Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
4 / 7
Lokacinda za ku yi wannan abu da baka bari daga kai sai Wilson ba, wannan ne dalilin da ya sa ya gudu, wato maana an sayeshi dole ya bata a duniya kafin a tona asirinka wanda in har ya jima da narkewa a wata kasa zai yi wahalar fitowar sunansa ta cutar da shi". Ya rage surutun ganin wanda ake wa ya kasa cewa uffan, ya duba agogo ya mike. "Na gayyaci wasu kwararru don jin raayinsu, amma fa a iya tawa kwarewar, halin kasa kawai za a iya yi a yi ruf da ciki kan wannan lamari, amma zai yi wuya a tsira hannun hujjojinda na ga an ajiye a kasa, a dan duba lamarin Master, na bar ka lafiya" Ya juya ya fice daga duhun falon 78 Mafiyan Masoya-2 Rahma Abdulmajid wanda gunkin Na'ibin ne kawai ke zaune yana wurga ido har zuwa a kalla mintoci hudu a yayinda kwatsam abin mamaki gareshi ya faru wato bayyanar Farida a gabansa. Itama ba maganar take jin yi ba wucewa tayi har inda katon katakon tara kayan shay-shayen yake ta zauna a karbunsa ta sunkuyar da kai na dan wani lokaci. "Me yasa baka gaya min kai ka kashe shi ba ka bar ni a duhu father?" Ta furta cikin sanyin murya na amincewa da aikin gama ya gama. "Ban kashe Hadi ba, ban kuma yi niyar kashe shi ba, Wilson ne yayi,na kuma nuna damuwa a kan haka" Tayi murmushi sannan ta dago kai ta dubi wanda har yanzu baya duban ta. "Ka daure ko rana daya father ka gaya min wata gaskiya da ko ina na tuna ka na san gaskiya ce ta ratsa tsakanin `ya da uba" Ya kashe tabar a hankali wadda ta fara lashe masa hannu. "Gata nan na gaya miki....Ban kashe Hadi ba, Wilson ne ya kashe shi, ban kuma ce a kashe shi ba, na dai ce a koya masa darasindea shi da dansa ba zasu sake yin hanyarkı ba. Wannan ce gaskiyar da zan iya 6 79 Mafiyan Masoya-2 Rahma Abdulmajid gaya miki yau, ko ba don Allah da kauna ba na fada don duniya ta gaya miki wadda ta fi ta a kaina" Sun hada ido a yanzu da farida me murmushi da hawayen zafin zuciya. "Kenan Bally na da gaskiya, ba tsautsayi ne ya kashee mahaifinsa ba, gidanmu ne... kuma kuka yi abin ta yadda zai zaci da hannuna ya ki ni "na gaya miki Wilson ne yayi shi kaďai, ba zan yi raguntar laka masa ba don na kubuta na wuce haka...a yanzu na gane cewa an sayi yaron ne ya gudu domin ya cutar da ni..." "Amma ba Bally ne zai sayi makashin mahaifinsa su kulla aminta don ya cutar da kai ba, muddin duk soyayyarmu zai iya jin ya ki jini na a kan zargi kawai" Na`ibi ya kada kai. "wannan tohon ciniki ne... ina jin ma an yi shi ne tun kafin Wilson ya fara aiki tare da ni. Tsohon shiri newanda ina da alammominsa da aynzu nake hangowa kuma su ne suka hana ni magana tun jiya da ake baza wannan zance...Amma Richard zan dulmava kafin komai ya cika da ni" Bai rufe baki ba suka ji karan Maman SO Mafiyan Masoya-2 Rahma Abdulmajid Farida daga kafar bene da wata shakakkiyar murya me nuna gajiyawa. Babu wanda ya kalli wani suka rankaya a gujc zuwa sama. Tana tsaye da remote a hannu tana nishi a zagayayyen falonda ke jikin kafar benen inda take kallon Italabiji, duka suka dube ta, amma ganin idanuwanta na kan faifan sai su ma suka raja'a a kai, cikin zumudi tana tariyowa. "Dubi abinda ubanki yayi Farida...wannan kwafin a gidan mai aka bani cewa in jira zuwa dare zan gan shi a labaru don tuni CNN ma na da kwafe ballantana gidajen talabijin din gida". Faifan ya soma aiki a yayinda ya nuna Merry tana kuka cewa ita daduron Na`ibin ce duk da kawar 'yarsa fiye da shekarunda suka yi suna daduro, bai bar ta tayi aurere ba amma ya ce ba zai aureta ba ta zubar da cikin da take da shi don bai son haihuwar shege.. da dauke wannan jawabi sai aka fara nuno faifan bidiyon Na'ibin da Merry wanda suke kan gado suna daf da soma masha`a. Farida ta iya barin wurin a guje inda amai ya tirnike ta ta karaso kan matattakala ta zube tana amai da mummunan kak ari. Wannan ne ya dauke mata ganin faduwar mahaifiyarta wadda ta taho don ST Mafiyan Masoyа-2 Ralima Abdulmajid tambayar mijinta da yake tsaye a yanzu yana hawayen da bai san na menene ba, ta iso gare shi don ta cakume shi ta ji dalilin cin amanarta, sannan jin mutuwa kusa da makogwaronta sai ta ji bukatar shakeshi su tafi tare, sai dai duk cikin burirrikanta babu wanda ta cika domin faduwa tayi kasa da rai ko babu, amma dai ba nunfashi. Duk da halinda Farida ke ciki zaune kan matattakala tana fama da kirjinta, jin ihun mahaifinta da ke kiran matarsa cikin kuka ne ya sa ta dafa matattakalar tana gsanin bibiyu don ta karasa inda suke *** *** *** Kamar yadda su Richard suka tsara haka komai ya wakana. A wannan rana mutuminda dama ba a gama yayinsa ba wato fan takara da postersa ta yadu ko ina,ga shi kuma an ja hankalin mutane da yi masa tuhumar kisa, sai gashi a daren ana kallon masha`arsa da wata yarinya, har ma an yi posta na wani sashi ana likawa, tuni a daren mlamai da manyan mutane da sauran talakawa suka fara Allah wadai da yada zanga-zangar su fa garin addini da shara`a ba zas zauna da fajiri ba ballantana a ce ya mulke su. Mafiyan Masoya-2 Rahma Abdulmajid Wayewar gari kuma aka tashi da wani sabon labarin, shine na faifan kisan gilla da wasu matasa suka yi wa Merry a matsayin `yan aike daga wanda ta tonawa asiri wato Mansur Bici. Tattaruwan labaran ya sanya har mkwabtan jihohin sai da suka taya wannan jiha jimamin wanna abu. Duk wannan badakala bata sami iyalin Na`ibi a gari ba, domin kuwa jirginsa na musamman ne ya debe su da gangar jikin matarsa zuwa kasar Ghana inda aka wuce da matar asibiti don ceton ranta da ake tun a cikin jirgi inda shi ya tsaya yin wayoyi don ganin yadda zai laddafa abin, amma hakan ta bai wa `yansanda damar cafke shi, musamman ma ganin cewa a wannan awoyi tuni bai da gata, domin kowa ya nisanta kansa da shi babu wanda yake kira a waya ya dauka, kamar yadda aka je aka yi zdai-dai da ofisoshinsa da kamfaninsa da na iyalinsa 83 Mafiyan Masoyа-2 Rahma Abdulmajid Babban BAKWAI asibiti ne a birnin Acra wanda an san babu mai dosan hanyarsa sai masu mulki da iyalansu, nan mahaifiyar Farida ke kwance take jinya cikin matakan tsaro na musamman tare da suturta zaman nasu ga kowa, daga ita sai Farida sai kanin Faridan wanda ya baro makaranta ya zo taya ta jinya da jumamin wannan rayuwa da suke ciki.Sati biyu dattijuwar na ci gaba da yin nunfashi ne da taimakon na`urar zuko nunfashin bata san a inda takc ba. Kenan bata san halinda iyalinta ke ciki ba, musamman mijinta wanda a halin yanzu yake sakayc hannun yansanda bayan da mutanen gari suka kona kusan duk wasu gine-gine da a ka san karara nasa ne kafin jami`an tsaro su farga, wanda ba wai lallai masu kishi bane suka shirya hakan ba sai abokanan siyasar sa.. Ya dan sami damar yin magana da su Farida a waya wajen sau uku sai dai basu tattauna komai kan halinda yake ciki ko musababbabi ba illa va kan tabbatar wa Farida cewa ta gaya wa matarsa S4 Mafiyan Masoyа-2 Ralma Abdulmajid cewa, yana son ta kuma ta yafe masa,zancen kenan, kuma shine Farida bata saba da shi ba take cin kuka in ta saurara, amma a maganar su ta karshe ya kara da wasu kalamai guda biyu sune na tabbatar wa Farida cewa shi bai kashe Hadi ba, bai kuma kashe Merry ba, sannan ya jaddadda kaunarsa garesu da kuma neman gafara. Washe garin wannan hira a waya ne aka tashi da wani mummunan labarin cewa Allah Yayi wa Mansur Na`ibi rasuwa a inda yake tsare hannun jami`an tsaro sakamakon bugun zuciya mai tsanani. Shafik kanin Farida ne ya koma Najcriya don halarta jana`iza mai radadi da ban tausayi ta mahaifisnsu sakamakon kasancewar Farida da mahaifiyarsau duka a gadon jinya domin Faridar ta sami bugun zuciya daga jin wannana labari wanda ya so kai ta lahira daf da mahaifin nata. Duniya kenan. Fadan kamfani ya lashe Hadi ya Lashe Na`ibi saura Farida da Balala abokan gaba biyu wanda a kafar leken asirinsa ya sami labarin inda farida take ya silalo ya zo don yi mata gwalo, da ner an ta daga farar tuta don ya gama ramuwa, amma hada ido 85 Mafiyan Masoya-2 Rahma Abdulmajid da Faridar wadda bata jima da farfadowa ba ya sanya shi zubar da makamansa ya shiga wani yanayi da bai san ma`anarsa ba. Faridar wadda tayi kama da me jinyar kanjamau din da ta tsere wa mutuwa a watanni shidan farko saboda ramewa, baki, muni da rashin kula da kai. Ta juyo ta dube shi kanta jingine da gwiwarta sannan tayi murmushi ga mutumin da bai iya motsawa daga inda yake tsaye ba, ta dan nisanta kwayar idanunwasa da inda yake. "Ka zo ne ka gaya min ka yi nasara a kaina Bally? Na amince ka yi nasara. Ka kashe, Father, ka kwantar da mahaifiyata, ka kwantar da ni, ka bata wa duk me rabe da sunanmu suna. Wannan babbar nasara ce kwatankwacin babbar hasararka" Ta tashi dakyar zuwa jikin wundon ta dafa tana kallon waje inda ta ba da baya wa mutumin da baya iya kifta idanunsa sai don su bi ta duk inda za ta cikin satar so da tausayi da bai san lokacin da suka iso masa ba. "Ka yi hasara ta duk dukiyarka da ka dilmiyar don ruhe Nalibi. wadda ina da tabbacin ka yi mata sarar da ba za ta sake So Mafiyan Masoya-2 Rahma Abdulmajid tashi ba. Kayi hasarar hana zuciyarka kusantar abinda ta fi so a duk duniya inda kayi musu shingen da ba za su sake haďuwa ba har abada duk da ita ma zuciyar taka ba za ta dena son ba har a bada..." "Ta tattako zuwa gabansa a yanzu cikin kwalla da zafin rai. "Mafi girman hasararka,ita ce ta hada karfi da makasan ubanka da kake daukar wa fansa don ku kashe ku dulmiyar da wanda bai da hannu a kisan.... Hasarar da ya kamata ka yi min gori da na yi wanda ba zan warke daga faduwar da nayi a gabanta ba itace ta son ka da nayi...Bally, daya-dayar hasara ta itace mika wuya da zuciyata tayi ga soyayyarka wanda na kasa denawa.Wannan soyayyar ce ta sa na sanya matukar tausayi a yakinmu inda ban yi saurin hallaka ka ba kafin ka hallaka min iyaye da suna, ita ce ta hana ni ganin fatar dabban da ke kwalkwalwarka ta inda na kasa fahimtar kai wane irin naman daji ne...na zamo duk wani karamin duka inna yi maka sai na koma gida nayi jinyar radadinsa a naman zuciyata ...ban san cewa kana dauke da dutsen da ba ji ne kawai baya yi ba, a a! Har gangarowa か 87 Mafiyan Masoya-2 Rahma Ahdulmajid yake son yi ya fasa kaina..." Kuka ya ci karfin Farida a yayinda ta sanya hannunta na dama tana dukan 6arin zuciyar Balala tana nunawa. "Nan ne inda na taba dauka a matsayin laimata idan duk duniya ta zamo rani a gareni, nan nake shiga na sami yanayin damuna, ban san cewa a she gobarata wadda za ta zo daga kogi bayan ta kona duk wani ruwa da zai iya kashe ta za ta sami hanyar zuwa gare ni ne ta wannan mafaka tawa wato zuciyarka Bally" Tayi kamar ta kifa a kan kirjinsa don jin lallai tana bukatar mabuya daga azabar da take ciki, kuma mafakar ta zamo irin wadda ta yarda da ita take jin dadinta jiri ya fan zari zaren kwanyarta amma ta kada kai ta ja jikinta da karfi cikin kuka. Kasancewar idanuwanta a rufe suke a yanzu bata san Balala ya riketa ba sai da ta ji bata tafi ba kamar yadda ta bukata, ta bude idanunta a kan nasa wanda suke zubar da hawaye fiус da nata, yana nishi kamar ransa zai fita. "Farida har a yanzu kina gaya min baki da hannu a kashe mahaifina?" Ta karkatar da wuya abinda ya bai wa NN Mafiyan Masoya-2 Rahma Abdulmajid hawayenta damar sauka ta dama inda ta dan yı murmushi. "ka sani sarai ban kashe shin ba Bally, ka rike wannan hujjar ne don ka cika zuciyarka da Kıyayya me hujja. Amma ka sani Baba Naibi har ya mutu yana shaida min cewa bai kashe mahaifinka ba...Na kuma yarda, saboda na san wanda ya kashe din, Balala wanda yake raba idanu cikin kuka har da majina a yanzu a kanta. bai sake ta ba. "Na san da kunya na fada... Na san ba lokacinda ya dacc ba ne...watakila lokacin fadın ya wuce na yi latti...amma bani da zabi dole in fada, shine Farida ban taba dena son ki ba... Na azabtu matuka a yayinda so da ki suka hadu a zuciya daya tak da take kirjina kowanne ya kasa kayar da dan uwansa don zaben abu daya, wannan ya sanya na kasa samar da ingantaccen zabi a rude nake Farida, a rude nake..." Ya kamo kumatunta da tafukan hannunsa. "Farida i yi min alfarma, koda ban dawo da jiya yau ba a rayuwar mu ki bari na 89 Mafiyan Masoya-2 Rahma Abdulmujid sake sanya ki a mafakarki,a laimarki, a matsuguninki wato zuciyata, tana nan da duk adon tarairaya da tausasawa da kika yi mata, ki bari na cire ki daga wannan azabar da bata yiwa idanuwanki da labban ki da zubin fuskarki kyau ba.Farida ki bari sashin soyayyarmu ya biya wajibinsa na nema miki sassauci" Tayi murmushi sannan a hankali ta zarc hannayensa daga fuskarta ta sakar masa su a kasa. "Haka na so a lokacinda na nemi kada mu yi wannan karawar amma ka ki, yanzu an yi latti. Bally ka kwatanta yadda ka ji a yayinda mahaifinka ke kwance cikin azaba kana jin wani ne ya kashe shi. Shin soyayyata ta tsirar dani a wurinka? Sam! Bata yi tasiri ba har saki na ka yi...Dubi gefen can uwata ce kwance babu tabbacin tashi, mahaifina ya mutu har an binne. sunanmu ya juya daga launin fari zuwa fin baki duhu...Yaya kakc jin ina jin ka yanzu Bally? Je ka, na gan ka na kuma ji sakonka. amma ka sani kiyayyata ga wuta da azabarta za su iya yin takara da Kiyayyarka zuciyata, ina da tanadin inda zan karya ka. O Mativan Masorа-2 Rahma Abdulmajid cikin ruwan sanyi,yakin farawarsa kenan" Ta juya ta bar wajen a hankali inda ta shige dakinda mahaifiyarta ke jinya ta rufo Kofa *** * ** Daga shi sai singileti fara da jan gajeren wando yana kykyata dariya ya juya yana kallon wadda ke rataye a bayansa a goye wato Farida.... Wannan ne hoton kawai da ya sami hasken fitila a cikin duhun faicn da Balaia ke kwance a doguwar kujera tamkar matacce in ka cire idanuwansa dake kan wannan hoto nasu da Farída cikin hawaye.bai san me yake ji ba baya da tuna halin da Farida ke ciki. Zai dai iya tuna cewa an zo an ce Richard na son ganinsa yace ya shigo amma koda ya shigo ya tsaya kansa, ya jima kafin ya tambaye shi duk da bai juyo gareshi ba. "Me kake so Rich?" Richard yayi murmushi. "Na zaci zan same ka cikin farinciki kana biki, sannan a yi murnar dani na karbi sauran balane dina na bace dga wannan rayuwar...Ban sani ba ko Faridar da ta fice a 91 Mafiyan Masoya-2 Rahma Abdulmajid karo na karshe a rayuwarka ce take son baka kewa" Har yanzu Balala bai juyo ba ya sakc magana cikin gajiya. "Me kake so Richard, me zan baka bayan abinda na baka? Ginin kamfanin kake so na baka tunda komai ya kare?" "Tunda baka son magana zan takaita, Nayi aikina na cika duka bisa alkawari, kai ne ya rage baka cika min ba, wato ragowar hannun jari hudu da za ka bani...ina jin wannan kuma hakkina ne da duk da abinda za ka biya ni zan karba" "Kangon ginin kamfanin mu zai isa ya biya hannayen dai?" Balala ya tambaya ba tare da ya juyo ba. "Abinda zai ragu babu yawa, zan iya yafewa" こ Balala ya tashi, kwanyarsa da zuciyarsa motsa shi kawai suke babu tunani ko digo, ya dauko wasu takardu ya zo ya rattaba musu hannu sannan ya mika su ga Richard. "Ga su in za su ishe ka, kadai suka rage min bayan gidaje, da motoci, da 92 Mafiyan Masova-2 Rahma Abdulmajid Kananan abubuwanda za su ishe ni cin abınci har komawata ga Allah. Wannan ginin idan ma na rike hutun jaki ne da kaya a ka don ba zan iya kula da shi ba a yanzu, sannan ba zan iya wani damben tara abin duniya ba a tsayin rayuwata, tunda lokacin da nake dasu, basu cece ni daga bakin cikina ba. basu bani abinda nake so ba, basu shiryar da ni ga abinda ya dace ba, basu kuma sanya ni a kan hanya ba...kenan kai da su kake so ba abinda za su samo maka ba gara ka rike su" Richard ya karbi takardun cikin farinciki. "Sorry, da alamar kana cikin wani hali na kunar zuci, amma ba abinda ya shafe ni bane. Na gama nawa zan kuma bace daga rayuwarka don na san zai yi wuya ka sake mallakar abinda zai ishe ka nemana, don haka ina maka fatan ci gaba" Ya juya ya fita ba tare da Balala ya ko kalli wajen ba, sai da ya fice ne ya ji yana bukatar dukufa yayi kuka tamkar yaro Karami. *** *** *** Mafiyan Masoya-2 Rahma Abdulmajid Farida ta sami halartar gagarumar addu'ar ukun da akayi na mahaifinsu bayan da `yan uwar mahaifiyarta na jini suka iso daga kasarsu don tsayawa tare da ita a asibiti. Addu`ar ukun bata sami halattar 'yan siyasa da marigayin ya rikide zuwa zamowa daya daga cikinsu ba a yanzu, sai dai ya sami halartar daruruwan abokanan sana` arsa daga ciki da wajen kasar sai ma`aikatansa da dangunansu da wadanda ya taimakawa da wasu Fandations dinsa musamman wadanda suka ci gajiyar gidauniyarsa ta tallafawa marasa karfi don yin karatun kimiya a matakin jami'a wanda Allah Yayi yawa dasu. Wannan ya sanya wasu `yan siya babu shiri cikin borin kunya suka dan leko ganin cewar bai sami irin kyarar da suka guda ba. Ganin abin ya hada da masu addinai daban-daban sai addu`ar ukun ta kasu gida biyu, wato daga masu addu`ar fidda`u sai masu ranar bangirma ga Gwarzo Na`ibi. Farida da Shalik cikin rakiyar aminai da suka hada da su Farid, suna sahun gaba wajen taryar jama'`a iri daban-daban. Faridar wadda ke cikin din auta kasancewar a yau ne ta iso gidan da babu mahaifinta sai 94 Mafiyan Masoya-2 Rahma Abdulmajid hotunansa sanyc da bakaken kaya da bakin tabarau don gudun nuna idanunta, itace ta fara hango Balala wanda ya iso da `yar tawagarsa cikin bakaken kaya da kin tabaran shima wanda bai boye gajiyar dake fuskarsa ba. Babu Gata lokaci ta bar layin jama`a don shigewa inda zata iya nisanta da hotunan a yayin da ta kasa jurewa. Koda ya gama gaisuwarsa a waje ya so saduwa da iyalin marigayin, sai dai abin bai samu ba kamar yadda ya bukata. Ya san me ya janyo hakan sai bai matsa ba ya koma. A cikin falonsa ya hadu da Wilson wanda ya sanya duk da mutuwar zuciyar da ya zo da fatan zaman da yake ya ji ya kasa da ya sami Wilson din a zaune a falon jira. "Daga ina me ka zo yi a nan?" Wilson ya mike da dariyarsa ta keta. "Na zo nayi maka barkan rasawa da muka..." Fita min daga gida kafin na yi wani abu da bai dace ba" "Allah Ya gani sai na gaya maka abinda ke tafe dani kafin na fita...Ina so ne nace maka yanzu mun zama daya...Su 95 Mafiyan Masoya-2 Raıma Abdulmajid Na`ibi duk sun rasa rayukansu yayinda mu kuma muka rasa Farida ni da kai" Ibrahim Balala ya tsaya cak a yanzu dan ya ji abinda Wilson ke son cewa don duk haushin da yake ciki kamar fa zai ji abinda bai taba ji ba. Sai ya sami kansa yana turo iskar murmushin raini. "Ni da kai mun rasa Farida kace?" Wilson ya zauna ya dora kafa bisa `yar uwarta. "Haba Bally! Kana zato kafi kowa ido? Doguwar kyakkyawa kamar Farida dake zagaye da samari ke baibaye da ita a ce ni ba zan ga mafarkina tare da ita ba? Kawai dai duk cikin samarin kai na ji na ki jini kasancewar kai ta baiwa zuciyarta, don haka nayi amfani da ofishina wajen saukar muku da hasara...Bayan ka auri Farida har ina da tabbacin ta je da kai inda ban je ba a ilahirinta har kun sami ciki, na yi amfani da mahaifinta wajen shirya kashe ku...Ba da sona ba ka ci sa`a ka tsira, amma ban fadi ba, domin Farida ta rabu da kai da" Ibrahim Balala yayi cikinsa da sauri don neman mutuwar kasko, amma tuni ya nuna masa bindiga yana kada kai. o Mafiyan Masoya-2 Rahma Abdulmajid "Um-um! Ban da garaje Bally, daga baka tarihi sai ya zama fada...Me zai hana ka tambaye ni cewa...me yasa azabar bata tsaya kanka kawai ba na hada da Megidana da masoyiyata? Da na baka amsa cewa, wanna 6angaren ba nawa bane Fansar Richard ne wanda yayi amfani da kai da kudinka ya dauki fansarsa a kan Na`ibi har ya ci riba saboda kai wawa ne.Richard, Merry, da Wilson duk gamayyar `yan daukan fansa ne wadada sune ainahin Mafiyan Masoya ba ku ba.Richard, ya so mahaifiyar Farida, wadda aji da addini ya sa ta zabi Na`ibi Mansur tayi fatakali da shi, wanda adalilin soyayya da nuna mata iyakarta ne ya taso Na`ibi a gaba ya kuma ingiza shi gasar kasuwa da Ubanka don dukiyarsa ta kare...duk wani abu da ka ga muna yi har zuwa kwana uku baya a tsare yake shekaru masu tsayi, wato Richard ya kashe Na`ibi ya tozarta matarsa da mutuncinsu a idon duniya ya kuma ci ribar kudi, yayinda ni nake son ganin bayanka kai da ka kwace min lFarida" Yayi nishu da kakari sannan atishawa a yayinda Balala ke ta hankoro bindiga na 97 Mafiyan Masoyа-2 Rahma Abdulmajid tsorata shi, domin tuni har ya soma hawaye na takaici da rashin mafita Kasan me ya sa nake bayar da wannan dogon labari? Ka san me yasa na zabi na baka labarin ba Farida ba? Saboda ka fi Farida jahiltar lamarin...Saboda awoyinda suka rage min ba zasu isa na sami zama da Farida har na fayyace mata ba kafin ta mutu, domin yadda ka ganni KUAnan...Mintoci suka rage min a duniya...Nida Richard mun sammace junanmu saboda hadama da gudun kada wani ya fara kashe wani...Bikinmu na farincikin nasara a gidana na sanya wa Richard magani don ya mutu yayinda nima ya sanya min wani a Cocain don na mutu. Duk da ba shiryawa muka yi ba, amma dabarar mu ta zo daya ta mu sanya maganin da zai debe mu a woyi bamu mutu ba don kada mu cika a gidajen juna, wannan ya sa bayan mun fahimci mun ha`inci juna ni da shi, mun gaya wa junanmu cewa mun sammace junanmu cikin mayen kayan da buguwa da tuna Merry ta ukunmu da muka kashe, mun zabi mu mutu a wurin wafanda muke so mu kara goga wa kashin kaza" 8o Mafiyan Masoya-2 Rahma Abdulmajid Yayi wani yunkuri a yanzu da idanunsa ke kara yin jajawur na azaba. "Zan mutu a hannunka bayan da na sanar da duniya ka sammace ni don ka mutu a sarka na kara nisanta ka da Farida, kamar yadda Richard na hanyarsa ta isa Gahana don dubo masosiyyarsa ya cika a kusa da ita...Kada ka musa haka don in ka yi wani yunkuri Za ka riga ni tafiya don haka ka tsaya kawai ba so nake na kashe ka ba tunda na riga na kashe soyayyarka da Farida za ka iya ci gaba da zama a duniya in har baka matso kusa dani ba" A yanzu Balala ya kasa amincewa da ya jira umarnin kamar yadda Wilson ya tsara, amma yaya zai yi? Ji yayi tau! An harbe hannun Wilson bindigar ta fadi inda ya sunkuya ya rike hannunsa yana kallon gefen Balala cikin mamaki abinda ya ja hankalin Balalan shima ya juyo Farida ce rike da bindiga.Duk da tana cikin bakaken shiri bai hana ta juyo cikin dauriya tayi wwa Balala wani kallo na soyayya da ya sanya hantar cikinsa kadawa ba, sannan ta dubi Wilson a yayinda ta lalubo hannun Balalan da ya zama 99 Mafiyan Masoya-2 Rahma Abdulmajid mutummutumi ta rike tana murza su a nata. "Ashe kai ba gwani bane Wilson...Da kai gwani ne da ka san cewa ko mutuwa bata daukan ran ran soyayya sai dai ta raba ran masoyin da masoyinsa. Kenan kayi kuskure na barin Farida da Bally a raye, domin wata dama ka basu ta sake kara wa soyayyarsu nunfashi" Ta sanya kai jikin kafadar Balala a yayinda ta yi wani murmushi na nuna Kauna. "Bally na sona, ina son sa har yau duk da wannan Garna da kuka yi...Ina fatan wannan sako ya isheka zuwa lahira" Wilson ya rike zuciyarsa yana kakari cikin kallonsu, a yayinda jami`an tsaro suka iso falon don tattara shi kafin ya karasa. Ana ficewa da Wilson Farida ta mayar da fuskarta murtuke ta zare hannunta daga na Balala wanda yayi maza ya rike ragowar yatsarta ta tsakiya "Farida" Ya ambata cikin tafasar nunfashi. Ta juyo suka hada ido da nasa mai yayyafi. "Farida da gaske ne abinda kika fada. ina son kilIUHU! Farida na yarda ni na yi 100 Mafiyan Masoya-2 Rahma Abdulmajid asara ni na sha kayc a wannan fadan, ba da kudi ko suna ko wani abu ba, na sha kayc ne da na rasa igiyar aurenki wanda na salwantar da ita da hannuna a wannan cacar...Farida yaya za ayi na sake samin wata dama da ba zan baki kunya ba a cikinta?" Tayi murmushi sannan ta karbi dan yatsanta Wannan wasan kwaikwayon da nayi a gaban Wilson nayi ne a matsain sakon hasara da zan iya ba shi na karshe ya je lahira dashi ba don wai lamarin haka yake ba.Bally na dauko bindigar nan ne na zo har gidanka don na karar da wannan wasan dake tsakanina da kai ta hanyar kasheka na kashe kaina don gudun bai wa wata soyayya damar rayuwa wadda na lura a cikin nunfashin mu take. Na yarda da hukumcinka a lokacinda babanka ya mutu na kokarin yanke duk wwata zumunta tsakanina da kai...Amma na kasa kashe ka ne bayan da na ji sakon Wilson na cewa na sauya dabara, na kayar da kai a wani sabon yakin Mafiyan Masoya" Ta juya za ta fita amma Balala ya sako tareta. "Idan ko haka ne kada ki fita sai kin 101 Mafiyan Masoya-2 Rahma Abdulmajid kawo karshen rayuwata, muddin kin san cewa ba zaki sake rayuwa da ni ba kamar yadda na san ba zan iya rayuwa bakkc ba.Ko da baki kashe kanki ba ki kashe ni Farida ko kuma ki sake bani wata dama ta so" Farida ta juya tana dariya ta fitar da waya inda ta buga asibitin mahaifiyarta dan jin ko Richard ya iso kamar yadda suka ji a bakin Wilson? Kanin mahaifiyar ya tabbatar da cewa, lallai an ce wani mutum ya iso har ya saci hanya ya shiga dakin mahaifiyarta inda ya mutu a jikin gadonta kuma an same ta ta bude idanu

Chapter 4 of 7