Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
2 / 8
ango. Suka kara amsawa arnarya..." ko kafin ya kara cewa wani abun ta kawo mishi bugu da kafa tana fadin, "ya ishie ka Samir wannan ma ai wulakanci ne aikin kawai haka kawai ku dinga sa yarinyar mutane kuka. Dariya ya saka a`ah, kawar amarya daga kuma ina wake amaryarımu sai kuma bugu." Kyale ta Samir abin 'yar taron dangi ce, cewar yassar. Mahbub. Ya ce to ai sarkin yawa ya fi sarkin karfi ko ya kuka ce. To fa ta ga dai ba ta da yadda za ta yi musu sai ta ja bakinta ta yi shiru. Lallai kam kawarta ba karami n ikin jidali ta shigo ba, yadda yake haka nan abokanan nasa suke. Misalin Karfe goma sha biyu da rabi ta ci kuka har ta gaji, kowa ma ya watse ya bar ta, zuciyarta ta gama dugunzuma da kiyayyar mutumin da aka yi kasassabar hada su, lallai kam duk wanda ya yi wannan kasassa6ar gaba kadan zai gano kuskurensa. Ta gama ta yadda za a yi wannan zama da mutumin da take tsananin kiyayyarsa, har abada ba ta fatan ta so shi sakamakon mikin da ya dasa mata da ba zai taba gushewa daga zuciyarta ba. Sai kuma kuka ya kwace mata lokacin da ta tunano masoyinta shi ke nan an raba su, never, never wallahi Tahir kai nake so kai kuma nake ra'ayin zama da kai nan da lokaci kanknai zan dawo gare ka. Wannan aure kam babu inda zai je balle ya kai, domin babu komai a cikinsa face tarin rikici da fitintinu kala-kala, don haka ta gana shirya wace za ta fisshe ta. Har zuwa lokacin ba ta ji motsin mutum ba ba ta ma damu ta ji din ba, duk da tsoron da ya cika zuciyarta 18 sakamakon tangamemen gidan da take ita kwal a cikinsa da haka har bacci ya kwashe ta, ba ita ta farka ba sai safiya misalin karfe bakwai da rabi. Ta yi wanka ta kintsa zama ta yi zugum ta rasa abin da yake mata dadi misalin karfe tara dai-dai aka kwankwasa kofar ta. Kamar kar ta bude sai dai ta mike don ta ga vanene. Dogo ne baki me manyan kofofin hanci sanye yake da fararen kaya nau'in na masu hidima a hotel. Ya russura yana gaishe ta cikin gurbataccen turanci. sannan ya jiye katon tray da ke hannunsa ya shiga gabatar da kanse, "Sunana Peter, ni ne me hidima da abincin gidan nan. Muna maraba da zuwanki matar Oganımu, da fatan za mu kasancc cikin farin ciki a tare da ke." Duk dai cikin gurbataccen turancin ya fada. Wani kallo ta sakar masa sai dai be kula ba ya sa kai ya fice cikin girmamawa. Ko kallo abincinta be ishe ta ba, domin ba zaman cin abinci ta zo yi ba, jira take ya zo a yi wacce za ayi, ko ta yi gaggawar bar mishi gidan. Misalin karfe goma dai-dai abinci na alfarma ya iso daga gidan surukanta, shi din ma ba ta ci ba, domin duk kanwar ja ce, zaman kadaicin ya ishe ta yunwa ta addabe ta sai dai ba ta iya cin abincin gidan mutumin, gwanda ma yunwa ta kasheta kowa ma sai ya huta tun da kowa ma ba yá son ta an ma manta da ita kwata-kwata, wayewar gari har kawo yanzu babu wanda ya tuntube ta ko ba a fada ba daman ta san an daina son ta. Gefin azahar kannan mijinta Lubuna da Lubabatu suka iso gidan, a cikin katafaren falon nata suka same ta ta yi zugum. Gwanin ban tausayi, kallo daya ta yi musu ta 19 gane su dan tsananin kama da suka yi da yayansu, ta dan saki fuska barkanku da zuwa? Ya kuka baro Hajiyan? Lafiya lau Antinmu, in ce ko kin tashi lafiya? Muna can muna ta kokarinmu isowa da wuri don mun san antin namu a yau gwauruwa take, ba ta dai fahimce su ba, lubuna ta ci gaba da cewa, Mum tana gaishe ki ta ce a gaishemata da 'yarta idan kuma da abin da kike bukata ga waya nan sai a sanar mata. Iko sai Allah su kuma haka tsarin nasu yake? Ta ayyana hakan a zuciyarta, gaskiya anti mun so a ce yaya ya tafi da ke ashe wai kuan da wani case ne a nan ofis dinkuhaba Antinmu ba sai a dau hutu ba. Ni kam ban ga dalilin da zai sa kwana daya cal da aurena angona ya gudu ya bar ni saboda kawai uzurin ayyukan ofis ba. Cabdijam aikin me? Irin wannan time yana da mutukar mahimmanci a rayuwar ma'aurata, har abada ba za su taba mancewa da wannan lokaci ba. Duk dai in ji lubabatu. Take ta soma fahimtar inda zancen ya dosa, ai mommy ma ta so tafiyar nan da ke ta yi ta fadan ya hakura da tafiyar har zuwa lokacin da za ku kashe case din da ke ofis naku, to dan dai uzurin yayan babba ne shi ne ma har Dady ya kyale shi ya tafi. Ajiyar zuciya ta yi bayan da ta gama fahimtar komai, kai! Ina ma ya wuce har birnin Sin ya yi zaman sa muddun rai, da hakan ya fiye mata komai lallai kam ba karamin hasashe ya yi ba na nisantar junansu, kila da tun a daren jiyan an yi dan karamin yaki a gidan, domin ba za ta taba yadda ta zauna da mugun mutumin ba don ba ta kaunar sa ba ta ko kaunar ganinsa. Zuciyarta ta yi fari tas duk wani damuwar da take ciki ma sai ya gushe, fatanta ya zamanto cewa ya wuce ke 20 nan ita da shi haihata-haihata (lallai "KI" ya yi “KI”). Nan da nan ta saki hankalinta suka shiga hira da kannen mijinta, abincin ma da ta ki ci ta janyo ta ci ta yi kat abinta wanda take ki din ba ya nan shi ke nan bakin cikinta ya gushe. Shi dai daren angon tun a ranar da za a kawo amaryar ya yi bankwana da gidan dungurungum ya tare a Hotel tare da abar kaunarsa Zeenatu cikin dan kankanin lokaci ta kawar mishi da 6acin ran da yake ciki har ma yake jin wannan aure shi da babu duk daya ne, nan da lokaсі kankani komai zai zama tarihi inda zai maye gurbinta da abar kaunarsa, Zeenatu me sanya shi farin ciki me gusar mishi da 6acin rai. Wayewar gari ya yi sallama da iyayensa da abis zatonsu ya yi salama da iyalinsa ma'ana a gidansa ya kwana tare da iyalinsa ba su san ba hakaba ne iyalin nasama ba su saka shi a ido ba ballantana su san da tafiyar. Ko da yake tafiyar ma kafin a yi ta ya fuskanci rashin goyon baya daga gurin iyayansa, don dai sun san abu ne mai muhimmanci daya riga ya fado a cikin lokacin, jinkirin zuwan nasa ka iya sa su yi asarar abin da za a samu baki daya, sai dai babu wanda ya san cewa da tsohuwar budurwar tashi ya tafi ba sai fa babban aboki Samir, ko shi din ma bai so hakaba, don dai babu yanda zai yi da shi ne. A kullum ta Allah a kan kawo mata abinci na alfarma daga gidan General duk da cewa a nan dinma kukun gidan na iya bakin kokarinsa a duk safiya mommy Fatima ta kan kira ta ta ji lafiyar surukarta, haka nan kannan mijin nata suna mutukar daraja ta gami da debe mata kewa sai suka zamo ma tamkar kawayenta, sun yi 21 sabo ainun a cikin'yan kwanakin da suka yi, hakan ce ma ta sa ta kwantar da hankalinta ta yi kyau ta yi fresh. Kimanin makwanni biyu ke nan da zuwanta gidan wanda ya yi dai-dai da kwanaki goma sha uku da tafiyar angonnata, misalin karfe hudu na yammacin ranar lahadi suna zaune ita da su lubabatu a babban falon da zai sada ka da sassan gidan falo ne mai kama da aljannar duniya dan Kayatuwa sanye take da cotton lace mai mutukar kyau, ita daman shigar ta ke nan ta sa leshi, leshin ma mai mutukar tsada dinkin da akai wa leshin shi ya yi mutukar fito da ita, babbar riga ce mai gajeren hannu (Bubu) da siket wanda aka yi mishi dinkin zamani, kanta ba dankwali domin ba al'adarta ba ce, illa gyara da gashin ya sha. Ta yi kyau ainun. Sallama suka jiyo yayin da dukkaninsu suka waiga, ya kalle ta ta kalle shi sai kuma ya yi saurin kawar da kai gami da tamke fuska, murna suka sa oyoyo Yaya barka da zuwa. Barkanku dai in ce ko kuna lafiya? Yana tafiya ya ci gaba da cewa, kawai kuma sai ku tare a nan ku bar mummy ita kadai, saboda farin cikin wata? Ba su dai fahimci inda ya dosa ba domin suna hargowar fairn cikin ganinshi ita kam da a kai abin domin ta ta sani ta ma fahiinta, zuciyarta ta kawo wuya be sani ba ta ma fishi tsanar shi kai ita ko kaunar ganinshi ba ta son yi, don haka ne ta fauke tunanin dawowarshi har ma ta kwantar da hankalinta. Anti ai si а tashi a tari yayan naınu da alama dai antin namu akwai kunya. Cewar Lubuna. Ta mursuye kamar ba ta ji su ba. antinmu ki tashi mana yayanımu yana bukatar kulawarki. Ta dan harare ta sai dai ba ta sani ba da gasken hararar ta take, har ma da jin zafinta. dariya ta saka ni kam ina 22 mamakin antin nan namu ko mu da muke youngers ba za mu yi haka ba. Cabdi jam, yaushe ma zan yi haka rawar kai ma kawai ta ishi angon ke kila har ma sai na gundure shi, cewar lubuna. Ta rasa yadda za ta yimusu kawai sai ta mike suka hau sowa yauwa antin tamu haka muke so. Daki ta shige abinta ta ma fare gado ta vi kwanciyarta to sai dai fa ba bacci take ba, lalubo hanya mafi, auki da za ta rabu da kallagaggen mutumin ta ke yi. La'asar sakaliya ya kintsa ya fito sanye da bakin trouser hade da farar T.Shirt wace a ka yi wa ado da fenti me cuw an azurfa (silver colour), ya yi kyau ainum kamshi ne kawai ke tashi a jikinshi da gani ka san yana cikin kwanciyar hankali, akwai alamun hutu a gare shi, babu alamar walwala a tare da shi ya ce idan kun gama kintsawa ina jiran ku. (Da yake momin ce ta ce ya turo su gida). Daga haka be kara cewa komai ba ya sa kai ya fice. Sunkuyar da kai ta yi wani irin kululun bakin ciki ya turnike zucıyarta har suka gama kintsawa suka zo yi mata sallama ba ta hayyacinta ta dan girgiza ta lafiya anti? Babu komai lubuna, haba! Anti ji bi, fa inda kika yi. Cewar lubabatu, hannunta ta riko ina kewar tafiyarku ne, za ku tati kubar ni ni kadai. Dariya suka saka, ka ji anti da wata magana, ai in muka ci gaba da zama sai rashin hankalin namu ya yi yawa, ba ki ga yadda yaya yake wani cika yana batsewa ba? wai shi an hana shi sake wa da amaryarsa. Ta tarbe su da farin ciki 'yan matan momy an dawO lafiya? Kun tafi ko neman momin naku ba kwa yi, in ce ko 'yar tawa tana lafiya? Allah ya sa dai ba ku buwaye ta ba. don na san hali. Dariya suka saka haba momy antin namu za mu buwaya? Allah Mum antin namu akwai kirki ba ki 23 ga yadda ta dinga yi mana ba, kamar ma kar mu taho don wallahi ba ki ga yadda ta damu da za mu taho ba. Allah sarki ashe da ban sa an dauko ku ba tun da tawowar taku ya Gata ran 'yata. Eh Allah momy ko mu kona? Cewar lubabatu da yake ta fi wauta. Dariya ta saka lubabatu na ga ran da za ki daina wautar nan. Yana jin su duk be ce komai ba ya hada rai gaba daya haushin kananan nasa yake ji, masu karamar Kwakwalwa daga ganin yarinya har za su fara yabonta, bayan ko ba su san ba karamar tsagera ba ce. Ta katse shi daga tunanin da yake. To kai ka ji sai fa ka gode Allah ka kuma rike matarka hannu bibbiyu, ba karamin alheri bane katari da mace ta gari yana daga cikin alheran da manzon tsira ya lissafa mana, sai fa kai hankali ka kula ka rike amanar da Allah ya danka maka. Jin ta kawai yake, bayan ba ta sani ba shi ne mafi rashin sa'ar abokiyar zama, babu wani alfanu a cikin aurenshi da yarinyar da ko kadan ba ta da tarbiyya. Ta rasa me yake mata dadi duniyar ta gama kuntata a gare ta. karan farko ta yi kokarin neman masoyinta a layi (Tahir) duk da cewa wayoyinsa da dama sun shigo ta dai Ki dagawa ne, text message kuwa har ba ta iya kidayawa. Take bakin cikinta ya gushe, ilahirin bacin ranta ya kau farin ciki gami da nishadi ya mamaye zuciyarta, lokacin da ta jiyo muryar masoyinta take ta manta da komai ta shiga babin masoyа. Da dare ta yi wanka ta kimtsa ta yi kwanciyarta bayan ta gama karance-karancen da ta saba da yake ma'abociyar karance-karance ce, musamman ma Hausa 24 Novel. Har zuwa lokacin da bacci ya kwashe ta ba ta san sanda ya dawo ba ba ta ma damu da san da ya dawo din ba. Zaman dai na su ya ci gaba da tafiya a haka babu girma bare arziki, tun da babu ko me iya tankawa dayansa, a haka har hutun da ta diba ya kare, ta rasa hanyar da za ta bi ta fara zuwa ofis, domin tana kyashin 6ata yawun bakinta ta nemi izininsa, sai kawai ta yanke shawarar yi mishi letter ta je ta ajiyc a kujerar da ta fuskanci yakan yawaita zama a kanta. Ilai kuwa da dare misalin karfe tara .da rabi ya dawo, tun da shi zaman gidan ma be dame shi ba, ya yi wanka ya kimtsa yayi duk abin da ya dace ya fito sanye da farin trouser da farar singileti idanunshi ya kai kan takarda a lokcin da zai zauna kan kujerar hannu ya sa ya dauka sannan ya zauna ya kuma kunna TV cikin tashar NTA yana kallon labarun Kasa. Daga can kuma hankalinshi ya kai kan takardar, karamin note ne da bai wuce layi biyu ba, abin da kawai takardar ta kunsha shi ne, "Hutuna ya kare ina son fara zuwa aiki idan har zan sami damar hakan." W Tana kallon shi ta window be ce komaisbanya ajiye takardar ya ci gaba da kallon sa. Da sanyin safiya Mr. Obi ya shiga knocking din kofarta, rissuņawa ya yi ya gaishe ta, bayan da ya bayyana matsayinsa ną matsayin Driver da zai dinga kai ta wurin aiki Ya miką mata sakon da Ogan ya ce a kawo mata. v Wraper biyu ce sababbi ful wato dubu isihirin hade da wata 'yar guntuwar takarda ga abin da takardar ta kunsa: "Ga Direba nan ki fito ku tafi amma fa ba zai lamunci jira ba don ba bawa ba nе." 25 NIJ. I ps e Kalaman nashi sun mata mutukar Kuna har ma take ji kamar ta fasa zuwa to sai dai da yake ta san kanta ta cuta babu abin da ya rage shi sai kawai ta tītobayan da ta kimtsa, sai dai kafin ta fita din sai da ta bi ta ajiye mishi kudinsa a kan dai inda ta ajiye mishi takardar, tana jin cewa ta fi karfin ta karbi kudinshi ko da ko wace irin fatara take. Yana kallon su ta gilashin motarsa suka fice kwafa ya yi yarinya gwanda ma ki iya bakinki. Amarsu ta ango, lallai kam wannan amaryar ta ci sunanta, wai kin ga inda kika yi kuwa? Kamar wace ta tafi honeymoon a birnin Paris. Sera abokiyar aikinta take tsokanar ta. Har ma ba a bar Haj. Fatima, zubaida da kuma idris a bayaba duk dai zolayar tata suke, dukkaninsu abokanan aikinta ne, cikin shagwa6a-shagwa6a ta shiga fadin momy Fatima ke fa mamana ce ki bar biye musu, to na yi shiru diyata amma fa kyawun da kika yi ne ya wuce misali. Meye sirrin ne? fada min 'yata kona taimakawa su zubaida gwagware. Cikin dan gudu-gudu ta shige ofishinta momina ba ki dai daina ba, yau har dake a zolayata? Hankalinta ya dada kwanciya tun bayan da ta koma bakin aiki, yinin gidan ba yin shi take ba. Ya fice ta fice san da za ta dawo daga ofis shi kuna be dawo ba kafin ya dawo din ına tuni ta shige dakinta sai dai ko ta ji motsinsa idan ya dawo, da yake tsarin gidan kusan guda ne, kayataccen plat house ne na ganina faďa da aka yi mishi ginin kece raini akwai faffadar haraba a gidan shi ainihin gidan a cikin tsąkiyar farfajiyar gidan yake akwai 6angren ma'aikatan gidan daga can barin haka nan akwai boys quarters a can kuryar gidan. 26 Sashen mutanen gidan tun shigar ka za a ka fara shiga wani dan ziririn hanya ne (corridor) da aka lulube kasansa da ledar nasara (tiles) daga nan kuma za ka tarar da matsakaicin falo me dauke da kayan alfarma aka tanade shi don baki wadanda bana jiki ba musamman ma abokanan me gidan daga shi kuma matsakaicin lambu ne me dauke da bushiyoyin 'ya'yan itace kala-kala, kama daga tufa, inibi, fase dabur, 6aure, lemo da sauran su. A cikin lambun ne za ka terar da kofar da za ta sada ka da ainihin cikin gidan nan in ma kankarerren falo za ka tarar ya fi na farko komai da komai, dukiya kam an zubar da ita a wajen, to a cikin falonre kofofi kamar guda hudu suke, daya shi ne ainhin barin megidan me kunshe da katon room akwai bedroom, sitting room, toilet da sauran su. Daya kofar kuma nan ne 6angaren matar gidan kamar inda bangaren megidan yake haka nata 6arin yake ita ma. Daya kofar kuma da ke manne da tata bangaren da aka tanade shi don yara ne, dayar kuma da ke can kurya a nan kitchen da store yake. Ya yi sa'a ya same shi a gida ko ko suna da agender ne? daga shi sai `yar karamar farar riga me gajeren hannu hade da bakin gajeren wando me fauke da sunan ADIDAS, sautin kida ne kawai ke tashi a falon ko da yake daman ya san shi ma abocin sauraorin wake-waken turai ne, dakin gaba daya ya sanyaya da na'urar sanyaya daki (AC) har ma ba ka iya tunawa da yanayin zafin da ake ciki, zafin ma irin na Kano. Ya dube shi bayan da ya sami waje ya zauna kana hutawar ka mutumina, lallai amarci da dadi yake, harara ya sakr masa don ba ya son ya na yi masa irin wannan 27 magangar, wai ina amaryar ne ma ta zo in cashe mata? Yinin yau ta hana mana ganin ka har sai da na biyo sahu in ga lafiya. Ya dada 6ata rai ka bar 6ata rai ba zuwa na yi na sure maka ita ba, zuwa na yi kawai mu gaisa. Tana ina ne dan Allah?" oho! Da sauri ya ba shi amsa. Okey. Na fahimta tana cikin nan. Ya nuno dakinsa da baki, ya ci gaba shi ya sa ake min rowar ganinta, don ana shan amarci, cikin kufula ya ce, Karya kake ba ta kai nan ba wallahi, ta kai har ma ta huce za ku ma ka gasgata hakan nan gaba. Shi ma ya ba shi amsa, dauke kai ya yi ya na fadin shi dai mutum kulum cikin abu guda yake saboda ba shi daaikin yi. Ya tashi yana dariya na ji dai ko mameye na fada na kara fada ta kai har ma ta wuce nan din. Ta taso don ganin wanda yake mata bugu da rana tsaka, ko shi Peter ta gargade shi ya bar zuwar mata sashe tun da kawo abincin ya zame mishi dole sai ya yi parking din su a nan babban falon in ta yi ra'ayi ta fito ta di ba, domin lefin maigidan ya shafi kowa ma na gidan. Ta dada tamke fuska bayan da ta fahimci ko wanene, in ban da ta bude da ba ta bude din ba, amma da yake ta bude din sai ta ba shi wuri ya shige fuskarta duk babu annuri amam shi ko a jikinsa domin ya iya tafiyar da ita. Da zamansa ya fara amarsu tango, amaryar da ba ta lefi, ta bi ta kankame ko ina a gidannan har ma da mamallakin gidan, ta hana shi sakat ta hana zuciyarshi sukuni. Ta dada tamke fuska ina gajiya ta ce mishi duk dan ta kauce wa maganganun da yake. Gajiya kam mu ne da ita amaryarmu, domin mu kam har yanzu muna nan a ma'auninmu ba mu da mai lallashin mu balle ya tarairaye mu, an bar mu da yawan 28 gidan abinci (restaurant) da gidan gashin fulawa (bakery) ba mudamai girka mana. Shiru dai ta yi ba ta ce masa komai ba, ya ci gaba, wai shin dan Allah me ake wa abokin nan namu ne na ga ya canja ya yi kyau yayi haske ya yi, fresh? Ko ba ki ma fada ba an san yana samun kulawar da ta dace daga gurin iyalinshi, kai muma Allah ya bamu ya tashi. Da sauri ta datse shi, dakata Samir cin fuskar ya ishe ni haka fa ta ja tsaki mtssss! Allah ya tsare ni ya kuma yi min katangan Karfe a tsakanina da. mugun mutumin da kake alakanta ni da shi Ta dube shi da kyau, kama shaida mishi ba zan so shi baba zan taba sonshiba muddun rauwata.: Mikewa ya yi yana kada kai, lallai kam yau hirar ta fi kwarfina bari in bar miki dakin tun kafin ki kai ga kwankwatse min kwakwalwa. Harara ta bi shi da shi bayan da ta tabbataneta yi maganinsa, in ba haka ba yanzu ya ishe ta han ma ya cika mata ciki ta ji kamar ta tashi ta shake shi. YADDA ZAMAN NASU YA KAYA Suna kasaa zama guri guda: ballantana su fahimci junansu ko sa afuwanta wa junasu tun da zama ne Allah ya riga ya hada. Watanni takwas babu abin da ya sauya, babu me kula wani balle ya shiga hurumin sa, irin zaman nan ake na ban ma san da kai ba. Yau babu aiki don haka tana gida yayin da ta yi wanka ta feshe ta hade cikin suit na mata launin ganye, kyawunta ya dada bayyana tana jin fitarshi a mota ta ji 29 wani sanyi a zuciyarta, ta kan kasance cikin matsi da takura har ma ta ji tamkar a kan garwashin wuta take a duk lokacin da yake gidan, dan ma Allah ya so ta zaman gidan be dame shi ba ko da a ranakun Karshen mako ne (weekend). Ta baje a babban falo kan 2 seater, ko dayake ba ta iya zaman falon kai ba ta iya ko kusantar sa muddun yana gidan, tana jin wani irin nishadi, kiran farko ta same shi a layi take duk wani kunci da take ciki ya gushe ko da yake hakan ce take kasance wa duk lokacin da take waya da Tahir. Tsawon lokaci suna hiirarsu ta soyayay tare da bayyana kaunar da suke wa junansu, har credit dinta ya kare ya kara kiran tata nan ma sabuwar hirar aka dasa. "Tahir kai nake so kai na zaba kai nc kuma zabina don haka nake so nake kuma kara gayamaka ka kwantar da hankalin Heedaya ba ta kowa ba ce face Tahir dinta. Tuni na riga na gama mallaka maka zuciyata har da gangar jikin baki dayanta.... Finciko ta aka yi bayan da aka yi cilli da wayar ya doka ta da kasa ya kuma doka ta da kasa sannan ya bi ya take ta. Danko dantsanta ya yi ainun idanunshi ya kada ya yi jawur, cikin masifa da bala'i ya nuno ta da yatsansa, ni din nan da kika gani na fi karfin kowa ne dan iska balle fa ke fa kucaka ce ko a cikin yaran iskan, na kuma fi karfin ai min wannan iskancin a gida. Ya yi facali da ita cikin fusata, babu alamun tsoro ko fargaba a tare da itata shiga fadin komai ka yi ka yi a banza don ba na son ka ba na kaunarka, wanda nake so din nan dai shi nake so babu kuma me hana ni kaunar sa, ko ka sake ni ko kar ka sake ni duk dai daya ne Tahir dai shi ne zabina shi ne kuma abokın rayuwarta..... 30 Tasssssss! Ya wanke mata fuska. Hajijiya ta yi har ma ta ji gidan baki daya na juya mata ya sa kai ya fice cikin fusata. A duniyar nan ya rasa me yake masa dadi wannan rashin mutunci haka. "Tuni na riga na gama mallaka maka zuciyata har da gangar jikin baki daya...." wadannan kalamai su suka fi komai tsaya masa a zuciya, to wai me yake jira ne ma da ba zai sake tan ba? 'yar uban wane ne ita da ba zaı sake tan ba? take kuma wani sashe na zuciyarshi ya shiga tu nasar da shi irin mummunan 6acin ran da zai fuskanta daga mahaifinshi, kai an cuce ni ya sa hannu a ka ya dafe. Zucivarshi ta saukaka ne lokacin da ya tunano cewa wannan aure fa babu inda zai je ba ya son ta ba ta son shi don haka zaınan ba zai taba yiwuwa ba. Fatan shi dai koma meye ya bullo daga gare ta inda ko kadan mahaifinshi ba zai ga lefinsni ba gashin kuma kam zai yi wa yarinyar za kuma ta gane shi ba sa'an yin ta ba ne. Ta kimtsa ta shirya tana jiran isowar direba shirushiru har misalin Karfe tara, har ma ta hakura ta kwanta abinta, wayewar gari ma hakan ce ta kasance, kai wasawasa sai da aka yi kwanka hudu cur babu direba babu batunshi, me hakan ke nufi ne? ta tambayi kanta. Da yammaci ta hango Obi yana goge motar ogan, Peter ta sa ya kira mata shi ta shiga bin bahasin rashin zuwan nasa cike da girmamawa ya shiiga bayyana mata ogan ne ya ce ta samu hutu wajen aiki don haka ya jira har zuwa lokacin da za ta koma. Ta gane shirinsa wato ya hana ta zuwa aiki ke nan ai ko ya yi kadan ta dube

Chapter 2 of 8