ta kunshi
yawancin 'yan Nijeriya sai kuma Girkawa, a nan muka sha yinin
mu, don Sulaiman yana daya daga cikin manya- manyan abokan
Yaya, haka ni ma na amince wa zuciyata, Kubra ita ce babbar
aminiyata a London.
Da daddare ne bayan na kintsa yara a dokinsu na yi musu
brush na yi musu wanka kowa ya sa rigar barcinsa, sannan na ce su
yi addu'a su yi barci sai da safe. Na kasha musu lantarki tare da rufe
musu kofa, sannan na nufi dakin maigirma Abubakar Saddiq na
shiga da madara a cikin kofi, na ajiye masa kofin, ya gama lazumin
da yake yi ya sha don madara tana, daya daga cikin abin da yake sha
kullum darce kafin ya Kawanta.
Ina kwance, har Yaya ya gama dukkan abin da yake yi na
al'adar reyuwarsa, tukunna ya zo ya kwanta kusa da ni muna
hirarmu irin ta Ma'aura mai dadi, Yaya ya ce "Rukayya bana ya
kamata ke ma ki je ki sauke farali don ya kamata ki je ki aikin Hajji
tun da saura wata uku a fara tafiya, zan fara yi miki shirin tafiya in
yaso sai ki tafi daga nan Na yi murmushi na ce" Yaya na gode,
Allah ya kara arziki. Yaya kada ka sa na kasa yin barci don murna"
Sai Yaya ya yi murmushi ya ce. "To kin ga kuwa in kika sami ciki
kafin tafiyar ai sai dai a fasa don ba za a je a lahantamin da ba" Na
ce "Haba Yaya, ai bai yi wani girma ba, abin da zai faru" "A'a ban
farda ba, ko don lafiyarki".
Yaya ya ce "Yauwa, daman Rukayya ina son na fada miki
wannan maganar amma don Allah kada ranki ya baci, kin san dai ku
biyu ne ke da Maryam ko? Kuma kin san tun da muka zo ban je
Nijeriya ba, shi ne ga za ya kamata cikin satin nan na je na dubota,
kin ga na bar ta da ciki, ko Yaya kika gani.?" Na ce, "Haba Yaya,
wannan ma sai ka tsaya ka nemi amince wata, ai hakkin ta ne a
kanka dole ka cika mata, don haka ni wallahi har ga Allah don ka je
gun Maryam raina ba zai baci ba, ai matarka ce, kuma uwar
'ya'yanka
Washegari na kasha zuwa Lectures dina makaranta, muka
tafi sayayyar kayan tsaraba, komai wanda ya kamata a saya wa
iyali, na ce Yaya ya sa ya Maryam, haka kuma duk wani abu na
fanning baby na ce a saya a tafi mata da shi, sannan tsarabar
mahaifiyarsa da kannensa da baba Ado da iyalinsa.
22
Yaya ya tafi Nijeriya ya bar ni ni da Yara, amma duk dare
sai ya yi min waya mun bata kusan awa guda muna hira koyaushe
ya yiwo min waya yakan ce wai ya yi missing dina, sannan ya kan
ce wai anya kuwa Rukayya ke kuwa kin damu da ni kamar yadda
nake begen ki a kullun, don Allah ki yi ki haifa min baby wanda ya
yi kama da ni, ni kuwa nakan ce to “Yaya Allah ya bamu.
A cikin wayar da yake yi min ne ya shaida min wai baba
Ado ba shi da lafiya har an kwantar da shi a asibiti, na ce Allah ya
sauwake, ya sa zakkar jikin ce.
Ranar da Yaya zai dawo daga Nijeriya na shirya masa
abinci na musamman, sannan na tafi airport don taren Yaya tare da
su Nusaiba da Sa'ima.
Daga saukar Yaya daga jirgi muna haduwa ya kamo ni ya
rungume tsamtsan, na ce Yaya ga fa su Nusaiba suna yi maka sannu
da dawowa, Tukunna ya sake ni ya dauki Sa'ima, ya sumbace ta a
fuska, haka ma ya yi wa Nusaiba, muka jero muka shiga mota sai
gida, a lokacin nan ni nake jan motar.
Don tsananin kulawa ta musamnan a wannan ranar abinci
ma ni da kaina na rinka diba ina ba shi a baki yana ci, har ya koshi.
Yana cin abinci ne ya ce "Rukayya ai a Kano na ci wani Special
abinci, Maryam ta yi min, "A gaskiya fadin da Yaya ya yi wai
Maryam ta yi masa special abinci har ya sa raina ya baci, wai shin
yaushe Maryam ta ajiye kalacin nata ta iya abinci har da Yaya zai ci
ya zo yana yi min santi.
"Kai Rukayya na gode Allah da kika kasance mace mai
tsabta da iya abinci, ai abincin da Maryam ta ba ni ranar da na sauka
a Kano Kasa ci na yi, don kuwa ina deban miyar sai ga kuda a cikin
abincin, wallahi har na je na dawo abincin Otal nake ci, don kuwa
abincin ko an yi shi ba shi da dandano. A wannan ranar lokacin
kwanciya da yayi tare muka yi wanka da Yaya sannan na ba shi
hakkin sa iya son ransa, a nan na tabbatar ya yi missing dina, komai
yana tafiya yadda ya kamata tsakanina da mijina, duk abin da na san
ai dadada wa mijina rai shi nake aikatawa, wato yin na yi, bari na
bari, sannan ladabi da biyayya, duk kuma abin da na san zai bata
23
masa rai tsakanina da shi katangar karfe, ba ni taba aikatashi ko da
wasa.
Bayan sati daya da dawowar Yaya daga Nijeriaya aka yiwo
masa waya aka sahida masa jikin baba Ado ya tsananta don har an sake mai dashi asibiti.
A nan Yaya ya yanke shawarar mu tafi tare mu je dubo shi,
tun da ana hutu a makaranta. Washegari karfe biyar na yamma mun
sauko a filin jirgin Malam Aminu Kano, mun sami diręban Yaya
wato Usman yana jiran mu a filin jirgin, mun wuce zuwa cikin gari gidan Inna Sa'a, amma tun daga kofar gida ganin taron mutane ya tabbatar mana da cewa baba Ado ya rasu, sai mu ce Allah ya jikansa, mu kuma Allah ya kyauta namu karshen in ya zo.
Na wuce cikin gida tare da yara na bar Yaya yana gaisawa
da mutane a kofar gida, cikin gidan ma a cike yake da mata, duk
ana ta sharbar kuka ni ma na shiga cikinsu, na yi wa iyalen
mamacin gaisuwa tare da addu'ar Allah jajikansa.
Kwanan mu bakwai muna zaman makakin mutuwar baba
Ado, ina nan zaune a gidan Inna Sa'a don ban tare na tafi gidan
Yayà na Sani Mainagge ba. Yaya ya shigo gida bayan sun gaisa da
Inna, ta sake yi masa gaisawa, sannan suka shiga labarin irin zaman
da aka yi da baba Ado, mutum mai mutunci da riko amana ga
hakuri, a zamanin yanzu samun irin su baba Ado da wuya, To sai
dai mu bi shi da addu'a, shi kadai ya rage a tsakanin mu da shi.
Bayan sun gama hirar su da Inna, Yaya ya shiga daki inda
nake kwance ya same ni, ya ce "Madam, ai ya kamata ki shirya mu
tafi gida ko, na fara 'yar gardama don ba na son zuwa Sani
Mainagge, ba don komai ba sai don masifar Maryam, amma Yaya
ya ki amincewa, dole na shirya muka kafi.
Mun isa gida, Yaya ya bude min daya sashen da yake rufe
na gidan, ya mallaka min, ya ce,. "Wannan shi nehe sashen kwanana
sai na wuni a gidan ban ga idon Maryam ba ita ma ba ta ga idona
ba, kowa yana shiyyarsa, a kwana na biyu ne a cikin gidan da dare
ina kwance na ji ana buga min kofa, na farka daga a barci, a tsorace,
na ce "Wane ne" Sai na ji Murya Yaya yana cewa, "Rukayya bude".
Na byde kofa na ce "Yaya lafiya kuwa," Ya ce Lafiya, yanzu na kai
Maryam asibiti, ta haihu, ki zo ki yi mata shayi "Nace "Yaya
Maryam ta haihu, mai ta Haifa? "Ya ce Mace" Na ce "Allah ya raya
"Yace, kin ga na sami Rukayya Junior", Na ce, "Kai Yaya kada ma
24
ka fara wannan hadin" Ya ce "Allah Rukayya zan sa mata, don har
na yi mata hudu ba ma da sunanki daga haihuwarta" Na ce " Tо
Allah ya sa ta amsa sunanta," Ya ce "Amin"
Mun isa asibitin, muka sami Maryam a kwance a kan gado
ita mayar a kwance a kan gadonta, na leka na gan ta na yi wa,
Maryam sannu na gaishe ta; amma Maryam ko ta daga kai ta kalle
ni sai dai ma hararata da ta yi.
Yaya ya ce na hada mata shayi amma Maryam ta ce wai ita
ba za ta sha ba, sai da Nurse ta zo ta hada mata ta ba ta sannan ta
sha,
Yaya ya yi wa likita magana a kan ya sallami Maryam, tun
da dai ita da jarriyarta duk lafiyarsu kalau. Likita ya rubuta mana
takardar sallama muka tafi gida tare da Maryam jaririyarta.
Bayan mun dawo daga asibiti ne, gidan mu ya cika da baki
duk kannen Maryam suka zo, su Amina da Farida da kuma Fa'iza,
sannan da iyayenta, haka ma, su Yaya Ai'sha da Maimuna da
Hadiza su ma sun zo.
Gidan ana ta aikace - aikace saboda baki don Yaya ma ya
yi baki abokansa daga Sokoto, don haka mun hadu har da masu
aikin gidan muna ta girke - girke.
Kannen Maryam duk inda na juya sai harrara ta suke yi, ni
kuwa a cikin raina na ce "Oho dai, ku kuka sani kuma."
*
Ana sauran kwana uku suna Yaya ya zo ya same ni a
dakina, ya ce na yi masa lissafin duk abubuwan da za a bukata na
suna, sannan da wanda za a yi na kauri don ya ba ni na je na sayo
komai da komai,
Na ce, "Yaya ba haka za ka yi ba, ka samu mai jego ita ta
san irin abubuwan da take bukata na hidimar sunanta, ko kuma ka
kira Yaya Ai'sha ka ba ta ta sayo komai da komai tun da daman ita
ce mai hado kayan hidimomin suna a kowane suna in Maryam ta
haihu".
Ya ce "To yanzu ban ga damar kiran Aisha ba ke na ga
damar sawa, ko ba za ki yi ba?". Na ce, Yaya zan yi mana, "Ya ce"
In ke ce kika haihu ai Maryam ce za ta yi komai na hidimar suna, ai
25
magana, ya ce; "Na tara ku ne ba don komai ba, sai don na yi muku
magana a kan abin da ya faru yau, ina son in sanar da ku cewa, ba
zan dauki fada a gidana ba, don haka wannan ya kasance na farko
kuma na karshe, ku yanzu baku jin kunya a ce wai matana da girma
na da mutuncina a ce wai kuna fada har da kokawa, wannan ai
rashin mutunci ne. don haka ku sani, ba zaman fada na tara ku mu
yi ba, zaman lafiya na tara ku mu yi, kun ji ko, don haka ku yi sulhu
a tsakanin ku tun daga nan". Sai a nan Yaya ya numfasa ya bar
magana, ya tsaya yana kallon mu,... Maryam kuwa don tsaurin ido
sai cewa ta yi "Yo ai fada kai ka janyo a yi a gidan ka, tun da ka
auro Rukayya, kuma yanzu aka fara fada tun da ba zan dauki isa da
mallaka da iko ba".
Yaya ya ce, "Maryam, ina magana kina maida min don kin
mai da ni ban isa na yi muku magana ba ko? To sai ki yi abin da ka
ga ya fi zamar miki alheri a gare ki, ai ke za ki sha wuya ni ba ruwa
na".
Da dai na ga ran Yaya ya baci sai na kwantar da kaina, na
ce, Yaya ka yi hakuri in Allah ya yarda irin haka ba za ta sake
faruwa ba". Maryam ta kalle ni ta ce "Kinibibi kawai, to tun da ya
zama mijinki menene na ce masa Yaya Ai sai ki kira shi darling
kawai" Na kalle ta na yi murmushi cikin kissa, na rangwadar da kai,
na ce "Mantuwa ta sa na ce masa Yaya, darling ka yi hakuri...
"maryam ta doka tsaki ta fice ta bar dakin. Yaya ya daga kai ya bi ta
da kallo yana girgiza kai.
Cikin rana kunnan kafin suna, muna ta harkar arziki ni da
mifjna, yadda Maryam ta tsame hannunta daga al'amuran Yaya shi
ma ya yi burus da ita.
Ranar suna ta zo aka rada wa jaririya sunana, wato
Rukayya; wai --wai-wai ranar nan Maryam tamkar za ta kasha kanta
don bakin ciki, ita da kannenta. Don haushi ma lunchin da aka hada
za'a yi Maryam kin halartar wajen ta yi. Ni kuwa tare da kannen
Yaya da aminansu, tare da bakin da Inna Sa'a ta gaiyato, zuwa
matan bokan Yaya. muka kayatar da liyafar, ga kuma Barmani
Coge ta zo, ina rawa, Yaya ya zo ya dinga yi min likin wazobiya.
Haka dai muka sha hidima har biki ya watse.
Bayan suna da kwana uku muka tattara ya namu ya namu
muka koma England. Zama da kishiya abu ne mai wuya don ni ba
an sami mace mai hakuri da wayo da kuma iya kissa, ba to kinaji
27
kina gani sai a raba ki da mijinki kuma ba yadda kika iya, don wani
abin in za a yi miki ba za a yi miki yadda za ki gane ba, ta bayan
danga za a yi miki, wato kisan mummuke. Haka dai muka kasance
da Maryam, ina London amma tana shirya min mugunta a Nijeriya
daman tun da na je Nijeriya Hadiza take sha da min ko da malamai
sai ta fitar da ni daga gidan Sadiq, don haka kullum tana hanyar
gidan bokaye da malamai. Amma wai Inna Sa'a ita ma ta tsaye a
akaina ni da Yaya, tana nan tana taimaka mana.
Bayan mun dawo daga Nijeriya ne da wata daya muka tafi
Makka ni da Yaya don aikin Hajji. A can Saudiya ne aka tabbatar
min ina da ciki na wata daya, wanda Yaya ya muna min farin
cikinsa wanda ba zai iya misaltuwa ba.
Bayan mun dawo daga aikin Hajji na fara shiga wasu 'yan
matsaloli a tsakani na da Yaya, kamar yadda na gaya muku duk
wata, Yaya yakan aika wa Maryam kudin cefene da sauran
hidimomin gida, to haka ne, amma Maryam duk lokacin da ta bushi
iska sai ta yi wa Yaya waya ta ce tana bukatar kudi za ta yi wasu
hidimominta na daban, Yaya ko duba nawa ne ba binci ke, haka zai
dauki ya aika mata, in na yi magana sai ya ce wai ni bai aika ba
yanzu sai ya zame masa masifa shi da ita, shi kuma ba ya son abin
surutu. To amma in ni ne na ce ya ba da kudin cefane ko na wata
hidimar gida sai mun kai ruwa rana, kafin ya bayar ya dinga cewa,
wai yaushe aka yi cefane har ya kare, ko kuma Rukayya kin cika
kasha kudi, da dai sauransu.
Wannan ya dada tuna min da wata rana na dawo daga
makaranta, na zo na sami Yaya a gida ya dawo daga wajen aiki,
nace, Yaya "Yau har ka tashi daga wajen aiki?" Yace "Wallahi ban
tashi ba check book dina nake nema na bankina na Nijeriya, Inland
bank, ko kin gan shi?'! Na ce, "Ai yana cikin Jaka a rufe;" Na je na
bude na dauko masa. Ya ce "Yauwa, daman Maryam ce ta yiwo
min waya, wai wannan satin za a yi bikin kannenta, shine ta ce na
aika mata da kudi don za ta yi sayayya, "Na kale shi kawai na ce
"To!" A gabana ya rubuta mata check din zunzurutun kudi Naira
dubu dari biyu, ya aika mata.
To me zai faru" Washegari ne muna cin abincin
dare, na yi kwalliya da wani skirt da rigi, wannan dai shigar Turawa
ce, Yaya yana ta yabon kwalliyata, sanna yana ta ji da ni, yana ririta
ni.
28
Bayan mun gama cin abinci muna zaune a falo muna kallo,
na ce "yaya ya kamata mu je yau mu yi shopping, saboda kayan
abincin gidan nan ya kare, kuma dama ka sani yau ne ranar da muké
zuwa yin shopping." Kawai sai yaya ya daure fuska ya сe
"Rukayya kin cika son kashe kudi, yaushe muka yiwo shopping a
gidan nan da har za a ce sun kare?. "Abin mamaki, yaya fa a gaban
yara yake cewa wai na cika barna ta kayan abinci. Da na ga abin zai
yi yawa. Kuma bai kamata yana fada ina mayar masa ba a gaban
yara, a sai kawai na tashi na bar masa falon na tafi daki na kwanta.
Har lokacin barci Yaya ya shigo, amma bai tanka min ba, ni ma ban
tanka masa ba. Ya gama komai na al-adar rayuwarsa, kamar yin
wanka, da nafila dá shan madara, sannan ya kwanta, amma sai ya
juya min baya, ni kaina ban iya nayi barci ba don wani abu ne mai
daci yake zuwa ya dawo a kirjina. Haka shi ma yaya bai iya ya yi
barci ba. Da na ga bazan iya wannan kwanciyar ba sai kawai na
tashi na sa yar saman rigar barcina na bude kofa zam bar dakin,
yaya ya ce "Rukayya! Rukayya" Ban dai amsa masa bai na wuce
zuwa dakina na yi kwanciyata. Da safe ma ban jira yaya ya tashi ba
na shirya masa breakfast, daman shi da safe madara yake sha, sai
Ya'yan itace (fruits) na ajiye a kan tebur, ko gaishe shi ban yi ban
na shirya su Nusaiba muka tafi makaranta.
Da yamma ne bayan na dawo daga makaranta, na shiga
kicin na ga an yiwo shopping an ajiya min komai da komai an sayo,
har abin da ba na bukata ma an sayo. Na tambayi Esther (wato mai
aikina) wa ya kawo, ta ce "Oga ne da kansa ba dan aike ba." A raina
na cewa ya gaya maka Barno gabas take?".
Na idar da sallar magriba ina jan carbi, Yaya ya turo kofa
ya shigo dakina ya zauna daga bakin guda, sai da na yi addu'a na
shafa sannan na juya nace sannu Yaya, ya ofis?. Ya ce Alhmadu
lillahi yau kam".
Daga nan Yaya ya ce " Kin ga kaya a kicin ko?, to ki duba
ki gani in da akwai abin a ba da saya ba, sai ki fada a je a sayo"
Nace to".
Yaya ya ce Rukayya har yanzu fushin ne na ji ko amsa min
ba ki yi ba?. Na ce "Yaya na ce maka to" Cikin shagwaba da kissa
nake magana. Yaya ya ce "Haba, Rukayya, abin da bai kai ya kawo
ba ki rinka fushi a kai, Yau wallahi kin hana ni sauraron meeting a
ofis, don ana yi hankalina yana tunaninki, ai kwakwalwata rikicewa
29
ta yi tun da na tashi da safe na ga kin tafi makaranta ba tare da na tashi mun gaisa ba. Don Allah Rukayya kada ki sa ni na shiga wani hali a dalilin ki Na ce "To Yaya ka yi hakuri”. Sannan na ya yi murmushi ya ce. Dadina da ke ko ba ke ce da lefi da kin iya bada hakuri.
Kin sa kuwa an ce matar na tuba ba ta rasa miji. a ya sa a kullum, kike kara shiga raina. Kawai sai Yaya ya janyo ni zuwa barin jikinsa. Na ce "kai" Yaya, Shi ma ya ce, Ke Rukayya." Muna dariya muka rikice a kan gado. Muna kwance ne Yaya ya ce na shirya zan yi masa rakiyar aiki zuwa China za mu yi sati daya a can, don haka sai na shirya mana kayan tafiya don gode za mu tafi, yara kuwa daman ya shirya da Sulaiman a gidansa za su zauna. Hakan kuwa aka yi, washegari muka tafi China, mun sauka
a babban birnin China wato Beijin, a Yamasite, a wani babban otal mai suna, chang Hong leq hotel, yana daya daga cikin manya manya otal na kasar China.
Tun da muka je China ba abin da ya dame mu sai dai in Yaya ya je meeting da yamma ya dawo mu fita yawon shakatawa, sai kuma soyayyar mu wacce ita ta fi damun mu a wannan lokacin fiye da duk wani abu na rayuwa.
shida.
A China ne aka tabbatar min da cewa- cikina ya shiga wata
Sannan har ranar haihu wata sai da likita ya shaida min. Satin mu daya muka dawo daga China. Bayan mun dawo daga China da sati biyu, Yaya ya yi shiri ya tafi Nijeriya gun Maryam. Zuwan Yaya Nijeriya ne Maryam ta matsa masa a kan sai su je Umara tare, amma Yaya ya nuna mata shi ba shi da niyyar zuwa Umara yanzu, amma Maryam ta matsa sai sun je, amma da Yaya ya tashi sai ya biya mata zuwa Umara ita da Yaya Ai'sha da Maimuna da Hadiza da Inna Sa’a sannan da matar marigayi Baba Ado, wato gwaggo Kulu. Kodayake Maryam dai ba haka ta so ba, tun da ita dai ta fi son zuwa da oga kwatakwata.
*
Sanin irin zaman da muke yi da Maryam ya sa duk sati nake sauke wa kaina Al-kur'ani, sannan nafilar cikin dare wannan
kullum ne ba fashi, tare da addu'ar Allah ya shiga tsakanina da 30
makiya, ba na rabuwa da wuridin ya Haiyu ya Kaiyumu, kullum na
yi sallah.
Sannan kullum dare nakan karanta suratul Mulk da Suratul
Iklas da Falaki da Nasi, don tsari daga sharrin mutum da Aljan.
Tun da muka sami sabani da Yaya yanzu in marayam ta
yiwo masa sako sai ya bincika in gaskiya ne tukunna yake yi mata
aiken kudi, to da Maryam ta ga haka ne sai ta canza dabara. Lokacin
cikina Yaya da wata takwas na shada wa Yaya ni fa a Nijeriya zan
hai fu don haka ina son na yi sayayyar kayan. Yara, Yaya ya dauki
kudi. Ya ba ni wanda zan yi sayayya ta baby kuma wacce zan yi
tsaraba, To me zai faru, da yamma ne Yaya ya dawo daga ofis ya ce
"Rukayya don Allah ba ni kudin nan da na ba sayayya, ki yi hakuri
in mun je Nijeriya ma yi shopping din don yanzu zan yi amfani da
kudin." Nace "To Yaya ni na dauka shi zai yi amfani da kudin, sai
cewa ya yi. "Wallahi ban san yadda zan yi da Maryam ba yanzu,
wata rigima ta dauko min, wai business din da suke yi da Hajiya
Hauwa shi ne kudi ya bata a wajen ta, to yanzu suna ta rikici da ita
Hauwan har ta dauko mata dan sanda shi ne ta yiwo min waya a kan
na taimaka na aika mata kudin ta biya". Na ce "To yanzu kudin da
ka ba ni su za ka ba ta ta biya kudin rikicin da take yi yace "Haba
Rukayya kin san yanzu ba kudi a wajena kuma kinsa gobe asabar ba
za'a bude banki ba, kuma Hajiya Hauwan ta ce a yau take son
kudinta in ba haka ba 'yan sanda za su tafi da ita, to kin ga kuwa da
girma na da nmutumcina bai kamata a ce an tafi da matata" police
station ba a kan 'yan kudin da ba su taka kara sun karya ba. Haushi
ma ya kama ni, na rasa abinda zan ce masa, sai kawai na tashi na
bar masa falon.
Ina kwance a dakina ina tunanin abin yi, wai shin me Yaya
yake nufi ne zai ba ni kudi don in yi shopping din haihuwa, sannan
ya karba ya aika wa Maryam bayan na san karya take yi ni na san ba
gaskiya take fada ba, ni fa abin da Yaya yake yi min ya fara isa ta,
koyaushe sai ya debi makudan kudi yana aika wa Maryam a kan
karyar banza, amma in ince nice yi magana daidai da kudin cefene
sai mun kai ruwa rana kafin ya ba da kuına yanzu yana nufin ba zan
yi shopping din baby ba sai na je Nijeriya tukunna? Sannan ita
Maryam lokacin da take da ciki ni da kaina muka je muka yi mata
shopping din haihuwa tare da Yaya. Kai ba za ta yiwo ba a ce a kan
karyar banza in zauna ana kwarata ba.
31
Na yi niyyar in yi waya na gaya wa Inna Sa'a amma sai na
yi tunanin ai bai kamata ba don sirrina ne zan tona. A ranar nace
komai za ta faru sai dai ta faru. Da yamma ne na dauki motata na
nufi loveal shopping complex, wajen mary ked wadda mun riga
mun zama abokan ciniki don kullum a wajenta muke zuwa yin shopping, don haka na ce mata, ina son kayan jarirai, daga baya
Yaya zai kawo mata kudin in ya taso daga ofis. Na shiga na debi
kayan yara iya son raina, sanna na yi wa su Inna Sa'a tsaraba, shi
kansa Yaya sai da na yi masa sayayyar kayan sawa. Na sa aka debi
kaya aka sa min a mota, wanda loveal sai da suka ba ni wata motar
ta rako ni da wasa kayan.
Na zo na ajiye kayan a gida ba tare da' na gaya wa Yaya
cewa na yi shopping ba, wanda na sayo masa kuma na jera masa a
cikin carboard din sa,
*
"Wai shin Rukayya mai kika saya ne a loveal haka suka yi min
waya wai na kai musu kudin? Yaya ne yake yi min wanna
tambayar bayan kwana biya da zuwa loveal yin sayayya, na ce
Yaya, shopping din haihuwa da na tsaraba na je na yi? "Ya ce
"Rukayya ba na ce ki bari in na je Nijeriya sai mu yi ba tun da
kudin da na ba ki na karba," Na ce "To shi ke nan Yaya in ba za ka
biya ba ai sai ka bari inya so in 'yan sanda suka zo suka tafi da ni
kaje ka yi beli na" ya ce wai Me ya sa ne Rukayya ba ki fahimta?
Na gaya miki rigima Maryam ta shiga shi ya sa na karbi kudin na
aika mata. "Na ce Yaya tsaya na gaya maka, in kai ba ka san
munafuncin mata ba