Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
2 / 7
dora musu asara a wanda suka saya lallai da hannun su za su karyar da wanda suka sayar, ta nan sun hutasshe ni" Ta zauna da sauri "Ba mu da isasshen lokaci don in suka kai sha biyu ko da minti talatin ne na gobe za su sami riba ko yaya wadda ni kuma na ke son hanawa. Kana da awoyi goma sha biyar ka nuna mana kwarewar ka don samar da hujjojin ga wannan zato da tuni su Bally ke kashe kudi don kada ya tabbata" Farid ya gyara tsayiwa don maye gurbin fargabanrsa da kwarin gwiwaa. "Bani awa sha biyu kadai ki cire uku" Farida 1a kwashi Jakarta ta sake tura masa wata doguwar takarda. 25 Mafiyan Masoya-2 Rahma Abdulmajid "Ga jerin jaridun da za ka karanta da jerin wadanda za ka tura wa sakon hasashen don sune ma`abota kasuwar hannun jari ke hulda dasu. kada ka manta wannan ne gwajin ka na farko...ka kasance online zan je wani taro, amma zan kasance tare da kai online" Ta fice daga ofishin tun kafin ya fita. "Best of luck" 20 Mafiyan Masoya-2 Rahma Abdulmajid ☑ C τ BIYU Sanye da jan gajeren wando da farar singileti yana dauke da kofin jan shayi yana motsawa ya doso kofar da ake kada wa Karaura. "Please am coming" Budewar ke da wuya sai ga `yansanda guda uku sun bayyana a gabansa. "ko kai ne Wilson Albert?" "Yea nine akwa wani abu ne?" Wanda yayi tambayar ya juyo ya dubi ragowar guda biyun. "Arrest him" Suka shige shi yana kokarin binciken ko menene amma basu tanka shi ba suka jefa shi a mota. *** *** *** Ibrahim wanda ya tara jaridu a gabansa ya duba duka labaran babu sa`Ida ga kamfanin su ya yi jifa da waccan yayi jifa da wannan. Baban gida dogon saurayi da ke aiki da shi yayi biz sai wayoyi yake bugawa amma babu wadda aka 27 Mafiyan Masoya-2 Rahma Ahdulmajid dauka. Yajuyo ya dubi Ibrahim "Ranka ya dade abu kamar hadin baki? Duk suna ringin amma an ki dagawa. Ko kuma duka manyan brokas din sun shiga taro ne?" Ibrahim ya zaro ido don huce a kalla rabin fishinsa a kansa. "Kamar hadin baki fa kace? Bama hadin bakin bane kama ne? Da alamar ba inda za ka a wannan aiki don har a gama halakar da mu ba za ka san ina aka dosa ba. Hannun jarin kamfani uku da muka dogara da su a matsayin kadara tun ba a fara komai ba su taru su fadi ka ce hadin baki? Muna kiran duka brokas basa dagawa tunda sun san ceto zan so a kawo ka ce kamar hadin baki...Baka san aikin su Farida ba yaushe za ka iya aikin hallaka ta?" Ya daki tebur ya manna kansa da bango, Babangida ya biyo shi da niyyar cewa 'am sorry sir' amma ya dakatar da shi da hannu ba tare da ya juyo ba sannan ya daga murya "Fita min daga ofis wawa, ina so in ga kaina ni kadai" Babangida ya fice babu 6ata lokaci. Σ ס a al 28 Mafiyan Masoya-2 Rahma Abdulmajid Ibrahim ya gangaro zuwa kujera ya zauna yana motsa jiki kamar wanda ake mintsina yana fadın Kalmar. "milyaan dari hudu duk awa goma sha biyu. In na bar abin nan haka kamfanin ma ba zai kai jibi ba. Dole in yi wani abu...tsaya ma...zaman me nake?" Ya zabura ya jajibi suite din ya fice. *** *** *** Farida wadda take ta 6arzar dariya tana juya kujera bata kallon Farid wanda yake duba takardun a hankali yana girgiza kai. "Sai da na gaya wa Ibrahim cewa kada ya shiga wannan wasa da ni ya ki...da zan kara awoyi ina wasan nan da sai dai abin da za su yi gwanjonsa. Amma ba zan yi haka ba... dole in kyale masa abinda za mu yi haduwa ta biyu" Farid ya yi dariya ya kale ta da gefen ido. "Chairman ya gama zaba miki suna. Farida wato ta daban. Ke fa ta daban din ce... na ga aikin abin nan fiye da abin da mu muka saki". 2 Mufiyan Masovа-2 Ralima Abdulmajid Ta daga wayar da ke mata kara "Yes Father" "Farida ina dawowa jibi, amma yanzu ki tura Lauyan mu ya je ya nemi inda aka kai Wilson wai yansanda sun kama shi. Bana son shi a bayan kanta na ko awa biyar. . "Ok Father" *** *** *** Yana zaune a kan wani benci yana kallon kasa a yayinda lauyan ya shigo tare da rakiyar wani dansanda. Ya tsaya yana gyara gaban rigarsa har Dansanda ya fita sannan Wilson ya dago yana murmushi. "Garkuwa... how may I help you?" Lauyan ya yi murmushi ya zauna kusa da shi "Wilson ka cika pride, har yau har a nan kai ne mai taimakawa.? Yaya dai ka zo nan? Chair man yace na zo na yi belinka sannan na dauki kes din yana dawowa jibı ko za ka gaya min..." Wilson ya juyar da kai yana dariya "Garkuwa kenan ka gayawa Mast ka yı latti,bana bukatar lauya daga wurinsa" Mativan Masoya-2 Ralma Abdulmajid Lauya ya dan taba baki. "ban gane ba?" "Ka gane Lauya...na riga na dfauki lauya dake kula da lamarin kuma nine bana son fita a yau sai na ga master din ido da ido, amma kace masa in yana son komai da tsari kada ya bar haduwar mu ta kai jibi, don 29 ba na so na jira shi har zuwa jibi a nan Lauya ya dan matsa a kallon sa. "Wilson ba na jin kana bukatar yin fadin rai. An kawo ka ne nan da tuhumar kashe wani babban mutum da ko master din sai yayi ta maza yakc kayar da shi. Kа bari....." "Na fi ka sani garkuwa kuma shiyasa na ce ka bari master ya zo, don ni ba zan fito daga nan ba" *** *** *** Farida tayi kwalliya iya iyawarta wadda ta kara maishe ta Farida ta tsaya a kofar gidan su Farid wanda yayi maza ya fito yana jin ham dinta. Ta kale shi tayi dariya "Let the destruction begin " Ya dan bude mata kofar motar. 31 Mafiyan Masoya-2 Rahma Abdulmajid "Ko za ki bar ni na tuka motaar to?" Ta mikar da yatsarta na tahiya ta na kadawa cikin dariya mai janyc hankali "Ni ce direbar hallakarwar ta yau, kai me duba hanya ne, shiga na tuka ka" Ya wuce mazauninsa da yake bai iya musu da ita....ta ja motar da sauri yana mai kallon hanya da idanunsa amma zuciyarsa na satar kallon ta. Tun da ta shigo wurin bikin akasarin jama`ar suka mai da hankali kanta ba don ko wacece ita kawai ba a a har sai don kyawunta da kwalliyarta da yake jan hankalin har bani jinsinta mata ba maza kawai ba, hakan ya sanya mai gabatar da bikin koda ya gama gabatar da ita ya ci gaba da yaba wa da yin maganganun da suka shafe ta a yayinda take bin mutane suna yin gaisuwa cikin yalwar dariyar da fara`ar yaushe gamo. Tana tafe tana gabatar da Farid wanda shi ma yake nasa kokarin na kada a bar shi a baya cikin manyan mutanen da akasarinsu basu san shi ba duk da sun san Farida. Ibrahim na cikin mutanen da ke tsayc bai dena murmushi ba duk da hakoransa ne 32 Mafiyan Masoya-2 Rahma Abdulmajid kawai a waje, don tunda Farida ta shigo ya fara hangen ta ya ji ya takura ya matsu da abinda bai san ma`anarsa ba. Ta yi kwalliya tayi kyau ko musawa baya yi don ya san natar tasa akwai kwalliyar asali da ta kasuwa, abinda bai iya sani ba shine ko damuwar me take haddasa wa zuciyarsa? Baya taba yardà amsar ta zo kusa da so don yana ganin ya yaki haka kamar yadda ya iya yakar idanunsa da hana su satar kallon ta duk da kunnuwa da idanun zuciyarsa na bin ta da duk takunta a wannan falo. Kafada-da kafada suka karaso inda yake ita da Farid "Ran Ibrahim ya dade" Ta ambata can kusa da kunnensa. Ya juyo rike da kofi ya dube ta sannan yayi murmushi. "Hajiya Farida ina gajiya?" Farid ma ya mika masa hannun suka gaisa sama sama da yalwar dariya. "Ashe kin zo bikin manyan angwanai...." Tayi dariya sannan ta yi fari "Irin ku sun zo ai dole mu zo... da dama abokanmu a ga sun daure sun fito basu ji faduwar hannun jarin nan uku ba bai a A 33 Mafiyan Masoya-2 Rahma Abdulmajid hana su zumunci ba" Ya dan kashe ido daidai yunkurin sa na бoye adadin kaifin wannan magana. Yana jijjiga ya dubi yatsunsa "Ko kadan ba za su ji ba don faduwar duk cikin shiri ne. dama ai ba za su ce suna kasuwar gasa ba za su fuskanci irin wannan ba" Farid ya ja da baya a yayinda yake jin kamar yana tsakiyar aljanna da yake umartar duk abinda yake son ya faru cikin kunfa yakun. Ita ma tana jijjiga da kofin a hannunta. "Abinda na fi jiye wa mutanen shine yaya za a yi a ce kullun ku ake duka ku bakwa iya duka?' "Um`um ba basa iya duka bane suna so suyi dukan karshe ne kada ki zaku" to Allah Yasa dai faduwar darajar bakin karfe a yau ba zai taba su ba, don na ji an ce wasu sun sanya kudi a bakin karfe yayinda gwanjon namu a jiya ya fadar da kasuwarsa wadda za a so dogara a kai" Ba da saninsa ba ya ji shi sit taye yana kallon ta Lallai wannan wani babban duka ne da in fa an kawo masa to dole ya 34 Mafiyan Masoya-2 Rahma Abdulmajid fasa masa hanci. A boye a sirri suka yi cinikin badin karfen kuma ya jida don bayar da tasa kwangilar ga kamfanonin sadarwa masu shirin yin wayar karkashin kasa, bai san ta ina zancen sirrinsu ke ketarawa zuwa ga Farida har ta bata musu ba. Wannan tana son ta fi mahaifinta `yan leken asiri... yana matukar bukatar ya bar wurin don ya ji labarin kasuwar bakin karfe don ya tabbatar da abinda baya fatan tabbatar sa. "Bari na ci gaba da sada zumunci babban mutum na gaishc ka" Ta zare jiki ta bar wuriin bayan da ta janye haannun Farid. Ya bi hannun Farid dake hannun Farida da kallo har suka kule abinda ya ja lokacinsa kafin ya dawo ta kan kasuwar bakin karfe kenan. 35 Mafiyan Masoya-2 Rahma Abdulmajid UKU Richard ya dinga duba takardun nan faya bayan daya yana gyada kai, sannan ya dubi dan sandan da ke tsaye a kusa da kafadarsa. "Su za ka lika a cikin kwanon abincinsa kada ka damu ku zuba miya akai, zai gane abinda nake nufi ba sai ya karanta ba" Dansandan yayi dariya. "An gama mazaje in dai za ku ce mu yi ai ba mu da ja" Richard ya dago damin kudi 'yan dubu-dubu da dansandan ya dade yana kallon su kan tebur ya mika masa. "Ga kafin alkalami, dama ka jima da sanya musu arwa" Ya karbe su hannu biyu yana dariya "ranka ya dade ai na san nawa ne indai kudi na gabanka kamar a gabana yake... yau zai ci wannan takardar in dai Wilson ne kada a damu" 1 1 1 こ 1 1 *** *** *** 36 Mafiyan Masoya-2 Rahma Abdulmajid Na`ibi tsayc a wurin ganawa da wadanda ake tsare dasu ya kasa zama duk da Wilson a zaune yake yana murmushi. Ya kasa zaman ne a dalilin kasa fassara matsayin Wilson din gare shi da kuma alwashin san a rashin yarda da bayar da kai a gaban karamin yaronsa duk kuwa da yaron Kashin bayansa ne na can kusa da keya ma. "har yanzu sai zaurance kake baka gaya min dalilin da ya sanya ka ce in zo da kaina ba, baka kuma gaya min dalilin da ya sa ka ki karban tayin lauya da kamfani yayi maka ba" Wilson yayi dariya a hankali. "Master kenan uaban gidana...Kana manta cewa Wilson ya san ka fiye da Farida yar cikinka. Master tare muke kashewa mu raya in dai matsala ce, kenan in dai da hannunka a abu babu wata nakira י, da za ka shiga in kasa ganewa... Ya dan ci farce ya gyada kai. Wilson ya ci gaba "ch na san ni bani da basirar shinshina danja ko jin radarta daga nesa, 37 Mafiyan Masoya-2 Rahma Abdulmajid amma fa ina da idanun ganinta kuma na iya kerata Da a ce na iya wadannan abubuwa da tun ranar mutuwar Hadi zan ji kamshinsu a jikinka musamman da kayi fishi kana zargina da ragon azanci na kashe shi" Na'ibi a karo na farko a rayuwarsa ya nuna razana da duba duk kusurwoyin dakin kada maganar na fita. "Wilson maganar me kake ? Me kake son gaya min?" Wilson yayi dariya. "Me gida kada ka ji tsoro ba kowa a nan, ina mgana ne kan abin da ya kawo ni nan. Na sami labarin duka sirrin da daga ni sai kai ne muka san shi yanzu yana hannun `yansanda. Wani abu da ya hana ni amincewa tunani na na cewa kо `yansandan Najeriya ne suka kware a bincike suka gano lamarin shine rashin fitowar sunan ka a kowanc daga cikin laififukan. Idan 6ullarsu babu hannun Me gida da lallai ya kamata a ce muna nan tare" "Wilson kana nufin ni ne na fadi 38 Mafiyan Masoya-2 Rahma Abdulmajid laifin da ya kawo ka nan?" "ko kadan Masta, ina nufin dai kaine ka bayar da hanyar da za a kawo ni nan ka ga sai ka huta da ni kada barazanar da kake jin zan iya kawo maka ta tabbata. Kuma ga shi ka fara samun hutu. Farida cе ke juya ofis, ka kade Wilson da Hadi kenan? Haba Masta na sanwannan dabarar tare muka kera ta kan tsohon wazirinka da na maye gurbinsa Madwin" Na`ibi Ya dan matso kusa da kunnen "A sakale a bayan talabijin dina ta bango a ka sami lambar wayar direban da ya kashe Hadi, kuma 'yan sanda sun kama shi. Waya san da wannan lamba ban da kai masta? Kuma Mujitaba ne dansandan da ya je bincike gidana wanda in ka so kada ya motsa ba zai motsa ba. Wani karin abin mamaki shine an gano ina da hannu wajen kashe Racheal. Master me yasa duk kisa da hannunka bai fito ba shi ake tuhuma ta da shi, amma wanda ka fito karara ba a thumua ta da shi Yayi dariya ya kawar da kai. 1 39 Mafiyan Masoya-2 Rahma Abdulmajid "Allah sarki! Talaka baya huta ba sai manya irinku. Sai dai inda baka huta ba shine baka da me kawar maka da duk wani abokin gaba, domin abu ne da Farida ba za ta taba yi ba. Na san hakan kuma ga shi kana tafe da gamuwa da adawar sabon jini dake shirin kawo ka gadon asibiti. Anya baka yi saurin gamawa da ni ba?" Na'ibi yayi ajiyar zuciya ya kada kai. "Wilson ban san ma'anar maganar da kake ba sannan mamaki ya hana ni fahimtar ka...Amma ka sani babu abinda zai sanya na yi maka makarkashiya, kuma har ma na zo gabanka ina cewa bani bane. In kayi min wannan zato zan yi saurin raina tunaninka" Ya matso kusa da kunnensa. "Duk da haka zan baka shawarar kada kayi saurin yin wani abu na kwarewa kafin ka gama kai wa ga tantance zatonka don za ka ji jiki, ka san Na'ibi" Ya bubbuga kafadarsa ya mayar da hannayensa aljihu ya juya ya fita a i a a r a 1 e e e 1 a 40 Mafiyan Masoya-2 Rahma Abdulmajid *** *** *** A bakin ruwa Richard yana dafe da makaran karfen da ta raba shi da ruwan bai juyo ba a lokacin da Ibrahim ya iso gare shi yana masa kallon fishi a yanzu "Ban san me kake nufi da game dina ba. Ka karbi alkawarin kudi tsugugu don ka ga faduwata ne ko me? Farida na ta narka min tsiya babu wani motsi daga wurinka". Har yanzu bai juyo ba kada kai kawai yayi "Akwai motsi mana ranka ya dade...zuwa an jima za ka ji an baza neman Wilson cewa ya tsere daga wurin hukumar `yansanda" Ya juyo a yanzu ya kalli Ibrahim "Ba zai sake damun ka ba" Ibrahim Ya kwance tay dinsa har Karshe yana jijjiga. "Ba matsalata Wilson kawai ba ka sani...Hasalima yayi cara ne da yawa in ba haka ba me zan yi da Karen farauta. Ina nufin Na'ibi da `yaarsa da suke son fin karfina..." ف 41 Mafiyan Masoya-2 Rahma Abdulmajid Ya katse shi. "Dakata ranka ya dade, ni ban iya irin wasan su Farida ba, wannan yarana suka dauko suke yi musu, amma ni babba ne na girma bana wasa biyu daya nake yi. A yanzu maganar da nake gaya maka su Farida basa samin riba, sun kasa karfinsu gida biyu ne, daya suna dukan ka da ribarsu daya kuma zuba shi a sabon abinda baka bukatar sani ni na san shi. Kuma duka daya nake so in yi musu duka a huta. Ba za su sake tashi ba. Trust me..... ni na rubuta contract din nan da kai ba wani ba, just give me a braek. Kai fa kana so ne a karya Na`ibi a cikin gida da waje" Ibrahim yayi ajiyuar zuciya yana ta duban inda zai samo hakurinsa a kusurwoyin ruwan. "Well na ba da wannan satin ina son in ga aiki" 42 Mafiyan Masoya-2 Rahma Abdulmajid HUDU Farida ta dinga kade iska daga kanta tana yawo na takaici. "Father me ka dauke ni? Father ni ce 'yarka ta fari ba Wilson ba, ni ce zan iya tsayawa a matsayin me dukiyarka ba Wilson ba..." Ta karaso gabansa ta ritsa shi da idon fishi. "Sannan da rayuwata aka yi wannan wasan ba da ta Wilson ba, ni ce me abin yi a wannan fadan yaya za a yi rana tsaka ka zo ka ce na bai wa Wilson kujerar Staff Head yayi komai na koma gefe?" Na`ibi sarkin sanya hannu a alihu, ko gezau yana kallon ta. "Saboda wannan ne kawai hanyar da Wilson zai dena zargina da yi masa makarkashiya a kan daure shi da aka yi" Ta yi alama da yatsa. "Dalili na daya, ina son jin na gaba" "Saboda Farida kina 6arnar dukiya da yawa a wannan rikicin wanda in Wilson 2 43 Mafiyan Masoуа-2 Rahma Abdulmajid ne ina ga ba za a kai haka". "Dalili na gaba, ban da wannan" "Babu wasu sai wannan Farida tayi dariya sannan ta gimtsc. "Bari na kwance dalilan baya Father. Kawai saboda kada Wilson ya zarge ka ba dalili ne bane, don ka fi karfin damuwa da zargi ko na gwamnati ne ballantana na yaron kamfaninka har ka gwammace 'yarka ta zarge ka maimakon yaron naka...Dalili na biyu ko kama da hankali bai yi ba domin ina da record na dilmyar da kwantena dari da kuka taba yi don kayar da Hadi a kwantena biyar kacal, tun baku zama masu kadara irin ta yau ba, da wa aka yi wannan ba da Wilson banc? Me zai hana Father ka fito ka gaya min dalilin cewa akwai abinda kake boyewa kai da Wilson wanda baka so nisantarka da shi ya fito da abin...gara ka gaya wa Farida tunda ka san 'yarka za ta sinsino" Faduwar gaba ce ta sanya Na`ibi dako tsawar da bai yi niya ba. "Eh! Ina da abinda nake 6oyewa kuma shine sirrin kamlanina da duk 44 Mafiyan Masoya-2 Rahma Abdulmajid Wilson ya san su, kina tsammanin idan ban sasanta da Wilson ba a wannan yakin har muka rabu abokan gaba suka yi zawarcinsa ya koma hannunsu za ki iya yakar kwanyarsa da ta Balala da ta sirrin mu da ya tafi da su? Farida na kyale ki ki sake a matsayin yarinyar da ta kware, amma kada ki raina dabarata...Ni ne me wannan mulkin kuma na zartas da hukumcin ki hada karfi da Wilson ku yi aiki wannan ne hukumcina" Ya juya zai tafi amma Farida ta sha gabansa "Za a yi yadda kace Sir, amma ban yarda da wannan dalilan da ka bayar ba Father, Na san ka ba yau ba, abubuwan da ka nuna na tashin hankali ne basu taba zama maka tashin hankali ba, dole akwai abinda yake sama da haka, wanda na baka damar ka yi shawara ka gaya min gaskiya, kafin na binciko da kaina" Ta juya za ta fita daga ofishin a yayinda suka ci karo da Lauyan da ya fado a guje. "Sir, yanzu labari ya iso mana 45 Mafiyan Masoya-2 Rahma Abdulmajid Wilson ya kubuce daga hannun hukuma, دو an baza nemansa... Na ibi ya juyo da karfi. "guduwa? Me Wilson ke nema da batun nan ne?" "Shine abinda nake tsoro tunda mun ba shi beli ya ki maimakon ya fito a mutunce ya kara lalata lamarin da guduwa...Ina tsoron yaron don ba zai yi haka da gangan ba sai in da wani tsari" Na`ibi ya dubi Farida sannan Lauyan wanda tuni ya gane karatun beben ya dan dauke bakinsa. Farida ta dube su da kyau sannan tayi murmushi ta kada kai ta bar ofishin. *** *** A ofoshin Farid take zaune tayi tagumi bata komai sai nishi da kada kai. Duk wani yunkuri da yayi zai yi magana sai ta tsayar da shi 'kada ka watsa min kwanyata' A haka aka share mintoci ashirin da takwas inda ta bugo wata tambaya. "Me Wilson ya tsorata Father da shi 46 Mafiyan Masoya-2 Ralma Abdulmajid shine nake son sani, shin batun kamfani ne ko na cikin gida? Ni ce ba a so in sani kawai ko duniya?" Farid wanda babu matsalar da ta dame shi ban da wadda Farida ta mayar matsala yanzu ya sami abin cewa don da alamar ta yanke shawarar yin magana. "ko ma me ce ina jin ta kare... Oga Wilson ya gudu ya bar rayuwarkи. Maganar Chairman ya bukaci ki bar masa kujcrarki shi da kansa ya kashe miki wutar" Ta dubi Farid da haushi. "Kana zaton kujera ce ta dame ni? Ina da offer ta aiki a kamfanunuwan da suka fi Na`ibi G. Karatuna, kwarewata da sunan Family na za su iya sama min kujerar da ta fi wannan da nake kai...Amma bukata ta bata wuce in yaye murfin da ke rufe da wannan damuwar ta Father kan Wilson ba..." Ta dauke murya dan ta karasa ragowar abinda take jin nauyin fadi a cikinta. "Ko dai zargin da Bally ya dage A 47 Mafiyan Masoya-2 Rahma Abdulmajid cewa Father ne ya kashe masa uba akwai gaskiya ciki? Wilson ana tuhumar sa ne da kisa amma Father ya hana in ji ko kisan waye...Idan ba Kisan Hadi ba wane babba za a kashe da zai damu Father? Wane ne za a iya bin kadin ransa da Father ko Wilson?....Ina samin Father da Wilson da nayi suna magana daf da zuwan su Hadi neman aurena inda suka ki karasa zancen Wilson ya fita? Lallai ban kara ganinsa ba ko a ofis sai bayan mutuwar Hadi da hatsarin Bally" Ta zabura a haukace, abinda ya mikar da Farid. i a a ar ita m n a a n "Lafiya?" Ka Tayi masa ishara da hannu ta fice da sauri *** *** *** kur. Richard yana yiwa Balala kallon "ka gaji mahaifinka matuka, fishi ne ya hana shi nasara kan Na'ibi har ya rasa ransa, wanda in ka ce da wannan gadon za ka yi fada da Na`ibi kai ma zai ga 48 Mativan Masoya-2 Rahma Abdulmajid bayanka, don mutum ne me kwantar da kai da zuciya yayi tunani Ibrahim ya tattara goshi don nuna damuwa. "Wanc irin hakuri kake so inyi? Ina biyanka Milyoyi ina hasarar milyoyi babu wata riba? Har yau sai... "Idan dukan a sake tashi a kara kake son yi wa Group din Mansur Na'ibi to zan hada ka da yara da za su yi maka, amma kada kayi mamaki in Na'ibi ya biya ni ka ga ina ja da kai da yaran nawa, don ni dankasuwa ne kuma ina zaben abinda ya dace ne da ribar kasuwancina. Ina son in dakar maka Naibi inda da kafarsa zai gudu ya bar ka, abinda ka biya ni nayi kenan, wannan ko zai dauki watanni don Na`ibi babban giwa ne, zan baka dama nan da kwana hudu ka yi wa Na`ibi babban dukan da zai zamo fashi ko siyasa ne kawai za su iya farfado da shi, na san a nan zai zabi siyasa, a nan zai karar da garkuwar kudinsa inda ana sauran zabe kadan zamu yi masa fallasar da ko iyalansa ba za su saura da shi ba ballantana 49 Mafiyan Masoya-2 Rahma Abdulmajid masu jefa kuri'a. Idan kayi hakuri Bala Hadi, Na'ibi ya kare" Sanyin da Ibrahim ya ji a zuciyarsa ya bayyana a kan fuskarsa ta hanyar murmushi da gamsuwa. "Da me za mu kayar da shi nan da kwanaki hudu?" Richard ya fake da fuskarsa yana kunna kakkaurar tabar. "Yayi odar Screen din tare haske daga cutar da ido wanda tuni yara sun sanya sinadarin kokewa a kan milyoyi kamar yadda aka sanya gubar cutar da ido ko nunfashi a cikin wasu dubbai da za su kasashen ketare masu saurin dago barna da daukar mataki ba irin kasar nan ba. Nan da sati za a iza binciken da zai gano cewa kayansa ne suka yi wannan 6arnar. Sanin ka ne za ka ci riba da dama kamar shagala da zai yi da wannan matsalar ya mance da yaki da kai, sannan zai yi ta 6arin kudi don kashe maganar inda a karshe dole ya biya diyar da za ta kara karya shi har ya kai ga neman manyan kudi cikin gaugawa. ba shi da zabi ban da lasisin siyasar da yake ji S Mafiyan Masoya-2 Rahma Abdulmajid ya fi karfi wato takarar gwamna. A nan yara sun samar da kayan karya shi amma fa sai a na daf" Bally cikin dariya yake magana yanzu. "Idan ko haka ta faru ina jin ko takarar gwamnan ba zai iya ba don a yau din nan kamfani na yayi nasarar kwace babbar kwangilar da suke dauka a matsayin sabon jari wato na kera wa China makamashin Sola a jikin cajar waya me sauki. Ya narka kudi a kai, amma mun bayar da namu kasafin babu ribar naira daya a ciki don mu haifar masa da hasara, sannan mun sayar da fasahar caji da iska wadda ta karya fasaharsa ta caji babu igiya rugu-rugu Suka tafa. "Yanzu ka fara sanin muna aiki kenan? Sannan Wilson ya 6ace daga rayuwarsa ba za a sake jinsa ba ballantana ya dame ka" 1 4 소 *** *** *** Ji kake Tau! Sai da kumatun Farida ر 51 Mafiyan Masoya-2 Rahma Abdulmajid ya waskace na 'yan sakanni, ita ma kuma mamaki bai sanya ta juyo ta kalli mahaifiyarta ba wadda ke cikin fishi. "Me kike daukan kanki? Fekewa da iyawa wanne kika fi mu? Ubanki za ki tsaya kina tuhuma da kisan makiyinsa dan kin nace kina son dan shi duk da cutar da kc da yake? Idan ke wata isasshiya ce ba za ki mayar da hankali kan hasarar da aka hango za ku yi ba wadda ke son haifar masa ciwo sai ki kara iza wuta? Kina zaton sunan kamfaninku zai sake saura idan aka yada wa duniya cewa har da mutane irinsu Prof Yinka Bowale da duniya ta ba su kyautar Nobel a cikin wadanda kamfaninku zai biya diyya ya bata musu ido. Kina so ki ce min baki san abinda hakan ke nufi ba?" A yanzu Farida na kallon ta ne rike da kumatu cikin zuciya wadda ta bayyana a idanunta.. "Na gode Mama, amma ki sani babu abinda ya kai zuciya yanci na zaben abinda za ta mayar da hankali a kai. Ko me dauke da ita a kirjinsa in ya ce miki yana e e n za 52 Mafiyan Masoya-2 Rahma Abdulmajid bata zabi karya yake, balle uwarsa ko ubansa...Na gode da mari, amma kiyi hakuri na zabi abinda zuciyata ke mayar da hankali a kai" Ta juya za ta fita. Na`ibi dake da alamar rashin lafiya yayi tari kafin ya samu ya kira ta. Ta tsaya ba tare da ta juyo ba. "Kiyi hakuri da hukumcin mamanki, tayi ne cikin damuwa da halinda nake ciki wanda ina ga shi ya kamata a ce kin mayar da hankali. Farida Na guji bacewar Wilson saboda rana irin ta yau ga shi kuma ta auku. Bani da tababa ta wurinsa aka san batun Screen har aka lahanta ni da shi, ta wurinsa aka san fasahar Caji

Chapter 2 of 7