Amina ma za
TK A !nghutunsyya Kare Yaya ya ce AeKira u
"To. su su
damR saya na makaranta".Ani Maryam ta kira su
iv Faride, u z9 suka fara yi masa lissafin suke Tem ש
so don tafiya makaranta tamkar wani mahaifinsu wanda
.. БО
s I USUK
7iJvapiAbin ke mahaifinsu пahaifinsu, ba zai saya musu ba. amma dorlon SASY Be ta lissafin Karya da gaskiyva ya dauki
ess LASTIALITHU
Va 2
Hannan Xaya ya seana Rukayya ita ba ta
a makaranta?" Ya sa Nusaiba ta kira ni, ina
dakin girki Nusaiba ta ce in zo in ji Baba. Na bar aikin da
入 B2eOWEX BXUZ hib 251 pake yi na tafi dakin Anti Pa Б уК sallama na shiga, na ce
i Yа се "Ke ba abin da kike Iע bukata, na 90 BV ΝΛΑ ΠΣ makantaA yi shiru ban ge komai
ce pa don na san in na p 099102 0
'fada Anti za ta yi tazagi na ne, shi ya sa na yi shiru, Yaya 27 R5
ya ce "Ki fada mana, kin ga ni gobe zan tafi". Na ce "Ni dai
kudin littattafai zan saya". Ya ce "Shi ke nan? Wai mai ya sa
Rukayya ba ki son fadan abin da kike so har sai an tambaye
ki, sai ka ce wata bagidajiya? To ga wannan kudin ki je ki
saya". Ya miko min damin kudin kamar yadda ya bai wa su
Farida ni ma haka ya ban, Naira dubu biyar biyar. Nan fa
Anti ta galla min wata uwar harara ta wutsiyar ido.
Na yi godiya zan fita, har na bude kofa zan fita sai na ji
Yaya ya ce "Rukayya kawo min warwarayen da na sayo
miki don ina son na koma da su zan yiwo miki canjin su, ke
ma Maryam ki kawo naki, zan canzo muku gaba daya, Nan
fa na juyo na ce "Yaya wadanne warwaraye, ni ai ba ka sayo
min wasu warwaraye ba". Yaya ya ce "Maryam ina
warwarayen da na ba ki ki bai wa Rukayya?". Nan fa Anti
Maryam ta fara in-ina wai warwarayen ta dauka nata ne ita
daya shi ya sa ta raba wa kannenta, don ta ga me za ta yi da
guda goma sha biyu.
Yaya ransa ya 6aci, ya daka wa Anti wata umar tsawa
wanda mu kanmu sai da muka razana. Ya ce "Stupit kawai!
Daman na sayo ne don ki ba kannenki? To ni ba na son irin
wannan munafuncin, ai na san da su ko su, ban kawo musu
tasu tsarabar ba, za ki dauki kayan Rukaiya ki ba su? Kuma
ina zannuwan da na ba ki ki ba ta, su ma ba ki ba ta ba kin
bai wa kannenki? Wallahi ki ji tsoron Allah Maryam,
hakkin wannan marainiyar sai ya hau kanki in ba ki yi hankali ba".
Yaya ya juya wajen su Amina, ya ce "Ku kuma ku cire
min warwarayen nan ku ba ni, kuma ku dauko min lesin
nan da ta ba ku na Rukayyaa ku kawo min! Suka mika masa
warwarayen, ya ce su ajiye su, sannan suka debo zannuwan les din suka kawo masa.
Ni kuma ina daga gefe ina ganin ikon Allah. Yaya ya kalli Anti ya ce "Wallahi in 'ya'yanki suka biyo irin halinki ba su ji dadi ba, tun da ba namijin da zai zauna da su".
28
Anti Maryaın dai ta yi zuru duk kunya ta bi ta rufe ta ta
rasa ydda za ta yi, sai faman ba shi hakuri take yi. Yaya ya
yi banza da ita, ya kalle ni ya ce "Rukayya, ga wadannan
kayan naki ne, na kawo miki amma ba ta ba ki ba sai aka ba
wasu, don haka ke na san kin fi karfin kwncen wasu, sai dai
a sa kwancenki, don hakawadannan kayan zan bayar da su,
har warwarayen, ke kuma zan sayo miki wasu in zan zo, kin
ji. ki yi hakuri".
Washegari ya cikin fushi ya bar Nijeriya zuwa birnin
London na kasar England, tare da tabbatar wa Anti cewa yan
son zaman lafiya tare da kwanciyar hankali a gida, kuma ba
ya son wani abu ya biyo baya, bayan ya koma.
Bayan Yaya ya tafi wata gobarar masifa ta sauka a
kaina, inda Anti ta hada kai da kannenta suka yi ta yi min
eici-ciri tamkar za su cinye namana danye don bala'i, 'yan
kudin da Yaya ya bar min Anti ta karbe ta raba wa
Kannenta.
Kusan makarantar da nake yi ma Anti tana nema ta
salwantar da ita, ta hana ni zuwa don mafisar aiki da renon
'ya'yanta.
ta
Wani abu ne da kowa ya sani in mace ta kai mace har ta
isa budurwa tun ba ma a ce kyakkyawa ba ce, to dole a same
da samari, wadanda suke son ta, amma ni duk wanda ya
nuna yana so na, ko da wasa ne sai Anti ta sami hanyar da za
yi ta hana shi zuwa gidan nan waje na, don duk yadda za
yi ta ga na ci baya tana farin ciki da shi, ita dai ba ta son
ga na ci gabana kullum sai ci baya. Balle ma in ta ji wani
mai dan dama-dama ne, ta dinga zazzagin sa ke nan, don
haka ta raba ni da duk wani mai so na.
ta
ta
ta
Ita dai ta fi son na zauna, na zamar mata 'yar aikin gida.
Ba ni da abin yi kullum dare in na shiga daki na sai sallah,
ina rokon Allah ya fitar da ni daga kangin da na ke ciki,
sannan Allah Ya ba ni miji nagari wanda zai rike ni tsakani
da Allah, tun da dai Allah Ar-Rahman ne mai baiwa kuma
29
Ar-RabimAcMajiKan Muminai,Salar daiparike ina gi a
ce ŞalaoulyTasbihiu un zda Anpabi,Ya kwadaitar da yin 261 duk nwAnlgu wole kake vake da bgta Waien Allah Allah Zai biye in masad Samandda yuriginne Hayxu Y Kayyu Rahmauke Astaksn Ka d đan lafalasin da
aioAnk ha da da damo a wannan lokac uk dAA T
wadannan wahalhalu da nake yi na gida har wata slokata
kafa miR We beiniiahankalindomin idan na dawo.dega
unguwasba, nanki metaisanny da, zuwan Don heka, dolkarto1
ce, euk dokagmn da naji dirin, motarta taidawo dazalunguwa,п1
komai nake yi, tems tabbatar ne fita vajeda gudu na bude i
mata mola, sangan na kerbog jakarta, na yi matysanna da
zuweinKade RAsYardanta denaa hom fin moter ballohar
fito daga matar in nadikimukuwaita Da san saran. DO
hakavduk abin da naker yinin dai na ji dirin mojaryta ko zabuк
yanke na je na tarbe ta.Ba zan taba mantawa da wata raDes
ba, Antirlertafisgidan biki ita da yaranta duka,. wator Saimada
Nusaihe Ma irage niidayas sai Christy paeilaiki agikia gidayЛви
sai na ce wa Christy, lokacin yamma ta yi, don Alle rinka hura dasgirkini zan shigaina.den avatsa ruwa adikinaw
emsNa shiga bandaki ina wanka na shafa:kumfar/sabuld веі
a jikinabrsai nabjin ham din motan Anti,tana da danmawa, ab 61
ban ssad lokacin da na janyo zanina na daura ha, ne fito danun
gudus duksyikinankunfa, navisargabam mntari Antina bup1
matapana adest'Sannue daikdawowwašnsKawdijo ba zatoibia 6)
tsanmmani sainnamjibshukar maricaifuskatáy waniskanci ne yg BJ
sa nalshiga sankaignasjin tantiaya dar motal donsin sainuism
damar fadarwani abu ne yarhanamifitewalnh trbe tadfæcexed
"Ga Saimilta nyi barci kindaukota sannamdusaibaski cire
matairigartaz ki iyishmatidavankasico baultaabincidta cib"Ni sa
kumiliodal jikina yake jikesidan kunfasha askuls dAnagdaa şri
wankebat Sai da na gama hidimomindyayadta saninih najanse
na yimhawaswankan drimrwadahnarl abobuwa ma ishsld gh
30
sa
mallaks ppi Maryam Jas t imm
mantad9n,Aun zamarmin ji. "ox sb nionids io B swus il sd ox"
*** salut sind insw in st in ABABA A"trig niled saBY SWEN
Blaw nim dis BI UIUM sy sinisism sism, Oxis as strS
ទេມ
askiya Puk inda muum yake jdan ya kasance maj sasKLEWU aiki rikonamana kume,ga ladebi da biyayya sannan da A GLSI
tukura akani da Alah 9nKsargein gin nasara 19
dukkan Abin a Vasaa Babana duniya da Jahirayan sway sd
H sdik ya Kagantg fikin manyan akalaonids
da sukan REAL11
Kasashen wajc, Ba wai,
iliminses ko shekarunsa, ba suka sa ya samy wennab
matsatsAdin st gaskivarsa da rikon amanarsa, suka kai shi ga
samun WarnAR то виг don in shekarunsa ne baj kai
sheka AMZba shi aikin da yake nke da shibaon
ofishin jakadancin Nijgriya na England daga Jakadangai shE
a matsayi ន ទនgនm,នSIGI ST "isb sysy, aird BWUBY" da na kamm rAPnKame Bara ala Karatuna na sakandare Yayа O 92 ліссяяg Sadikal% kady kan duk kanmu da ita da ni da y ps ASLas SHU pS S UI gou UG
Saimgdada Nusalba ta yi manaa Passport Passport saboda. zai zo mu tati agk SD SIG JIKI AIL VIDS SIKI
ngland baki gaya Da Anuti ta tashi sai ta yi passport dinta, DIG, NEIGY, ADED BE GUBS 60 ID IS da na ya'yanta amma ba ta ngudio ta yi nawa ba, wai a nufin ta ni ba 1 of SUIAL oV. 916 16rWsdW"
zan jeba ni daman ko a raina ban damu da go ec SISWUEKK KORSAAS 23u0EMS ( Keps 26UCC
zuwa wata England ba ni dar fatana Allah Ya.ba ni miji
don na huta da fitifnar ta, domin na san ko mun je
SIKI Κκαλλς CCMα WAKI λ99 U
nagaranEm It Iswims 6757 A, 52. 51 yiends "ast nsbig Englagland ma ni zan.yi ta vi manata wahala gidanta. I62 In nODis ו J I 22li8 18V'
61
11 ) THA Bறு. Yaya ya zo ranar 25 gaa watan Disamba da nıyyar ya SIT OWED BY DISHI SU SIK AND DIRE KIMSI SCHOTS SUS
debe mu myu tafi bakakı daya, A ranar da ya sauka a gida 615299 ទ 29 ΕΥ
Nijeriva 60 8VVS da misalin Karte 30 daidAf TORAETh, H Abireik Ser
dare, na gama abinci na jera aa kan febinYaya shi dAnu
Maryam da yara sun zo sun' baírebini zaa ciabe
tana ta ji da shitamkar tsoka daya a miys ita yau inargidd ya
dawo, nta fesa kWalliya de Wata KwankWafattiykr sta
WS
61
mai kyan gaske super sannan samaada da Kasanta dük zinareke ke в
Hskasd magana, sun hau tebir za su fara cin abinci, Yaya ya kwala 3153
min kira, na fito daga dakin girki na ce ga ni Yaya. Ya ce, "Ke ba ki zuwa a ci abincin da ke". Na ce "A'a ni ma na debi
nawa yana dakin girki". A nan fa Anti ta yi wani 6ata fuska
tamkar an aiko mata mahaifinta ya mutu, ta zuba min wata
uwar harara, Yaya ya ce "A'a ki dauko naki ki zo nan mu ci
tare". Na ce masa "A'a ni ba yanzu zan ci nawa ba sai an jima zan ci". Wani abin mamaki sai Yaya ya ce "Kai ni ma fa ba yunwa nake ji ba, don haka ni ma sai an jima zan ci abincin". Kawai sai Yaya ya tashi daga kan teburin ya koma kan kujerar falo ya zauna yana kallon tashar talbijin ta CNN. Ya bar Anti tana cika tana batsewa tamkar za ta fashe. Ita ma ko iya cin abincin ba ta yi ba don haushi, sai yara ne suka ci. Yaya yana zaune yana kallo sai Christy mai aiki ta
zo da wata matsalar wajen Yaya, ta ce "Alhaji Sannu da hutawa". Bayan ta durkusa daga gefe daya, Yaya ya ce "Yauwa Christy, yaya dai?". Ta fara magana a cikin gurbatacciyar hausarta, ta ce, "Oga daman na kawo ma kara
ne don ni ma ba zan yarda ba fa, yaya Rukayya tana 'yar aiki, ni ma 'yar aiki amma za a ba ta ďaki a cikin gida ni a ce sai dai na zauna a dakin yaran gida?". Ya zabura ya ce "What!!! What are you trying to tel me! Ar you in your sence?. Ke ba ki san cewa Rukayya kanwata ce ba?". Wane
ne ya fada miki cewa Rukayya aiki aka dauko ta ta yi a
gidan nan". Christy ta ce "Anti ce ta gaya min wai ita ma 'yar aiki ce, kuma na ga ma har ta fi ni yin aiki, don ni sai in ta tafi makaranta kawai nake yin aiki amma idan ta dawo ita take yin komai na gidan nan, shi ya sa na san da gaske ita
ma 'yar aiki ce". Yaya ya ce "To na ji, amma Rukayya ba yarinyar gida ba ce "She's my sister". Yaya ransa ya yi matukar baci da jin wannan maganar ta Christy, amam sai kawai ya share bai yi wa Anti magana a
hankali.
kai ba, ba wai dan wani abu ba don dai ba ya son tashin
32
Suna zaune a falo shi da Anti da yaransu sai wani shan
kanshi take yi, shi kuwa ko kallo ma ba ta ishe shi ba, sai
kawai ya ci gaba da wasa da 'ya'yansa suna wasa da 'video
'game'. A lokacin nan Nusaiba tana da shekara hudu da rabi,
ita kuwa Saima tana da shekara biyar.
Can Yaya ya ce "Maryam ina passport din da na ce ki
yi muku, kin yi?". Ta ce na yi mana". Ya ce "To dauko ina
gani". Ta tashi ta je ta dauko masa, ya karba yana dubawa,
ya ga nasu su uku, ya ce "Yaya na ga naku ku uku, ina na
Rukayya". Anti ta ce "Ai ni na dauka ban da Rukayya za a
yi tafiyar shi ya sa ni ban yi mata ba".
Yaya ya daga kai ya kalli Anti ya girgiza kai, cikin
takaici ya yi tsaki a hankali ya će, "Amma kin san in ba da
Rukayya za a yi tafiyar nan ba sai dai kowa ma a fasa
tafiyar da shi, don ba yadda za a yi kowa ya tafi ita a bar ta a
Nijeriya. Kai Maryam ban san me ya sa yarinyar nan ta
tsone miki ido ba?". Cikin bacin rai da tsaurin ido da rashin
iya magana, Anti Maryam tana fada ta ce "Kai Sadik bari na
gaya maka, Rukayya ba ta kai matsayin wacce za ta tsone
min ido ba, balle har ta dame ni a raina. Na lara tun da ka
sauka a gidan nan kake nema ka shiga rayuwata a kan
wannan yarinyar, to passport ne ban ga damar yi da ita ba
don haka ban yi mata ba, in kai ka damu da ita za ka yi mata
ai sai ka yi mata, na ga matsayin naka na oga mai cikakken
iko, sai ka dauke ta ku tafi ku biyu ni na fasa zuwan in wata
tsiya ce".
Yaya ya ce "Maryam ni kike fadawa wannan
maganar...?". Ta katse shi, ta ce "Na fada in ka isa namiji a
gidanka sai ka dauki mataki a kan maganar da na gaya
maka". Yaya zuciya ta kawo masa wuya, ya taso zai banke
ta sai kuma wata zuciyar ta sa ya kyale ta, ya ce "Wallahi
yau kin ci albarkacin 'ya'yanki, kuma za ki ga matakin da
zan dauka, zan nuna miki ni namiji ne a gidana, kuma na isa
mai cikakken iko a gidana". Yana huci ya dauki dan
33
makullin motarsa ya fice daga gidan, ita kuma Anti ta shige
dakinta ta kulle. Wannan ita ce irin marabar da Yaya ya
samu a'dawowar sa gida Nijeriya.
Washegari misalin karfe shida na safe aka yiwo waya,
Yaya ne ya dauka ashe daga Kano ne gidan su Anti
Maryam, an bugo don a shaida mata mahaifiyarta ba ta da
lafiya. A lokacin nan Anti tana barci. Bayan ta tashi Yaya
ya shaida mata batun wayar, kuma ya shaida mata a kan ta
shirya yau ta je ta dubo ta.
Duk da 'yar tsamar da take tsakanin Yaya da Anti,
amma ya ba da mota a kai ta zuwa Kano, sannan ya ba ta
wasu kudi ya ce ko za a nema don magani, kuma ya ce ta
gaishe ta shi ma in ya sami lokaci zai zo ya duba ta. Karfe
tara na safe Anti ta kama hanyar Kano ita da 'ya'yanta, ta bar
mu a gidan daga ni sai Christy sai Yaya Sadik.
Rana Yaya Sadik yana falo yana kwance a kan kilishi
yana karatun jarida sannan ga talbijin ya kunna tashar MBС,
ga falon ya turare da kanshin turaren airfreshener, ga sanyin
'air condition', ya kwala min kira. "Rukayya, Juice nake son
sha". Na ce "To". Na zubo masa na hado da kofi na kawo
na ajiye a gabansa, ya ce "Yauwa na gode 'yar kanwata". Na
yi murmushi na juya zan tafi, ya ce "Rukayya ba ki karashe
aikin ki ba za ki tafi, ba ki zuba min a kofi ba". Na zo na
zuba masa. Ya ce "Ke ba ki sha ne.? Ki dauko kofi mana ki
diba, na dauko kofi na zuba ni ma, zan tafi dakin girgi ya ce
min "Wai ke ba ki zam afalo sai dai kullum kina dakin
girki?". Na ce "Ina girki ne". Ya ce "Ki barwa Christy mana
ta girka". Muna zaune a falo Yaya yana tambaya ta zancen
karatuna, ya ce ya ga sakamakon jarrabawata amma bai ji
dadi ba da sakamakon ya kasance ba yabo ba fallasa, don shi
yana son ya ga na yi karatu sosai na sami ilmi kamar yadda
ya kamata, kodayake yanzu ma ba laifi, in muka tafi
England zai nema min makaranta na yi certificate a can.
34
A nan ne Yaya ya yi min wata tambaya da ta daure min
kai, "Rukayya ko ba ki da sha'war ci gabå da karatun kin fi
son ki yi aure? Don kada na danne miki hakkinki". Na ce
"Nì kam Yaya na fi son na ci gaba da karatuna". Ya ce "A'a,
in dai kina da wani wanda kike so ki fada min". Na ce "A'a
Yaya ni fa ba ni da wani wanda nake so". Ya ce "Haba
Rukayya yaya za a yi kyakkyawar yarinya kamar ki ta ce ba
ta da saurayi". Na ce "Yaya wallahi ni fa da gaske nake yi
maka ba ni da wani saurayi". Yaya ya yi dariya, ya ce
"Rukayya kina ba ni dariya, ni ma wasa nake yi miki dama
don na ji bakin ki ne kawai". Ana yi kiran sallar La'asar. Ya
tashi ya tafi masallaci, ni ma na tashi na tafi don na gabatar
da tawa sallar.
Da daddare bayan na kammala abincin dare, tuwan
samobita miyar danyar kubewa, don yana daya daga cikin
abincin da Yaya yake so, sannan na hado da juice din citta
na jera a kan tebir. Yaya ya zo zai ci ya kira ni, wai sai na zo
mu ci tare don shi ba zai ci abinci shi daya ba. Na zo muna
cin abinci Yaya ya zuba min ido tamkar bai taba kallo na ba
sai wannan lokacin, har abin ya ba ni mamaki, na ce "Yaya
lafiya kuwa na ga ka yi shiru ka daina cin abincin kana kallo
na, ko na yi maka wani laifi ne?". Ya yi murmushi ya ceе
"Rukayya ba ki yi min wani laifi ba, tunani kawai nake yi".
Bayan mun gama cin abinci ya ce "yana so na raka shi
U.T.C. don zai yi sayayya 'shopping'. Mun fita zuwa U.T.C.
Muna shiga Yaya ya ce na zabi duk abin da nake so, dauki
cosmetic da kayan zaki kamar su chocolate da biscuits,
Yaya ya ce 'yan wadannan kayan sun ishe ki?". Na ce "E sun
isa". Muka fito daga U.T.C. mka zarce yawo cikin gari. Mun
je manya-manyan otal din Abuja kamar su Nicon Hilton
Hotel, Sharaton da dai sauransu, muna tafiya muna hira а
mota, a nan yake shaida min warwarayena ya sayo min wasu
sabbi wadanda ma suka fi wadancan kyau. Sai mun koma
gida zai bani. Ya juya yana kallona, ya ce "Ban ji'kin ce 35
komai ba, ko ba ki so ne?". Na ce "Na gode". Ya yi
murmushi ya ce. "Kai Rukayya muryarki ta yi min dadi,
kamar kada ki daina yi min magana, don kamar kina yi'min
sarewa a cikin kunne ne".
Na yi shiru ina tunanin abin da Yaya ya ce, wai me
yake nufi ne? Ni ban gane abin da yake nufi ba, yau ya
koma kamar wani sa'ana, Ya sake yana yi min surutu har ba
ya son yawan da muke yi ya kare, can ya juyo ya се
"Rukayya yanzu shekarun ki nawa ne?". "Shekaruna sha
takwas". Yaya ya yi murmushi ya ce "Lallai har yanzu ke
yarinya ce, don ni yanzu kin ga shekarata talatin da takwas,
na zama tsoho ko?". Na yi murmushi na ce "An dai
manyanta kam". Ranar ba mu muka koma gida ba sai sha
daya na dare.
*** *** ***
Washegari da safe bayan Yaya ya gama karin kumallo,
ya kira ni ya ce "Rukayya ki shirya yanzu za mu tafi Kano".
Na ce "Yaya lafiya, ko dai mahaifiyar Anti ce jikinta ya
tsananta?". Ya ce, "A'a ina so mu je ne ni da ke, amma ki
debi kayanki na sawa don zamu dan jima, za mu kai kusan sati a can".
A hanya ne Yaya yake shaida min, wai yau da safe ya
aika ofis dinsa a kan a samo min fasko da biza ta tafiya
England nan da sati daya. Mun isa Kano misalin karfe biyu
na rana, gidan Inna Sa'a.
Inna Sa'a ta yi mana maraba da zuwa sannan ta kawo
mana ruwa da abinci. Bayan mun ci mun huta na tashi don
na yi sallar Azahar shi kuma Yaya ya ce zai tafi gidansa na Sani Mainagge. Sai da dare zai zo hira wajen Inna.
Bayan na yi sallah ina zaune, Inna take tambaya ta ina
su Saima da Nusaiba, na ce "Ai Inna tun jiya suke garin nan tare da Anti Maryam, mahaifiyarta ce ba ta da lafiya tana kwance a asibiti, shi ne aka yi mata waya ta taho".
36
Inna ta ce "Assha, ai ni ban sani ba da mun je mun
dubo ta, amma bari in wannan yaron ya zo sai ya ba da mota
a kai mu mu dubo ta, tare da su Aisha za mu je in sun zo yi
masa sannu da zuwa.
Bayan sallar Isha ne Yaya Sadik ya zo, a iokacin nan su
Yaya A'isha da Yaya Maimuna duk sun iso, haka ma Hadiza
ta iso duk don su yi wa Yaya sannu da zuwa, mun hafu ni
da Hadiza, daman mutuniya ta ce, muka rungume juna muna
murna, muka shiga dakin Inna Sa'a, can cikin muna labarin
mu, mun bar su Yaya da Inna a falo su kuma suna hirar su.
Inna ta ce wa Yaya "Ashe Hajiya Sala ba ta da lafiya?
Ai ban sani ba". Yaya ya ce "E ba ta ji dadi ba, ita ma
Maryam din tana nan ta zo duba ta.
Inna ta ce "To ai sai Usman direba ya kai mu mu dubo
ta tun da tawa motar tana gareji wajen gyara".
Yaya Sadik ya ce "Inna ku kyale su kawai ba za ku je
dubo ta ba, ni ma ai ban je ba". Inna ta ce, "Me kuma ya faru
da zai hana ka zuwa dubo ta? Ai bai dace ba, in kai ba za ka
ba ai mu bai kamata mu ki zuwa ba". Ya ce "Wallahi Inna
ba komai ne ya hada mu ba a kan Rukayya ne, ni ban san
me ya sa.yarinyar nan ta tsone mata ido ba, yadda Maryam
take azabtar da Rukayya abin sam ba dadin ji, da na yi mata
magana shi ne ta gåggaya min bakaken maganganu tamkar
wani yaron ta". Inna ta ce To ai hakuri ake yi, aure da
haihuwa sai hakuri, Maryam kam ba ta kyautawa, amma
albarkacin 'ya'yanta sai ka je ka gaishe ta, don bai kamata ka
ki zuwa ba ko don albarkacin mahaifinta ai mutumin kirki'
ne".
Yaya ya ce "Inna ba wai na ki na yi hakuri ba ne, in
ban hakura ba ai ba zan ba ta motata a kawo ta Kano ba".
Yaya A'isha ta ce "Wallahi Yaya Maryam ba ta da
mutumci" Inna ta ce "To fadi ba a tambaye ki ba". Yaya
Maimuna ma ta ce "Inna gaskiya ne" Inna ta daka musu
tsawa, ta ce "Ni fa ba na son tone-tone". Yaya ya yi
37
a
murmushi ya ce "Inna duk abin da yake faruwa ina sane,
don ko kaya na aiko na ce ta ba ku ba ta bayarwa". Inna ta ce
"Kai kuma wa yake fada maka". Yaya ya ce "Inna yanzu
zancen duniya yana buya ne?". Inna ta ce "Gaskiya kam ba
ya buya, don yanzu an daina kiwon dabbobi mutum ake
kiwo, mutum ba shi da gadon ka amma yana da gadon
maganarka".
Yaya ya ce "Don haka Inna nake so na koya mata
hankali, ta san cewa ba kowa ne mutum ake yiwa gatse ba a
kwana lafiya. Don haka Inna, yanzu na riga na yi shirin
komawa England amma zan yi shekara hudu a can, sai dai
duk bayan wata uku zan rinka zuwa gida ina duba ki. Kuma
na riga na yanke shawárar ba zan tafi da Maryam ba zan
bar ta a nan gidana na Sani Mainagge, za ta taso daga Abuja
ta dawo nan Kano".
Ni da Hadiza a daki muna hira, amma da muka ji Yaya
ya fara magana sai muka yi shiru muna sauraron abin da
yake cewa. Sannan Yaya ya ce, "Gobe zan je gidan su
Maryam na shaida mata ta je ta shirya kayanta ta dawo da su
nan Kano, zan ba da mota a kwaso mata don na fi son a
gama komai kafin nan da kwana biyar saboda tafiyar ta ta
zo". Inna ta ce "To me ya sa ba za ka bari ta zauna a gidanka
na Abuja ba, tun da dai ka ce ka gama gini, kuma komai da
komai ka gama kintsawa a gidan?". digd
Yaya ya ce "Haba Inna, gidana na Aso Drived ai sai
amarya ce za ta zauna a cikinsa". Duk falon aka kwashe da
dariya don abin ya zo wa kowa a ba-zata, mu ma da muke
daki sai da muka jinjina don mamaki, Hadiza har da wani
tsalle tana doka kafa, tana cewa "Kai mun gode Allah"d
Inna ta ce "A ina kake neman auren?". Yaya ya yi ya ce
"Ai neman auren nawa ita ma wadda zan aura din ban sanar
da ita ba, kodayake na san