Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
1 / 8
An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels ME GARI YA WAYA? NA ZAINAB KABIR BIROMAN (MRS. SUNISU BRISCOE) KACIBUS MUGUN GAMO arkada makullan hannunta take gami da karkada K Kafa, "Kai ko abokinka ba ku isa ba, ba ku kuma kai ko matsayin da zan 6ata yawun bakina wajen magana da ku ba. In ce na gaya muku ba na ra'ayinku a kai kasuwa? kila har yanzu akwai ragowar matan da suke iya amsar kyautar saurayi, saurayin ma har saurayi me ji da kansa amma kuma ya rasa macen aure, kai tir da wannan abin kaico. Ni kam ga zabina nan." Ta nuno shi bayan da shi kuma, "Sai dai fa shi ba kyautar shi a ka yi min ba, a'ah! Ni na gani na ce ina so, kazalika shi ma haka, don haka muka aminta da junamu." Taku suke cikin isa da kasaita, ya ja ya tsaya dai-dai gabansa, da kallon raini cikin halin ko in kula ya ce, to kai fa abokina sai ka dangana, tun da ta kasa amsa kyautar da aka yi mata kamar yadda ta ce din dai sai a kai aksuwa, kila wata ta taya, ka san ba duka mata ne suke iya aınsar kyautar saurayi sukutum ba. Ko kafin ya furta wani abu sun shige cikin mota, ita take jan motar kamar ta taka su ta shige cikin gudu. Zaune yake a ofis din nasu ya rasa abin da yake masa dadi, ga tarin aiki a gabansa amma ko ya kula, ya yi sallama ya shigo da niyar ya cike wasu takardu amatsayinsa na Director (shugaba). Ja ya yi ya tsaya bayan da ya fahimci halin da abokinshi ya ke ciki, damuwar dai be wuce na abin daya faru da yammacin jiya ba,tun ajiyan babu wanda ya ce wani abu, kowanne da irin tunaninsa, 5 a dukkaninsu rayukansu a bace yake to amma ko katin safiyar yau tuni shi Samir din ya mance musamman dayake safiyar ne suka sami takardar yarjewar wasu kwangilolin gini da tiți da aka ba su, shi kam in dai a kan harkar kudi ne ya kan ınance da duk wani bacin rai da yake ciki. Ya fara magana, Da Allah Waheed kar fa abin jiyan nan ya dame ka, manta kawai ka share ka hada ka watsa a kwandon shara. Cikin matsanancin bacin rai ya dube shi, ka san Allah duk ranar da yarinyar nan ta sake ta shigo hannuna ta kade har ganyenta, na tsane ta, na tsane ta na dada tsanar ta tun bayan da na dada fahimtar me ke tsakanin su da wannan dan iskan yaron, me zan ci da ita? wallahi kow aye ya yi wannan hadin ya cuce ni ya kuma gama illata rayuwata. Kai haba! Wallahi zan ci uban yarinyar nan muddun ta sake ta shigo hannuna, ko waye ya yi wannan hadin zai gwaminace kida da karatu. Na tsane ta, na tsane ta ba zan taba son ta ba wallahi. a Hankalinshi kwance ya yi dai-dai a kan katafaren gadon gefen shi Helen ce yarinyar da yake hutawa da ita cikin daren hannunshi daya rike yake da karan sigari yana busawa, cikin matsanancin 6acin rai, ya shiga tuhumar kansa, me Waheed ke nufi da shi ne? Hakika ana shirin aiwatar da dan karamin yaki a garin nan, raiin hankalin ya yi yawa ya zama dole ya yi gaggawar daukan kwakkwaran mataki a kansa, domin ya gwada mishi shi ba tsaransa ba ne, be ko isa ja da shi ba. yana son Hecdaya son da baki ba zai iya kwatanta shi ba, don haka zai iya aiwatar da komai a kuma kan kowa in dai a kan Heedayansa ne. 6 Hello... hello..., wa ke magana? Shiru ba amsa, har ma ya dan fusata waye ne domin (no number) daga daya Garin a ka saki wata ‘yar dariyar cusa haushi Rival dinka ne ko da yake ba na kira ka da wannan kalmar ba, tun da an ce ba a son ka ba a ra'ayinka, kai ba a ma amsa kyautar da aka yimata ba. Ya ci gaba daman na bugo ne na ja kunnenka na kuma yi naka albishir wannan karon ka debo ruwan dafa kanka, ko Ja za a yi tashin dunva na uku ne sai na mallaki zoar so na heedaya ko da yake ko ma ban fafa ba ka riga ka sani ni tak so ni ake yayı, domin ni gani na ma aka yi aka ce ana yi ba gwanjo na aka yi ba. ka fahimta? Da sauri ya yi kokarin ba shi amsa dan kar ya katse layin ya bar shi da tarin miki a wuyansa, ya fara so abokina abin da nake so ka lura ka kuma gane, sai fa na aure ta ba wai don ina son ta ba a'a ko daya, sai fa don in cusguna rayuwarka, in saka ka cikin kunci kamar yadda na saka ka a baya, domin nuna maka cewa ko a cikin gayu kai fa fan rakiya kake, sli ya sa ma na zo mata a matsayin Bonanza, tun da na san ba ta kai ko matsayin yarinyar da zan iya tsayawa da ita ba da dai sigar so, ka ga ko tun da ka ga na zo mata a bonanza, na san abin da na taka ne domin shi ma Bonanzar zan kwasa, ka lahimta abokina.... ko kafin ya ba shi amsa ya yi saurin katse layin. Cilli ya yi da wayar bayan da ya shiga nadar abokiyar shashancin nasa fada yake tamkar ita ta kai zomon alhal rataya aka bata. Koda yake tamkar mahaukacin kareyake idan zuciyarshi ta baci. Yau fau lamarin da girma ko dan ya nunawa tsohon abokin nashi iyakarsa, ai ko ba ya son ta baya ra'ayin aurenta ya zama dole ma ya so ta ya kuma aure ta 7 ballantana ma akwai abin da yake so yake kuma m uradi irin ta zama mallakinsa? Tashin farko ya tuburewa mahaifinsa dangane da lamarina urensa da abar kaunarsa, iya kokari Dr. ElHussain ya yi gurin mahaifin yarinyar domin akwai sanayya a tsaknainsu amma fa ba nasara, ya kuma fahimci lamarin dan haka bai riki Ambassador da komai ba face alheri, ga Tahir ba haka nan ba ne a gurinshi ya tashi hankalinshi, kai kila da wani ne zai iya hakura ya bar mishi Heedayan ya rungumi kaddara to amma da yake babban abokin adawarsa ne kana makiyin da ba shi da kamarsa, ba ta yadda za a yi ya iya hakurce masa, zuka-zukan 'yan matan nasa har guda biyu? tamkar ma wani raini ne wannan da wulakanci, ya yarda ya kwace masa Zecnatu amma wannan karon kam karyarshi ta sha karya ko don ya gwada masa iyakarsa da kuma fifikon son da yake wa yarinyar. Heedayat da Zeenatu ko kadan ba ka iya hada su a ma'auni guda a zuciyarsa. Kwanaki hudu ya rage a daura auransu shiryeshriye sun kammala dagakowane Bangarori amma fa ban da gurin amaren, dukiya kam an kashe ta ana kuma shirin kashe ta daga kowanne 6angare, lefe ne na gani na fada da sai 'ya'yan wane da wane kai ko su din ma sai isarsu ta kai isa, duk kuma daga aljihun General da mai dakinsa da ma duk irin hidindimun da aka yi babu ko sisin Angon. Haka nan a bangaren amarya ma iyaye sun yi bajinta wajen' gwangwaje 'yarsu da kayan alatu irin na kasar Italiya, musaınınan a ka tafi donin hado mata kayan daki, haka nan kayan da za ta ci biki da su, musamman aka tafi birnin Mumbai na kasar Hindu aka hado mata su, to sai 8 dai fa amaryar ko a jikinta domin sun gama wshirya wace za ta fisshe su ita da abin kaunarta Tahir. Amarya ta sha kamshi. Ta fada gami da rangwada guda, ta dube ta da 6acin rai, ta nuno tada yatsa wallahi Sameera muddun ba so kike mu yi gagarumin tashin hankali ba kar ki kara gaya minwannan sunan. Amarya? Amaryar uban wace ce ni? Dariya ta saka to Allah yahuci zuciyarki, ta gyara zamanta, ga shi kuma ni da zuwa na yi mu tattauan game da bikin, to kuma ga shi an min wannan kashedi? Ba ta dai ce mata komai ba-ta dada tamke fuska alamar babu wasa. Sameeran ta yi shiru na wani lokaci domin momy Kaltum din ce ta wakilto ta, su tsara abubuwan da suke ganin ya dace da kuma abubuwan da suke bukata. Ta yi Karfin hali, Heedaya ina ga lokaci ya kure har ma za ki tsaya batawa kanki lokaci tun da dai haka Allah ya shirya ba sai a yi hakuri mu karbi zabinsa ba. kuma ni meye ma abinki a gurin mutumin nan da Allah ki so shi ki manta da komai..... Wani kundumemen ashariya ta sako mata, hakika yau na yarda ba ki da tunani har ma kike danganta ni da wannan mugun mutumin, to bari ki ji ba na son sa, ba na son sa ba, zan taba son sa ba domin ba shi da tarbiyya ko kankani. Ta yi saurin datse ta a'ah to in dai wannan ce hujjarki ba ki ko da madogara mai kwari, domin shi ma wanda kike abin a dominsa ba tarbiyyar ce da shi ba, kai ni ganina gwanda wannan din, kila in kika yi mishi da'a kika yi mishi biyayya sai ki ga kun zauna lafiya har ma wata rana ki so shi..... a 9 Cikin fusata ta ce, aikin banza kawai na yarda ba ki da mutunci wai har ke kike fadawa Tahir wannan kalmar.... Ta tari nufamshinta, a to maganar gaskiya ce ina wata tarbiyya a gurin Tahir? Shi din wanda kike abin a dominshi tarbiyyar ce da shi? Ina so ki tina idan ma kin mance ne rashin tarbiyyar da mutumin nan ya gwada mana tun daga farkon haduwarmu. Eh na yarda ba kuma na ce tarbiyyar ce da shi ba, to amma rashin tarbiyyar tasa ta kau na wanda kike hankoro a kansa ba, har ma kike kokarin bata ran iyayenki a kan kawai da namiji da ba shi da tabbas. fanimec Na ji dai duk dai abin da za ki ce na kuma ki na kuma gane matsayina a gurinki, domin ke munafuka ce, ne fuska biyu, mara son farin cikina, A baya kina nuna goyon bayanki ga Tahir a yanzu kuma kin sauya daga wata fuskar, to ki ji ki sani, ke din nan baki isa sanya ni na canja abin da nake so ba. Fice ki ba ni waje, ba ni ba ke kar ki Kara zuwa inda nake duk me so na dole ya so Tahir, duk kuwa me kinsa dole ne na ki shi domin ni yake ki ba shi ba. Kwana daya kacal ya rage a daura aurenta tuni gida ya cika ya batse da 'yan uwa da abokanan arziki, dangin mahaifiyarta na Yobe da kuma dangin mahaifinta 'yan usulin Dajin Falgore su suka fi kowayawa, ko da yake 'yan Yoben sun bi sun kankane komai 'yan Dajin Falgoren ba su da wani bakin fada a ji bare fa dangin Anty Na'ima da matsayinsu baiw uce na 'yan karo ba, ko kuma 'yan kalan dangi kamar yadda Hajiyan take fada. Ba ta wani sa wa zuciyarta wani darua ba saboda sanin abin da ta shirya misalin karfe takwas na dare Aunty 10 Na'ima ta yi kundumbala ta isa sashen Hajiya Kaltume, kallon biyu ahun da hajiyan take mata be sa ta karaya ba, haka nan 'yan uwan Hajiyan mutunta ta duk da dai babu wanda ya isa zuwa sashenta saboda akidar Hajiyan, sai dai fa in irin haka ta hado su su gaisa. Sun gaisa cikin mutunci ta ce Hajiya ina son ganin diyata ne? wa ke nan? Mardiyya ko mabruka? Ta san ta fahirece ta amma kuma ta cillo mata wannan tambayar Aunty Na'iman da take ma'abociyar kunya? cikin sanyin jiki ta ce a'a ina nufini Heedaya. Tamke fuska ta yi in ce ko lafiy a? Hajiya a tunanina mun zama daya abin da ya yi Heeday shi ya yi su mardiyya don haka abin da duk zan iya vi wa mardiyay ko Mabruka zan iya yi wa Heedaya.nasiha ce irin wacce iyaye ke wa 'ya'yayensu yayin da aurensu ya taso. Ta tabe baki au to ina ce wani kinibibin ne. Kwala mata kira ta yi, ta dube ta ki je Na'ima na son ganin ki, ita din ma wani duba ta yi mata na nuna ba ki isa ba. Haj. iMariya yayar Haj. Kaltum ce ta daka mata tsawa ba da ke ake magana ba ne? Ranta a bace ta dube ta bayan da suka isa dakinta, in ce ko ba wani abun kika kara kullowa a tsakanina da Dady ba? (Haka Hajiyan takemusu wannan hudubar, don cusa kiyayyar abokiyaı zaman nata da 'ya'yayenta). Zauna mana. Aunty Na'iman ta fada, ko kusa ko alama babu alaınun bacin rai a tare da ita, abin da ta Kudurci yi za ta yi shi ne domin Allah, tana zaune da su ne da zuciya daya haka na za ta iya yi musu komai albarkacin mahaifinsu, vana iya bakin kokarinsa wajen kyautata mata, abin da ke guda a tsakaninsu ta sani bayin kansa ba ne, sai 11 dai har kulum ta kan kasance mai shedawa Sarki Allah ba tare da zargin kowa a zuciyarta ba. Ta fara yi mata nasiha a bisa wajabcin bin iyaye, Allah Subhanahu wata'ala ya umarci 'ya'ya su yi wa iyayansu biyayya, biyayyar Ubangiji yana daga cikin biyayyar iyaye, sabawa Ubangiji yana daga sabawa iyaye. Albazzari ne ya rawaito. Haka nan Manzo (S.A.W) ya fada mana cewa, “Wanda ya riski iyayensa guda biyu ko daya daga cikinsui kuam bai yi biyayya a gare sup ba har yamutu, zai shiga wuta." Sai Annabi ya ceс, "Ки се Аmin." Sai muka ce Ameen. Hassan bin Malik ne ya rawaito hadisin. Manzo (S.A.W) ya umarei iyaye da su kasance masu aurar da `ya'yansu da za6a musu mazaje nagari ga macen da take budurwa (wacce ba ta taba aure ba). Wannan hakki a kansu ya rataya, kamar yadda Bukhari ya raiwato. Yana daga cikin hakkin iyaye a kan 'ya'yansu su sanar da su littattafai kuma su kyautata sunayensu, kuma su aurar da su bayan sun girma. Bayan hadisin Manzo (S.A.W) da suka yi maagana a bisa wajabcin biyayya ga iyaye akwai kuma wuraren da Allah (S.W.T) ya yi bayani a cikin littafi mai tsarki (Alkur'ani) a wurare da dama, misali aya ta 15 a cikin Suratul Ahkaf. Don haka ina yi miki nasiha ki bi umarnin iyayanki, bijircewa hakan tamkar bijircewa umarnin Allah da Manzonsa ne Maganganunta sun ratsa ta, zuciyarta ta raunana, har ma ta takara daga bijircewa iyayenta da ta so yi. Ba ta 12 taba jin kaunar matar ya kama ta ba irin na yau, domin ta fitar da ita daga cikin halakar da take kokarin jefa kanta. Wai shin menene dalilin da ya sa suke nuna kiyayyarsu ga matar? Sai kuma ta tuna mahaifiyarsu ce ke kokarin cusa wannan akida a zukatansu a ko da yaushe. mata Cikin yanayin kuka ta shiga bayyana kudurinta, da sauri ta ce A'uzubillahi, kai amına kuwa da kin yi kuskuren da zai ta bibiyarki mutukar ba neman afuwar iyayenki kika nema ba. Ki yi hakuri Heedaya shi lamarin aure haka yake, ni din nan inda zan ba ki misali a kaina za ki yi mamaki, to amma da yake ga wanda Allah ya kadarto shi ne mijina cikin kankanin lokaci komai ya wargaje, to amma da na yi hakuri ba ga shi har Allah ya albarkace mu da samun 'ya'ya. Kuka ta saka, lallai kam Aunty Na'iman ta yi gaskiya, a ce abin da za ta sakantawa iyayenta da shi ke nan? Duk da kulawar da suka nuna mata cinta, shanta, fitsarinta, kashinta, kai da ma komai nata su ne. Ta yi hakuri ta karbi zabinsu to amma fa wanda a kai abin a domin shi zai fuskanci masifa da bala'i da tashin hankali kala-kala, don ba za ta taba kaunatarshi ba, ya riga ya gama da rayuwarta, ya yi mata babbar illar da har ta mutu ba za ta taba mance shi ba. "Waheed! Waheed! na tsane ka sam ba na kaunar ka. Tahir kai nake so, ni kai kadai nake kaunata." Ta furta hakan a zuciyarta. Misalin Karfe goma shwa biyu na dare wato wa'adin da suka yanke za su gudu a di-dai lokacin shirushiru ba Heedaya bayan sun riga sun gama shirya koma, duk ya bi ya damu ya kagauta kada wani abu ya kawo musu cikas, wanda hakan ke nufin ya rasa Heedayansa. 13 "Never." Ya furta hakan da karfi, "Heedaya ba ta kowa ba ce face Tahir dinta. A dai-dai lokacin ne sakon ta ya shigo ta hanyar text message. Cikin sauri ya shiga duba sakon. Wani mahaukacin ihu ya saka game da cilli da wayar, "Heedayah! Heedayah!! Haka za ki min? me ya sa za ki yi min haka bayan kin san ke kadai nake so, ke kadai nake Kauna, never, never, Heedaya ni ne mijinki ba ki da wani miji face ni Tahir. Kirjinshi ne ya ba da wani dam lokacin da ya tuna da babban kalubalen da ya shafe komai, "Waheed! Waheed!! no... no...,. wallahi karya kake." Gaba daya ya hauka ce sai kuma ya ja motar cikin wani irin gudu na masifa ya fice ya bar unguwar. Zubewa ta yi a kasa kuka take me tsuma zuciya, tun farkon zuwansa har kawo tafiyarsa a kanidonta ne, wayyo Tahir kai nake so babu yadda zan yi ne sai kuma ta zube bayan da numfashi ya shiga gagarar fita. KARSHEN TIKA-TIKI-TIK Wayewar gari ne afkuwa ta afku, misalin karfe goma na safiyar ranar lahadi aka daura auren Engineer Abdulwahced Gen. Abdullahi tare da Barrister Heedaya А. Sa'ad. Daurin auren da ya hada gaggan mutanke daga ko ina a ciki da wajen kasar. Zuciyar angon in ta yi dubu ta baci, haka nan amaryar babu wani walwala ko nishadi а tare da su. 14 Da yammacin ranar ne General Abdullah ya umarce shi da ya je gidan Ambassador ya yi gaisuwa da kuma godiya a bisa karamcin da ya yi musu (wato kyautar 'ya sukutum). Babu yanda zai yi kamar yadda be isa ya ja da batun mahaifinshi ba ya fi kowa sanin shi ba kanwar lasa ba ne, ba kuma a kawo mishi wargi bare ya juri dauka. Ransh. a bace babu wani annuri a tare da shi suka isa gidan tare da Jamir, yau dai mutumin nasu ba ya nan domin yau aikin safe va yi. Tsa utsayi ne ko meye ba sai idanunshi ya gane mishi ita ba sun jero kafada da kafada da abokin adawarsa (Tahir) za u shiga mota, kai sai idanunshi ya shiga gane gane mishi abin da ba haka nan ba ne, ta gabansu suka zo suka shige a cikin mota ko kallo ma ba su ishe su ba duk da cewar sun san da su din a wajen, abin ya yi mutukar kona zuciyarshi, hannunshi ya fisgo, taho-taho mu bar gidan nan na fasa zuwa gan da uban nata, idan Dady ya tambayi dalili sai ka sheda masa. Haba wannan 'yar iskar yarinyar marar tarbiyya ake neman kakaba min, wallahi an cuce ni, an cuce ni, wallahi muddin ba a yi gaggawar janye auren nan ba za su yi kuka da idanunsu domin zan 6a66alla yarinyar mutane ne a banza a wofi. Yarinyar dan iskan mutumin nan ce fa? Wallahi an cuce ni, na fada na kuma fada hadin sam be hadu ba dama dai-su kwance wannan hadin domin shi ya fi alherі. Shi, kansa Samir din ya yi tsai yana nazarin magangarunshi, lallai kam akwai tarin rikici a cikin wannan aure, anya ma ko yarinyar tana da tarbiyya? Kamar yadda abokinshi yake zargi, yaro me tarbiyya dai ba zai yi haka ba, ko da yake ya fi ganin laifin iyayenta, don menene 15 za su bar ta zuwa wurin mutumin da ba muharraminta ba? har ma su fita? Alhalin da igiyar wani a kanta. Duk dai da rashin hadin kan amaren yadda ya kamata, an gudanar da gagarumin biki na kece raini daga kowane bangare, a ranar da za a kai ta ne ta gurfana a gaban mahaifinta tananeman afuwarsa a bisa turjiyar da ta gwada musu, kuka take me tsuma zuciya tare da bayyana nadamar rashin da'ar da ta yi musu. Jikin Ambassador ya yi sanyi yau dai ga ranar rabuwa da `ya mafi soyuwa a duk cikin yayansa. Cikin tausasa harshe ya shiga yi mata nasiha tare da bayyana farin cikinsa a bisa biyayyar da ta yi musu, a karshe ya sakamata albarka tare da fatan alheri, ita ma Hajiyan ta tofa albarkacin bakinta cikin karayar murya. An fara kai amarya gidan iyayen mijinta da ke cikin Nassarawa G.R.A. kan titin Tukur (Tukur Road). An yi musu karbar girma da karamci, daga nan a ka wuce da amarya gidanta da ke Badawa Layout Linck daura da titini Sardauna Creasent. To fa tashin hankalin a nan yake, kuka har da kururuwa da haka har aka watse aka bar ta da babbar aminiya Sameera, ita din ma ta yi iyawarta kukan ne dai ba ta fasa ba jikinta duk ya yi sanyi saboda tausayawa yar uwarta, ta sani ba abu ne me sauki ba raba ka da abin da kake kauna farat daya, a kuma kakaba maka abin da sam ba ka son sa ba ka ra'ayin sa ba ka ma kaunar sa baki daya. Duk da cewar angwayen sunshigo amma kuma hakan be sa ta tsagaita daga kukan da take ba, su kamar biyar ne duk da dai babu angon a cikinsu, sharif, mahbub, yassar, yazid da kuma shugaban tawagar babban aboki Samir, to fa suka fara tsokanarta ke ko an daina wannan 16 yayi kar ki ba da mu mana. Cewar yassar. Kai ko tsiyata da kai ba ka da saurin fahimta baka san gulmar mata ba ne? ai duk wanna kukan na farin ciki ne. Yazid yaba shi amsa. Wai haka? Wai haka amaryarmu? Shi kuma mahbub ya fada yana zolayarta. Bari mu gani hakan ne? in dai hakan ne za ta daina yi mana kukan nan koma sami damar siyan bakin amarya. Ai ko ta kara rushewa da kuka. Yana daga gefe sai faman dariya yake domin shi ya fi kowa ma zolayarta kai ku tsaya, ku tsaya ni na ma gano ko kukan menene bari ku ji ba kukan komai ba ne face na rashing anin angonta. Ah! Lallai kam dukkansu suka dauka cikin sowa da. tafi tare da fadin, lallai kam samir ba karamin tsinkaye ka yi ba da har ka gano mana lagonta. Ya ce ku tsaya akwai sauran rina a kaba, domin angon namu mai tsada ne, ke kawar amarya saiki miko kayan sayen bakin ango muddun da gasken kuna son ganin angon naku. Dama dai yasha zamansa, domin bamu da muradinsa cewar Sameera. Ah karya kike, wayo ne kawai dan kada ku ba mu kudin siyan bakinango, mu ko mun kiya domin angon namu mai tsada ne. cewar yazid da alama shi ya fikowa barkwancin idan ka cire samir din suka dada rikita ta sai faman kuka take lallai kam inda yake mugun mutum haka ma abokanansa suke. Ya rissina a gabanta ya dan janye gyalenta yana dariya yana fadin bari in fanshi ango in sai bakin amarya tun da kawar amaryar da ma amaryar duk marowata ne. ta kara rushewa da sabon kuka. Dariya ya saka gami da fadin, yazid tuna min wakar nan da makadan sudan din nan ke wa amare, yauwa, yauwa na ma tuna: “Amarya ce, amarya ce, amarya. A sama ta lalle." Suka amshe, "Amarya!". Ya 17 ci gaba in ta ki ta zauna, suka kara anshewa amarya, a kira mata

Chapter 1 of 8