Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
3 / 11
kama shiri tana mai caba ado da nufin taje unguwar 'yan gudun hijira tana cikin yin adone mahaifiyarta ta shigo dakin nata ta dubeta cikin mamaki tace yake "yata ina zaki je da yammacinnan haka alhalin magariba ta kusa? Lushmaira ta juyo ta dube mahafiyattata cikin murmushi tace "Ina sone naje naga ikon Allah wato naga kyakkyawar fukar da tafi tawa wacce a halin yanzu zancenta kawai akeyi a birnin nan da kauyikan kasar nan, Koda jin wannan batu sai Karimat mahaifiyar Lushwaira tayi murmushi sannan tace "yake 'yata kiyi sani cewa zuwanki wajen wannan 'yar attajiri bash. da wani amfani domin bazai haifar miki da komai ba face kishi, ban son a samu wani sabani tsakaninki da wannan bakuwar budurwasaboda musulunci yaharamta gaba da hassada, kada kiyi kiyayya ko hassada gareta saboda ta fiki kyau. 49 ABDUL'AZIZ SANI M/GINI TURBAR GASKIYA Lokacin da Lashmaira taji haka sai tayi murmushi tace yake Ummina na rantse da girman Allah babu wani abu a gabana face cika umarnin mahaifina ba wani abu bane yasa nake son naje naga wannan 'yar attajiri face gudun kada zuwanta garinnan ya hanani cika wasiyar mahaifina". Da jin wannan sai karimat ta dubi Lushmaira cikin alamun damuwa t ace "tayaya Shadilar zata hanaki cika wasiyar mahaifinki? Lushmaira tace "baza ki fahinta ba sai anan gaba idan lokaci yayi amma dai yana da kyau yanzu naje nayiwa al'amarin rigakafi, gama fadin hakan ke dawuya sai Lusmaira ta fita daga dakin da isa harabar gidan inda tai ski hadimen gidan nasu ruke da doki yana jiranta, da zuwa sai ta karbi dokin ta hau ta fice daga cikin gidan Kai tsaye Lushmaira ta nufi gidan 'yan gudun hijara, tana isa ta tambaya gidan da Shadilat take take aka nuna mata. Lushmaira ta kunna kai izuwa cikin gidan tana mai yin sallama, wata kuyanga e eta amsa mata sallamar wacce ta isketa zaune a falo tana hidima, Lashmaira ta dubi kuyangar tace "je ki ki gayawa uwar gidanki tayi bakuwa, ba tare da 50 ABDUL'AZIZ SANI M/GINI TURBAR GASKIYA garda ma komai ba kuyangar ta mike tsaye ta shiga cikin turakar sannan ta sake fitowa tace "shugabata t ace ki baiyana kanki, Lushmaira tace "Kije ki gaya mata cewa gimbiya Lushmaira ce 'yar marigayi Sarki yaki Hizanu, nan take kuyangar ta koma ta isar da Sako da jin haka sai Shadilat ta mike zumbur ta fito falo cikin farin ciki, Koda suka yi arba da juna ita da da Lushmaira sai kowannensu ya kurawa junansu idanu ko kiftawa basa yi,tsawaan 'yan dakiku suna tsaye kikam kamar gumaka sannan Shdilat tayi murmushi ga Lushmaira tace "lale marhabun da 'yar Namijin duniya dodon macijiya Burukul karsum, ga kujera ki zauna mu gaisa hakika yau ina da babbar bakuwa, Lushmaira da Shadilat suka zauna a tare akan kujeru da suke fuskantar juna a lokacin Shadilat ta umarci kuyangarta da ta kawo musu abin sha ta tafi cikin umarni, Shadilat ta dubi Lsuhmara cikin nutsuwa tace "hakika kina kama da mahaifnki a fuska, cikin alamun mamaki Lushwmaira taçe "taya akai kika san mahaifina hard a kamaninsa alhalin baki sanshi ba kuma baki taba ganinsa ba, Asalima ni kaina da nake 'yarsa ban taba ganin sa batunda aranar da ka 51 ABDUL'AZIZ SANI M/GINI haifeni ya mutu? TURBAR GASKIYA Shadilat ta gyara zama tana mai yin murmushi tace "yake Lushmaira kiyi sani cewa a rayuwata babu abinda yake burgeni sama da jarumi don haka sa'adda na sami labarin mahaifinki bisa jarumtakar da yayi sai na aiko manzo musamman izuwa ga nan birnin yazo yayi mini bincike akan tarihinnsa hard a kamaninsa ma sai da aka sa wani masanin zanen ya yazana min taswirarsa aka kawo min, domin ki gasgata zancena yana da kyau kiga zahiri. Nan take Shadilat ta mike tsaye ta shiga cikin turakarta, jim kadan sai ta fito da rike da wani allo a hannunta na Karfen zinare ta mikawa Luswairat, Koda Lushmaira ta dubi kan allon sai tayi arba da hoton mahaifinta yana yaki da macijiyar Burukul Karsum a alokacin day a sami nasarar suka mata takobi acikin idonta, hakika kamannin fuskarsa sak irin ta sarki ce banbamci kawai shi yana da dogon saje wanda ya zagaye fuskarsa, nan take Lushmaira ta kurawa fuskar mahaifinta idanu aikuwa sai kwallah ta cika mata idanu har hawaye ya zubo daga idanunta tad ago kai ta dubi Shadilat ta ce Nawa zaki siyar min da 52 ABDUL'AZIZ SANI M/GINI wannan hoton? TURBAR GASKIYA Koda jin haka sai Shadilat tayi sauri wuf ta karbe hoton daga hannun Lushmaira t ace "ai idan kika ga na siyar da wannan hoton sai idan nima nayi irin jarumtakar da mahaifinki yayi na soke daya idon na Macijiyar Burkul karsum an zana taswirata kamar yanda aka zana wannan. KOda jin haka sai Lushmaira ta tuntsire da dariya, al'amarin da yai mutukar baiwa Shadilat mamaki kenan ta dubeta tace menene dalilin yin wannan dariya taki? Lushmaira ta hade rai tace "gani nayi iska na yawo da mai kayan kara domin kuwa kina mafarki ne wanda bazai taba zama gaskiyaba, yaya abin day a gagari duk jaruman mazajen nahiyar nan gaba daya za kice ke zakiyishi? Ina son ki farka daga dogon mafarkin da kike ki fuskanci abin da zaiyiyo na zahiri yanzu ki gaya mini dinari dubu nawa zaki siyar mini da wannan hoton? Koda jin wannan batu sai ran Shadilat ya baci ta mike tsaye ta zaro takubi daga cikin kufensu guda biyu dake rataye ajikin bangon da cillawa Lushmaira guda daya ta café sannan ta ajiyc wannan hoto a tsakayar falon ta dubi 53 ABDUL'AZIZ SANI M/GINI TURBAR GASKIYA Lushmaira ta ce "kudi baza su iya baki wannan hotan ba amma idan zaki iya karbarshi ta kaifin takobi ko karfin damtsenki ya zamana ki na samu labara ke ma kin kuyi yaki a sirranci ba tare da mutane sun sani ba kama yadda nima na koya tun ina yarinya, Na sani cewa nayi miki fin tin kau a fagen kyau amma, a fagen bangaren jarumta ban sani ban a dade ina jiran wannan rana, kuma gashi tazo idan har kin cika 'yar marigayi Sarkin yaki Hizanu ki dauki wannan hoton ki fita dashi daga cikin gidannan. Koda jin wannan batu sai mamaki ya kama Lushmaira bisa yadda akayi Shadilat tayi wannan bincike akanta da mahaifnta haka kuma sai zuciyarta ta kama tafarfasa bisa jin tace idan ta cika 'yar marigayi ta dauki wannnan hoto da karfin damtse, nan take Lusmairat ta daga takobinta sama tana mai gyara tsayuwarta kawai sai ta falfala da gudu izuwa inda Shadilat ta ajiye wannan hotn ta sunkuya tana kai hannu domin ta dauki hoton, Koda ganin haka sai Shadilat tad aka tsalle daga inda take ta doki kafadar Shadilat da kafarta guda ta hantsaila can bayakafin tad au hoton, cikin zafin nama Lushmaira ta mike tsaye 54 ABDUL'AZIZ SANI M/GINI TURBAR GASKIYA zumbur ta tareta suka ruguntsume da azababban yaki tamkar kafiri da musulmi na kokarin hallaka juna ya zamana cewa suna kaiwa junansu sara da suka juriya da bajinta, nan fa suka tashi hankalin barori da kuyangi dake cikin gidan, Kuyangar ma da taho kawo musu kayan abincı taga ana irn wannan tashin hankalin sai ta saki faranti dake hannunta komai ya tsiyaye akasa ita kowa ta sulale kasa sumamiya. Said a Lahsmairat da Shamdilat suka shafc kusan rabin sa 'a suna kaiwa juna sara da suka amma dayanrsu bata sami nasarar koda lakutar jikin dayaba, Al'amarin daya fusatasu kenan sukayi watsi dad a takubbansu sukka ja da baya, kowacce ta duhkule hannayenta kuma suka sake rugowa da gudu da nufin su kacame da sabon fadan hannu kwatsam ba zato ba tsammani sai suka ga Yarima Zaiyan ya dako tsallac ya shiga tsakaninsu bisa dole kowacce ta ja da baya suka jifa da takobban dake hannayensu kuma suka kama murmushi kamar ma babu abin ya faru, Lusmaira ta dubi Yarima cikin alamun mamaki t ace mene ya kawo nan wajen a awannan lokacin, yarima ya daka mata tsawa yace" aike ya kamata ki gaya min dalilin da 55 ABDUL'AZIZ SANI M/GINI TURBAR GASKIYA yasa kika zo nan kike son ki hallaka daya daga cikin bakinmu mai daraja? Kafin Lushmaira t ace wani abu sai idanun Yarima suka kai kan wannan allon hoton na Sadauki Hizanu wanda aka ajiyac a tsakiyar falon, ciikin tsananin mamaki yarima ya kurawa hoton idanu ya karaso wajen ya dauki hoton, koda yaci gaba da kallon hoton sai nan take idanuwansa suka fara zubar da hawaye, kawai sai ya dago kai ya kale Shadilat yace "yaya akai kika samu wannan hoton kanin mahaifina? Shadilat ta num,fasa tace "nice nasa aka zanashi saboda bani da burin da yafi na zamo kamarshi akan wannan hoton muke wannan yaki kuma nici na baiwa Lushmaira damman ta yakeni domin na jarraba karfin jarrumtakata akan tata saboda nasan cewa itama ta koyi yaki a sirrance tun tana yarinya, Tabbas na na sha gabanta afagen kyau amma afagen Jarumta yanzu na tabbata cewa munyi kunnen doki bazan taba wuce tab a face Sarki ya amsa zai min alfarmar da na nema awajens. Lokacin Shadilat tazo nan aazanceta sai kan yarima ya daure ya cika da tsanannn mamaki kawai sai ya dubi Shadilat yace "to ke 56 ABDUL'AZIZ SANI M/GINI A TURBAR GASKIYA menene dalilin da yasa ba kyason Lushmaira tafi ki Karfi ko jarumtaka?" Koda jinwannan tambaya sai shadilat tayi ajiyar zuciya sannan tace saboda na fuskanci cewar zata iya lalata mini babban burina na duniya na son nd zama jarumar da babu kamata, a tunda ita kuma babban burinta shi ne ta auri jarumin da babu kamarsa a jarumtaka idan har yazamaía cewa ba n ice jarumar da tafi kowa jarumtaka ba lallai wanda zata aurane, babu wanda zaifin kowa jarumka a wannan zamani face wanda ya soke daya idon na Macijiya Burkul Karsum da izinin Allah nice zan samu wannan nasarar sa'adda Sahadilar tazo nan a zancenta sai tabmikawa Yarima hannunta tace bani hotona na jarumin jarumai, batare da gardama ba ya mika mata ta Raroa yarima ya dubi Lushmaira sannan ya dubi Shadilat sai yayi murmushi ya ce "Hakika duk ko biyun akwa wani abu a karkashin zuciyarku da kukë boyewa amma koma menene in ya mina yatube za muji wari, abin da nake so ku fahinta shitheryanzu abin dake gabanımıu yakiner tunda dał Sarki ya aika wad a Sarakunan can uku takardar raddita yaki babu makwan sai any! wannan yaki saboda haka ina mai shawartark 57ТNID\М ІMA2 SISA'JUCABDUL'AZIZ SANI M/GINI TURBAR GASKIYA ku bi yun nan daku ajiye duk wani bure burenku sai bayan wannan yaki yanu ke Shadilar nawa zan biya na fita da wannan hoton na Sarkin yaki na kaiwa Sarki shi domin ba kara min farin ciki zai yi ba idan ya mallakeshi don na tabbatar da cewa zai debe masa kewar marigayi, sa adda Shadilat taji wannan sai tayi murmushi tace "wannan hoton nawa ban a siyarwa bane da kudi sai dai siyeshi da jarumtaka idan har kana son na sai maka shi sai dai ka koyi mini yadda akeyin hawa dogowar ganuwar nan wacce ke tsakiyar gariinan har ka isa Karshenta aranar da kai da mahaifnka kka hau kan ganuwar har kuka rasa yadda zaki yi ku sauko kasa sai raga aka sa muku ku ka fado kanta, Loakcin da Shadilat tazo nan azancenta sai yarima ya cika da tsananin mamakin adda akayi tasan wannanal'amarin alhalin ba agabanta akayi ba asalima awanan lokacin tana can uinguwar su ta 'yan gudun hijira basu san abinda ke wakana ba tunda acan karshen gari unguwar take, Yarima Y ace Da ita "Zanyi tunani tukunna idan naga ya dace na koya miki hawa kan ganuwar sai na koya miki, Dajin haka sai Lushmaira tatari numfashinta sa. Ta ce "aikuwa sai dai ka koya 58 ABDUL'AZIZ SANI M/GINI mana tare" TURBAR GASKIYA Kafin yarima yabuſe bakinsa yayi Magana sai ya ga wani badakare ya shigo cikin gidan da sauri, da zuwansa sai ya risina ga Yarima yace "ya shugabana Sarki yace kazoo yanzn da sauri fada ana gabatar da taron gaggawa, Koda jin haka sai yarima ya dubi shadilat yace "kuyi hakuri sai kuma mun kara samun lokaci sannan zamu warware wannan matsala, nan take Yarima ya juya ya fice daga cikin gidan da sauri yabi wannan badakare abaya suka nufi fada, Da isarsu fada suka iske sarki tare da dukkanin 'yanmajalisa da kuma gaba dayan dattijan garin wannan jama'a sai jikinsa ya bashi cewa lallai yaki ya tsao domin duk sa'adda akayi irin wannan taro a afada in ba batun wata anno bad a ta shigo gari sai dai ko batun yaki, kai tsaye yarima ya nufi inda Karagar sarki take ya zauna daf da Sarki A lokacinne Sarki ya dubi gaba dayan Jama ar dake fadar y ace "yaku kjama'ata kuyi sani cewa labara ya zo mana daga bakin 'yan lekken asiri mu cewr kasar birinin Hizuba da birnin, Dakful da Birnin, Karsum sun tara 59 ABDUL'AZIZ SANI M/GINI TURBAR GASKIYA dakarun yaki sama dana mutun Miliyan goma acikin birnin Hizuba domin su zo su yakemu tun kafin amsar wasikar da suka aiko mana ta samesu, wannan yana nun da cewr daa so suke su baje kasarmu su kawar da addininmu a awannan nahiya gaba daya, lallai ba zamu zauna muna jiran so iso ba har nan bas u cimu da yaki, bazamu ji tsaronsu ba koda yawansu ya kaiyawan gaba dayan mutanen duniyar nan saboda munsan cewa muna kan TURBAR GASKIYA su kuwa suna kan turbar karya Koda Sarki yazo nan a zancensa sai fadar baki daya ta kauri da kabbara sannan Sarki yaci gaba da bayaninyace "kun sani cewa tunda na hau kan wannan karaga ta mulki ban taba yin yaki ba azamanina sai yanzu, rabon da ayi yaki awannan Kasa tun mulkin mahaifnna sa adda Dan uwana ya rike sarautar sarkin yakin a garinnan tun daga wannan alokaci kawo I yanzu amu da Sarkin yaki a garinnan saboda haka ni yanzu na nada yarima Zaiyan akan matsayin sabodan sarki yaki wanda zai iya jagoranciwannan yaki da zamuyiu saboda na gamsu da jarumtakarsa juriyarsa da hikimarsa da Allah ya bashi, uwa uba kuma ya kasance mutun 60 ABDUL'AZIZ SANI M/GINI TURBAR GASKIYA mai mutukar Sa'a bisa duk abin da yasa aagabansa. Lokacin da sarki yazo nan ab batunsa sai fadar tayi tsit 'yan Majalisar suka kama kus, kus kowa na fadin albarkacun bakinsa alamar cewar da yawansu suna da shakka akan jagoranci da yarima zaiyi na wannan yaki, Koda Sarki ya fuskanci abinda ke faruwa sai yai gyaran murya kowa ya nutsu sannan yace duk wanda yake da korafi akan wannan bayini nawa. bisa hukuncin da na yanke ya fito yayi hawabi tunda amfamin taruwarmu anan kenan domin mu zartar da hukunci da muke ganin cewa shi ne zai fishemu. Koda jin wannan batu sai waziri ya mike tsaye ya fuskanci jama'a y ace ni korafina guda dayane a tunanina bai kamata ace mutumin da bai taßa fi a yaki ba kuma bai taba fita filin daga ba ac yazamana cewa shi zai jagoranci mayaka sama da miliyan daya saboda bai san yadda ake yaki ba baisan irin dabarun da ake yi ba donin a yaudari abokan gaba asami nasara yaki akansu. Koda jin wannan batu sai Sarki yayi murmushi y ace ai ba yarima kade ne zai jagoranci wannan mayaka ba domin hard a ni za ayi wannan yaki duk wani abu day a shige masa 61 ABDUL'AZIZ SANI M/GINI ni zai taimaka TURBAR GASKIYA duhu masa, Koda jin haka sai hankalin kowa ya tashi ya dugunzuma, waziri ya dubi Sarki cikin alamun tsananin damuwa yace" ya shugabana abune mai tsananin hadari ka shiga wannan yakin domin jiya bay au b ace tabbas yanzu girma ya fara kamaka jaurmtakar da kayi a ada yanzu bazaka iya taba da zarar abokan gaba sun kyaila ido sun ganka acikin mayaka kokarin za su yi suyi maka rubdugu har sai sunga cewa sun gama da kai sannan hankalinsu zai kwantakasani cewa kaine mayakin da babu kamarsa awannan kasa tamu gaba daya idan gaba daya dakarun mu suka ga ka fadi zasu iya samun karayar zuciya su kasa ci gaba da wannan yakki yadda ya kamata idan kuwa haka ta raru cikin kankanin lokaci za amurkushemu tunda dama bamu da yawa. Sa adda sarki yaji wannan korafi na na Waziri sai ya sake yin murmushi yace "yakai Waziri kayi sani cewa kafin na yanke hukunci fita wannan yaki said a nayi la'akari da duk wadannan matsalolikuma nayi tunanin mafita akan su saboda haka ina mai tabbatar muku da cewa nasan abin da zanyi domin na kare kaina daga wadannan matsaloli a bin da nake bukata 62 ABDUL'AZIZ SANI M/GINI TURBAR GASKIYA daga gareku kawai shi ne ku tayi ni da addu'a. idan kuma akwa mai sauran korafi ya tashi yayi Magana. Fadar ta sake yin tsit har izuwa tsawan 'yan dakiku baa sake samun wanda ya sake yin wani korafin ba, Asannane Sarki ya dubi Yarima yace "kaje ka fara shirya dakarunmu gobe da Asuba bayan munyi Sallah zamu fita daga cikin birninmu mujes mu tari abokan gaba lallai Ashirya guziri duk da abin dake bukata ayau kafin ya raba. slinsd inidi bawuR" Yarima lya rissina yace an gama ya shugabana, Nan take Yarima ya mike tsaye ya fice daga cikin fadar ya tafi izuwa can fadar inda ya tura akirawo masa gaba dayan dakarunsa da zasu fita wannan yaki, mud onaya появява nuniiNan da nan kuwa labara ya bazu ko ina acikin birnin da kauyeka, Nanfa jama'a suka dukufa wwajen yin addu'a suna ta rokon Allah akan ya bayar da nasara akan wannan yaki da za fitanie s inesb sова и по вast swao idasi Al'amarin Gimbiyar Lushmairal kuwa lokacin da taji za afita wannan yaki amma banda mata face matan da mazajensu zasu fita domin tu taimakamusu wajen dafa musu abinci da kula 63ИТСМЕИAR SISA'JUQBABDUL'AZIZ SANI M/GINI な TURBAR GASKIYA da lafiyarsu alokacin da suka sami raunika sai hankalinta ya dugunzuma cewar komai rintsi da tsanani sai taji wannnan yaki domin ta bayar da gudummawarta ga addainin Allah kuma ta jarraba jarumtakarta da horon da ta samu na yaki nan fat a kasa zaune ta kasa tsaye ta dinga kai kawo tana tunanin mafita, said a ta shafe lokači mai tsawo sannan dabara ta fado mata Nan take Lashmaira ta shirya ta tafi izuwa gidan shugaban likitocin birnin wanda ake kira da Zauwad ibini hanifa. - Da isar gimbiya Lushmaira gidan likitan sai ta iskeshi tare da likitoci da yawa yaransa wadanda yake kintsasu domin su bi rundunar mayaka lokacin da gimbiya tai so tana sanye ta bakaken kayane kuma ta rufe fuskarta idanunta kadai ake gani da yake tare da wani hadiminta tazo wanda yake rike da dokinta sai ta umarci hadiman nata akan yaje ya radawa Zuwwad zuwanta batare da kowa yaji ba kuma ya sanar dashi cewa tana son su gana dashi a sirrance, nan take kuwa Bawan na yaje ya cika umarnin. Lokacin da likita Zuwad yaji cewar Lashmaira tazo har har tsoro ya darsu acikin zuciyarsa amma sai ya tura wani 64 ABDUL'AZIZ SANI M/GINI TURBAR GASKIYA hadimansayayiwa gimbiya jagora har izuwa cikin turakarsa. Da isar gimbiya cikin Turakar Zuwad sai tayi arba da abin da yasa zuciyarta ta harba da sauri da kuma buga. Ana zan dakata alittafina na daya sai mu shiga cikin littafi na biu don son ci ganan wannan labarin da kuma: yanda zata kasance mai Lushmara ta gani haka har yasa gabanta faduwa shin wace bukata tazo da ita gurin likita zauwad ina labarin Shadilar shin zata iya cika burinta na soki idanuwan Macijiya burukulb karsamo duk wannan amsashi suna cikin lit na biyu wanda a tare suka fito da na daya u2 onss UHS Daga marubucinku madakin ginos Hira tsakanin madakin gini da A a bature akan littafin Hikayoyina arabuan t whajara. aAbudul aziz madakin gime yane mai yabawa matashin maruci Abuduj salam adam shitu bature da cewar "agaskiya nayi mutukar farin ciki alokacin da na kasance mai karanta wannan littafin mai suna hikayiyin abu shajjara musammam hikayar kanina kuma dan uwa na Abudulsalam adamu shitu ya fara gabatarwa. Ban yi tsammani haka daga gareshi lallai na 65 иIXARABDUL'AZIZ SANI M/GINI jinjina masa mutukar jinjinawa, TURBAR GASKIYA shi wannan matashin maruci shi ne wanda ya kirkiri wannan labara kuma yazo min da batu alokacin azumi, nayi farin cki sosai gami da wannnatunanin da yayi kuma na yabawa kwanyarsa ta dalilin kawo min wannan bayanin cewar sa "Ina ganin ogana kamar yadda yake cewa dani ya kamata ace mun' tsaya mun fitar da littafi guri guda ma'ana tare dakai" lokacin da naji haka sai nayi mamakin batunsa atunanina ya za ayi ace muyi lattafi tare kuma guri guda. Bature ya ce da ni "ba ina nutin yazamana munyi labari daya tare da kai ba a'a ina nufin zamu zamo masu yin hikayoyin daya da daya acikin kowane littafi kuma zai kasance lattafin ya dinga fita aduk kan wata biyu biyu. Anan na fahinceshi na kuma sanar dashi cewa wannan ba matsala bace dukkaninmu sai mu dau damara yin dan muga inda zamu kama bakin zaren ayinni biyu kacal na kamala labarin kuma nayi mamakin yanda shima y agama nashi labarin ayini guda daga nan na tabbata lallaai bature ya dama danba nan take na tambayeshi wane suna za asawa littafin, batare da bata lokaci ba ya sanar dani cewar HIKAYOYIN ABU 66 ABDUL'AZIZ SANI M/GINI TURBAR GASKIYA SHAJJARA. Koda muka rabu dashi na jima ina nazarinsa da akan wannan labari wanda duk jimawata a harka littafi ban tabayi yin wânnan tuanniba na hada kaina da wani marubucin da mukayi zamani dasu kamarsu marigayi yaron malan da Shehu usman mohd dan haka sai na fara duban hikayarsa day a kawomin, Akwai rubuce rubuce da yawa agabana na so ne na dan duba labarinsa amma bisa mamakina ban tsahirta ba sai da yazamana ina ta faman bude faijika ina ganin faran takarda agaskiya na yaba masa mutuka dan haka ne yasa na barshi ya karasa wannan hikaya tashi har zuwa littafi na hudu sai ku saurareni da karashen tawa hikayar gami da sabowar d azan dasa a sabon labarina mai taken ARTABUN GUMURZU. Kadan Daga FARMAKIN ABOKAN GAMA Ya ku iyayena ni na tafi kuma bazan taba dawowa ba tunda na yarda da mutuwa Lallaai nayi da na sańi zuwane Birnin Basara kuma nayi danasani abinda na aikata badan tsoron yawan laifina ba said an kawai na so nayi tsawan rai 67 ABDUL'AZIZ SANI M/GINI TURBAR GASKIYA don in dauki fansar ran kakata da aka rataya tun a baya bisa laaifin kisan mahaifiyar Sarkin dan uwarka kuma makiyaki agare ka a yauzu tunda ayau nima na gurfana agaban inda suke rataye wanda suke aikaya laife a garesu sun rataye ni duk da cewar na kasance da ga dan uwansa Lallai mahaifin ka dauki dan uwanka abokin gabarka kuma kada ka taba yafe masa laifinsa ka dauki fansa akan daukacin al'ummarsa kada ka raga musu wannna shi kadaine zai nuna kai masoyinane acikin kuma shine zai nunawa masoyanka cewar mahaifiyarka ta haifeka a matsayin da mai Kaunarta Koda Sarki yazo nan a karatun sai ya sake fashewa da kuka mai tayar da hanakalin mai saurare ya kuma kwarara ihu mara dadin ji ya сe cikin kakkausar murya "Dana Kuhiaf zan dau fansa ko taw ace hanya zan dau fansar ranka akan Ulaisat Yar sarki Abulbashara, Sannan zan dau fansa bakan ta min zuciya da akayi akan duk wani raid a ke wanzuwa А Birnin BASARA 68 Zan kuma dau fansar ran mahaifiyata a ABDUL'AZIZ SANI M/GINI TURBAR GASKIYA akan Dan'una Sarki Abulbashara. Koda yazo nan kashedinsa sai ya. zare takobi daga jikin Zairul ya nufi Dakaru gami da kuyangun da Sarki yayi masa kyauta dasu Kuyangu da Bayi ya fara Sarewa kai Gaba daya hankalin jama'ar dake gurin hankalinsu ya tashi. WANNAN KENAN DAGA LITTAFIN MATSHIN MARABUCINKU AA BATUREGADON KAYA YANA NAN TAFE NAN BDA JIMAWA BA 08162707231, 07041591141,08124173211 Kadan Daga GASAR GWARZON KARNI K urdawa yake cikin kataren gidan sarauta sarautar hannunsa rike da muggan makai mai masu barazana ga rayuwar bil'dama, Duk yawan dakarun da aka zuba domin yimasa Katanga ga shiga cikin gidan, sunata kewaye kewaye yayin dashi kuma yake sadadawa a hankali cikin hikima irin tasa ta babban jarumi kuma gwarzon shekara a wanna lokaci duk badakaren da yayi rashin nasarar yin 69 ABDUL'AZIZ SANI M/GINI TURBAR GASKIYA ido hudo dashi to wannan ya zama tarihi karshe na rayuwarsa da haka har ya isa cikin turakar mahaifiyarsa, Lokacin daya isa ya sameta akwance amma bisa mamakinsa idanuwanta abude tarwai kuma kamar bata tare da wata cuta, Cikin ladabi ya ajiye makamansa yayi tattaki zuwa gareta a yayin da ita kanta ta zuba masa ido kuma batare da mamakin zuwan nasa ba awanan lokaci, a Koda karasuwarta zuwa kasaitaccan gadon sai ya duka ya gaidata, cikin irin nasu salon, kana ya dora da cewa "ya ummi nay naga kin kasance cikin halin rashin nuna mamakin ganina awanna lokaci duk da kuwa cewa rabon nasa idanuwa akan nake na dan tsawan lokaci, Koda taji shi wannan kalami sai yaga ta fashe da kuka al'amarin da yayi mutukar daure masa kai kenan ya dubeta cikin rudu" ya ummina ina dalilin wannan kuka nake nayi tsammanin cewar zakiyi farin ciki da ganina acikin wannan dare har hakan yazamo waraka cutar dake addabar zuciyarki, hi kuma na samu kwanciyar hankalina a gujewata ta barautar da 70 ABDUL'AZIZ SANI M/GINI TURBAR GASKIYA akemin, kuma da son ganin matata da fana, Sa'adda yazo nan ažancensa sai mahaifiyarsa taja dogowar majina ta dubehi a tausayi tace "Yakai dana hakika ka fada tarkon dan uwanka Ruhas domin suna sane da cewar zaka zo wannan birnin kota nalin kaka dalilin da yasa akayi shilar rashin lafivata kenan alhalin ni babu abinda ya sameni lallaı suna sane da shigowarka kuma bamu makawa sai sun samu nasara na kamaka kamar yanda suka kudurta da.domin da kansa sarki ya bada ammana akamaka a kashe saboda suna da labarin kana nan kana hada RUNDUNAR DAUAR FANSA, wanan daliline yasa ni zubar wanan hawaye Sa'adda Gwarzo jarumi Jamal yaji wanna batu sai ya dubi mahaifiyarsa batare da wani tashin hankali ya ce Kada ki damu ya Ummina ai tuni sun yi sakaci dan Zaki ya girma babu wata guguwar bala'in dazan yi shakkar tunkara a wanna lokaci dan haka yanda suka shirya nima na shirya A dai dai wannan lokaci dakaru gidan baki daya sun cika bakin kofar turakar mahaifiyarsa da kansa yaraima Ruhas ya shigo dakin cikin fusata Jamal bai dubeshi ba sai day agama sallama da 71 ABDUL'AZIZ SANI M/GINI TURBAR GASKIYA mahaifiyarsa ta cewar ta kwantar da hankalinta kamar ya tsira ya gamane. TURKASHI WAYE BAI KARANTABA WANNAN KASAIТАТТАCCAN LABARINE DAGA ABDULSALAMA ADАM SHITU BATURE GADON KAYA LALLAI KA NEMA DAN JIN WANNAN LABARI YANA NAN A KASUWA 1&2 NE. 72 ABDUL'AZIZ SANI M/GINI TurbarGaskiya 2 diaM DUL'AZIZ SANI KIN GINI TURBAR GASKIYA -2 a wani abu bane yasa zuciyarta ta buga B face Shadilat a zaune kan kujera ta harde kafafu tanna shan ruwan inibi acikin kofin zinare kuma fuskarta cike da annuri, Koda Lushmaira taga Shadilat sai ta juya da baya da nufin ta koma sai kawai taji Shadilat ta kirawo sunanta tana mai cewa "dawo 'yar uwata mu zauna tare aabin day a kaolo nan shi ya kawoni. Koda jin wannan batu sai Luhmaira ta tsaya cak sannan ta juyo a hankali cikin mutukar sanyin jiki da mamaki taje ta zauna akan kujerar dake fuskantar ta Shadilat ta cire mayafin day a rufe fuskarta suka dubi juna sosai tace "yaya akayi kika shai dani al halin fuskata arufe take? Da jin wannan tambaya sal Shadilat tayi murmushi tace "ai ko daga barci na farka bazan kasa tantance idanun kiba domin kece mutun na farko wanda na taba jin shakkarsa arayuwata. Kafin Lushmaira ta bude baki tace wani Abdul'Aziz Sani M/Gini a t TURBAR GASKIYA -2 abu sai Shadilat ta zuba mata ruwan inibi acikin wanikofin ta miko mata cikin alamun dari dari, Lushmaira ta karbi kofin ta

Chapter 3 of 11