Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
1 / 7
An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels MAFIYAN MASOYA RAHMA A.MAJI HAUSABOOK.COM 2 Rahma A. Majid 2 Mafiyan MASOYА 2 Mafiyan Masoya-2 Rahma Abdulmajid Copy right(C): Hakkin Mallaka (M) Rahma Abdul Majid An fara bugaawa: 2014 GARGADI Ba a yarda a sarrafa ko a kwafa ko a juyi wani bangare na wannan littafi ba tare da rubutaccen izinin mai hakkin mallaka ba. Kazalika wannan littafi ba labarin wani ko wata bane illa kagen nishadi daga basirar mai shi. ISBN:978-978-52359-9-9 3 Mafiyan Masoya-2 Rahma Abdulmajid Gabatarwa Hanyoyi da musabbabai na rubuta labarai sun bambanta kuma sun yawaitá da ba za a iya kirgawa ba. akwai masu rubutu don fadakarwa ko nashadantarwa ko rikitarwa ko tsoratarwa ko ban tausayi ko ban dariya, kana akwai masu bayar da labari don habaici ko zagi ko yabo ko fallasa ko girgiza sha`awa ko kashe ta. Har ma da masu rubutu don daukaka wani addini ko wata akida ko wani imani. Gasu nan babu iyaka. Sai dai Rahma Abdul Majid a wannan karo ta zo ne ba da daya daga cikin wannan dalilai ko wasunsu ba, dalilina daya shine taya makarantana hira wadanda sau tari sukan yi kewar rubutuna saboda dadewa da akan yi ba a ji duriya ta ba. don haka mai karanta littafin MAFIYAN MASOYA ya shirya yin hira ne da Rahma AbdulMajid a majalisar hirarta ta alkalami da takarda. A bangare guda kuma ina son yin amfani da damar nin in bai wa masu jiran DA HANNUN MAZA 2 hakuri na rashin ganinsa. Hakika labarin yadda hannun mazan yake yana cikin na biyu kuma shine ma ginshikin littafin. Sai dai wasu dalilai sun sanya ba zan ci gaba da labarin kamar yadda na so ba, maimakon haka na bar masu karatu su zana yadda suka so karshen littafin ya kasance wa zukatansu. Ina mai bayar da hakuri bisa faruwar hakan kamar yadda nake bayar da hakurin kan rashin jin filin masoya a wannan karon, wannan ya biyo bayan yawan da shafukan littafin ke da shi wanda ba zan so na kara muku nauyi bisa kudin sayar shi ba. Ga masu jiran jerin labaran DUHU kuwa kada a karaya. inshaAllah in da rai da lafiya za su ga guzirinsu bayan wannan hira ta kare. Da fatan za mu yi hira lafiya mu kare lafiya. Rahma AbdulMajid 28/01/14 4 Mafiyan Masoya-2 Ralma Abdulmajid DAYA a cire wayar daga kunnensa a Y hankali yana kallon gabansa cikin sanyin jiki. Can cikinsa yana jin wani jiri mai tausayi da cakuda kwazo da kasala wuri guda. "Farida na gaya min ta zubar da dana? Bata raini cikin ba...bata haife shi ba, ta kashe shi?" Dogon dake tsaye yana kallon sa rike da wasu takardu shine Mai Kudi, ya sake mai da hankali kan Ibrahim. "Ranka ya dade kana son ta kenan har yanzu?" Ibrahim ya mike tsaye a hankali ya zuba hannu a aljihu sannan ya yi ajiyar zuciya. "Kamar yadda na san har yanzu ita ma tana sona...Sai dai ba wannan ne abin damuwa ba.. abin da ya sanya Farida tayi asarar wannan da namu da hannunta ba karamin yaki ta shirya da ni ba...ta kuma soma nasara da kashe min da, amma zan yi A 5 Mafiyan Masoya-2 Rahma Abdulmajid nasara ta hanyar hana ta mallakar wani dan a duniya. Amma Na'ibi shine abokin wasa na ko ta ki ko ta so" Ya dogara kansa jikin makarar kafar benen. "Amma sun cuce ni sun kashe min uba sun kashe min da. Zasu biya ta hanyar da basa so" Ya juya ya hau sama. *** *** *** Na ibi da ke zaune a a hannun kujerar yana duba wata takarda ya dubi Farid da ya shigo ofishin wanda shi ma ya dan dube su duka biyu, wato Farida dake zaune tana juya kujerar ta ta me kamfani da mahaifin dake nasa muhallin na zaman bako a hannun kujera.Na`ibi ya dago ya kara duban shi. "Farid, ina so ka wakilce mu a wurin mitin din samar da sadarwar otel da GLOBAL SHARE suka shirya, ni kamar yadda ka gani zan dauki hutu na na karshen shekara wanda ogata Farida ta ba ni don ita ce za ta ja akala har nan da wata biyu in dawo. Sai ka taya ta aiki kamar yadda ka Mafiyan Masoya-2 Rahma Abdulmajid saba, amma abinda na ki jini shine kada ka je ka sanya hannu a wannan takardar ko ka saki wasu kudi sai da sanya hannun shugabar mu Farida" Ya jefa takardar a teburinta sannan ya daki kafadar Farid wanda tuni ya amsa masa. "Best of luck" Ya fice daga ofishin ya bar su. Farid ya sake ya kalli Farida wadda bai gani ba tsayin wata guda, amma ba wannan ne abin damuwarsa ba, ramar da tayi da karin haske wadda maimakon ta fitar da wahala sai ta kara mata kwarjini da kyau da yarinta a idonsa. "Ranki ya dade barka da dawowa" "Zauna Farid ina da hira da kai kafin mu duba wannan abin da Dady ke kira aiki" Ya dan balle maballai biyu na gaba kwat din sa don ya zauna babu takura. Ta cura hannayenta cikin juna tana juya kujera. "Kana da labarin abubuwan da suka same ni kuwa?" Ya dan kura mata ido. Ba za ee asuwar sirikinta ba don kamar sun yi 7 Mafiyan Masoya-2 Rahma Ahdulmajid gaisuwar wannan amma mene ne sabo da ya same ta baya da ya ji an ce tayi jinya kuma tun daga wancan loikaci kafar tsaigumi ta toshe masa? "Na ga dai kamar kin yi fama da jinya kuma ya fito a jikinki kwarai" Tayi murmushi sannan ta sunkuyar da kai tana hangen wata majalla a damarta. "Na rabu da mijina Bally na kuma yi asarar dana sune abubuwan da suka same nu Ya ji gabansa ya rikito kasa...Lallai sabon labari ya ke ji fil...Ba zai iya tantance matsayinsa na me murna ko akasi ba saboda sabuntar lamarin a gare shi duk da ya fara iya kimanta girman lamarin ga Farida. "Deal!!!" Wannan ce kawai kalmar da yake maimaitawa ya kasa sauke idanu daga kanta. Farida ta dago da yalwar murmushi "ba na gaya maka ne don hankalinka ya tashi ko ka tausaya min ba ina so in yi matashiya ne kan babban aikin da ke gabanmu" Ta dan nil baya a kujerar "Alakarmu da Bally ta tsinke kamar F 5 S Mafiyan Masoya-2 Rahma Abdulmajid yadda nayi asarar dana duk da girmansa a zuciyata da zuciyarsa, sai dai a yanzu mun fahimci cewa mummunar alakar dake tsakanin kamfanoninmu biyu ta fi karfin kyakkyawar alakar soyayyarmu don haka dole mu bi me karfi,daga ni har shi an raine mu ne ta hanyar biyyya ga abinda ya fi Karfi...Abin da nake so kawai ka karanta a wannan magana tawa shine jan aikin da ke gabanmu. Sati biyu kenan da muka kulla alkawarin gasa da ganin bayan juna tsakanina da Ibrahim, kuma za mu yi hakan ne karkashin jagorancin kamfanoninmu. Duk da cewa irin wannan yakin ba wanda ko wane bangare zai so ko mafarkin kasa yin nasara bane, kuma duk da yin nasarar mu kan su Ibrahim ba bakon abu bane, ina sane da cewa ya kawar da hannun kowa a nasa yakin yana rike da linzamin, don haka ne ni ma na yi kokarin kawar da Father da Wilson daga wannan fage ina son na rike shi da sabon hannuna wato gudunmuwarka. Na zabe ka ne ba don komai ba sai don yarda da tsarkin hannunka inda ke so sabuwar tawagar nasarar mu ta zano tana cimma り Mafiyan Masoya-2 Rahma Abdulmajid burinta ba tarc da tayi sanadiyyar halaka ko cutar da wani rai ban da na kudi da kadara ba, haka nan ba tare da ta dilmiya wadanda basu ji ba basu gani ba. Abin bukata a wurinka yanzu ba kwarewa ce kawai ba, ina so in ga kwakwalwarka ta manta da hutu dare da rana tana mai cikin shirin ko ta kwana da kiyasta irin ta yadda su Ibrahim za su bullo mana.Farid ban san asara ba ban taba yinta ba don haka ba zan so yin ta a yakin da ban taba yin irinsa ba shiyasa na hada team din Farid da Farida" י Lokacinda ta dauka tana magana ya ba shi damar sanin matsayinsa...yanzu farin ciki yake, Farida ta zo kusa ta kara motsowa gare shi, babu shamaki. Aikin da take cewa a yi don kamfani zai yi fiye da shi ba don kamfani ba sai don samun dauwamammen kusanci da Farida. Yayi asarar waccan dama don bai san kan yakin ba amma shi ma fa so yake kada yayi mafarkin asara a wannan sabon yaki nasa.... Ta Kura masa ido "Farid ina son ganin Ibrahim a kasa a karo na karshe..ina son darasin da a sh bai wa mahaifinsa ya zamo na wasa. 10 Mafiyan Masoya-2 Rahma Abdulmajid Wannan ya zamo na karshe,ina san kawo Karshen yakin kamfaninsu da namu" *** *** *** Can gabar teku madafar gahawar take an baibaye ta da na`urorin dumama daki da fitilu marasa haske. Zai yi wuya ka iya tantance fuskokin kowa ba don duhu ya kaurc ba sai don fitilun da aka tanada don kawar da gane fuskoki, hakan ya sanya da wuya ka ga wani ya doshi teburin wani in ba an ba shi lamba ya je wurin ba. Kuma ba a ci ba a sha ban da hadin ruwan gahawar da akan yi. Richard ya sosa goshinsa yayi murmushi ya sake dawo da idanunsa ga Ibrahim Balala. "Lallai ni nayi aikin horas da wilson kuma duk horon da na ba shi na ya iya kayarwa ne, babu komai a kwanyarsa ban da ya saukar da asara kuma ya horu fiye da yadda nake zato... amma ba zan ce kayar da shi ba zai yi wu ga malaminsa ba, sai dai zai yi min tsada sosai na kayar da yarona, kuma zai yi un sada sosai na bariaro na ya kayar da i1Dan samari bana zaton za ka E V Mafiyan Masoya-2 Rahma Abdulmajid iya biyan irin wannan tsada... Ina jin abin da za ka iya biya bai wuce na in yi masa nasiha ccwa ya kauce daga hanyarka ba, amma biyan in ja da shi da wuya don Na ibi yana biya da kyau amma baya iya biyan כ2 Balala ya fan dubi gefe ya kalato Kokari. "Fadi me zan iya baka ni kuma zan dora... Ba so nake a kawar da wilson daga. hanyata ba ina so ne a kayar da shi a gaban hanyata masu ji da shi su gani...." Richard ya sake yin dariyar nitsuwa "kana cike da fishi...baka danu da asarar ka ba....dama an ce biki da me zuciya ake yi...idan na in baka wuka da nama ne kan Wilson ba kudi zan caje ka ba...ummmm... ka san ni ban iya ciniki ba ban kuma iya harkar kasuwanci ba,,, wannan ya sa na ji ina son sayen hannun jari ina daga kwance ina cin riba...." Ya daga hannaye biyu "Kada gabanka ya fadi ba cewa zan yi mu raba kamfaninka ba ni ba zan ma iya wa kamfani ba so nake kamfanin ka ya biya hannun jarin da na yi ciniki da kamfanın 5 12 Matiyan Masoya-2 Rahma Abdulmajid Apple... basu da yawa guda dubu sha bakwai ne duk da dai manya ne....batun tsarin kayar da Na`ibi ta hanayar yarana dakc baibayc da shi pan dubu goma sha biyar ne zai raba ka da kowanne daya, Ina jin basu da yawa su hudu ne ko?" Ya tsaya yana lissafi da yatşunsa... "Dcal!!! " In ji lbraahim ya ci gaba. "Ka sanya hannun fara yi min aiki ni kuma zan saki rabin kudin ta hanyar waya yanzun nan. Richard yayi dariya. "Kawo takarda ina son haka ina son yin aiki da yara masu kwazo kamar ka..da haka babanka yayi da ba ku yi asarar da kuka sha yi ba......" ***** Ya ji gabansa ya fadi ba don tsoro ba sai don gudun samun tasiri ko mutuwar jiki. Da Farida suka yi arba tana shigowa shi kuma yana fita. Duk suka tsaya baya da ta fara tsayawa ta dube shi daga sama zuwa kasa sannan tayi murmushi. "Bally kehan yo look greate yaya shiryc-shirye?" 13 Mafiyan Masoya-2 Ralhma Abdulmajid Shi ma ya tsaya yana kallon ta. "Mun gama namu shirin In ku kuna kan yi. Kafin mu fara aiki da zan so yi miki nasiha ta karshe da cewa kamata yayi ki nemi ahuwa kan abin da kika yi komai ya koma kamar da kafin ki shiga yakin da ba za ki taba iyawa ba" Ta yi fari da ido. "Bally kana nan yadda na san ka.gaggawa da yarda da kai da kankamba, kafin in yi maka tawa nasihar bari na baka amsar taka. ka gama yanke cibiyar dake tsakanin da da yanzu don haka baka da iyawa ko tasiri kan mayar da yanzu kamar da. koda yake ba hakan ce za ta hana ni baka hakuri ba, ina ga ba zan taba bayar da hakuri ne ga laifin da ban aikata ba don haka na gwammace karon battar mu da hakan. Sai dai ni tawa nasihar gareka itace da za ka ja da baya kada ka shiga yaki da kungiyar nasara amatsayinka na mai wakiltar rundunar hasara. Ko ka manta ba ku taбa nasara ba ne Ibrahim??? ko a fadan Karashen nan ka duba irin asararka, ka rasa uba ka rasa shugaba,, ka rasa mata ka rasa da, ka rasa dukiya ka rasa kwanciyar hankali 14 Mafiyan Masoya-2 Rahma Abdulmajid duk ba ka ga rashin ba kan ka kake so ka rasa dungum?" Ya matso a fusace. "Ko ke ki rasa kanki a wannan karo" Ta daga hannaye sama. u`um!!!nayi alkawari ba za a yi haka ba, don bana yakina tsarkakakke ne... rai ko jiki bana so su salwanta, kimar kamfani nake so in yi cacar da shi amma ba zan mayar da kai Geran masallaci ba kada ka tsorata wannan alkawari ne" Yayi dariya "Farida kin cika wa kanki ido kuma wannan ne abin da nake son sauke miki a wannan kwanakin...in kin gama shiri ki sanar da ni, amma ke kamfani ya dama saboda imanin ki da gasa ya saba wa imanina da halakar ku ta ko ina...sai wata rana "Sai wata ran Bally duk lokacinda ka so haduwar wasan na shirya maka" *** *** Ta jima rabonta da ta shiga uwar dakinta, ku'lun a katon falon ko a karamin ofishinta na cikin gida bacci yake kama ta, 15 Mafiyan Masoya-2 Rahma Abdulmajid amma yau tana zuwa sambai ta wuce dakin don kada ma wani aiki ya ja hankalinta. Yau rana ce ta zakulo bacci duk inda yake don kwanya ta sami hakkinta kafin ta soma dasa Dan ba a a aikin da ke gabantanta. A cikin dakin ta kunna komai ta zare rigunan jikinta ta yafa ta wanka don ta watsa ruwa, amma daga nesa ta hangi hoton sa yana yi mata murmushi, hannayensa na dage kuma itace a cikinsu suna sanye da fararen kaya na aure. Ta jima bata yi arba da hoton nan ba, da ta san za ta ci karo da shi da bata shigo dakin ba, wani matsafin hoto ne da ke jan ta zuwa ga bara abinda bata son tunaninta gare shi. Ba da saninta ba ta gan ta daf da hoton wanda tuni ta dauke shi ta durkusa kan gadonta, da ka gan ta ka san bata cikin sabon shirin da suke da zuciyarta. Shafar Bally take da yatsunta can cikinta ta kasa tuna matsayinsa a yanzu sai kewarsa kawai. Ta matse idanuwanta da saninta don ta tuna abinda ya fi mata komai dadi wato zamansu da Bally. Ta dan yi sama da idanuwanta don su haďu da nasa da ta san suna kanta, ta ko yi sa`ar yana matso da bakinsa don ya sunbace 16 Mafiyan Masoya-2 Rahma Abdulmajid ta. "Yaushe za ka gaji da yi min kiss Bally?" Ya dan yi dogon tunani. "Umm! Nan da busa Kahon Karshe zan fara rage kwadayin la66anki Reeda" Ta dada masa duka a kirji sannan cakulkuli, yana dariya. "kenan ma za ka dena din kenan kо? Sai na zane ka tsaf" Suna dariya ya na kare dukan wasan da take masa a kirji har ta gaji suka sake komawa kallon juna. "Farida kin ga so yayi nasara kan ki ga shi ya kawo ki kan kirjina, na zamo na mijin farko a rayuwarki kamar yadda kike macen farko a rayuwata? Me ake da kiyayya da su Father za su gane?" Ta sa hannu ta toshe bakinsa. "Kada ka tuno mana da makiya a nan, bari mu more farinciki ba tare da sirkiya ba" "Kuma kin san so ne kawai ke da Karfin haka...Musamman irin soyayyarmu da ka iya dauke radadin duk wani gyambo" Ta bude idanunta ta kalli hoton, ta ji tana bukatar rungume shi a naman kirjinta 17 Mafiyan Masoya-2 Rahma Abdulmajid na dan lokaci cikin radadin kewa da so. Bata san iya mintocin da ta shafe a hakan ba sai dai sun ingiza ta ga lalubo wayar ajiye a dakin inda ta lallatsa lambobin da ta jima da hardacewa ta kwanta kan gadon ta sanya wayar a kunne. Ya jima da dauka da nanata hellohello, amma sassarfan hawaye da ratsa ta da muryar take ta hana ta cewa komai. Yayi tambaya "Me kike son gaya min da za ki kira ni kiyi shiru? Kin sa ranar fara wasan mu ne?" "Bally don Allah ka da ka yi wannan fafatawar da ni" Kwance yake a kan gadonsa, amma asirin yanayin Farida da ya bayyana a muryarta ya zaburar da shi zaune.ya jima yana rintse ido na jin yanayinta a tiririn kirjinsa. "saboda me?" ya tambaya da muryar shauki. "Bai, kamata ba... Bana son yin wannan fafatawar da kai Bally kana son takura min. Bana son ji maka ciwo?" Haushi dao duka suka tirmike shi, bai fasa jin shasshakar Farida a kunnensa ba 18 Mafiyan Masoya-2 Rahma Abdulmajid amma an ya ba wani makirci ne daga makirar Faridar me kashc masa uba da za ba. "Kada ki damu babu ciwon da za ki ji min sai dai ni na ji miki in kin shirya" "Bally baka son yin abinda kake shirin yi.. rufe idonka ka tuna Faridarka a gidan wanka, a kan gadon mu a kicin, a kan doki, a kan titi, cike da soyayya, duk za ka iya cin amanar wadannan ranakun? Hotonmu kawai na ranar biki na gani ya zubar min da makaman yakina, ka tuna fatanka na so yayi nasara a kan ki, ka duba rayuwarmu, ko da ba mu da aure a tsakanin mu mu bai wa soyayya mutuncinta Baby muna da rayuwar da ba za mu sake maimaita ta da waninmu ba. Ka tuna rana guda muka san yadda ake sarrafa juna tsakanin zuciya da gangar jikin namiji da mace. So da tarayyarmu akan junan mu muka fara...." "Ya isa makircin... idan tsoro kika ji fito ki yi saranda ba kissa ba" Ya kife wayar da karli ya tsinke layin sannan ya zauna yana nish Bai yi aune ba sai ji yayi hawaye na zub masa. Ya fadi 19 Mafiyan Masoya-2 Rahma Abdulmajid kashangare idanuwa a rintse. "Gaskiyar Farida, ke ce abin sona na sani har gobe, bana son yin wannan fadan amma dole sai nayi. Dole sai nayi Reeda ki yafe min kada ki kashe min jiki. Ban bai wa mahaifina komai ba yana raye, wannan cе Kawai hidimar da zan masa ya ji dadi" Ya dubi gabas da yamma. "Da gaske bana son yin wannan fafatawar kin sani Farida, amma kin kashe min uba kin kashe min da, duk da wannan kina karyar so yayi nasara? Don dai nine wawa soyayyar ki ta mayar da ni wawa?" Ya zabura cikin kuka ya doshi wani hoton Farida na katako karami zubin ofis da ke ajiye ya soma wurgi da shi. "Ban son ki ban san ganin ki ki fita min daga rayuwata" Abubuwanda yake nanatawa kenan yana jifa da hoton yana takawa wanda ko gezau bai yi ba har ya gaji zai tsaya ya huta amma suka sake hade ido da Faridar hoton da ta kashingida kan tafukan hannunta tana yi masa murmushi. "Me ya sa nake son ta? Me yasa nake jin ta, Me yasa na kasa cire ta daga 20 Mafivan Masoya-2 Rahma Abdulmajid rayuwata?" Ya dauki hoton ya rungume a yanzu kuka yake wiwi *** *** *** Farid da Mahdi da wasu mutane uku ne kawai a daukacin gidan abincin sin din wato Chines restaurant hakan ta sanya shiru kake ji musamman da ya zamto ba da cokula ake cin abincin ba.Mahdi ya debi wannan tsinken ya tsiyaya a bakinsa ya bi shi da wancan tsinken, amma mai gayyar sai daura taliya a tsinke yake yana kwancewa "Malam Ka ci abinci mana" Itace kalmar dake yawo a zuciyar Mahdi amma sai ya maye gurbinta da cewa "Yanzu da Farida bata da ciki bata da aure kuma kana 2.1.C dinta wace dabara za ka shirya wa damar ka ta yi nasara?" Farid Ya tsayar da katakon a nuna idanun "Na san dai ba cewa za ka yi ba za ka aure ta ba tunda kai saurayi ne" Farid ya zubar da tsinkayen sa dama abinda yake ta faman so kenan "1Dabarar farko shine rokon Allah da 2 21 Mafiyan Masoya-2 Rahma Abdulmajid Ya bar Farida cikin kadaicin da take ciki har ta gama amincewa da cewa ni ne kadai me kare mata kewa....Farida na da fadin zuciya za ka iya fadawa tarkon zaton son ka take saboda karamci yayinda sam! Zuciyar bata doshi nan ba a fadi kasa babu nauyi,shiyasa na ke ta bi a hankali, amma ina fa hangen nasara, ina hangen zan zamo namiji mafi saa idan maki daya da ya rage min ta cika wato Farida ta amince da ni...." Yayi ajiyar zuciya. "Yarinyar tana shiga matsala tana kara shiga raina...Amma fa tana ban tsoro, yadda ta iya danne son ta ga Ibrahim lokaci daya take aiki da manufofin kamfani kawai na nuna cewa za ta iya take duk wanda ya biyo kan titinta am telling you" "To shi Balalan yaya yake? kada fa ya zo ya bata muku tafiya ka san halin so". Farid ya 6ata rai "Malam Yaya kake wannan magana na ce maka mutum an rabu da saki uku da zubda ciki amma shegen bakin ranka fata ka ke ya dawo" Mahdi ya fashe da dariya "ba fata nake ba tambaya nake" 22 Mafiyan Masoya-2 Rahma Abdulmajid Wayar Farid tayi kara, ya dauko ya duba ya zare ido yayi wa Mahdi rada "Itace" "Hello ranki ya dade... Aaa! Bana komai na zo ne?...To gani nan zuwa" Ya katse wayar ya mike da sauri ya dauki hankici ya goge baki da hannu. "Ta kira ni, ka biyasu in ka gama ni na tafi". Mahdi ya bi shi da kallo na mamaki da tsokana "Malam yaya za ka gayyace ni cin abinci kace kuma na biya, Yama ma za a yi ka ce mata baka komai abincin fa muke ci?" *** *** *** Tana tsaye a jikin wundon ofishinta tana leken shukoki a yainda ya shigo. Ko da yayi sallama da gaisuwa ta amsa amma bata juyo ba ta ci gaba da magana. "Gobe za mu raba bulk sms da labarai a jarida kan shakku da ake da shi kan faduwar hannun jarin kamfaninn man fetur na Ondowa...ina so mu tabbatar da labarin za kuma mu kash kudi ya shiga kunnuwan jama`an da wannan shakku ya dama don : 23 Mafiyan Masoya-2 Rahma Abdulmajid dole hannun jarin ya fadi kafin sha biyun daren gobe" Ya ji gabansa ya fadi muryarsa ta zakulo kanta ba tare da umarninsa ba "Ban gane ba.. kamfanin da muka sayi hannun jarin sa na wannan shekara sama da kashi ashirin cikin dari? Ribarsa ce fa nake jin kawai ribar mu a wannan karon da ake gasar sadarwa ba neman riba ba" Ta yi murmushi sannan ta juyo ta dube shi. "Kai sabo ne a wannan tafiyar...Kamfanin Na`ibi Ya saba asarar riba don janyowa abokin gaba asarar uwar kudi. Ban ce za mu yi asarar uwar kudi ba י riba na ce mu yi asara" Ya dan yi murmushi na hango inda za ta. "Kashi nawa su Ibrahim Hadi suke da shi a hannun jarin yau”. Bally ya sai hannun jari uku a wannan satin don samar da kafar tsayiwa a yakin mu saboda yana da tabbacin a fasahar makamashi da sadarwa zan kayar da shi don haka ya fara leka wasu kasuwanni don neman tudun dafawa in na yi tsiyata. Amma 24 Mafiyan Masoya-2 Rahma Abdulmajid yayi latti, don tuni na amince da bana son tsiyata shi a makamashi sai na sa masa ido a hannuwan jari" Ta zaro wata takarda mai zane iri daban daban. "Sun sayi hannun jari akamfanunuwa uku a wannan sati kamar yadda su ma suka sayar da nasu wa sama da kamfani bakwai. na kamfaninsu bai dame ni ba don na san ragon da nake yaki da shi, idan na

Chapter 1 of 7