Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
4 / 11
kurbi dan kadan sannan ta dubi Shadilat tace "saboda me kike shakkata kuma saboda me kike son kije wannan yaki"? ebo Sa adda Shadilat taji wannan tambaya sai dariya ta subuce mata tace "ba komai yasanake shakkarki ba face ina ganin cewa ke kadaicee zaki iya hanani cika burina kamar yadda na gaya miki da farko dalilina da yasa nakee sona naje wannan yakin kuwa za ayi yakine irin wanda ba a taba yin kamarsa ba a nahiyar nan gaba daya tarihin wannan yaki bazai taba gushewa ba domin za ayi asarar miliyoyin rayuwaka fiye da has ashen mai hasashee, aawannan yakine manyan jarumai zasu yi jarumtakar da sunayensu zasu daukaka asallama musu aako ina acikin duniya, kuma arubutu sa acikin kundin tarihin kowace Kasa ta düniya lallai ina son sunanan ya zamu daga Abdul'Ażiz Sani M/Gini TURBAR GASKIYA -2 cikin sunayin wadannan jarumai. Koda shadilat ta zo nan azancenta sai Lushmaira ta tuntsire da dariya tace "ai wannan burin nake daidai yake da tatsuniyar yara. Gama fadin hakan ked a wuya sai ga likita Zauwad ya shigo cikin turakar. Likita Zuwada ya kasance dattaijo wanda she karunsa a akalla zau kai saba in da 'ya'ya ya kasance dogon mutun mai matsakaicin kaurin jiki, yana da dogon faring emu kuma mutun ne mai gwagwar mayar duniya. LIkita Zauwad ya zauna agefe daya bisa kan wata kujera dabam sannan ya dubi Lashmaira cikin girmamawa yace "ranki ya dade zamu iya tattaunawa agaban wannan bakuwa ko kuwa ta bamu guri?" Lushmaira tayi murmushi t ace "ai irin bukatar da tazo maka da ita nima na kawo. Koda jin wannan sai hankalin likita ya dugunzuma ainun ya dubeta su duk su biyun cikin alamun tsoro da damuwa y ace "waishin Abdul'Aziz Sani M/Gini TURBAR GASKIYA - me kuke so ku jifani acikine? Kuna so na zama makaryacii ne ko kuma na zama mai karya dokar Sarkin? Idan har na na batar da kamininku kuka shiga cikin yarana aka je wannan yaki a tare daku wani abu ya tba lafiyarku sarki bazai yafe mini ba kuma girmana da mutuncina zai zube a idon kowa, wacce hujja zakuuuuuu gaya mini wadda zata kawar min da wannan fargaba har na amince da bukatarku? Koda jin wannan tambaya sai Lushmaira da Shadilat sukayi shiru suka dubi juna sannan Lushmaira ta numfasa tace "maganar gaskiya bamu da wata hujja ta zahiri wanda zamu iya gabatar muku da ita amma ina mai tabbatar maka da cewa na rantse da girman Allah babu abun na sharri acikin zukatanmu sai alkairi bisa zuwa wajen wannan yakin zamu bayar da gaganumar gudun mawa wacce zata baiwa kowa mamaki, ka tuna da cewa ni 'yar marigayi Sarkin yaki ce na karanta tarihin duk Abdul'Aziz Sani M/Gini TURBAR GASKIYA -2 yake yaken dad a mahaifina yayi a cikin kundinsa don haka na sami ilimi mai yawa acikin wannan littafin, lallaii zan bayar da shawara wadanda. Ita kuwa Shadilat 'yar attajiri ce da babu kamarsa acikin wannan nahiya, ita kanta mashahuriyar attajira ce don haka zata taimakamana da guziri mai yawa kuma koda muna cikin yakine guzurin ya yanke zata iya tawa ko ina daga cikin Kasashen dake kusa a kao mana, ina mai alkawari zamuyi kokarin ganin mun kare mutunci da kimarka acikin wannan al'amarin. Sa adda wannan sai jikin likita Zuwad yayi sanyi yayi shir ya sunkuyar da kansa Rasa yana tunanin tsawan "yan dakiku baice komai ba al'amarin day a dugunzuma hankalin shadilat Da Lushmaira kenan suka fara atunanin ko Zauwad ba zai amince da bukatar suba daga can sai Zauwad ya daga kai ya dubi Shadilat yace "Mutun nawa jama'arki wadanda 8 Abdul'Aziz Sani M/Gini TURBAR GASKIYA -2 kikeson su je acikin jama'ata suyi wannan tafiya? Shadilat tace " ai akalla sun kais u dari uku, cikin alamun tsoro Zauawad yace "mutun dari biyu ne kacal sarki ya bani izinin tafiya dasu kinga kenan idan kika kawo nake jama'ar mun kusan linkuwa kenan bana zaton Sarki zai aminta da hakan" Shadilat tayi murmushi tace zai amince idan har ka sanr dashi cewa wannan yakin saboda na musammane tunda za atafi da mayaka sama da miliyan daya dan haka likitoci dari biyu sun yi kadan. Zuwad ya gyada kai sannan ya dubi Lushmaira yace ana dawo gareki shin mahaifiyarki tasan zakiyi wanan tafiya? Idan bar bata sani ba baza iya tafiya tare da keba domin zata sanar da Sarki cewa bata ganki ba kuma kin sani cewa da kansa zai duba accikin tawagar kinga kenan duk sharinmu ya wargaje kenanjin kunyane zai biyo baya Lushmaira ta numfasa ta ce "aimahafiyata tasan dukkan shirina kuma ta amince da nayi wannan tafiya Abdul'Aziz Sani M/Gini TURBAR GASKIYA -2 saboda wani babban sirri wanda bazan iya sanar daku shi sannan ya dubi Shadilat da Lushmaira y ace "kuje ku kamala duk shirye shieyenku na tafiya sannan ku dawo nan gidana bayan Sallar Isha'i Anan zako kwana tare da jama'ata tunda asuba zamu dunguma zuwa kofar gidan Sarki don na tabbata akwai wani labari da Sarki zai bayar kafin wayewar gari wanda tun mahaifnsa yana raye idan yana so yasa ka zuciyoyin mayakansa su karfafa yana sanar da so wani labara day a taba faruwa na manyan Mazaje dan haka kada mu bari ko daya wannan labara ya shge mu dan yana da mutukar anfani ga dukkan wanda zaije wannan yaki. Koda jin wannan batu sai Shadilat da Lushmaira suka kamu da tsananin farin ciki nan take suka yiwa Likita Zauwad godiya sannan suka mike tsaye a tare suka fice daga cikin turakar suka fito kafar gida ajere suna hira cikin nishadi tamkar sun kasance 'yan uwa 10 Abdul'Aziz Sani M/Ginl TURBAR GASKIYA -2 juna ko kuma minai. Wannan shine ya faru a birnin baitul harwal baya ga wasikar yaki ta riski sarki Abul zaiyan. A can kuma birnin Hizuba, kuwa Sarki madhan, Sarki Tarmas, da Sarki Husaka na tsaitsaye afilin kofar birnin suna kallon miliyoyin dakarun yakinsu dakae tsaitsaye asahu saho ruke da makamai jagoransu na basu horo sai aka hango wani ya matso kusa sai aka ga ashe wannan manzo en da aka aika shi birnin Baitul Haural nan take Sarki madkan ya kama murmushi yana mai duban Şarki Tarmas da Sarki Husaka yace "Ai da ganin yadda wannan manzo ya dade bai dawo ba sai yau nasan cewa Sarki Abu zaiyan yaji tsoro, tabbas ba zai yarda yayi yaki da mu ba tun yana da hankali, tunani da hangen nesa ni nasan cewa dole ya bamu mutanenmu da dukiyaoyinsu. 11 Koda jin haka sai Sarki Tarmas ta Abdul'Aziz Sani M/Gini TURBAR GASKIYA -2 Husaka suka bushed a dariyar farin ciki Sarki Husaka y ace "to aima ko ba a gwadaba linzami yafi karfin bakin Kaza ka dubi yawan akarun nan namu ka gani ta yaya za a kwatantasu da Dakarun birnin Baitul haural wadanda 'yan liken asirinmu suka ce basu fi su miliyan daya ba da doriya shi kuma sarki Tarmas sai y ace to ai koda ma yawan dakarun yakai namu.dolene mu sami nasara akansu tunda su rabonsu da yaki ankai shekaru ashirin baya. Duk manya zakakarun mayakansu wadanda suka san kan yaki sun mutu wasu kuma sun tsufa tukuf yaddama ba zasu iya fita filin daga ba. Koda jin wannan batu sai Sarki Madha ya girgiza kai yace "Ai ba anan take ba mahafina ya gaya mini cewar mutane birnin Baitul Harwal suna da zuciyar zaki wato basa gudu kuma basa ja da baya sannan sunyi imanin da ubangijinsu bisa cewar indai suna ambatonsa bakinsu sai sun sami nasara abinda 12 Abdul'Aziz Sanl M/Ginl TURBAR GASKIYA -2 suka sa agaba su dolene muyi amfani da dabarun yaki na musamman wajen ganin mun sami nasara akansu kamar irin su kai hari na mamayar bazato a. lokacin da basu taba tsammaniba amma idan mukayi la'akari da tsananin yawanmu akansu mukace ayi gaba da gaba zasu iya bamu mamaki". Koda jin haka sai Sarki Tamas da Sarki Husaka suka dubi junansu cikin alamun mamaki sannan suka dubi Sarki Madhan cikin alamun rashin gamsuwa, kafin daya daga cikinsu yace wani abu sai ga wannan manzon ya iso daf da Sarki. Da zuwansa sai ya sauko daga kan dokinsa ya zube gaban Sarki ya kwashi gaisuwa sannan ya mika masa wasika. Nan take Magatakarda ya karbi wasikar ya budeta ya shiga karantawa a fili kamar haka-: 13 Sako daga sarki Abu zaiyan na birnin Abdul'Aziz Sani M/Gini TURBAR GASKIYA -2 baitul Haural zuwa ga Sarakuna uku ma'abota jahilci da toshewar basira, koda magatakarda yazo nan akaratunsa sai Sarki madhan ya daka masa tsawa..... Magatakarda ya tsuke bakinsa ya kama karkarwa saboda tsoro Sarki Madhan Sarki Tarmas, da Sarki Husaka kuwa suka jikinsu ya kama tsuma saboda fishi zuciyoyinsu kuwa suka kama tafarfasa kamar zasu kone jin aibatawar da Sarki Abu zaiyan yayi musu kai hatta miliyoyin dakarun da suke gabansu said a suka nutsu suka shiga taitayinsu akayi tsit har izuwa tsawon 'yan dakiku sannan Sarki madhan ya baiwa Magatakardar umarnin yaci gaba da karanta wasikar hannun magatakarda yana karkarwa bakinsa na tuntuben harshe yaci gaba da karanta wasikar yace-; Yaku wadannan Kazaman Sarakuna kuyi sani cewaa komai zai faru bazan baku jama arku bad a dukiyarksu saboda sun zama 14 Abdul'Aziz Sani M/Gini TURBAR GASKIYA -2 Dakarun dake gabansa yace" Na rantse da darajar iyayena da kakanina daga cikin ku duk wanda ya saro kan Sarki Abu Zaiyaan ya kawo min sai na raba dukiyata gida biyu na bashi rabi. Koda jin haka sai gaba daya dakarun yakin suka kama ihu gami da shewa, kowa ya fara tunanin sallama ransa da lafiyarsa domin samun wanan gagarumin matsayin, nan take akakirawo Sarakan yakin kasashen uku suka gaba ta wajen su Sarki Madhan aka basu Umarni suje su fara suje su fara shrye shiryen tafiya domin a adurfafi kasar Baitul Harwal, Nan take kuwa Sarakan yakin suka bi umarnin sukab farab shiryajama'arsu. Idan mutun yaga kayan yakin da aka tanada da kuma dinbin abincin d aka taho dashi sai yayi zaton cewar wannan duniya tamu da wata duniyar daban za afafatayaki. Haka dai dawakairakuma, da alfadarai, sula dauki hanya sahu sahu zuga-zuga suka bar birnin 16 Abdul'Aziz Sani M/Gini TURBAR GASKIYA -2 Hizuba, Tawagar su Saarki Madhan ce atsakiya, Dakarun tsaro sun kewayesu ta ko ina ko tsuntsu bai isa ya gifta ta samansu ba face ma giwa, Komai dakewar zuciyar mutun da jarumtakarsa idan yaga wannan runduna dolene ya firgita domin yasan cewa duk abinda ta tunkara sai buzunsa, haka dai wannan runduna taci gaba da tafiya hart a kustsa cikin daji ta nausa sosai aka daina hangota daga birnin Hizuba. A can birnin Baitul harwal kuwa kamar yadda likita Zauwad ya tsara haka al'amarin suka kasance wato gimbiya Lushmaira da Shadilat 'yar babban attajiri agidansa suka kwana kuma shadilat tazo da ma'aikatant mazaje guda dari uku dauke da guzuri n abinci mai yawan gaske ninkin wanda zasu iya amfanin dashi sau goma sama da kwanaki ashirn, shi kansa likita yaga yawan wannan 17 Abdul'Aziz Sani M/Gini TURBAR GASKIYA -2 abinci guziri sai ya dubi Shadilat cikin tsananin mamaki ya ce "mai za ayi da wannan guzirin abinci mai yawa haka?ba kya tunanin cewa yayi yawa kuma ba kananan kudade zaki kasheba wajen tafiya da wannan kaya. Shadilat tayi murmushi tace "indai akan daukaka lamarun Allah ne banki na salwantar da duk abinda na tara", koda jin haka sai Zauwad yayi murmushi yace "Allah ya saka miki da mafi tsoka. Batare dad a 6ata lokaciba Zauwad ya nunawa kowa dakin da zai kwanta gimbiya Lushmairat da Shadilat kuwa sai ya kaisu dakin guda, Dakine yalwatacce dauke da shimfido guda biyu irin na attajirai Atsakiyar dakin daga sama jikin rufin an sakale wani dankaramin Keji mai dauke da wani dan Karamin kyakkyawan tsuntsu abin sha'awa. Shadilat da LUshmara suka je suka kwanta akan shimfidon biyun suna masu fuskantar juna. Adai dai lokacin wata kuyangar 18 Abdul'Aziz Sani M/Gini TURBAR GASKIYA -2 Likita Zauwad ta shigo cikin dakin da sallama tana dauke da faranti abinci da tambalun ruwan inibi da na ruwa, Lushmaira ta amsa mata sallamar ita kowa Kuyangar nan sai ta ajiye faranti atsakiyarsu ta fice, Fitar Kuyangar ked a wuya sai Shadilat da Lushmaira suka mike zaune a tare kamar hadin baki kowacce ta kai hannu domin ta bude kwanon abinci sai gashi kowacce ta ruke murfin kwon, Al'amarin day a basu dariya kenan suka kyakyta a atre sannan Shadilat t ace ashe dai ita yunwa bata da hankali kuma ba ayi matajuriya sai hakuri, Shammilat tayi murmushi t ace abin da kika fada gaskiya ne amma amma dai mu mutane yanzu dai muna da mutukar lalaci kuma muna da rauni zuciya shi yasa yunwar ma take galabartar damu amma bayin Allah na gari wadanda suka gabacemu kwana suke su yini da yunwar amma saboda ko yaushe tsoron Allah da gudun duniya acikin zuciyoyinsu 19 Abdul'Aziz Sani M/Gini TURBAR GASKIYA -2 yunwa batayi musu illar komai. • Lushmaira ta numfasa tace "hakane 'yar uwata amma mu dinma tamu da sauki nan gaba wadansu daruruwan shekaru da za su zo bamu san yadda zuciyoyin musulmai zasu kasance ba domin kawa dukiya da mulki zasu iya sawa su bar kan TURBAR GASKIYA sai dai kawai muyi musu fatan gafarar Allah. Shadilat tace "ameb sannan suka fara cin abinci acikin nutsuwa da kwanciyar hankali kai kace babu wata matsala atsakaninsu. Bayan sun kare cin abinci suka bude babin hira Shadilat ta dubi Lushmaira tace "yake 'yar uwata naji kince ke baki da burin day a wuce ki auri jarumin da babu kamarsa a wannan nahiya shin zaki iya gaya min dalilin da yasa kika sa wannan babban buri aranki mai wuyar kasancewa? Na yarda cewa jarumi da yafi kowa nuna jarumtaka a wannan yakin da zamu muje zaiyi suna duniya amma hakan bata nufin cewa shi ne yafi kowa jarumtaka ba 20 Abdul'Aziz Sani M/Gini TURBAR GASKIYA -2 tunda baiyi irin jarumtakar da mahaifinki yayi bat a soke idon Macjiya barukul Karsum, ina mai tabbatar miki da cewa da izinin Allah n ice wacce zata soke wannan dayan idon na macijiyar Burukul karsum kinga kowa idan na samu wannan nasara na ruguza dukkanin burinki tunda na kasance 'ya mace babu halin ki aureni. Koda Gimbiya Shadilat tazo nan azancenta sai Lushmaira ta kyalkyale da dariya har sai da kwalla ta cika mata idanu sannan nutsu ta dubi Shadilat tace "aini gidanmu kirarin sa'a ake mana tunma kafin a haifeni, ko kakana, babana da ni kaina bamu taби за wani abu a gabanmu face mun sami nasara, na gayawa Allah wannan bukata tawa tun ina yarinya karama har na girma na cika budurwa balagaggiya ban taba fashin addu'a ba dare da rana akan wannan buri nawa an sha nuna min biya bukatata a mafarki babu adadi shin kina zaton wani furuci na bil adama zai san a sare 21 Abdul'Aziz Sani M/Gini TURBAR GASKIYA -2 har na fitar da rai ga samun nasara?. Koda jin wannan batu sai Shadilat tayi wa Lushmarai murmushi t ace "tabbas na yarda kin riga ni gabatar da bukatar ki awajen Allah to amma ai naji ance shi Allah maji rokon bawansa ne a kowane lokaci kuma ako ina koda kuwa a bakin kura yake, idan Allah yaso zai iya biya mini tawa bukatar kamar yadda zai iya biya miki taki in yaso tunda arzikin sa bashi da iya in ya bamu ma atare babu abin da zai rageshi daga cikin arzikinsa ni dake duk sai mu jira loakaci domin shi ne kadai zai iya awarware mana wannan kullin dake tsakaninmu. Lokacin da Shadilat tazo nana zancenta sai jikin Lushmaira yayi sanyi tayi shiru bat ace kalaba kawai sao ta mike tsaye ta shiga kewaye tayi alwala ta dawo ta fuskanci alkibila ta fara sallar nafila itama Shadilat sai ta mike taje tayi alwalar tazo ta kama nafilar kamar masu yin gasar ibada. 22 Abdul'Aziz Sani M/Gini TURBAR GASKIYA -2 Bayan yin Sallar asuba Sai likita Zauwad tare da dukkanin tawagarsa sukayi hawa suka nufi filin fada a inda Zau hadu gaba daya kuma a inda Sarki zai hau manbari ya fara bada wannan Hikaya. Koda zuwansu sai suka ga kowa ya zo su ka dai ne basu halarci gurin ba sarki ya hau kan Mambari ya na shirin farawa dab haka su kai sauri suka karasu wajen, Awannan lokacin sarki da yarima sunyi gagarumar shigar yaki mai tsananin ban tsoro da kwarjini duk su biyun sanye da bakaken kaya na sulke rigar karfe gami wandon karfe kuma sun rataya zabgegeyar takubba a bayansu, A wannan lokaci yarima ya tattare gashin kansa ya daureshi ya zuba a gadon bayansa har izuwa kasan kafadunsa. Nan fa kyawunsa da shigar da yayi suka ribaci zuciyoyin Lushmairat da Shadilat, take kowacce taji ya burgeta ainun amma sai suka kasa tantance irin bugewar acikin zukatansu shin burgewa c eta kamau da 23 Abdul'Aziz Sani M/Gini TURBAR GASKIYA -2 sonsa ko kuwa rudewa ta kyan adon da yayi amsar da suka kasa baiwa kansu kenan. Nan kowa ya dukafa yana jin amon muryar sarki cikin tattausar murya. Acikin wannanlabarin d azan baku a halin yanzu kafin mu fara yin tattaki izuwa wannan gagarumamin yaki lallai ina mai umartarku da ku nutsu ku saurari wannan labari kasancewar aduk lokacin da irin wannan ta tashi acikin wannan birnin namu mai tarin albarka Idan za a tafi yaki duk wanda ya samu shugaba awannan lokacin yakan kasance yana mai tausar dakarunsa da Kara musu karfin gwiwa gami da abinda yake gabanmu da wannan dama ne Sauran sarakan da suka gabata suke bada tahirin Annabawa ko kissoshi daga irin Kissar ma aiki dan muuyi kuyi da juriya da kuma dadurcewa afilin daga, wasu kuma sarajan suna bada tarihin wasu jarummai dan suka rike amana juna ko wasu sarakai da 24 Abdul'Aziz Sani M/Gini TURBAR GASKIYA -2 suka bata da kuma yanda karshensu ya zo to ayau dai, zan gabatar da wani labara gareku mai nuni da rikon amana da kuma dadrucewa awajen ganin ka samu nasara a duk inda ka dosa, musamman ko dan jimawar da mukayi bamu fita filin daga ba sai ku saurara kuji wannnalabari wand azan baku hi a yanzu kafin wayewar gari, Acan wata daula baya da shekaru ashirin da bakwai baya anyi wani attajirin kuma hamshakin Karkarfan Sarki wanda yake mulkin kasar Garzab ana kiransa da suna Muhuddu ibn Asar, shi dai wannan Sarki ya kasance musulmi kuma mai tsananin kaunar musulunci da ci gabansa, wannan daliline yasa ya tsaurara ra ayi akan adanninm musulunci har yazamana idan akwai tarin laifika da idan mutun ya aikata na sabon Allah ya tanadar maka iziya mai tsananin wanda uban gijinmu bai tsaurarawa bayinsa kamarsa ba domin shi ko sata aka kama kayi sai an fille maka kayi idan kowa 25 Abdul'Aziz Sani M/Gini TURBAR GASKIYA -2 zina kayi sai yasa an tsire ka kuma an kama iyalanka an tafi dasu izuwa wata fursuna inda anan ne zasu Kare rayuwarsu. Wannan Sarki manyan malamai masana Addini musulunci sunyi kokarin gaske awannan lokacin akan ganin sun ganar dashi gaskiya dan bazab manta ba mahaifina ya taba bani labarin cewa har sai da kakana wato baban mahaifina ya so ya yakeshi, duniya ta hana saboda ana ganin musulmine kuma mai bada gudunmawa akan wannan addininmu idan aka yaki shi baza aci nasara akanshi ba kuma anyi wa musulunci mummunan 6arna da domin a Nahiyar da yake kasar sa ce kawai kasar Muslul mai dan haka sai aka kyaleshi aka dinga tura masa da malamai ta karashin kasa dan su ganar das hi gaskiyar lamarin amma fafu yake daukar abinda suke gaya masa. Da haka aka zuba masa idanu dadintama jama'ar Kasarsa basu fiya aikata laifiba sai yazaman hukunci shi yafi yinshi akan kafurai masu 26 Abdul'Aziz Sani M/Gini TURBAR GASKIYA -2 zuwa kasarsa yin kasuwanci ko kuma yin wani abun daban, Sai yazamana duk wanda yazo kasar yayi wani addin daban to babu shakka sai yasa an fille mishi kai da wannan aka samu dan sauki tunda jama'arsa sun yarda kuma suna kiyayewa. Shi dai wannan Sarki dan sa guda daya ne Wato Arfan, kamar yanda Sarki yazama gagara badau ta fannin Sadaukantaka sai ya zamana Aufan shima aduk cikar birnin da batsewarsa babu wanda yake iya koda wasa jini dashi saboda gudun kada ya wahalar da kai face Ansaru ibin Tamkar, Ansaru Abokine ga Aufan wanda su dukan Suka koya horarwa daga wajen Sarki Muhaddud tun suna yara suka taso ta babu wani abu day a taba shiga tsakaninsu koda wasa wanda zai sosa zuciyar dayansu da yake shi Ansaru ya taso ne daga cikin gidan maraya ne bashi da iyaye tun yana karami iyayensa suka rasa rayuwarsu, dan haka 27 Abdul'Aziz Sani M/Gini TURBAR GASKIYA -2 komai Sarki idan zaiwa Arfan tare yake musu yana kaunar Ansaru kamar yanda yake kaunar Arfan, Shi idan ubangiji idan ya kawo gyara babu ta inda baya bayyanar da hanyarsa dan daidaita tsakanin al'umma da shuwagabaninsa, Lokacin da Ansaru ya zama babban Sadauki acikin wannan masarauta ya zamana sewa shi da Arfan sun zama man yan zakuna aduk nahiyar wannan kasa baki daya, Sai yazamana Ansaru ya kasance cikin bakin cikin irin yanda sarki yake tafiyar da mulkinsa a duk ilimin day a koya daga gurarin malamai da yawa bai taba cin karo da inda Allah (S.W.T) ya bawa wani bawansa dammar yin hukunci irin wanda wannan Sarki yake, Dan haka sai ya tafi izuwa ga Sarki har cikin turakarsa ya sameshi a zaune ya gaisheshi sannan ya dubi shi cikin ladabi da biyaya cikin murya atausashi ya ce "Ya abbana wata 28 Abdul'Aziz Sani M/Gini TURBAR GASKIYA -2 muhimmiyar Magana ce na zo da ita gareka kuma ina son ka karbeta kuma kayi aiki da ita domin kaucewa fushin ubangiji da samun nutsuwa ga wannan addini namu na musulunci wanda shugabanmu Annabi mohd yake jagoranta," Koda jin wannan batu daga bakin Ansaru sai ran Sarki ya fara 6aci domin ya san cewar karshen zancen domin shi kansa yasan cewar tunda yaron ya fara neman ilimi sai watarana yazo ma sa da zance makamancin haka, don haka cikin nuna bacin rai ya dubi Ansaru yace "zan saurareka idan har maganarka baza ta zo daya da manyan malamai suka sha sanar da niba sai dai kuma zan gargadeka akan cewar idan har kasan wannan Magana tayi kamancеce niya da irn kalamansu to kayi gaggawar barin wannan guri ko kaifin takobina ta ratsa jini da tsokar ka alokacin da ba ka zaci haka ba" Tun tasuwar Anwaru ya kasance mutun mai tsananin taurin kai da nuna isa awajen da 29 Abdul'Aziz Sani M/Gini TURBAR GASKIYA -2 aka ce wani ya sabawa mahaliccinsa ko waye sai ya gaya masa Magana koda zai rasa ransa dan haka sai yayi murmushi ya kara duban Sarki akaro na biyu, ya ce "yakai mahaifna umarnin Allah zan sanar da kai ba umarni ba kuma idan zan fadi umarnin Allah bana bukatar ace sai na tsira da rayuwata, tabbas koda zaka kasheni sai na sanar da kai" koda yazo nan azancensa bai yi aune ba sai jin hucin takobi yayi ta nufo kanshi da niyar za asare kanshi, cikin tsananin zafin nama ya rike kaifin takobin batare day a ko daga kai ya kale Sarki ba ya ci gaba da cewa "kabi turbar da ubangijinmu ya umarcemu da shuwagabannin su ladaftar da al'umarsu kana izaya da wuta face babu wanda yake wannan face Allah mahaliccinmu kana kasha rai aka aikin da ubangiji bai bamu umarnin kisa ba kana yanke hukunci akan musulmai wanda hakan zai sa dayawan kafurai su ji tsoron shiga cikin wannan addininmuidan har ka sake ka mutu a 30 Abdul'Aziz Sani M/Gini TURBAR GASKIYA -2 haka to na tabbata ba kai ba rahamar ubangiji ka daina ganin wannan yawan ibadun da kake yi zasu fisheka idan har akwai hakkin wani akanka dan haka ka tsayar da wannan dokokina naka dan ba na Allah bane," cikin tsananin fusata Sarki ya kwarara wani uban iho ya sake takobin wanda jinin jikin Ansaru ya mai da ta ja ta rine da sauran gurin da jininsa yake kwarara. Ya nufi jikin bangon dakinsa ya dauko wata falleliyar takobi guda ya ja daga ya ce "Ganin isa yasa kake wannan dagiya agareni yau zan tabbatar maka da cewa tsofana bai tafi da juramtata ba don haka ka rike takobin hannunka yanzu ni da kai gawar dayanmu cе zata fita daga cikin wannan turaka idan kuwa ba haka sai na sa an kama an azabtar da kai mafi munin azaba waninka bai taba gani ba" Koda Ansaru yaji wannan batu sai hawaye suka zubu daga idanuwansa jikinsa yayi sanyi ya sunkuyar da kansa kasa yana mai 31 Abdul'Aziz Sani M/Gini TURBAR GASKIYA -2 sheshshekar yin kuka, Sarki na tsaye yana jiran yaga ya dauki wannan takobi sai yaga shi cikin wannan hali koda faruwar hakan sai shima sarki jikinsa yayi sanyi kuma ya kamu da tsananin mamaki ya dubi Ansaru cikin sanyin murya, y ace dashi "tun kana karamin ka taurin kai yake dawaniya da kai ya kai wannan da nawa banda abinka ina kai ina kawo min wannna bataccen zace ina so kayi sani shi ilimi ilimine a wani lokacin mutane suna fassara alkur ani a wata fassarar daban dan haka ka kiyaye na yafe ka ka tafi" Koda jin wannan zance na Sarki sai Ansaru ya yi taku bakwai acikin falon sarki wanda shi ne ya kaishi har izuwa bakin kofar fita said a ya je wannan gurin sannan ya juo ya dubi sarki ya'ce "hakika kayi nisa da yin kira agareka zai zama 6ata lokaci dan haka ina son kasani daga wannan ran azan bar maka wannan gida naka na tafi can wani gurin inda zanci gaba da rayuwata cikin rainon muluncin da 32 Abdul'Aziz Sa TURBAR GASKIYA -2 yanda manzon shugabanmu ya koyar. Amma ina mai sanar da kai daga bari na wannan kasa zuwa kwanaki ashirin masifa zata sauka acikin C birininka wanda za a rasa hanyar maganceta zai zamana idan baka aminta ta dadi rai ba zaka aminta ta wahala, sannan ina mai rukonka akan kada ka sanar da Aufan cewar munyi Magana da kai maka manciyar irin wanda mukayi yanzu da kai domin ni kaina da badan hurumin Allah da ka taba babu dalilin da zaisa nayi maka gardama har takai ranka ya baci saboda bani da wani uba face kai kuma bani da wata uwa face kai, Koda yazo nan azancensa sai ya sa kai ya fuce idanuwansa na masu zubar hawaye Sarki Muhadud ya tsaya ya bishi da kallo cikin takaicı nan take kuma sai wani tunanin ya fado masa koda yin wannan tunanın sai ya kira wani hadimansa yayi masa umarni da yake gidan sarkın yaki Asbasya sanar dasni cewa yana mai 33 Abdul'Aziz Sani M/Gini TURBAR GASKIYA -2 S- AYIНГА ЯАДИТ kiran gaggawa. sy unsdsgudг поsпв sbnEV tennow sir ind sgeb is sh se is Nan take wannan hadimi ya tafi yaje ya sanar da Sarkin yaki Asbaz kafin ma hadiman ya koma gida tuni Sarkin yakin ya iso cikin bin umarnin Sarki koda zuwan sai saarki yaja shi izuwa cikin turakarsa suka kebance nan take ya MC SIA БО ТБПS2 БК EDEX USKS shada,masa cewar yana son duk yanda zasu kada su bar Ansaru ya bar wannan garin su je su kamashi su kaishi kurk goinyana kurkuku kyautata zaton ya samu matsala 2. 60 Hing i ivea b ine Aikuwa kafin wani. yunkuri na sarkin yaki tuni Ansaru ya baci daga cikin birnin an EIR eCSI BWU BI rasa kuma ta inda yabi domin masu tsaron 29ε gyeuconρς USD. λSNO κοσς kofar birnin sunce basu ganshi yazo ya wuce ba koda faruwar wannan abu, sai aka, shigi 129di 5 Mb 25LK cikin mamaki.Aufan ya shiga neman abokinsa 2SP KAB ISKC USU KSICI Ansaru har ya gaji bai ganshi ba kuma da ya nςικς migs y kogς usas sanar da mahaifinsa sai ya ce"aishim nemansa Acas yake kuma ya shiga, wani hali, na rashinsa dan haka sai aka koma nemanshi 34 insd zisA'lubdAbdul'Aziz Sani M/Gini TURBAR GASKIYA -2 asirrance batare da an gano inda yake ba da wannan hali har akwa kwashe kwanaki goma sha takwas daga nan kuma sai

Chapter 4 of 11