Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
5 / 11
Sarki ya zuba idanu ya sa aka zuba dakarun tsaron ako ina cikin wannan birnin ana mai tabbatar da tsaro amma kuwa dake cikin wannan birnin bai san dalilin da yasa aka sa wannan tsaro ba, dan Sarki ku Sarki yaki bai sanar dashi wannan dalili ba, Da dansa Arfan ya tambayeshi dalili sai yace akwai dalilin yin hakan idan abun ya bayyana zaka gani" da wannan koya ya samu kansa cikin shakkar zamansa ko ina acikin kasar. A haka kwanaki ashirin day a Ansaru ya furta cewa masifa zata fara kankama acikin wannan kasa, dan haka sai tsaron yafi na koyaushi kuma hankalin Sarki ya gaza kwanciya gaba daya rana har akayi sallar magriba babu abinda ya faru a wannan lokacin sarki ya fara ganin cewa kawai Ansaru ya fad wannan maganane dan ya tsaoratar da ni dan 35 Abdul'Aziz Sani M/Gini TURBAR GASKIYA -2 haka sai hankalinsa ya fara kwanciya. Misalin karfe goma na dare labari ya isarwa Sarki cewa anzo cikin garinsa duk masu gadin kofar shigowa an yakesu an fatattake wasu wasu kuma sun sha da kyar. Koda jin wannan batu sai hankalin sarki ya tashi zumbur ya mike daga kan gadonsa na mulki ya fito waje ya tsaya ya kuma umarce da akawo masa dakarun da suka sha kyar,? Nan da nan aka gabato dasu gaban Sarki ya zuba musu idanu daga bisani sai ya dubi daya daga cikinsu yace "yakai wannan badakaren ko zaka iya sanar dani abinda ya faru daku a halin kuna zaune abakin kofar wannan birni namu" Badakaren ya daga kai gami da numfasawa yace "ranka ya dade kware zan iya sanar da kai iya abinda ya faru damu a halinmu na shiga cikin wannan hali, muna zaune kamar yanda muka saba idan dare yayi mukan kunna wuta dan mu ji dimi haka kuma muna hirarmu 36 Abdul'Aziz Sani M/Gini TURBAR GASKIYA -2 tare da kula da aiyukanmu muna cikin hakan kwatsam sai muka ga wani mahayi bisa doki ya fito daga cikin gari fuskarsa arufe da wani jan mayafi hannunsa rike da wata sharbebiyar takobi koda yazu inda muke cikin mamakinmu mu azatonmu ko wani dan aikine daga cikin gari kawai sai ya sauka daga kan dokinsa ya kuma rataye takobinsa ajikin dokinsa ya nufo mu cikin wata iriyar guguwar bala'I domin a yanda ya nufo mu mu a zatonmu bashi bane iska c eta biyo ta bayansa ta kawo mana hari sai kawai muka ji duka babu kaukautawa cikin tsananin zafin nama saboda tsananin razana babu iya daukar makamanmu ba sai muka shiga kare kanmu wasunmu kuma suka ruga suka tsallake katangu suka haure duk kuwa da cewar katangar wannan birnin tafi gaban mutun ya haureta amma sai gamu muna tsare kama Katanga wanda sukayi kokarin kare kansu kowa suna can sun samu raunika saboda azabar da suka sha awajen wannan mahayin 37 Abdul'Aziz Sani M/Gini TURBAR GASKIYA -2 dokin daga karshe kuma ya gargadesu da cewar gobe idan ya dawo yaga dayasu to da takobi zai yakemu kuma sai ya kasha dukkaninmu, sun ce yana gama fadin hakan ya koma yah aye kan dokinsa ya dawo cikin wannan gari. Koda Sarki yaji wannan al'amari sai ya shiga cikin wani irn hali na damuwa yayi shiru na dan tsawan lokaci daga bisa ni sai ya dago kai ya ce ya dubi Sarkin yakin Asbaz yace "gobe ka je ka zauna abakin wannan kofar birnin kaida jama'arka sannan kayi dabarar da zaka kamamin wannan mahayin dokin araye ba a mace ba.kazo dashi izuwa cikin wannan turakatawa da kaina zan hukantashi. Koda Sarkin yaki Asbaz yaji wannan sai yai gaisu ga Sarki ya kuma nufi kofar fita daga cikin gidan. Washe gari kowa alokacin da jama'a suka kasance cikin cin kasuwancinsu anata hada-hada kwatsam ba sai ganin wasu dawakai 38 Abdul'Aziz Sani M/Gini TURBAR GASKIYA -2 SAYDIАД ЯАДЯТ akai guda hudu bassun shigo cikin kasuwa acikin masifaffanngudu hannayensu dauke da taköbil tsirara kai tsaye saijsuka jufin rumfunar Sarkin garin suka ifara bari da kayan shaguwa wanda: damaenlayiulguda no duk masarki Mahaddad ne manrda nan suka tashi layin pikia dam kankanini lokaci kasuwar ta rude hankulan mutane syasadügunzumawakaltinka BHÍALBAİS gami da iface iface, kafin kace kwabo luni an korivnskowasndake arkasuwari sainswadannN mahayan guda hudui bisa dawakai ana cikin wannan abuner sairga wasu Dakarunan sa dasvun arba'in bisa dawakai sunnufu sikiД kasuwar asukwaned ridio ageb soad sala is Koda wadannan mahayan suka wadannan Dakaru sais u dukaisukadsaya kuma sukais gyaration takobbansu 2 SURAI TIR wadannan idakanu, koda eisuwar dakarun suka bnufo su idaltiyarnsuw yakes28 ik tsanánin fusata daya daga oikin Mahayan yayi fitar burgu cikinsud cikin matsanencin gud 39 inGAM inse sisA'luhAbdul'Aziz Sani M/Gini OA TURBAR GASKIYA -2 tamkar guguwa ya fara ragargazassu, idan kaga yanda yake fada dasu kai kace basu hororwa yake domin baya bari ya samu su kaifin takobinsa sai dai kotar takobinsa baya bugunsu a makasa sai dai dai duk fuskokinsu sun wulakanta domin yayi musu munanan rauninka duk yawansu sai suka zama na banza domin dukkaninsu sai sukai wanwar a kasa daga mai dafe kunci sai mai dafe kogu sai mai dafe kai ko rike hannu, koda gama yi musu wannan aika aika sai ya zaburi dokinsa saura suka rufa masa baya cikin tashin kora suka bar gurin dukkaninsu fukokinsu arufe suke da jan mayafi bat suka 6ace daga cikin birnin aka nemesu sama ko kasa aka rasa Alokacin da Sarki yazo ya ga barnar da akayi masa sai hankalinsa ya dugunzuma ainun har wata kwalla ta fito masa daga cikin idanuwansa, a wannan lokaci sai ga dansa Arfan tare da hadimasa a baya suma sun shigo cikin kasuwar, cike da bakin cikin faruwar 40 Abdul'Aziz Sani M/Gini TURBAR GASKIYA -2 wannan al'amari, Arfan yana zuwa gaba mahaifnsa sai yaga wannan kwalla da take duga daga idanun mahaifinsa nan da nan hankalinsa ya tashi ya dubi mahaifinsa yace "ya abbana ya kake zargi da yin wannan mummunan aiki ga dukiyarka wa kake zargi da 6arnatar da wasu daga cikin dakarun ka, lallai nayi imani da Allah day a halicceni idan kayi mini izinin neman wannan la'antaccen makiyan naka sai na kamo maka shi har gabanka aduk irin yanayin da kake muradi ya mhaifina kayi mini lamuni daga wannan sa'ili na tafi izuwa neman wannan kaskantaccen bawanka ko amace ko araye, Sarki Muhadda ya daga da kai ya dubi dan nasa kana ya sunkuyar da kansa kasa, tabbas yasan cewa yarima Arfan zai iya duk yanda zai yi ya gano wanda yake yin wannan aika aikar amma sai dai da ranar da yaga cewar amininsa ne kuma shakikinsane da yin wannan dan yan aiki to ya tabbata ba zai iya kama su 41 Abdul'Aziz Sani M/Gini TURBAR GASKIYA -2 ba kuma koda ya gano shi to babu makawa rabuwarsa da dan nasa ya zo domin Ansaru yana da hujjujin da zaiyi amfani dasu dan yajenye dansa yabi shi su hada kai domin sanin cewa shakuwar da ke tsakanin Arfan da Ansaru bata tsakanin sa dashi koda ma akwai haka azcuiyarsa yasan cewar dan nasa ma yana adawa da irn mulkin da yake gudanarwa akasarsa na tilastawa da yin dole ga bin addinin musulunci wanda tun shekaru masu yawa malamai masu ilimin suke son ganin sun kure wannan 6arna daga kasar sa amma sun kasa, dan haka sai ya kara dagowa akaro na biyu ya dubi Arfan yace "Ka kwantar da hankalinka ya kai dana abin muradina ba kada ka damu kanka da wannan aikin kafi karfinsa bazai yiwu na saka acikinsa ba tunda ba yaki bane da zamu tunkari rundunar mayaka miliyan dubu dan haka ka kwantar da hankalinka Sarki yaki ya zuba matakan tsaro dan binki tamana wadanda suke 42 Abdul'Aziz Sani M/Gini TURBAR GASKIYA -2 mana mummunan ta addanci, Koda Sarki yazo na azancensa sai yarima Arfan ya dago ya dubi sarki cikin alamun gamsuwa kana y ace " ya abbana ya maganar binkicin da akiyi gami da bata dan uwa Ansaru sanin kankane idan har rayuwa taa ci gaba da tafiya batare da Ansaru akusa dani ba tabbas zan iya rasa rayuwata dan haka ina son ka bar ni nayi tattaki izuwa makobtaka wannan yanki dan gano inda yake, Koda Sarki yaji wannan batu daga bakin dan sa sai yayi tunanin mai zurfi daga bisani ya dago kai ya ce nayi maka izini ka tafi har tsawan kwanaki goma neman Dan uwanka Arsaru kuma ka tafi nan da kwanaki uku masu zuwa, ba wani tunanin sarki yayi bay a bar yarima ya tafi neman Arsaru said an kawai yasan cewa Ansaru yana cikin kasar nan yayi hakane domin yarima yayi nesa dashi dan gudun kada watarana Arfan su hadu da dan uwan nasa tabbas duk alokacin da suka hadu 43 Abdul'Aziz Sani M/Gini TURBAR GASKIYA -2 sai ya shaidashi musamman idan suka gaba da gaba da fara yin Artabu wanda kuma indai Arfan yana cikin birnin watarana zai je kai dauki ga gurin da yaji sanarwar Ansaru ya kai farmaki dan haka yayi wannan dabara yasan cewar kafin cikin kwanaki goma sha uku sai an ZO י Ansaru" ma da Da wannan Sarki ya koma gida tare da zugarsa shi ma Yarima ya tafi gida cikin takaicin wannan mummunan abinda yake faruwa amma sai ya bari azuciyarsa kafin ya bar birninsu sai ya fara dan yin bincike akan wannan lamari. Washe gari tun sassafe labara yaje wa Sarki cewar an sace wani babban limamin garin sannan an rushe wani gidan gonarsa gaba daya tare da tafiya da amfanin gidan gonar duka, sannnan awannan karan ansanar das hi cewar wadanda sukayi wannan 6arnar suna da yawan gaske dan akalla zasu kai sama da mutun arba'in sannan kuma suna rike da tutar 44 Abdul'Aziz Sani M/Gini TURBAR GASKIYA -2 musulunci a hannunsu basa kisa basa tabа kayan kowa face kayan da wannan masarauta ta tanadar. Lokacin da Sarki Muhadud yaji wannan batu sai da yayi shiru na wasu lukuta sannan ya dawo daga duniyar tunaninsa ya dubi dakarun da suka kawo masa wannan labara y ace "ku je ku sanar da Sarki yaki Asbaz ina nemanshi yanzu kuma ya sameni anan fada kafin na tafi cikin gida ya kuma waigawa gefensa ya ce da Wazirinsa da galidima koma idan da wanda yake da uzuri yanzu ya kamata ace yaje yayi domin dole zamuyi zama na musamman mu hudu galadima waziri tare da ni Da Sarkin yaki, Koda suka ji wannan sai suka jinjina atare suka ce da sarki babu wani uziri da muke dashi ayanzu face wanda zai tabbata anan dan haka aje akera Sarkin yakin muna nan muna jira. 45 Suna nan zaman jiran Sarkin yaki sai ga Abdul'Aziz Sani M/Gini TURBAR GASKIYA -2 Badakaren da Sarkin ya aika tare da wasu manyan yara Sarkin yaki sun s shigo cikin fadar hankalinsu tashe, Koda isowarsu sai suka zube suka bada gaisuwa ga Sarki suka kuma mike zaune daya daga cikinsu kamar yayi kuka saboda tsabar takaici ya dubi sarki yace "ya shugabana kayi sani cewa ayanzu haka Sarki yaki bamu san inda yake domin a dasu da safiyar yau muna zaune a bakin kofar wannan gari da tabbatar da tsaro kofar shigowa cikin wannan birnin sai ga mahaya dawakai daga cikin garin nan fuskokinsu arufe babu inda kake gani ajikinsu face idanuwansu sun kai kimanin arba 'in da doriya, koda muka gansu duk sai muka tabbatar da cewar wadannan makiya namu ne wanda suke ta fama 6arnatar mana da dukiyoyinmu suka kawo mana farmaki. Koda shugabanmu sarkin yaki yaga wannan abu sai ya zare takobi shi kadai ya kuma fito gabanmu ya tsaya, bisa mamakinmu 46 Abdul'Aziz Sani M/Gini TURBAR GASKIYA -2 sai wani daga cikinwadan nan mahaya shima ya fito daga cikinsu ya shiga gabansu ya tsaya kekam, tamkar gunki yana ruke da takobi wannan abu shi ya fusata Sarikin yaki yayi gurnaninsa na mazaje yace da wannan mahayin, Kayi gagganci babban da ka baiyana agabana ayanzu domin na tabbata duk burin da kake dauke dashi daga wannan rana yak au domin a yanzu ne zan yake ka kai da sauran mabiyanka kuma na tusa kiyarka izuwa gidan Sarki dan cikin umarninsa" Koda Sarkin Yaki yazo nan azancensa sai wannan mahayin dokin ya tuntsire da dariya, daga bisa kuma ya turbune fuska yace "daga yaune zan cika kaso biyu na daga cikin abinda na sa agaba na maid a baki daya jarumar garin nan su zami suna tare da ni kuma babu gudu babu ja da baya tun da ayanzu nayi nasara mallakar jarumai sama da arba'in acikin wannan tafiya tawa tabbas a yau zan tafi da kai 47 Abdul'Aziz Sani M/Gini TURBAR GASKIYA -2 bisa kafadata bayan na sagarmaka da duk wata mamaro sannan na tafi da kai, Na tabbata daga wannan rana kai ma zaka zama makiyin sarki kamar yadda 'yan dukkanin wadanan mutane suka zama makiyansa badan kuma basa sanshi ba sai dan kawai rikon na addinin gaskiya da son abi hanyar gaskiya a acikin wannan birnin". Koda yazo nan azancensa sai Sarki yaki yayi kururuwa yayi kan wannan mahayin cikin tsannanin fusata nan suka hau sara da suka babu kakkautawa nan muka zuba musu idanu muna kallo wannan artabun wanda yasa muka manta da cewar wannan fa makiyane ga sarki wanda kuma ake nema dan ayi masa hukunci sai muka shiga kauyenci ganin im yanda yake yaki tamkar jarumi da yafi ko wane jarumi jarumta aduniya duk da cewar Sarkin yaki ya tbuka abin azo agani sai ya zamana ya zama rago domin yanda wannan mahayi yake yakarsa kai kace yana yaki ne da dabbar ta 48 Abdul'Aziz Sani M/Gini TURBAR GASKIYA -2 yake son yaga ta samu sannan ya dauketa ya yanka ta said a ya zamana ya daga Sarkin yaki sau uku yana bugawa da kasa kuma wani abin mamaki tun da aka fara fadan sai ya ajiye. tabkobinsa, da aka dauke dakika goma ana wannan fadan bayan Sarkin yaki yasha kayi sai uku sai muka yunkura domin mu shiga mu kwace sarkin yaki domin ya galabaita ainun, sai saurn wadannan dakarun suka rufar mana babu ji babu gani suna duka itakaice maka wadannan mahayan basu bar wannan guriba har sai suka ga mun gudu da kafarmu wasu kuma daga cikinmu suka kamasu suka tafi dasu acikinsu hard a Sarkin yaki wanda ya kasance akan kafadar wannan shugaban mahayan mai rufaffiyar fuska. Koda wannan mahayin yazo nan labarinsa sai sarkin Muhaddun yayi wani irn iho mai firgitarwa hankalin gaba daya mutanan da suke gurin ya tashi ainun daga nan kuma sai Sarki ya dubi wadanan dakaru yayi musu 49 Abdul'Aziz Sani M/Gini TURBAR GASKIYA -2 umarni dasu tashi su tafi kuma su sanar da kowa kada wanda ya zo fada a halin yanzu suka tashi dan bin umarninsa suka bar wannan guri koda suka tashi sai ya maida kansa ga Waziri da kuma galadima yace "tashin hankali da gaskie ya tunkaro wannan kasa tamu kuma duk halin da muke cikin a yanzu kun ji dalilinsa ayanzu sai dai ina so na kara muku baya ni akan wanda yake mana wannan mugun ta annacin wanda ba kowa bane face Sadauki Ansaru wanda kafin lokacin sai da ya sanar dani cewar idan har ban janye wannan munanan aiyuka da nake yi acikin kasata ba lallai sai masifa ta rufe mu mun rasa inda zamu tsira daga dukkan alamu haka ta fara bayyana tun gashí ya tafi da sarkin yaki kuma sanin kanku ne a yanzu idan ba Ansaru ba ko dana Arfan ko shi sarkin yaki Azbas bamu da wasu Sadaukai da ake shayinsu acikin wannan kasa domin ni yanzu tsufa yazo mini bani da wani kuzari d tabbata 50 azan iya yaki dashi dan na Abdul'Aziz Sani M/Gini TURBAR GASKIYA -2 Ansaru zai iya bani kunya wanda zai iya yaki dashi shi ne Arfan har ya iya samun nasara kanshi amma kuma bana son suyi gaba da gaba dan na tabbata idan ya jashi shima shi kenan sai dai mu hakura mubishi kamar yanda yake so muyi asara irin makodan dukiyar da kasar Assasunnufur suke bamu na tallafi wato kasar yahudawa wanda da wannan dukiyane kadai muka tara dukiyar da aduk wannan nahiyar babu wanda yake da mallakin koda kaso daya daga cikin kasu goma wannan sirrin mune mu uku nan babu wanda ya sani dan haka sai mu nemi mafuta yanda zamu magance wannan matsala dan haka na taraku anan da naso asanar da Sarkin yaki ne dan mu kara samun karowa dan tsaro yafi yawa acikin lamuran nan amma tunda haka ta faru dashi sai muyi saurin yanke shawara atsakaninmu Koda yazo nan azancensa sai duk su dukan sukayi shiru na dan lokaci, Galadima ya gyaran murya yace "wannnan abu shi ake kira 51 Abdul'Aziz Sani M/Gini TURBAR GASKIYA -2 sarkakiya kuma dole bazamu ci gaba da rayuwar da ta bakunce mu ba kuma baza mu yarda kasar Assasunnurfur su janye tallafin da suke bamu ba illa kawai mu shirya makarkashi ga Shi Sadauki Ansaru na nuna cewa mun janye wannan dakokin da ake ammafani dasu acikin wannan Kasa munan cewar yafi mu gaskiya daga wannan lokaci sai musa akamashi bayan ya bayyana kanshi idan kun aminta da wannan shawara to babu shakka zamu iya cimma nasara idan kuma akwai wanda yake da wanda tafi wannan sai ya sanar da ita mu ji". Waziri yayi murmushi yace hakika ka kawo shawara amma sai dai ina son ku sani cewar a halin yanzu Ansaru ba zai yarda ya sake jiki damu koda an kamashi an daure muka dawo da wannan dokoki za akara zamu 'yan tawaye daga cikin wannan birnin fiye da na yanzu aciki ina kyutata zato Yarima Arfan ya shiga ciki kuma sai sun futo da Ansaru daga cikin wannan kurkuku da zamu kaishi kunga 52 Abdul'Aziz Sani M/Gini TURBAR GASKIYA -2 kenan idan aka samu wannan rarrabuwar zai kasance za ayi yaki ne mu dasu abinda nake so muyi shi ne mu ci gaba da da awar cewar duk wannan dokoki daga da suke faru daga fadar Allah s(S.A.T) suke sannan mu je izuwa babban gidan littatfan Allah da manzonsa acikin wannan Kasa tamu mu konesu mu yi tattaki izuwa Kasar Assasnunufuf don su juwar da zancinkan Allah na wannan littafi ya dawo izuwa iri daya ga littattafan mu idan yaso sai mu mu nemi taimakon Dakarun yaki daga kasashen da suka daure mana gindi dan su zo sukawo mana tallafi mu murkoshe wannan Sadaukin yaron kun ga she kenan koda bayan ranmu a haka za aci gaba da tafiya batare da asirinmu ya tuno ba, Koda a Sarki Abu zaiyan yazo nan labarinsa sai yayi kabbara sau uku jama'ar dake gurin sai suma suka kaure da kabbara sannań aka ci gaba da ti da wadannan shuwagabannin hawaye fce face afuskarsa ya 53 Abdul'Aziz Sani M/Gini TURBAR GASKIYA -2 ci gaba da bada labarin Koda suka ji wannan shawara sai sukayi imani da ita suka kuma yarda sannan waziri ya kara da cewar yana da kyau a yau Ka shirya danka ya bar wannan garin dan mu yi shirin cikin nutsuwa da kwanciyar hankali. Sarki yace ai dama munyi dashi ayau zai bar wannan gari domin tafiya neman Ansaru dan ban sanar dashi ba abinda ya faru tsakaninmu ba kun ga kenan faduwa tazo dai dai da zama. Da wammam wadammma shugabanni suka tashi taga wannan taron Sarki yaje gida ya sukayi sallama da dansa Arfan ya hadashi da dakarun 'yan rakiya mutun ashirn da biyu Lokacin da Arfan ya nufi hanyar fita daga cikin birninsu sai ya yi sha awar ya shiga cikin kasuwa ya danyi siyayya kai tsaye sai yayiwa 'yan rakiya Magana akan su je kasuwa dan haka sai suka huya suka nufi kasuuwar garin da zuwansu sai Arfan ya shiga siyayyan 54 Abdul'Aziz Sani M/Gini TURBAR GASKIYA -2 abubuwan da yake da bukata wanda yake son ya tafi dashi yana cikin wannan siyayyane sai ya hange Huwailat ta nufoshi da kunshi kayanta a hannu idanuwanta na zubar da hawaye, Ita dai Huwailat wata kyakkyawar budurwa ce wanda suka taso tun yarinta cikin tsananin son juna ta da Ansaru dalili kuwa tare da Ansaru sukay zaman maraici agidan Sarki dukkaninsu basu da iyaye Arfan shi yake taimaka musu da kuma mahaifinsa wato sarki Muhadudu tun za ilin da ta nemi Ansaru ta rasa hankalinta ya tashi ainun dan haka kullum dare da rana sai ta zubar da hawaye n abkin cikin rabowar ta Ansaru kuma ta ji labarin cewa yarima Arfan zai je dan nemo shi wannan daliline yasa ta biyo bayanshi dan yi masa rakiya. Koda ta karaso inda Arfan yake sai ta dubeshi ta yi masa gaisu ta kuma ce dashi "ya babban abokin amini'na hakika ban ziya jure 55 Abdul'Aziz Sani M/Gini TURBAR GASKIYA -2 rashin ganinka ko ANsaru acikin wannan kasa ba domin kai daya ne kake sharemin hawayen rabowata dashi dan haka na yanke shawara nabi bayanka dan na tayaka neman masoyina aduk inda yake kuma komai ruwa komai iska, ina mai neman yardarka idan kwa har kaki amincemi na tabbata zuciyata baza ta ci gaba da zama jiranku ba dole ne nima na tafi nemansa a duk inda yake. Har Yarima ya bude baki zai yi mata Magana kenan sai kawai ya hango taron jama'a daga nesa suna ta faman rubdugu aguri daya koda ganin wannan abun sai ya tura dakarunsa dan gane masa abinda yake faruwa. Batare da 6ata lokaci dakaru biyu suka ji gurin suka karbi abinda jama'a ke dubawa ba komai bane face wani Sako arubuce, koda ganin haka sai suka garzayo suka kawowa yarima wanan takarda. Yarima ya karba ya fara karantawa afili kowa yana ji abin dake kunshi cikinta, 56 Abdul'Aziz Sani M/Gini TURBAR GASKIYA -2 Jama'a duk wanda yake jinkan wadanda aka kashe ta hanyar mummuna kisa wanda ubangijin mu bai bada umarnin hakaba to muna masu yi masa maraba da ya shirya dan binmu aduk inda yaga munzo mun kawo har acikin wannnan birnin dan kifar da wannan masarauta da take ci mana kasha kuma take ammafani da son zuciya ta kore zamanzancen Allah ta kawo nata. Aduk inda ku ga mahayan doki masu rufaffiyar fuska to ko garzayo ku bi sahunmu dan hada karfi da karfe muga bayan shugabanmu. Yarima yaji gabansa ya fadi lokacin da yazo karshen wannan karatun wasikaya dubi sauran dakarun dake gurin da sauran jama'ar da suke wajen sai faman gyada kai suke suna jin dadin batu wannan wasikar dan haka sai hankalinsa ya tashi tabbas ya san cewar mahaifinsa bayayin aiki da ilimi amma bai kamata ace ta haka za abiyo masa bay a kamata 57 Abdul'Aziz Sani M/Gini TURBAR GASKIYA -2 ace an samu gagarumi zama da manyan malamai, dabadan yayi sallama da mahaifnsa ba kuma yana kan hanya ne ta neman dan uwansa da sai yace sai ya zauna yaga bayan wannan al'amari amma tabbas yasan idan yaje ya samu Ansaru cikin saukin lamari sai ANsaru zai kawao karshen wannan abu domin sanin da yayi masa na da durcewa akan abinda ya zama hakkin Allah ne da al'umma dan haka sai ya dubi Huwaila yace "dole na tafi dake tun da kin shirya sai ki bi bayanmu nan ya nandade takadar ya sata aljihunsa kuma yayi gargadi akan kada wanda ya sake ya kara yawo da zancen daganan suka dausa suka ci gaba da tafiya har suka zo tsakiyar gari. Alokacin da suka zo tsakiyar garine sai suka ga dandazon jama'a bakin gurin da ake yanke hukunci ga wanda suka yi laifi ga sarki wani katon mutun yana shirin zai fille ma wannan mutun kais a boda laifin day a aikata na satar wa wata mata abinci alokacin da 58 Abdul'Aziz Sani M/Gini TURBAR GASKIYA -2 yunwa ta koreshi. Koda ganin wannan al'amarin sai yarima ya tsaya yana kallon cike da tausayawa, kamar walkiya wani farin doki ya bayyana asukwane babu shiri yazo gaban wannan mahaunin wanda zai yaanke kan wannan mai laifin sai wannann Mahayin ya dokin makoshin wannan Mahaunin sannan ya dauke wannan mai laifin ya gudu dashi akan dokin koda ganin haka sai Yarima shi ma yayi sauri ya hau yabi bayan wannan mahayin doki nan da nan suka kasa tsre cikin tsannain gudu tamkar walkiyace take giftawa Adai dai nan Sarki ya dubi taron jama'a yace lallai mu shagala da wannan labarin har gari ya waye dan haka sai dai mu kara hakuri har zuwa filin wannan yaki idan mun samu sarari sai mu karasahi na san duk da rashin karsashinsa da yawanku kun tsinci abubuwa da yawa acikin wannan labara domin ayanzu mun gane cewar duk wani musulmi wanda yakc 59 Abdul'Aziz Sani M/Gini TURBAR GASKIYA -2 aikata aiyuka munana wanda Allah bai umarceshi da aikatawa to bamu shakka shi kansa bayahude ne kuma bayahuuc basa kunar musulunci sannan kuyi koyi ga yanda mutun daya yake kokarin ganin bayan taron sarakai marasa tsoron Allah, dan haka anan gaba zaku ga yanda aminci tsakanin Yarima Rfan da Ansaru sai mun. Alokacin da Sarki yakai dubansa izuwa kowane rukuni na rundunoninsa sun hallara sai ya kai dubansa ga Likitansa wanda yana kusa dashi yace "yakai amintaccen likitane yaya akai da na gaya maka cewar kada ka taho da sama da mutane duba dari biyu naga kuma kazoo da ninkinsu? Ko da jin wannan tambaya sai Zauwad ya rissina cikin biyaya y ace "tunani nayi naga cewar wannan yaki da zamu je yakine irn wanda bamu taba yi ba, idan bamu da isassun likitoci wadanda zasu rinka duba dakarunmu zamu wayi gari babu sauran 60 Abdul'Aziz Sani M/Gini TURBAR GASKIYA -2 dakarun a tsaye wadanda zasu fuskanci abokan gaba. Koda jin wannan batu sajikin Sarkin yayi sanyi amma day a sake duban tawagar yaga tarin guzurin da aka taho da ita wanda ya kusa kai wa adadin. na dakarunsa sai ya cika da mamaki har ya budi baki zai yi Magana sai yarima yace "yakai Likita Zauwad hakika kasamu taimakon guziri da yawa daga wajen jama'ar gari, Koda jin haka sai yace "kwarai kowa ai jama'ar gari suna kwadayin ladan da zasu samune a wannan jahadi da zamuyi. Koda jinw annan batu sai Sarki ya samu nutsuwa a cikin zuciyarsa, Alokacin ne yarima ya shiga cikin tawagar likita Zauwad ya fara kallon mutanensa daya bayan daya kuma takan maza ya fara. A wanan lokaci Shadilat da Lushmairat ne cikin sahun likitoci mata kuma kowacce ta rufe jikinta gaba daya da fuskarta idanunsu kawai ake gani amma dudda haka sai zuciyoyinsu suka kama dakan uku-uku suka 61 Abdul'Aziz Sani M/Gini TURBAR GASKIYA -2 kama sunkuyar da kai kasa don kada yarima ya shaidasu, bayan yarima y agama duba mazan sai ya dawo kan layin matan, su Shadilat akan sawun gaba daga gaba kawai sai suka ga yarima ya wucesu baiyi ba yana mai ci gaba da duban fuskokin matan wasu ma idan yazo kansu sai ya bukaci su bude idonsu ya gani sannan yayi gaba. Al'amarin da yasa su Shadilat suka sami kwanciyar hankali kenan da suka ga an wucesu ba ace dasu su bude fuskokinsu ba. Bayan yarima yaje kan mace ta karshe dake kan layi sai kuma ya dawo farkon layin ya tsaya agaban Shadilat y ace da ita dago da fuskarki na gani, zuciyar tan a dakan uku uku da dago kai ta dubeshi itakuwa Lushmaira tana baya ta sunkuyar da kanta kasa har jikinta ma ya kasa tsuma domin t agama Saddakarwa asirinsu y agama tunowa i aLokacin da Shadilat taď ago dakanta sukai Yarima yayi arba da dararan idanunta 62 Abdul'Aziz Sani M/Gini TURBAR GASKIYA -2 masu tsananin haske sai zuciyarsa ta buga da karfi, har ya budi baki zai ce da ita bude fuskarki ya gani sai Sarki ya kwala masa kira, acikin hanzari yarima ya juya ya ruga izuwa wajen mahaifinsa da zuwansa sai Sarki ya dubeshi yace lokacin tafiya yayi imaza ka hau doki mu tafi, Batare da gardamar komai ba Yarima yah aye dokinsa suk jera shi da sarki suka wuce gaban gaba dayan dakarun yakin. Kaji mazajen kwarai wadanda basa tsoron yaki bare mutuwa kuma basa kwadayin duniya tunda gashi sun wuce kan gaba suna jagorantar al'ummars sun sallama rayuwarsu don daukaka addinin Allah sabanin su Sarki madhan da

Chapter 5 of 11