Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
5 / 7
suna hawaye. Wannan sako ne ya sanya Farida ta mance da Balala don ta bar wurin da sauri.... 102 Mafiyan Masoya-2 Rahma Abdulmajid TAKWAS Ta kalli faffadan farin falon da babu komai sai fitilu da kura, tayi ajiyar zuciya. Koda kuka bai zo idanunta ba amma ta ji wata karaya hade da kewa sun yi wa zuciyarta dafa-duka. ta dafa karfen wundon tamkar tana neman agaji na ya taya ta tilasta kanta yin murmushin da zai 6oye wa har zuciyarta irin karayar dake tattare da ita. Nan ne gidan da ta zabi ta koma nesa da garinda aka santa ido-da-ido. Wannan ya faru ne bayanda suka amince da kulle duk wani abu da yaragu da sunan mahaifinsu kasancewar komai ya kare saura wanda in za a rike za a sha wuya ne kawai a kiyaye sunada a ganinsu tuni an yi masa illa. Don haka fatansu a kashe sunan Na`ibi don mancewa da abinda ya faru ma dashi. Mahaifiyar Farida ta yi doguwar jinya a Paris inda tana fara samin sauki ta koma kasarsu don zama cikin jama arta ta karasa murmurewa da kuma son yin nisa da inda zai dinga tuna mata danasaninta na jefa mijinta a mummunan hali da tayi wanda ko 103 Mafiyan Masoya-2 Rahma Abdulmajid da ba shi ya kashe shi ba shi ya kashe masa suna. Kanin Farida Shafik wanda ta mallaka masa duk ragowar gadonsu don ya je ya gina rayuwarsa, shi ma ya koma inda ya fi kauriwato kasar Jamus don soma sabuwar rayuwa nesa da duk wani bakin ciki da tambarinda suka fuskanta. A nan gida Farida ce ta tsaya tayi hudubar bankwana ga dimbin ma`aikatansu bayanda ta biyasu hakkokinsu na aiki da sallama, sannan ta yi musu fatan samin aiki a wani wuri.Akasari sun zubar da hawaye musamman matan ciki, amma wanda idanunsa ya bushe bai yi kuka ba kuma hakan ta baiwa kowa mamaki saboda kusancinsa da Farida shine Farid, wanda ashe shirinsa ba na tafiya bane, na bin Farida ne duk inda za ta, kuma hakan ya gabatar mata, duk da tayi musu da shi karshe dole ta amince masa cikin godiya. Ko a yanzu tare suka iso wannan sabon matsugunin na Farida "Gida dadi...gida dadi. Ko da bamu tsira da komai ba a karshen game din nan, koda na rasa har mahaifana a wannan karon battar,na tsira da usilina wanda ko ba komai zai dinga zura ruhi a cikin rayuwar tuna- 104 Mafiyan Masoya-2 Ralıma Abdulmujid baya" Ta shari wata kura a jikin wundon tana dubawa. "Nan ne gidan Father na farko... Koda ba a haife ni a gidannan ba nan aka haifi Kanina Shafik, lokacinda Father ya sai wannan gidan bamu da wani suna ban da `ya`yan dan baiwa kuma `yan baiwa... Babu wata me aiki da muka dauka duk da an kawo mu daga Turai. Ni da Father da mummy muka zba Omo da ruwa muka wanke, abin sha`awa abin dadı, mum da dad na komai tare babu wata husuma ko nisa da juna a tsakaninsu, ni `yarsu ina taya su da abinda zan iya daidai shekaruna" Ta kakkane ido don ja da hawayen da ya ciko kwandon idanunta ya fara tsiyayewa ba tare da izini ba. Ta bar jikin wundon da sauri domin ta doshi wata mfakar. Farid wanda bai ce komai ba don bai da abin cewa a fatar baki sai a zuciya ya ci gaba da binta da kallo. "Yau babu Father, babu mom ba dan karamin kanina, daga ni sai wannan gida, amma ba zan karaya ba zan wanke shi ni adai don na sake farawa daga farkon faifai 105 Mafiyan Masoyа-2 Ralma Abdulmajid دو na rayuwar Farida kadaitacciya a rayuwarta Ta shiga bayan gidan da aka tanada a falon don baki ta dauko roba cike da ruwa ta fito. Bata iya foyc mamakinta ba a yayinda ta ga Farid tsayc ya nade kafafun wandonsa ya cire rigarsa ta sama sauransa singileti ya dauko soso da Omo. Bata iya ce masa komai ba kallonsa takkc a hankali ta ajiyc ruwa. "Bakc kadai bace ko yanzu a rayuwarki.. kina da Farid wato ni...ko zaki amince min mu wanke sabon gidan rayuwarki tare don fara sabuwar rayuwa tare?" Ta waro manyan idanunta ta tayi sama da kasa da kanta na al`adarta ta neman tafsiri kan wani abu da bata gama ganewa ba. Ya dan lumshe ido ya yi murmushi sannan shima ya gyada kai na nuna mata lallai yana nufin abinda ta fahimta. "Me zan ce maka Farid?" Ya karbi bokitin ruwan ya fara yayyafawa a fadin falon. "Kada ki ce komai so nake ki sunkuya mu wanke gidan nan tare" Sama da mintuna goma sha biyar suna zube a Kasan falonnnan suna goge shi 10o Mafiyan Masoyа-2 Rahma Abdulmajid da wasu kananan tawulai hudu da Farid ya fita ya sayo musu, amma gaskiyar lamari Farid ke wankewa da iya karfinsa, ita kuwa Farida jikinta a mace take dan goge-gogen babban aikinta shine satar kallon sa da mamaki da tuhuma da shauki da neman tafsiri kan dalilinsa na taimakonta har zuwa wannan mataki na karshe da ma`aikatanta duka basa son hada sunansu ma da kamfaninta balle ita.Da alamar Farid ya lura da hakan shiyasa yake kara samin allurar zage karfi musamman ma da duk lokacinda yake tsayawa ya share gumi sukan hada ido da Farida su yi wa juna murmushi. A haka suka kammala wankewa da tsanewada busar wa sannan Farid ya wuce ya kunna fankar tsaye mai karfi wadda iskar farko ta fara da kado rigarsa da ya rataye jikin `yarsandar ratayar suite da ta ragu a falon. Farida ta fi kusa da rigar don haka a guje ta cafe don kada ta fada jikakken falon ta jike, amma hakan sai ya haifar da wani abu da zai bude sabon shafi a ryuwar Farid da Farida, wato dan karamin akwatin zobe ja ya fado wanda Faridar ta bi shi da kallo ta kuma gane shi da abinda ke cikı a yayinda Farid 107 Mafiyan Masoya-2 Rahma Abdulmajid ke saurin daukewa. A karo na farko kenan da ta dan ji kishi taa son tambayar abinda ba dole bane ta so jin amsar ba. 'Za ka'nemi aure ne Farid?" Ya goge akwatin a jikin wandonsa yana murmushi. "zan dai nemi soyayya kafin aure ko Allah Zai sa na samu?" Tayi murumushin da ta saba a duk lokacinda take son danne wani ciwo. "Bana jin ba Za ka dace ba don duk macen da ta sameka dacentaaa ya fi naka yawa" Yanzu kallonta yake da iya hangen idanunsa yana tattaro dauriya ta karshen tika-tika. "Har ke Farida?" Ta dube shi ta yi fari da ido ta koma za ta rataye rigarsa. "Ni ce kan gaba" "to ki karbi zoben nan a hannuna in har zan iya samin soyayyarki" Ta jima tana jin nauyin juyo wa har da ma rikicewa da jin sabon yanayi, amma da ta samu ta juyo din sai ta sami idanuna cike da soyayya suna kanta, yana mika mata 1 19 IL 108 Mafiyan Maxoya-2 Rahma Abdulmajid zoben. "Ka ce min wasa kake Farid?" "Ban taba wasa da gurbin kia zuciyata ba. Gurbi ne da wanin ki bai taba shiga ba, na kuma gama tabbatar da ba bu me shiga... Ban taba kasancewa kusa dake don wani abu ba sai don kada na nisanci abinda zuciyata ke son kusanta. Mota gida, albashi da matsayi a ofis bai taba zamowa muradina sama da ke ba Farida, wannan ne matsayinki a zuciyata a tun gani na dake na uku har zuwa yau, har kuma gobe" Farida ta dinga kada kai na rikita tana kallon sa tana daukewa. "amma me yasa baka gaya min ba... Oh God! Me yasa za ka kunshe wannan kunshi a ranka kai kaďai? Farid a ina soyayya ta taba kunsuwa a zuciya daya rak babu ko agajin fatar baki ballantana ido?". "saboda bana so na rasa ki, bana so neman kusanci ya janyo na kasa ko ganinkiSaboda kin mini nisa... ba a dukiya ba Farida lokacinda na zo da neman hadin soyayya kin riga kin bai wa wani..Na zauna ina gaya wa zuciyata karyar wata ran za ki zo gareta in kika gane ta, amma a da ranar 109 Mafiyan Masoya-2 Rahma Abdulmajid ban tayi da auren soyayya kika zo... san yaya zan yi ba. Ko a yanzu da nake gaya miki, duk da ina fatan ki amsa soyayyata din, amma in baki amsa ba din ya isheni na sauke nauyi....ya ishe ni na ji na baki gudunmuwar tarayya da baki tabbacin ba ke kadai bace a rayuwar da kike zaton ke kadai ce, ki sani wani na tare dake yana neman ku yi tarayya a duk daci da dadi na rayuwarki" Farida a yanzu murmushi take tana kallonsa, zuciyarta ta kwanta da shi matuka, ta ji dadin abinda yake fada mata kuma tana son ganin hakan a aikace "Farid kana sona?" Ina son ki Farida... Ina son in rayu 59 dake a sauran abinda ya rage wa rayuwata "Ka ko same ni da yardar Allah...Ban taba kinka ba, amma ban taba bari zuciyata ta yarda ta soka ba don kada na sauya wa yadda ka zo gare ni matsayi, amma yau zan fara son ka a sake babu kaukautawa, zan bude sabon shafin rayuwa don kai" S da da 1a k 1 32 31 a *** *** **** Tarihin fara soyayya tsakanin Farida da Farid ya tsaya inda masoyan suka shiga Mafiyan Masoya-2 Rahma Abdulmajid sabuwar rayuwa ta farinciki ta inda bacci ke raba su. A yayinda duniya ke jiran sake Sullowar Faridar wadda tun bayan me aukuwa ta auku aka dena jin duriyarta, ba a fitar da ran za ta sake motsi ba kasancewar an santa da salon daukar gayya, amma ga mamakin jama`a bacewar Faridar ta ci gaba ba tare da kowa ya san me take ciki ba kasancewar sun lullube soyayyar tasu ita da masoyin nata har suka amince da yin aure babu wanda ya ji sai a ziyarar da suka kai wa mahaifiyar Farida wadda har yanzu take kwance a kasar Faransa ban da ido babu abu me motsi a jikinta *** *** **** Farida zaune a hannun kujerar guragun da mahaifiyarta ke kai hannayenta na matsa hannun mahaifiyar tata tana matse hawayenta cikin murmushi. Suka kalli Farid wanda ke tsaye cikin tagumi Maman tayi murmushi ta dan motsa baki kamar tace wani waani abu amma babu dama. Farida ta amshi maganar da alamar ta san me take son tambaya "Shine mum...shine sabon masoyina 11 Mafiyan Masoya-2 Rahma Abdulmajid da zamu yi aurc nan da wata guda in kin sa albarka....muna són junanmu fiye da inda kike zato, zamu sake gina kanmu nesa da rigingimu, zamu sake zama' iyali a lokacin kin sami lafiya ki zo ki zauna fare'da mu da jikokinki Ko Fidi?" bokm : i Farid ya gyada kai. "insha Allahu Mama..Allah Zai baki lafiya ki kasance tare damu ckin annishuwa" *** *** **** Wannan haduwa a asibiti ce ta isa hannun yan jarida har suka dauka suka sami na bugawa cewa Farida ta zamio sabuwar mutum za ta yi aure. Ibrahim Balala na zaunc a mazaunin da ya saba zama wato Rafar beneyana motsa shayinsa kahsa a sunkuye yana sauraron sakatare. mesa kin godiva "Me nene;abarin Faridan sohon "Jiya ta bayyana wasu jaridu sun kawota" Da sauri Ibrahim ya ago kaf. "Me suka ce a kanta? Bani jaridar" Sakatare ya jatyo jaridai a aljihunsa yana murmushi ganin ya kamabin faranta 12 Mufiyan Masoya-2 Rahma Abdulmajid ran me gidansa. "Ta bayyana a faduwar karshe inda ta amince da Kaddararta za ta auri tsohon yaronta mara asali wai shi Farid" Ibrahim ya saki kofin shayin ya bude jaridar yana dubawa a haukace. Bai san ta inda kishi fishi da haushi ya shige shi ba "Farida za ta yi aure? Farida za ta so wani kenan bayan ni?" Sakatare ya tsaya yana kallon mamaki. "nan da wata daya Farida za ta yi aure? Farid da na sani shi za ta aura? Son sa take?" "Ranka ya dade kana sonta ne har yanzu kake so ku yafe wa juna bayan duk abinda ya faru? Maimakon ya amsa sai ya haukace a falon ya fara yayyaga jaridar yana dukan kirjinsa. "wa ya ce maka bana son ta? Bata isa tayi wani aure ta bar ni ni kaďai ba" 113 Mafiyan Masoya-2 Rahma Abdulmajid TARA Ango da Amarya sun yi sallama da masu taya su murna suka hau motarsu su biyu don kai kansu ga sabon gidansu su kadai. Farid ke tuki yayinda Farida ke jingine da jikinsa cikin wani nashadi da ya hana hakoransu gajiya har zuwa kofar gidan nasu inda suka sami mota ta kakare kofar gidan da mutum a gabanta tsaye. Farid bai gane ko wane ne ba sai kashe ido yakc yana lekawa a yayinda Farida ta tashi zaune zumbur don ta gane Ibrahim Bally. A waje suka faka motar Farid yayi ta maza ya sauko don ganin ko wane ne amma Farida ta gagara zama a motar ta biyo shi. 'Bally? Me ka zo yi mana a daren amarcin mu ?" Tayi saurin fara magana kafin Farid Ya dube ta yayi murmushi ya kada kai sannan y dauko farar tuta yana kadawa "Na zo1 na ba da gari na yi miki 114 Mafiyan Masoya-2 Rahma Abdulmajid murna cewa kin cinye fadan namu, kin yi nasara, kamar yadda kika ce kin san ta yadda za ki kayar da ni a ruwan sanyi" Ya juya baya a yayinda Farid ya doshi bayan nasa, amma Farida ta rike shi da kada kai don ta fahimci sanyin da mutumin nata ya zo da shi. "Na zo ne na mika wuya na yarda da kin yi min dukan karshe da ba zan iya ramawa ba" Hakika kudi, da suna, da rayuwa duk sun tafi a kan yakin mu Farida, amma ban taba mafarkin ke za ki tafi ba sai yau da na ga da gaske kin yi aure za ki bar duriyata da gani sai wajc. Ko ba komai ke in kin tuna zafin abinda ya faru za ki iya samin me kawar miki da shi yayinda ni יי bana jin zan samu" Ya dan lakaci hancinsa a yayinda ya Karaso gaban Farid dake hucin jiran artabu "Farid kai ne zan ma murna don yau za ka san Faridar da ba ka san ta ba a da. Farida a matar namiji ya kammala kamalar kamilallu. Kada ka yi wisa da magana ta Jomin ina da shaidar nine na mijin farko a 115 Mafiyan Masoya-2 Rahma Abdulmajid rayuwar Farida kamar yadda take matar farko a rayuwata ta waycwa da magega matsayin mace. Wannan Wani gwaji ne da ba za mu manta da shi ba amma ina s,kа kwatanta mantar da Farida ranakurк na rayuwarta in har kai na miji ne, ba faura auren ba ne nasarar ba, mantar daa wannan mintocin farkon a nan yakin yake" A yanzu ne Farida ta fahimci muhimmancinta na shiga tsakanin mazajen a yayinda ta lura da Farid na dunkula hannunsa na dama bayan da yansaki hannunta da ya rike da fari.Tar kamo hannun ta sake zura duka nata bjyn a cikin su Bb Bent sti "mun gode da shawarwarinBalala, ka je gida muna bukatar lokagin junan yshe ni da miji na ba na 3rd party ba1 Ta wuce da Farid wanda ke waigen Balala zuwa cikin gida suka bar shitsayg KS ***** ωςλ λς κ « 1..A gefen gadonstaune yakhiyana ake kamar, harsyanru kalmomin Balalgina yanshiramma bayanso amarya ta gang ya araya musamman nda lake la zumudvida 116 Mafiyan Masoya-2 Rahma Abdulmajid nuna murna tana ba shi labaran muhimman abubuwanda suka faru a bikin. Farida ta Karaso da dan karamin kofi na energy drink ta tura shi gefen gadon ta zauna kusa da shi "Baby na ba dai batun Ibrahim ne ke rarraba hankalinka ba?" Ya dan juyo yana neman abin gaya mata a yanzu amma ya rasa sai turo nunfashi. "ba abu ne me sauki ka iya mancewa da wani babban abu mafi dadi daya taba faruwa a ajuwarka ba Farida?" Ya dan kamo fuskarta ya matso da ita kusa da tasa. "Ina mia à ce hine wannan na miji ná farko a ravuwarki" Farida ta lumshe ido na dan wani lokaci sannan ta lalubi mazaunin zuciyarsa ta dora kanta. <<7a ka iya mayar da kanka in ka so Farid. Kavi komai ka zamo namijin farko da zai bani wani salon a rayuuwa da zai yaudare ya juya mafarkina. Na san za kaа iya tuma 1 Mafiyan Masoya-2 Ralma Abdulmajid tunaninka kai kaďai. Farid kada ka manta mutumin da yayi maka takamar shinc namijin farko a rayuwata shi dinnc dai wanda ya koya min darasin bakin cikin da sai kai ne ka goge shi, shi ya kakkarya zuciyata ya gustsittsira wanda sai kai ne ka sake hade min ita wuri guda. Don Allah ka yi komai na karkade wannan darussansa daga kwanyata. Na shigo rayuwarka ne don ina so in zamo sabuwar Farida wadda bata da tarihi sai Farid" Farid ya dago ta ya sake zuba mata ido da kallon nacin kauna. "Farida ki yarda zan yi komai, in nace komai ina nufin kowace irin dabarata don mayar da kaina na farko na karshe a rayuwarki" "Komai Farid kayi, ni ma ina nufin komai kayi ka karasa sauyanin da ka dauko yi, na san inda na kai yanzu ba za ka sha wahala ba" *** *** *** Tatsiyayo giyar wuskin a dan siririn 118 Mafiyan Masoya-2 Ralma Abdulmajid kofi ta dunfaro shi, ganin idanunsa a kanta baya kiftawa ya sa ta rage sauri a tafiyarta zuwa mazauninsa domin ta sami damar yin duk wata tafiyar rausaya da ta san ta taba yi ta ja hankalin namiji da ita har ta iso gare shi ta dogara da gwiwarsa bai dena kallon ta ba "big boy, ka kora wannan kofin ka hada da ni ka ga in za ka kwana da tuna wata abu Farida" Ibrahim yayi murmushi ya karбi kofin ya zura masa ido. "me nene aikin wannan shi kadai kafin naki "Aikinsa shinc ya mantar da kai rayuwar baya da nauyinta, ya sa ka zamo sakayau a hannun dadin ka wato ni "A cikin rayuwar baya har da Farida?" Ya bukata Ta langaba wuya "ita ce kan gaba" Yayi murmushi a hankali ya saki kofin kasa ya fadi ya fashe. Ban taba neman abinda zai mantar 119 Mafiyan Masoya-2 Rahma Abdulmajid da ni Farida ba ko a halal ballantana a haram irin giya, masoyin da ya nemi manta masoyinsa bai kai rukunin so ba Fresh Lady.Tun 'a baya ban nemi abinda zai mantar da ni Farida ba ballantana Faridar yau, wadda ke cikin kwalliya da farinciki na amarci.." Ya ture ta ya mike tsaye yana duban sama "Tayi kyau ta tuna min kyawunta na farko a ranar amarcinmu, amma wai yau tana jikin wani namiji ba Bally ba kuma tana farinciki. Ni kuma gani a nan ina cikin kadaicin da ko a Stadium nake me cike da dubban jama`a zan dinga ji na ni kadai don babu Farida a jikina a lokacinda na fi bukatarta" Ya daki teburin gilasin da hannunsa wanda ya fashe ya yanke shi, amma bai ji ba ya soma kuka. "Farida mc yasa kike samin hanyar ci na da yaki ne kullun? Duk nasarata yau kin zubar da ita da nasarar da ba zan taba yi ba.Kin sake shuka min rayuwar kadaicin da zan ji tamkar a kabari na nake 120 Mafiyan Masoya-2 Ralma Abdulmajid tunda ban zaci akwai me irin ciwo na ba, ko matar da a kayi wa kishiya a daren da mijinta ke wajen wata in ta gan ni za ta gode wa Allah da Ya tsirar da ita daga tafasa irin tawa... Me yasa kike nasara a kaina Rida? Ko dai sirrin shine don ba zan iya dena son ki ba?" Jinin da ke zuba a hannunsa da ke 6ata fararen kayansa ne ya tsorata Fresh Lady ta dan karaso don ta agaje shi, amma ga mamakinta sai ta ga ya shako ta ya zare ido yana nishi dai dai. A tsorace ta kasa cewa komai har lokacinda ya zaro wasu daurin daloli ya watsa mata. a "Wannan kike so? To ga su kwashi ki fita, amma ki sani ni ba mace nake nema ba, Farida nake nema, ita nake so matsayin abin son zuciyata ba mace ba. Ki bar nan kafin nayi wani abu da ya fi haka lalacewa" Tana makyarkyata ya daka tsawa, ta kwashi kudin ta fice. Bally ya tafi da durkuso a cikin jininsa da ya dige ya fara kuka wiwi 121 Mafiyan Masoya-2 Rahma Abdulmajid **** **** **** Mahdi yayi dariya har da tintsirawa. "kana nufin sai da kayi arba'in sannan ka fito sai kace me jego?" Farid yayi dariya יי "in kana zaton wasa nake lissafa mana ka gani...yau auren mu kwana arba'in wallahi, ba za ka fahimta bane tunda kai ban da kanka babu wanda kake so, ni ko ban da Farida babu wanda nake so.. .yanzu haka da ba dan kada na gundire ta ba inna koma Allah wani arba'in din zan kara yi" Suka tafa "To dakata. Yanzu ba batun arba`in ba, ka ce Farida ta baka wuka da`nama na ka sauya ta don ka zamo na mijin farko a tare da ita kana ga haka zai yiwu?" Farid ya kada kai. "zai yiwu ko ba zai yiwu ba ba bukata ta ba kenan. Bukata ta ita ce in sauya Farida daga irin matar da Ibrahim Hadi ya taba sani zuwa irin nau'in macen da zan iya zama da ita" 122 Mafiyan Maxoya-2 Rahma Abdulmajid Mahdi ya jima yana gyada kai "Ko za ka iya zana min irin matar da kake so?" "Kana nufin kace ka manta zane na?" "Wancan na da lokacin da muke kauye ban manta ba, amma tabbas na san ya sauya tunda ka auri irin Farida don..." "Ko daya cikin zanen babu wanda ya sauya,kuma Farida nake son mayarwa hakan da karfin soyayya" Mahdi ya fara kidayar yatsu cikin mamaki. "zanen ka fa shine kamar haka...Mace mara aiki sai rainon yaranka, macen da bata kwalliya sai daddare in ka dawo,Macen da bata ja da kai a komai sai yi na yi bari na bari...Macenda bata hulda da kowa sai wanda ka yarda ko biki ko gaisuwa ko jaje sai wanda ka amince... ina jin sune zanen ko ka sauya wasu ne?" Sune dai mutumina ka cika shegiyar kwanya wallahi sai ka сe CD" "Kuma su kake son ka mayar da ba ma wata 'yar Sakandire ba Faridar da ta 2 123 Mafiyan Masoya-2 Rahma Abdulmajid san duniya duniya ta san ta? Farida me kwana a ofis duk da tana shugaba don son aiki.. Faridar da a da da tace ina zuwa bari in je gida in yi wanka za ka ji ta bugo waya da ga China? Duk ita za ka yi wa wannan sabon horon ba ma wata yar jami`a da asalinta daga kuayenku take ba?" "Kwarai kuma zan sake baka mamaki kamar yadda na baka mamaki da na auri Faridar da ka zaci ba zan taba isarta kallo ba" "mutumina kayi hattara! Ka kunna hasken aurenka kada ka kashe shi kwana kusa da taurin kai da son ra'ayin rikau" "Ba ruwanka malam. Kai naka ido.. komai sai ka ce mutum ba zai iya ba anya ma ba zan' dena shawara ko gaya maka sirrina ba kuwa?" "Allah Ya baka hakuri, da alamu dai bana tababa zaman kwanaki arba'in na soyayya zai sake nanata adadin a zaman tinkiya". *** *** **** Farid na tsaye a kicin din yana yanka musu 124 Mafiyan Masoya-2 Rahma Abdulmajid lemo Farida ta garzayo da gudu ta rungume shi ta baya. "Ridy tayani murna.... taya ni raba murnan nan kada tayi min yawa" Ya liko hannayenta a kirkinsa ba tare ya juyo ba yana dariya.. "Me muka samu Baby na? Kasa murnan hudu ki ba ni kashi uku kada ta wahalar min da murmushinki" Ridy.. na sami Offer. Mister Kosvisky abokin Father ne yake son ba ni Merketting Manager na kamfaninshi ba tare da an yi ko interview ba, yace yana son ya ga yadda zan kayar da kasuwar kowane me gasa da shi ne wannan zai zamo dalilin samin kason farfado da kamfanin mu na.... Bata karasa ba Farid ya ajiyc wukar a hankali ya juya zai fita. Da sauri Farida ta ruko shi. "Hey! Ridy me ya faru ne? Na bata maka rai ta wani wuri ne?" Ya langaba kai na tausayin kai. "Ban san duk kokarin da nake na in yalwata miki bai isa ba sai yanzu" 125 Mafiyan Masoya-2 Rahma Abdulmajid A gigicc Farida ta soma kada kai. Nooo! Sam! Ba haka bane baby...Wallahi ba kudi ko wani matsayi nake yiwa ba...me zan nema bayan duk abinda kayi min..Farid ko wanke gida na da muka yi tare a ranar da ka gabatar min da soyayyarka ya ishe ni koshi ballantana abubuwanda kake yi min. Don Allah ka yi hakuri ba haka nake nufi ba" Ya ruko hannayenta yana dubawa. "To me zai sa ki je ki wahalar da kanki kina wani aiki?, ki takura wadannan kyawawan yastun da rubutu bayan na dauke miki komai kuma zan iya ci gaba da kwadago don ki ji dadi har iya rayuwata um Ruhina" Farida ta tallabo fuskarsa a zarazaran yatsunta. "Baby na san kana komai ne don ka faranta min rai, amma aiki ba don komai nake so ba, sai don an raine ni da aiki, sai na ji kamar bana nunfashi in babu gwagwarmaya a gabana wanda ina jin dadin yin ta fiye da duk wani wasa. ka daure ka bar ni na yi aikin nan ko da 126 Mafiyan Masoya-2 Rahma Abdulmajid kyauta ne" Ya kura mata ido na iya lokacin da ya janyo maganadisun kaunarsa da ya janyo karaya a zuciyarta. "Baby bana so kiyi aiki...ki daure ki bar abinda zai dami masoyinki mana um rayuwata? Kada ki manta kin bani wuka da nama na in iya sauya rayuwarki, kuma ina son na cire ki daga irin rayuwar da za ta sanya na ji akwai wani na mijin da bani ba a wata tsohuwar rayuwarki,ina so in nisanta ki da duk wani zubi naki na da da zai iya farfado da waccan Faridar da kika ce na cire a zatin ki...Don Allah kiyi min wannan alfarmar mana" Suka sumabci juna na tsayin lokaci sannan Farida ta tsawaita dubansa cikin karaya "Ina matukar son aikin nan.. ban san za ka hana ni ba.. amma tunda baka so na bari" Da sayuri ya rungume ta idanunsa a lumshe yana nanata godiya, Fairda wadda ta karbi rung nar kuwa idanunta kallon kofa suke do ta kasa rabewa tsakanin 127 Mafiyan Masoya-2 Rahma Ahdulmajid dumin jikinsa da tafasar ciwon asarar aikinta da take *** *** Katon fili *** Katon gida a cikin na shukc-shuke ya ji fitilu da kwalliya irinta gargajiya, girman ne ya lamushe jama'an da ke kara-kaina suna ta aiyukan taryar baki, maza akasari da dogayen riguna da rawani mata kuwa da laffaya. Babban falon ko ina ka juya cure yake da manyan shimfidar abinci da kayan lambu masu iya daukar cikin mutum ashirin-ashirin. Farida da Farid na can zaune kusa da mahaifiyarta wadda a yanzu take cikin gidan nata mahaifin a birnin Asmaran kasar Eritria wadda tun bayan da wasu sassan jikinta suka soma motsawa har ta fara samin baki ta bukaci a kai ta cikin 'yan uwanta dake jibge a gidan gadon don yin zaman jinya. Wannan shine zuwan Farid na farko garin duk da farida ta zo wajen sau uku duba lafiyar mahaifiyartata tun bayan dawowarta, wannan ya sanya mahaifiyar ta 128 Mafiyan Masoya-2 Rahma Abdulmajid sanya kowa ya taya ta murna da bikin murna inda dangi suka cika ko ina aka yi wa Farid da Farida shigar amarya da ango na kabilar Tigre aka yi rawan gargajiya da wake-wake, aka ci aka sha aka gaggaisa har zuwa dare inda Farida ta dauki mijinta zuwa kallon wata tiyata da za a yi wasu wasannin kwaikwayon na kan Stage. A wurin kallon suna makale da juna ita da Farid cikin annishuwa da duhun dakin tiyatar dukansu suna cin cingam don kara gauraya nunfashinsu da kamshi wanda a yanzu suke shaka. Wannan ya sanya suka bukaci kara cin wani abu bayan da aka kammala tiyata ta farko kafin a shiga ta biyu. A dan falon kofi da guggurun ne wani dogon saurayi me

Chapter 5 of 7