4 MADAKIN GINI koda ya jawo Sarki Gaban Sarakan Sai ya cire wani katon gatare daga jikinsa ya daga shi zai sare kan Sarki, har idanuwan jama'a ya rufewa kawai sai gani akai Yarima Yażid ya taho cikin iska ya doki wannan Sadauki ya fadi kaka ya fada kan gatarin ya cire masa makogaro cikin sauri ya dauke Mahaifinsa da yake ta faman a man jini ya kaishi sansaninsu. Kafin ya dawo filin dagar kuma sai suka ji wani irin nishi mai karfi ya karade filin gurin baki daya, wannan al'amari sai ya dugunzuma hankalin duka jama'ar da suke wannan gun, suka saka idanuwan sosai. Aikuwa kafin kiftawar idanuwa Sai ga Macijiya Burukul Kursum ta bayyna cikin tsananin tashin hankali. A nan take Yarima Zaiyan ya dakata da yunkurinsa domin daga zuwanta har ta yabcari kadan daga cikin al'ummarsu ta yi musu loma daya. 56 TURBAR GASKIYA --4 MADAKIN GINI Daga Abdul aziz sani madakin gini mai debe muku kewa akowane lokaci sai mun hadu a cikin littafi na biyar dan jin ci gaban wannan labari na TURBAR GASKIYА SHIN SARKI ABU ZAIYAN ZAI SAMU LAFIYA? WAYE ZAI KARASA KARAWA DA WADANNAN ADAWAN DA SU SARKI HUSAKA SUKA ZO DA SU? SU WAYE ZA SU NASARA A CIKIN WANNAN GAWURTACCEN YAKI A TSAKANIN RUNDUNAR MUSULUNCIN DA KUMA RUNDUNAR KAFURCI? YA YA ZA AKWASHE DA MACIJIYA BURUKUL KURSUM A CIKIN WANNAN HALI. A TSAKANIN SHADILAT DA GIMBIYA LUMSHAIRA WACECE TAFI KAUNAR YARIMA YAZID.? 57 TURBAR GASKIYA --4 MADAKIN GINI WANE NAMJIN КОKARI GIMBIYA LUSHMAIRA ZA TA YI HAR TA ZAMO YARIMA YAZID ZAI AMINTA DA JARUMTAKARTА. Sai mun hadu a littafi na biyu 58 TURBAR GASKIYA --4 MADAKIN GINI TALLLA! TALLA!! TALLA!!! A wani zamani can baya mai tsawo da ya shude bayan shudewar mulkin fir'auna na birnin misra an yi wata azzalumar sarauniya mai suna Zuhaira bin Masrud. Sarauniya zahuira tana mulkin wata babbar kasa ce dake bakin gabar tekun bahar sufiya kuma ta gaji sarautar ne a wajen mahaifinta sarki masrud bin Zaurid Sarki masrud ya kasance gawurtaccen mayaki wanda yai shuhura zamaninsa kuma shi a rayuwarsa babu abinda ya tsana sama da ma'abota addinin musulunci ba komai ne ya haddasa mummunar gaba tsakaninsa da ma'abota addinin musulunci ba face akwai watarana da wadansu fatake ma'abota addinin musulunci da suka zo giftawa ta birninsa, sai suka yada zango a gefen garin domin su yada zango. A wannan lokaci akwai wani takadirin aljani a cikin birni na Sufras wanda muatena ke 59 TURBAR GASKIYA --4 MADAKIN GINI bautawa a matsayin ubangijinsu. A kullum sai an yankawa wannan aljani raguna uku, shanu, uku da rakuma uku, kuma Sarki masrud ne da kansa yake jagorantar wannan hadaya da ake yiwa aljanin mai suna burrata. A ranar da wadannan fatake suka ya da zango a bakin birnin Sufaras ne wata annoba ta zo birnin ya zamana cewa gaba daya dabbobin garin da tsuntsayensu sun kamu da wata irin cuta ta gudawa don haka sai suka rinka mutuwa wasu kuma suka lafke ya zamana cewa ko ta shi basa iya yi. Bisa ka'idar hadayar da ake yiwa aljani burrata ana yanka masa lafiyayyun dabbobi ida kuwa aka kuskura aka yanka masa mara lafiya koda guda daya ne kacal a ranar babu wanda ya isa ya yi barci a garin kuma duk kanannan yar dake garin sai sun kamu da cutar da zasu yi ta mutuwa haka kuma idan aka saba lokaci na yin wannan hadaya to fa sai wannan bala'i ya afko. Sarki marud. yana samun dukkan biyan bukatarsa a wajen aljani Burrata bisa wannan dalili ne baya yarda a sami matsala a ko kadan akan yi masa hadaya. 60 TURBAR GASKIYA --4 MADAKIN GINI Lokacin da ake yin wannan hadaiya ga aljani Burrata da yammaci ne sakaliya daf da magruba tun da rana wannan annoba ta afku a cikin birnin na Sufras al'amarin da ya dugunzuma hankalin Sarki masrud ke nan ya baza dakarunsa ko ina a cikin birane da kauyuka na kusa a kan a nemo lafiyayyun dabbobin da za'a yankawa aljani Burruta kafin rana ta fadi. Ai kuwa har gefen la'asar ba'a sama dabbobinba sai ga Dakarun da aka tura sun dawo cikin gigita da dimauta, shugabansu ya zube kasa a gaban Sarki masrud ya ce, Ya shugaba mun duba ko ina a cikin biranc da kauyuka dake kusa da wannan kasa tamu babu inda wannan annonba bata je ba, mun rasa lafiyayyun dabbobi amma akan hanyarmu ta dawowa mun ga wadansu bakin fatake kuma suna da dabbobi lafiyayyu fiye da adadin da muke bukata. Koda Sarki jin wannan batu sai farin ciki ya lullube Sarki Masrud ya ce, "Maza ku koma wajen wadannan fatake ku siyo daddbobin da muke bukata a wajensu komai tsadarsu kuwa, idan suka ki siyar muku ko kwato su da karfin tsiya ku zo mini da su, domin mu hanzarta zuwa 61 TURBAR GASKIYA --4 dakin bauta. _MADAKIN GINI Koda jin wannan batu sai Shugaban dakaru ya mike tsaye da sauri yana mai cewa an gama ya shugabana, nan take ya jagoranci dakarunsa kimanin su dari biyu suka hau dawakansu suka zaburesu da gudu izuwa gfen gari Su dai wadannan fatake da suka ya da zango a gefen birnin sufras gaba dayansu basu fi su ashirin ba kuma duk zur'a dayane na wani attajiri da ake kira Abu Salhaif. Acikin wannan Zuri'a akwai matarsa guda daya da kuma dansa shima guda daya jal wani matashin saurayii wanda baisfi shekara goma sha hudu ba, shi ake kira da suna Salhif, sauran mutane goma sha bakwan daga kannensa sai matansu, da 'yayansu. Abu Salhif na tsaye tare da dansa Salhif yana koya masa yadda ake yaki wato suna kaiwa junansu sara da suka cikin gwaninta a gefe daya kuma matarsa da sauran abokan tafiyar na tsaye suna kallonsu sai kawai suka hango kura daga can nesa ta turnuke sama, sannu a hankali suka hango dakaru bisa dawakai a sukwane sun 62 TURBAR GASKIYA --4 durfafosu. MADAKIN GINI A zaton su Abu Salhif yanfashi ne suka kawo musu hari, har mazajen cikinsu sun yunkura zasu zare makamansu su tari mahayan sai Abu Salhif ya daka musu tsawa, ya hana su, don haka sai kowa ya tsaya a inda yake har mahayan suka kara so daf da su suka yi turjiya suna sanye cikin kayan yakin dakarun birnin Sufras. Koda Abu Salhif da jama'arsa suka ga cewa ashe dakarun birnin Sufra ne sai hankalinsu ya kwanta suka mayar da takubbansu cikin kufe. Cikin biyayya Abu Salhif ya risina ga shugaban dakarun ya yi gaisuwa sannan ya се, "Ya ku Dakarun Sarki Masrud me kuke bukata daga garemu har da zaku kawo mana ziyarar bazato a irin wannan lokaci alhalin ko shigowa cikin birnin naku ba mu yi ba? Koda jin wannan tambaya sai Shugaban Dakarun ya sauko daga kan dokinsa ya matso daf da Abu Salhif ya ce, "Ya kai wannan attajiri tsohon abokin cini kinmu ka yi sani cewa Sarki ne ya tro mu gareku domin ku siyar mana da raguna uku, shanu uku rakuma daga cikin 63 TURBAR GASKIYA --4 MADAKIN GINI dabbobinkudomin mu bayar da jinin su ga abin bautarmu gunku Burrata." Koda jin wannan ba tu sai hankalin Abu Salhif ya dugunzuma ya ce, "Subhanallahi ya kai wannan badakare ka yi sani cewa mu musulmai ne wadanda suka yi imani da bautar Allah Sarki guda daya wanda shi ne ya halicci komai da kowa har da shi gunkun da kuke bautawa, ta yaya zamu bayar da dabbobinmu kuje ku aikata wannan mummunan sabo da su, ai idan muka baku tamkar muma mun yi imani da abin da kuke bautawar ke nan, ku koma ku gayawa Sarki Marud cewa ni attajiri Abu Salhif nace ya yi hakuri ba zamu iya siyar masa da dabbobinmu a, koda jin wannan ba tu sai shugaban dakarun ya tari numfashin Abu Salhif yana mai daka masa tsawa ya ce, "Sarki ya bamu umarni idan har baza ku bamu wadannan dabobbi ba lallai mu karbe su da karfin tsiya koda jin haka sai Mazajen ayarin na Abu Salhif suka zare takubbansu da nufin su yaki dakrun Sarki Masrud, amma sai Abu salhif ya sake daka musu tsawa a karo na biyu ya ce, "Baku da hankali ne ta yaya zaku iya yakar dakarun kimanin dari 64 TURBAR GASKIYA --4 MADAKIN GINI biyu alhalin gaba dayanmu bamu wuce mu goma sha ba." Nan take mazajen suka sake mayar da takubbansu cikin kufe suka koma bayan Abu Salhif suka tsaya a wannan lokacin ne bakin ciki ya lullube Salhif har zuciyarsa ta kama tafarfasa kamar zata kone jikinsa ya kama tsuma koda shugaban dakarun ya lura da halin da Salhif ke ciki sai ya bushe da dariya mugunta sannan ya dafa kafadar Salhif ya се. "Yaro ka yayyafawa zuciyarka uwan sanyi idan ba so kake yanzun nan jini zuri'arku gaba daya ya zube anan ba." Koda jin wannan ba tu sai Saihif ya sake fusata ya yunkura zai kaiwa badakaren Sara da takobin hannunsa amma sai Saihif ya yi wuf ya ruke hannunsa kuma ya zabga masa mari har ya fadi kasa, cikin tsananin mamaki Salhif ya shafe kuncinsa sa'adda hawaye ya zubo masa ya kurawa mahaifinnasa idanu saboda wannane karo na farko da ya taba marinsa amma ko bakar magana bai taba gaya masa ba, nan take Abu Salhif ya dubi Shugaban dakarun ya се. "Za mu baku dabbobin da kuke bukata 65 TURBAR GASKIYA --4 MADAKIN GINI amma ka gayawa Sarki cewa bukatarku ba zata biya ba ta hanyar amfani da da dabbobin ma'abota addinin musulunci koda gama fadin hakan sai Abu Salhif yasa aka kwanto raguna uku shanu uku da rakuma uku aka baiwa dakarun suka tafi da su. Bayan tafiyars ue Abu Salhif ya mikawa Salhif hannunsa ya kama ya tashe shi tsaye sannan ya dube shi ya ce, "Ka yi hakuri ya kai dana inda ban mareka ba bisa kuskuren da ka aikata da tuni an kasheka a gaban idanuna kasani cewa kai ne ka dai a gareni ni da mahaifiyarka don haka ba ma son mu rasaka ku ta shi mu kimtsa mu bar garin nan domin abin da zai biyo baya ba mai kyau bane,." Koda jin haka sai kowa ya ta shi aka hau kimtswa nan da nan kowa aka gama shiri aka kama hanya domin ci gaba da tafiya izuwa birnin na gaba.inda za'a gudanar da harkokin fatauci. Al'amarin Sarki Masurd ana kai masa wadannan dabbobi sai yai shiri ya tafi izuwa dakin bauta aka yanka dabbobin aka bayar a jininsu ga aljani Burrrata kamar yada aka saba Faruwar hakan ke da wuya sai suka ji aljani Burrata ya kwarara uban ihu al'amarin da ya janyo 66 TURBAR GASKIYA --4 MADAKIN GINI dakin bautar ya kama rugujewa, mutane dake ciki suka dimauce suka rinka zubewa kasa sumammu, Cikin firgici Sarki Masrud ya zube kasa gaban gunki Burrata yana tuba. Nan take gunki ya bude baki ya ce, "Maza ka tura dakaru su je su kashe wadannan bakin fatake domin jinin dabbobinsu bai magance mini kishirwata ba face Karuwata kuma ka sani cewa lallai sai an yi asarar dubban rayuwaka a cikin Kasarka saboda fishina idan baka hanzartaa samomin jinin da na saba sha ba ko wa sai ya dandana kudarsa." Koda jin wannan batu sai Sarki masrud ya sake dimaucewa ya mike tsaye zumbur yana mai kwalawa Sarkin yakinsa kira ya fice da gudu. Kadan ke nan daga cikin littafin JAHADI wanda zai zo nan bada jimawa ba. Naku har kullum Abdul'aziz sani madakin gini Dukkan mai son wannan labari da kuma sabon labarina WASIKAR JINI SAI KU SAME SHI A SABON BRANCH NA JAKRA CITY BOOK SHOP DAKE KASUWAR SABON GARI MARKET KUSA DA MADAKIN GINI BOOК SHOP ДБЕМ Sai mun ji daga gareku za a iya samunmu a wannan numer kamar haka 67 TURBAR GASKIYA --4 MADAKIN GINI 08162707231-08069524699 TALLA! TALLA!! TALLA!!! SAKON MUTUWA A tsakar dajin mai yalwar korayen ganyayyaki suke tsaye su biyu a tsakiyar koraye ganyayyaki wasu jibgajibga aljanu suna tsaye a gefensu kowane su rike yake da jariri a hannunsa cikin tsananin farin ciki da ganin juna. Sarakuna ne masu ji da sarauta suturun dake jikinsu kawai zai tabbatar maka da haka kowane yana rike da jariri a hannunsa Sarki 2 Madhan shi ne Sarki kasar Arfat, sai Sarki Azkam shi ne Sarkin kasar Yuhud abokane ne su wadanda aka yi 68 L TURBAR GASKIYA --4 MADAKIN GINI shelar a duk duniya babu abokai masu kaunar juna da amincin sama da su, sannan babu wasu sarakai masu girman masarauta da tumbatsar arziki face su, kuma duk da sun kasance abokan gugayya a bangaren sarauta dukiya gami da jin kai, basu zame masu yiwa juna bakin ciki ba haka ma shi yafi musu dadi a rayuwa domin basa so ace a cikinsu wane yafi wani, sun fi son su zama suna tafiya daidai da juna. Abu guda ne ya banbanta wadannan Sarakai Sarki Madhan yana mutukar son ganin ya haifi 'ya mace ya yin shi kuma Sarki Azkam kuma ba shi da burin da ya wuce ace ya samu haihuwar da namiji, amma sai aka samu akasi a shekarar da matarsa zata haihu sai ta haifi 'ya mace shi kuma Sarki madhan sai matarshi ta haifi da namiji, wannan dalili ne yasa suka yi wa juna alkawarin musayar yaran ta yanda 69 TURBAR GASKIYA --4 MADAKIN GINI babu wanda ya san da haka, face aljanunsu guda biyu kuma masa rike sirrikansu. Ranar daya lokaci guda aka samu wannan haihuwa a lokaci da matan suka haihu sai Sarki Madhan da Sari Azkam suka badawa matansu hodar banjo sukа kama barci ta wannan yasa suka saka aljanunsu suka kwashe su zuwa wannan daji. Koda Sarki madham da Sarki Azkam suka dubi juna sai farin ciki ya baibaye su, Sarki Madhan ya ce, "Ya kai Aminina hakika godiya ba zata kare ba bisa yanda muke mututta juna kuma muke daraja juna lallai daukakarmu da boyayaryamu ba zata taba rugujewa face an samu ranar da dayanmu zai ji bazai iya rufe sirrin dayanmu ba, dan haka ina mai horonka da ka yi yaki da zuciyarka wajen gujewa wannan, sannan ina mai kara jadda maka akan ka tsare wannan sirrin kamar yanda zaka tsare rayuwaka dana ya zamai naka 'yarka ta zama tawa, har abada 70 TURBAR GASKIYA --4 MADAKIN GINI babu wata rana da zamu saka ido akan wani daukaka da zata biyo baya a lokacin da yaran nan suka girma, in har mun kawar da wannan to babu shakka amincinmu zai cika gaba da daurewa har abada." Koda Azkam ya ji wannan ba tu sai ya mika jaririyar dake hannunsa ga amininsa shi ma amininsa ya mika masa jaririn. Sannan Sarki Azkam ya ce, "Babu wata rana da zuciya ta isa ta kawo mana sukar junamu halas malak na bar maka wannan yarinya kamar yanda halas malak ka barmin wannan yaron, dan haka koda masifar wuta da ruwa zasu cudu a cikin kasata ya zamana bani da maganin wannan masifar face ďanka to ina mai tabbata ba zan taba bukatar shi daga gareka. Da jin haka sai Sarki Madhan ya yi murmushi ya rungume Sarki Azkam suna masu murmushi. Da haka kowannensu ya koma ya haye kan aljaninsa. Suka Bace daga cikin dajin cikin tsananin farin ciki da nishadi. 71 TURBAR GASKIYA --4 MADAKIN GINI n Tirka shi, kirarren labari ne da na ratattako muku shi mai suna SAKON MUTUWA yana nan tafe daga ni Abdulsalam Adam shitu bature gadon kaya D A 08162707231 Ni Abdulsalam ina kara yiwa makarantana tuni da fitowar littafin DAKARU KASHI NA HUDU SANNAN NA BIYAR SHI MA YA FITO TARE DA WANNAN LABARI IN BAKA SAMU GARAZAYA KA NEMI NAКА. MUNA KARIN SANAR DA SHAHARARREN MARUBUCIN YAKIN NAN MARUBUCIN GIMBIYA ZAHRA DA ADDININA WATO MUKTAR KWALISA YA ZO MUKU DA SABON LITTAFI MAI SUNA RANAR GAMO YANA NAN A KASUWA An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da

Chapter 10 of 11