ba
ta ganshi ba kai ba ta ma lura da shi ba, tun lokacin da
ta hango Waheed gaba daya hankalinta, tunaninta,
ganinta kai da ma zuciyarta ta tattara gare shi, tana son
sa tana mishi wani irin sọ mai ban mamaki.
Kasa motsi ya yi ko da da kafafunsa ne kai sai ya ji
duk ya bi ya muzanta a idanun al'ummar wajen. Dariya ake
masa, wasun su kuma na cizon yasa, kai yarinyar nan ta
88
bonsa Tahir, abin da galibi suke fada ke nan. Shi ko gogan
naku ya harde yana yi mishi wani kallon rainí me kunshe
da sakon na riga na yi maka fintinkau, sai dai hakuri kawai.
Tana sakale da shi ya zo shigewa ta gabansa ya ja ya tsaya
yana yi mishi wani dubana raini, kai ko ba ka da sa'a
abokina, me zai sa ka nemi sa'a ko ko jininka ne baki? ban
sani ba dai, na dai fahimci sam-sam ba ka da farin jinin
jama'a, musamman ma gurin 'yan mata, hakika ina jajanta
maka ba karmain tawaya ba ne mace na gudun mutum.
Yatsu ya shiga daga mishi, one. two, three ya
Kidaya hannunsa duk na yi maka fintin kau. Murmushi ya
saki na tura haushi, ya shige abinshi har yanzun dai tana
manne da shi. Zahhirin gaskiya sai yanzu ne ta lura da shi?
Tahir ne, sai kuma ta fan tabe baki to menene ai shi ne ya
jawa kansa? daman ai tana ciki da shi na nuna zarin shi ga
'yan mata, kare da doki duk shi ne ta sha yi mishi korafi
amma sai ya share ra'ayinsa ke nan. Amsar da yawanci
yakan ba ta don haka ne ma hankalinta ya fi karkata ga
Waheed duk da wulakancin da yake nuna mata da fari, ta
lura da kyau ko da yake dan bariki ba kowa ce karya yake
kulawa ba, shi gentle man ne, be cika ma sauraron
Kadangarun barikin ba saßanin shi Tahir da yake tamkar
bunsuru, in dai akan mace ne.
Dariyar aka kara sawa, kai wanda ma be yi dariyar
ba da fari ya dara din, yau rana ta kwacewa Tahir, wane
irin tsautsayi ne ya kai shi gå afkawa tarkon Abdulwaheed?
Abin da galibin abokanansa suke cewa ke nan. Shi kansa
Samir din da ke gefe dariyar yake, daman dai babu komai a
tsakaninsu sai tsantsar adawa, lefin Wahced ya shafe shi kai
ba ma ya wani tantance tsakaninsu dan haka shi ma Samir
89
din ya fita harkarsa, ko da yake koma ba haka ba muddun
za ka taba dan uwanshi (dan kam ya fi danganta shi da
wannan matsayi) tamkar ka tabo shi ne.
Kada kai yake, kai fan uwanshi ya yi mishi kata i a
yau ya yi musu maganin tsageran yaron me shegen
fangimar tsiya, to amma dai a wani 6arin yana jiye mush
tsoro, Tahir fa ba kyau, kai tamkar ma ba shi da imanı wani
sa in.
Ranshi ya yi masifar baci na tozarcin da aka yi wa
Tabokinshi, cikin matsankancin bacin rai suka baro
mashayar. Ya dube shi da bacin rai, na rantse da wanda
raina ke hannunsa sai na tagayyara mutumin na sai na kuma
wulakanta rayuwarsu, domin zan nuna masa shi Karamin
dajn iska ne, in ga kuına uban da zai kwace shi, matsiyaci
dan matsiyata. zan gwada mishi na dare shi da komai.
komai yake takama da shi na fi shi, be ko isa hada kafada
da ni ba ballantana ya ja da ni.
Fada yake tamkar yana wajen, shi kansa Faisal din
a wannan karan ba ya ganin laifinsa, a yawancin lokuta
musamınan lokacin rikicin Heedaya, ya kan ga laifinshi har
ma ya dinğa tausar shi a ganinsa akasi ne kawai aka samu
amma ba da gayya ya yi masa haka ba, idan aka bi abin da
idon basira to amma a yau duk ta kau ya daina ganın laifin
shi kai da gangan ma yake ganin laifin abokin nashi,
gaskiyarshi tsabar rashin mutunci ne da raini kawai
Waheed din yake gwada musu, in ban dahaka har ya za a yi
a ce 'yan mata har uku ya yi masa kwacen su? In ban da
daman akwai wata a kasa, tabbas wannan karon yana
goyon bayan abokinsa.
90
Alwashin tozarta shi ya ci gaba da yi kai babu
sauran alamun mutunci fa a tare da Tahir hannu ya sa ya
dafa kafadunsa abokina ina bayanka sai dai fa duk
hukuncin da za a-zartar a yi tsinkaye a cikinsa, kada mu zo
mu yi aikin da-na-sani.
Kishingide take kan kujera hannunta rike da littafi da
alama karatu take, ya shigo bayan da ya yi salama, Assalamu
alaikum. Amarsu ta ango in shigo ko ko in juya? Na ga aląma
yau amarcin ne ya motsa, angon yana gida. Yau da gobe ta ki
wasa, har sun saba ta ma saba da halinsa, ta fahimce shi kawarai
yana da halin kirki ga barkwanci ya kuma fi abokinshi da'a da
mutunci, duk da cewa ta fahimci jirgi daya ne ya kwaso su.
Ta mike da sauri me zan kawo maka ne tun kafin a ishe
ni? kullum a ka zo sai an cinye mana abinci. Ta kada kai matarka
dai kam ta shiga uku da wannan ciki naka mai kama da
mazurari, komai aka miko mishi sai ya lashe dariya ya saka, ke
zauna ni yau na wutasshe ki, na biya gidan amaryata na ci
dadddan girki ba jagwalgalo ba irin naki.
Ta yi kwafa haka ka ce to in an yi zuciya a satin nan ta
tare mana mu gani, ko a bar kwanoninmu su huta. Baki iya tabe
ke da wasa nake, ni fa har yanzu a duk cikin'yan matan garin nan
ban ga wacce ta yi min ba.
Sai dai ku lalata rayuwarsu? Ta ba shi amsa. Baki ya
kara budewa, a'a Barrister kada ai mana sharri, ina mu ina
wannan aiki? Sai ku gayawa karamin yaro ina jinshi zai fi yadda
da hakan, tun da yana da raunin tunani. Dariya yake to ya isa dai
a bar maganar kada a Saro mana wani sabon aikin, domin na lura
yau sharri ake shirin yi mana. Sharri ko gaskiya abin da kuke
aikatawa ne.
Ya sauya maganar, wai ina kawar nan taki? Ni fa da
gaske nake na ga kina yi min wani wala-wala, Allah ya tsare ta
da faďawa hannunku. Ya shiga magiya Allah da gaske nake, ita
91
ma ta zama serious, kai Allah ba ta nan ta tafi yi yo wani course
na shekara daya a kasar faranša, kada kai ya yi, cabdijan ki ce an
shiga uku, domin a hakanma ya aka cika domin ba wai course
din da ya kai ta kadai za ta yi yo ba har ma da na rashin kunya
da fitsara, har yanzu fa ina tunawa da murguda bakin nan da aka
yi min ana yi min wani iriin kallo kamar kashi don haka nake
tuna ranar da duk na aure ta zan saisaita yarinyar na ga ta bakin
tsiwa. Ya ishe ka haka ai damanna gaya maka Allah ya tsare ta
da fadawa hannun irin ku.
To shi ke nan na ji abar dan kara mana magana ni ma ina
nan ina shirin kawo zankadediyar yarinya ba irin kawarki
ba mai gajeren hanci, mita ta fara yi mishi ai wallahi
karyarka haushin rashin samu ne, samun mace kamar
Sameera sai an tona. To na ji dai a bar maganar kada ma a
kai gaba tun tonowar kin san muddun aka yi tonowar
kawarki za ta yi kwantai ne.
Ya dubi littafin hannunta, yauwa ni kin tuna min
ma, karasa min labarin 'BILKISU MAI GADON
ZINARE'. Dago mishi littafin ta yi ba ka ga yanzu an fara
kashi na ukun ba ga shi kuma ka zo ka hayyace ni
ballantana in Karasa karanta shi, in zo in karashe maka
labarin duk dai da hakan a dan gutsura min na kagauta da
sauraron labarin nan.
Ka dai takura min bayan ba wani abin kirki na
karanto ba face kayan takaici, ta riga ta fada tarkon yayanta
yana cin zarafinta son ransa bayan ya raba ta da masoyanta
na gaskiya. Ta dube shi kai kusan dukkanku maza haka
kuke babu komai a cikinku face keta da mugunta, burunku
ku tagayyara rayuwar 'ya mace ku sanya ta cikin kunci da
wahala ku kuma yasar da ita.
92
Maganarta ta raunana indanunta ya ciko kamar za ta
yi kuka sai kawai ta sunkuyar da kai hawaye na zubo mata,
shi ma sunkwi da kan ya yi jikinsa ya yi la'asar, tabbas ana
zaluntar yarinyar, abokinshi ya ki ya yi adalci a kan
yarinyar, ya gwammacewa kadangarun bariki, gaskiya ne
abin da ciwo.
Ya fara magana cikin kyakkyawan lafazi kai ba ka
ce shi ba ne. Hakuri za ki ci gaba da yi Heedaya, komai
kika gani mai wucewa ne babu abin dayake dawwama face
sarki Allah Mai girma da buwaya, na san abokina ba ya
kyauta miki, to amma fa gaskiyar magana ke ma da naki
lafiin, kai kusan ke ce da daukan kaso mafi tsoka, kin kasa
ba shi hadin kai, kin kasa ba shi fuska kin kasa yi mishi
biyaya, ya karyar da kansa duk da shi ne ke sama da ke, ya
nemi sulhu amma duk kika turje kika nuna adawarki da
hakan. Saboda Allah me kike so ya yi miki? Duk fa halinda
ya shiga kina fa da kamasho a cikinsa me ya sa za ki nemi
jefa kanki cikin halak Heedaya? Kar fa ki manta ita
aljananr mace a karkashin kafafun mijinta take, manzon
Allah (S.A.W) ya bayyana mana da da wani abun halitta da
za a bautawa da ya umarci mace ta bauta wa mijinta saboda
mutukar kimar dayake da shi a wajenta. Kar fa ki manta ga
iyaye da sauran dangi be ambace su ba sai fa miji.
Ya sassauta murya, so, a gaskiya laifi naki ne
Heedaya, ya zama dole ki yi masa biyaya, ki manta da
komai ki share ya wuce kawai ku yi kokarin shimfida
kyakyawar rayuwa, wacce 'ya'ya da jikokinku za su yi
alfahari da ita.
Kanta na sunkuye hawaye na zubo mata, jama'a da
damà na ganin laifina ne bayan ko mutumin nan ya sha
93
fada min ba ya sona, ba ya kauna ta, bama zai taba sona ba,
so, ya za a yi zamanmu da wannan bawan Allah ya fore?
Kada ka mance kiyayya fa wata aba cemai illa. Kuka ta
fashemishi don Allah ku bar ganin laifina, mutumin nan fa
na gasa min aya a hannu, sam-sam ba shi da halin kirki,
mutumin arziki ne zai dauko mace yakwana da ita cikin
tsakiyar iyalinsa? me ya fi wannan kuna? A da abin kam ba
ya damuna amma yanzu kam ya dame ni, ni da za ka
taimaka min da ka neme shi ya sahale min, zamanmu ba zai
taba armashi ba, ba zan taba ganin kima da darajarsa ba,
saboda wani abu da ni kadai na sani, wannan abu shi ya
hana har ma na kasa yimasa biyayya har ma yakan kıra ni
da yarinya mara tarbiyya bayan ko shi ne ya aikata rashin
tarbiyya mafi muni, ba na son sa, ba na son sa zamanmu ba
zai taba đorewa ba domin ba zan taba daina ganin shi da
wannan abu ba.
A tunaninshi bai wuce abubuwan da suka gudana a
baya ba, don haka ya shiga lalhashinta yana ganin abin is
easy be- sani ba babba ne, kai dungumeme ne ma.
Yawancin jama'a na ganin laifinta musamman a lokacin
aurensu, bayan ko ita ta san abin da ya shuka mata.
Harara ya sakar masa, ca nake ai sai gobe za ka
fito? Bai saurare shi ba don ciki yake da shi, aikin banza
ana yi ma magana kana ji, ko ko ka je ta gama zuge ka ne?
dan na san kai karamar Kwakwalwa ce da kai. Kila da ba
dan harkar karuwa ba ce da ba ka fito ba yanzu? Be dai
tanka mishi ba yanufi cikin motar.
Sai da ya harare shi sannan ya ja akatar in tar, aikin
banza mutum kulum in za a je wajen arziki sai daa ya buge
da motar aro, wayo ya hana ya sa kudi ya shrga motar
94
kirki, in ma mutum ba ci ba ai zai mutu wasu su ci ne. Wai
yaushe ma za ka yi aure ne?" Banza kawai, ya kasa
daurewa sai da ya kwashe da dariya. Sai san damatsoratan
maza suka kauce suka bawa maza na hakika da ba sa
tsoron matansu.
Fuska ya daure me kake nufi ne? cikin gatsali ya ce,
a'ah, inanufin matarka barrister Heedaya. Ko ko daurin su
na lauyoyi kake tsoro ne, ban dai tantance ba, uban waye ya
ce maka ina tsoron ta bare wani aikinta? Lauyan banza da
wofi. A'a, ban da fa cin mutunci abin da idona ya gane min
ne, kai ka kasa shiga sashen matarka, don kana tsoron
hukukcnin da za ta zartar maka. Ya harzuka zan kwa ci
zarafinta, haka ta ce maka? Ya yi kwafa za kwa ta gane ni
ba sa'an wasanta ba ne, kamar gaske bayan a gidan kamar
zabo kake. Ya dada harzuka, komai dai meye na fi ka kai
kuwa fa da ruwan ido ya hana ka auren? Ai ka sanni namiji
ne mai aji har ma baa iya kyautar da ni sai dai na zaба па
darje, kuma ni dole ne mace ta bi sharudfana, ni zan juya
ta ba wai ita ta juya ni ba, sai kuma abin da na ce mata shi
za ta yi. Ita za ta yi min wanka, ta tarairaye ni ta ma ba ni
abinei a baki, ba wai in tsaya ina sanda ba har ma ina
shayin shiga wajen ta. Idan kuma mutum ya yi zuciya daga
yau ya fara in har yana son shiga rukunin maza na hakika,
ba wafanda suka yi yowa mata rakiya ba, rakiyar ma da be
fice ta rikon jaka ba.
Burki ya ja ji take kиииuuии! Ya fa ishe ka, ka
fice ka bar min mote Malarn get out. Ya fada da sauri, ban
da raini ma shi za a cewa dan rakiya, rakiyar ma ta mace?
Macen ma har irin fitsararriyar yarinyar nan? Ya zaina dole
ya sake sabon salo a kanta, don ta san shi fa ba na wasa ba
95
ne. Abin da yake nufin sa shin ba zai yi ba in dai a kan
fitsararriyar yarinyar ce, ba rukon jaka ba a ce mishi ma
abin da ya fi haka in dai sai ya aiwatar da haka ne za a
janye mishi wannan suna.
Yau ya riski kansa cikin wani irin yanayi na farin
ciki, yarinya me aji da ya mato akanta (Zeenatu) ta ce ba ta
ra'ayinshi, sai fa shi tsadaddan yaro, dayar da yake
kwakwa yake mata mayataccen so (hidaya) ya riga ya
mallake ta har ma tana rabe a inuwarsa, ita ko dayar
dungurungum ta nuna ba ta ra'ayinsa shi take so, domin
tuni ta riga ta gama yayinsa. Tahir na yi maka kata'i zan
kuma ci gaba da kasancewa da taurarin nan naka uku duk
dai domin in kuntata maka.
Zahirin gaskiya dukkansu ukun babu wata da zai ce
yana yi mata wani mayataccen so, shi daman bai iya
wannan ba, ba kowane lokaci ne matan ma suka damke shi
ba, ita daman dayar babu batunwani so a tsakaninsu, face
tarin rikici kala-kala tun daga farkon haduwarsu, ita ko
Zeenatun ba zai iya cewa yana yi mata wani mayataceen
soba ya yarda dai yana son ta ne dan faranta mishin da take,
ita ko dayar da ake tsaka da rikici a kanta ba wani son ku
zo mu gani yake mata ba, kai yana ma son ta ne yana kuma
kasancewa da ita ne duk dan ya kuntata masa, duk da cewa
yarinyar ta mallaki duk wani abu da mace za tayi alfahari
da shi daga dai kyawun halitta.
Ya daga wayar a lokacin da yake kokarin gano
wanda ya kira shi saboda rashin fahimtar nambar (no
number). Cikin kakkaurar murya aka fara magana, abokina
ka daukowa kanka da kanka ruwan dafa kanka, kada fa kа
yi tsammanin kai mai cin galaba ta ne, a'a, bari kaji ba haka
96
bane, tun farko na hakur ana bar maka Zeenatu ba, wai don
fin karfina ba a'a sai don na san tuni na gama yayinta, don
haka na bar maka sidi ka san a yadda nake din nan na fi
karfin a bar min sudi sai dai ko sabo dallele.
Karo na biyu na hakura na kuma janye dan na san
bani da wata barazana a kanka wanda har hakanya ba ka
damar ka aure ta to sai dai fa kada ka mance Heedaya ni
kadai take so a fadin duniyar nan, ni kadai ne mutumin da
ta yi amananr zai ni'imta mata rayuwarta don haka ne ta
mai da kai soko sha ka tafi da bai san ciwon kansa ba,
domin zuciya da gangar jiki tuni ta danka su a hannun
Tahir, abin da nake so ka fahimta anan Tahir shi ke dealing
da zuciya da gangar jikin yarinyar da kake ikirarin matarka
ce, don haka ne ma ta kasa ba ka hadin kai ta mai da kai
wani sha-ka-tafi, ka duba gaban durowar teburin office din
ka za ka ga sakon da zai tabbatar maka da hakan, in kuma
har kana musanta haka to ka je ka tuhume ta cikin da ke
jikinta mallakin wanene? Na tabbata za ta ba ka
gamshasshiyar amsa don ba ta kaunarka ba ta kuma
shakkun ka. Tahir ne abin kaunarta don haka za ta bayyana
maka tsiron da ke cikin mahaifarta mallakin Tahir dinta ne.
Kashedi na gaba da kuma karshe zan maka, ka fita
harkar yarinyar nan (Farida) dan ba ajinka ba ce ko kadan
baka dace da ita ba, kai ka tsaya dai a second hand finka,
shi ya fi maka alheri, ka sani ka kuma sani ina son Farida
ina son ta, yes dole ne kuma in mallake ta ko da tsiya ko da
arziki ne. kashedi na karshe a gare ka ka fita harkar
yarinyar nan idan ka ki bin umarnina ka samawa kanka
lafiya idan ko ka sa kafa ka shure ka kwasowa. kankа
masifa har da bala'i. Da fadar haka ya katse layin. Tsayawa
97
ya yi wani sororo kamar wani gaula duk cikin kalaman
nashi babu wanda ya fi tayar mishi da hankali ya ma
tafashe zuciyarshi baki daya irin maganganunshi na tsakiya
wato a kan matarsa.
Biye mishin kuwa ya yi kamar mahaukaci ya shiga
bincika dirowar da ke jikin teburinshi, gaba daya ya
hargitsa takardun dake ciki hankalinsa ya kai kan wata
Katuwar, envelope, hannu ya sa ya dauko ta, cikin
matsanancin sauri ya bude hannunsa har kakkarwa yake.
Hotunan kam babu ko kyawun gani, wani a kwance wani a
zaune, wani kuma a kishingide, a wani hoton kuma ga cikin
nan har ya tura.
Jifa ya yi da su ya bi ta kai ya taka, ya tattaka, kai
sai ya dauko ashana ma ya kyatta musu zan kone ku kamar
yadda zan kone ma mallakan cikin hotunan, na tsane ku, na
tsane ku, yau za ku tabbatar da tsanar da nake muku don
zan raba ku da duniyar, maciya amana, masu keta haddin
Ubangiji.
Zaune take ta hada kai da gwiwa, Tahir din ya riga
ya gaına fanfata, ji take zuciyarta na yi mata wani irin
tafarfasa, wane irin cin zarafi ne wannan? wane irin ki ne
mutumin nan ne yake mata? Har zai je yana ta gayyara ta a
gari yana 6ata sunanta. Ciki! Ciki!! Uban waye ya yi mata
cikin? Har yana ikirarin ba nasa ba ne? tun da take in ban
da shi din da ya keta haddinta ba ta taba kadaitaka da wani
namijin ba, duk lalacewar tata ba ta kai nan ba, haka nan
duk rashin tarbiyyar da yake ikirarin ba ta da shi ba ta ko
kai nan ba.
bayan cin zarafin da ya yi mata ya keta alfarmat a
shi ne har zai je yana yi mata wannan dungumemen
98
sharrin? bayan ko shi ne lalataccen a kan idanunta ına
lalacewar yake. Hotunan da shi Tahir din ya ba ta ba su
wani ba ta mamaki ba, tun da akan idon tama yana aikata
hakan. To sai dai fa hotunan sun mata ciwo, galibanshi da
wata kyakkyawar mace ce kai don kyau kamar aljana take,
ba wai hotunan ne ma suka fi bakanta mata ba face yanayin
shigar dake jikinsu da kuma sigar da aka yi hoton karshen
lalacewa kam sun yi ta a nan.
Bayan wannan din ma akwai wasu hotunan da wata
yarinyar dai duk da dai ba su kai wadancan muni ba to
amma şu ma ba su da wani kyawun gani, fitsara cе
tsagwaron ta aka yi ta ita din ma yarinyar kyakkyawa cc sai
dai ba ta kai fayar ba. Zeenatu haka ya ce mata sunanta ita
kuma dayar Farida ko menene, to ta dai fi jin zafijn
Faridan, tana jin wani irin kishinta a zuciyarta, mutumin
nan ya cuce ta ya cuce ta. Ya magana da rayuwarta.
Tana cikin wannan dumamar ne, wacce ta kira
kanta da Faridan ta neme ta a layi, babu batun sallama, ta
ce, cin zarafi, kai hakika ta ci zarafinta ta kuma goronta
mata rashin kaunar da maigidan yake mata har ma ta kira ta
da kaska mai bakin naci in ta raße kai da kacire ta sai an
sha bakar wahala
Cacar baki suka tsaya yi har ta gaji ta kifa layin,
zuciya kam ta gama kawo mata wuya, takaicinta daya
wanda a ka ci zarafin nata a domin sa bayan ko ba su san
cewa ta ma iowa Riyayyarsa a duniya ba. Zamanta kam
ya zo karshe ya ma kare a gidan nan dole ne ma ya sahale
mata ta je ta auri abin kaunarta.
Ya shigo cikin fusata kai tsaye sashienta ya wuce, bugu ya kawomata da kafa sai da ta hantsila sannan ta kifa
99
bai saurara mata ba ya kara kawomata bugun da dai kafar
idanunsa ya kada ya yi jawur sai tsuna yake, uban waye ya
yi miki ciki? Uban waye na ce? 'yar iska matsiya ciya mara
tarbiyya, uban waye na ce ya yi miki ciki ya kara nanata
tambayar. Duk da tana cikin dimuwa hakan be sa ta kasa
jin wani karfi a zuciyarta ba, cikin daga murya ta ce uban
waye kake ganin ya isa ya yi min ciki a duk fadın garin nan
da ya wuce abin Kaunata Tahir.
Mari ya sakar mata ya kuma kawo mata marin kai ya
haukace ma dukanta yake ta ko ina har da kansa ya gaji ya
dakata, ja ya yi ya tsaya ya nuno ta da yatsa cikin masifa da
bala'i, zan je in fara kawar da masoyin naki daga doron kasa da
duk ma wani mai hannu a cikin lamarin nan, daga bisani sai na
juyo na aiko mishi da ke can lahira dan babu shegiyar da ta isa
haife min cikin shege a cikin gidana, never..., never... na tsane ki,
na tsane ki... ya fice cikin fusata.
Durkushewa ta yi tana kuka babu wanda ya ja mata
wannan face iyayanta, ita ta riga ta san mutumin maketaci ne
mara halin kirki, yana kinta yana mutukar kiyayyarta don haka
zai iya yi mata kowane irin sharri, duk domin ya batą mata suna.
Tabbas Tahir ya yi gaskiya, mutumin nan fa sam ba ya kaunar ta,
in ban da rashin kauna har yaushe zai aiwatarmata da wannan
aiki ya kuma zo ya bi ta da wani dungumemen sharrin bayan
6ata mata sunan daya yi? Tun daya san sharri ya aiwatar mata
meye kuma zai zo yana tuhuamr ta? Shi da ya riga ya kagi
abinda kansa ai ko ko za a sata a turmi a kirba zainansu ya kare
da mutunin nan. Tahir dinta take so dole kuma a bata, kai sai
yanzu ne ma take jin haushin kanta, me ya sa tun farko ta ki
amincewa bukatar Tahir din, na su gudu, ta ba wa kanta amsa
duk dai Aunty Na'ima ce ta ja mata saboda ta riga ta hango irin
musibar da za ta afka muddun ta auri maketacin mutumin.
100
Burinta ke nan su tagayyara kamar yadda momin ta sha
gaya musu, wani lokacin tana ganin bekenta ashc ko da
gaskiyarta.
To sai dai ta dau alwashin wutar rikicin ba fa wai
kanta kadai za ta tsaya ba, a'a har da ita wacce ta shiryo
mata wannan gadazzaren sai ta gwammace wa zaman cikin
garwashi da dai zaman gidan mahaifinsu.
Kai tsaye mahadarsu ya nufa, kai duk inda yake
tunanin zai ga Tahir din ya je amma kuma be gan shi ba,
zuciyar nan tashi kamar wuta dan Kuna.
Farida ce ta kira shi a waya ya zo da gaggawa tara
son ganinsa, be yi niyyar zuwa ba amma dai sai ya tafi don
su shirya wace za ta fisshe su, zai aure ta kamar yadda
wannan shi ne ra'ayinta ba don komai ba sai don ya
Kuntatawa abokin hamayyarsa, tun da ya hakikancewa
zuciyarsa yana kaunarta kamar yadda yabayyana mishi. Kai
da da hali ma har ita Zeenatun zai hada ya aura duk dai a
lokaci guda, to amma kuma sai ya gano rashin alfanun
hakan, tun da ya riga ya san ra'ayinsa a kanta (wato ya
gama yayinta). Ita ko dayar zai sahale mata ne bayan ya
tagayyara ta kamar yadda tayi mishi wannan tozarci, daga
nan sai ya ga ta karshen so ta je ta gani idan shi Tahir din
zai yadda ya aure ta, kai wannan yarinya kam ta riga ta
gama da rayuwarshi, zai kuma yi mata tozarci irin wanda ta
yi masa. Ciki! Matarsa da cikin wani, wanin ma makiyinsa.
Hotel din da take da zama ya nufa wanda shi ya
kama mata daki a ciki. Ta nuna matukar mamakin ganinsa,
ban yi tsammanin zuwanka ba yanzu don haka ne ma nake
haramar kwanciya. Duk da ranshi a Gace yake amma ta
sami nasarar ssasutar da zuciyarshi daga kaso hamsin
101
cikindari, saboda tsabagen farin cikin da ya tuna nan da
sa'o'i kalilan ta zama mallakinsa wanda hakan ke nufin ya
gama karshen kuntatawa abokin hamayyarshi. Shi kam ba
wai tsabar kyanta ne yake rudarsa ba face wannan dalili.
Duban shi ta yi, Da gasken fa nake ban sa rai da kai
ba a dai wannan lokacin. Harara ya sakar mata cikin wani
salo, amma kika ishe ni da waya. Zaro idanu ta yi? Ni? ke
mana. Wayc yake da zazzakar