murmushi uhm ko da yake an fa ce wanzami bai son
jarfa.
Hada inasu inasu suka shiga yi, ta dube su da
gasken tafiya za ku yi tun yanzu? Anti gwanda mu hada
inamu inamu karonmu dayaya ba zai yi kyau ba баббalla
mu fa ya ce zai yi? Kin kwa san halin yaya? wane hali ne
yake da shi? Ta tambaye su a duniya tana so ta ji wani abu
da yake bakanta ransa domin ta sami damar aiwatar mishi,
lubabatu ce ta fara ba ta amsa, kin ga yaya ba shi da yawan
fada amma fa in ya yi fushi babu kyau don idonshi yakan
45
rufc har ma ki yi zaton yana hauka ne. Ba ya son kuma
raini, kin san shi mutum ne me son girma ga zuciyar masifa
shi kansa Dady yana yimishi fadan hakan balle kuma
momy.
Lubuan ce ta katse ta da sewa, ni kin san abin da ya
fi damuna ma? Kar fa ya je ya hada mu da Dady ina jin
koke da kika zo family namu kwanan nan kin fahimci halin
dadin sam ba ya yi wa mutun ta dadi.
Ta yi shru tana nazari, gaskiya ne ko waye ranshi
zai baci, ita da kanta yanzu ta soma gano rashin kayutawar
rayuwar da suka yi da Tahir, duk da dai iyakar
mu'amularsu be wuce rike hannun juna -ba ko kuma dai irin
su zauna guri guda, sau daya ne za ta taba tunawa ya hado
ta da jikinsa shi ma din ba da son ran nata ba don dai ta
cunkusawa abokin fadan nata ne (Waheed).
Ta dan numfasa, to ai kuma dai ba ku kyauta ba irin
abin dakuka yi haba da Allah? Na dai kare ku ne don in yi
escape dinku a gurin yayanku amma dai ba ku kyauta ba
Allah. Haba anti kamar ba ki san soyayyar zamani ba?
Allah kin ji mun rantse ba fa wani abu da ya gudana irin dai
wanda yaya yake nufi. Ko ma meye ba ku dai kyauta ba.
Mun gode da kika cece mu gurin yayanmu kuma
zamu yi kokarin kiyaye afkuwar hakan a gaba, to ainma
anti ini tambaye ki? Cewar lubabatu. Me ya sa ne nake
ganin kamar akwai matsala a tsakaninki da yayanmu? Ba
ma kamar ba ne, akwai matsalar. Lubuna ta karashe mata.
Murmushi ta yi na karfin hali babu komai ku ne dai kuke
ganin hakan. A'a anti kar ki rufe mu, suka dai matsa mata
ta dube su da kyau, me kuke so in ce muku? Ko ko za ku ce
min ba ku san halin yayanku ba n? To anti ko ma meye ai
46
matsalar taki ce abin da kika so shi zai yi, amma ji bi fa
antinmu sam fa ba kya ba shi kulawar da ta dace, irin meye
da meye din nan duk ke ba ki iya ba? kada fa kimanta idan
ke ba ki mishi ba ba ki kuma ba shi kulawar da ta dace ba
akwai dubban matan da irin wannan damar kawai suke
jira, Me kike ganin zai afku?
Me take ganin zai afku ko kuma me yake afkuwa?
A dan zaman da suka yi tana jin ta fi kowa sanin shi
kwararren maneminmata ne, to tun yaushe ma ta san
hakan? Ta bawa kanta amsa.
Suka sa ta a gaba fa sai fada suke mata, dariya suke
ba ta wai 'yan fici-ficin yaran nan su ne za su koyar da ita
yadda za ta zauna damiji, suka ishe ta, kai ku kyale ni fana
dai fahirnta ta ron dangi kuke son yi min ku dayayan naku
baki faya. Dazu ya ce zai 6ab6alla ni yanzu kuma kun zo
za ku cinye ni da baki. Dariya suka saka, haba Antinmu.
Ko zama be yi ba ya faramita, ni meye ne za ka bi
ka cika ni da waya, har ma kana barazanar kashe min
dodon kunnuwana da karar wayar.
Zancen dai be wuce zai tuina... Zeenatu.. wace се?
Wace ce? To ni dai ka bar cika ni da maganar 'ya'yan nan
iskan harkar arziki ce a gabana, haka kawai ina cikin kula
wace za ta fisshe mu kawa ni ishi mutane da waya? Tun
dakai da alama kudin sun sihe ka har ma sun maka yawa
sai kuma ya ce ka ma mai da hankalinka ba zai yiwu ni ina
can ina shan rana ba kai kokana can 'yan iskan bariki sun
dauke maka hankali har ma kana yi musu facaka da naira
kamar ya yi a bola saboda ba ka san zafin neman su ba.
Eh! Na ji ko menene gwanda ni ina alheri ina cin
kuma dukiyata son raina ba wai kadangarun barikin kadai
47
suke cin arzikina ba wani fa? ko cikinsa bai iya hiidimtawa
sai dai fa Kadangarun barikin nan kadai ke cin arzikinsa.
Kuma ka sani ba wannan maganar ce ta sani kiranka
ba, na kirawo ka ne domin ka shedawa waccan mara
kunyar yarinyar, nan fa ba bariki ba ne gidan aure ne, don
haka ta bar taramin Karatan banza da wofi.
Ban fahimce ka ba. Ya fada fuskarshi a yamutse,
Tiryan tiryan ya labarto masa komai ya kuma kara
da cewa, don haka ka sheda mata ka kuma gargade ta
zaman aure fa ta zo ba zaman bariki ba.
Au ka amince matar taka ce ke nan ko? Da matar
uban wace ce? Ya fada cikin kufula. Kamar haka na ji ka
cc abaya, amma tun dayanzu ka ımaince wa hakan shi ke
nan sai mu shiga kokarin samo mafita. Shawara ta ka
hakura ka sauke rawanin tsiyar nan da ke kanka ka nemi
sulhu gurin matarka kuma ka nemi soyayyarta idan har an
dace tana ra'ayinka sai ita ma ta so ka shi ke nan ka ga sai a
yi sabon aure harına a bude sabon amarci. Cikin daga
murya ya katse shi, never! Never!! Never!!! In so ta
ballantana har in nemi soyayarta, bana sonta ba zan taba
son ta ba. na tsani yarinyar nan ba na ra'ayinta don an ce
mata ta ce ba wai hakan na nufin na so ta ko ina son ta ba,
na tsane ta, na tsane ta ba zan so ta ba na ce. Ranshi ya yi
mummunan 6aci, ai ban san wannan rashin mutuncin za ka
shuka ba da ban zo ba, aikin banza kawai ka ajiye yarinya
kana gasa ta, to ka sani Allah sai ya saka mata. Kuma abin
daka yi wa wani shi za a yi wa naka, na san wata rana ba za
ka so hakan ba, to saika shirya wa hakan tunda dai
takidinka ne wulakanta ‘ya'yan jama'a.
48
Na ji dai kome za ka ce ka ce amma fa ka lura ka
gane kafin ka yi min nasihar ka fara yi wakanka tukun,
aikin banza kawai yaran jama'a nawa ka yaudara ka kuma
ci zarafinsu abaya ko don shi gwano baya jin warin jikinsa.
Ya mike ko dai me na yi bai dai kai naka ba, tunda
kai macen sunan kake yi wa wannan wulakancin ni kuwa fa
kadangarun bariki ne, meye ko aibun yi musu hakan? Ai
kowa ya sai rariya yasan za ta zubar da ruwa ne. Zan kuma
shiga in shaidawa 'yar mutane kar ta raga maka a duk
lokacin da ka nemi keta ta.
Ina jin dai lokacin da za a yi hakan ba ka nan,
saboda haka zan ma samu damar cudada 'yar mutane ne.
Ya tarar da ita ita kadai a falonta yi zugum da alama
tunani take, kâwai sai ya ji ta ba shi tausayi, yau ba karatun
ake yi ba ne? ta dago ta dube shi har yanzu dai babu wani
sakinf uska a tare da ita suka gaisa na zo ne a cikan
alkawarina. Na me? ta tambaye shi na "BILKISU."
murınushi ta yi, ayyah har yanzu na kasa kammala labarin,
why? Aikin ofis ya hana ni sakat, idan na dawo kuma saika
ga gajiya duk ta saukar min,to yanzu ba zan sami wani
karin bayani ba a dangane da halin da Bilkisu ke ciki? Za
ka dan sami karin haske amma kadan ne don iyaka ta
Karshen kashi na biyun.
To kafin a fara ba ni labarin BILKISU MAI
GADON ZINARE a kawo min abinci tukun, yau ma dai da
yunwar na iso,amma fa wannan karon kar a kawo min
kwamacalar Bilkisu. Ta harare shi kana zolayar BILKISU
wallahi zan gayawa safwan dinita ko dayake a karshen
littafin yama ba ni haushi. A'a Hecdaya, kar ki min haka, ki
hada ni da safwan, kin san fa abokinmu ne.
49
Da gaske? Ta-fada cikin sauri, da gaske mana, ya ba
ta amsa. Kada kai ta yi kai haba gaskrya mana ashe
abokanai kuke shi ya sa hali ya zo daya.
Dariya ya saka kai Heedaya sai fa a bar ki, ina na
san wani safwan a Kamaru a ka ce yake ko a ina ne to ina
ma aka taba yin haka daga labarin alınara (kagagge) sai a
ee an san mutum? Ajiyar zuciya ta yi gami da gano
wautarta, ta dube shi, ka san Allah tun dana karanta labarin
nan na ji kaunar bilkisun ta shige ni dama ita kanta kasar ta
Kamaru, tunanina a ko da yaushe ta yaya za a yi na je kasar
Kamaru cikin birnin Douwala ko na ga bilkisu, wallahi ji
nake kamar in na je zan gan ta. Labarin ya tsaru, kana
karanta shi kana hango hotunan abubuwan da ke wakana.
Allah duk ranar da na sami dama sai naje kasar kamaru, a
birnin Douwala cikin unguwar New-Bell, a yankin
Marobiya mahaifar bilkisu, jinake da gasken zan ga
bilkisun da ma mamanta Saudatu.
Kada kai ya yi yana dariya, an gaishe ki Heedaya,
abin ınaki baba ne to ni kuma na yi alkawarin duk ranar da
aka tashi zuwa Kamarun nan zan biya kudin tikiti har ma
da komai da komai na tsaraba.
Kai ta kada lallai kam inda kuka tsąnenin nan
yaushe za a yi haka. "Heedaya." Ya kira sunanta, a'a bari
dai in je in hado maka abincin tun da yau ka ce ba ka cin
kwamacalar bilkisu.
Kitchen ta nufa ta fara hada mishi "Dillaf Rice
wato a dafa shinkafa a tsane a sami yankakken koren
tattasai, jan tattasai, albasa, a zuba a tukurya bayan an zuba
butter a .ciki a soya sama-sama, a zuba talasasshen koda,
karas, tumatur na gwangwani, gi magi, curry, thy me a
50
juya a a dauko soya sauce da kuma shinkafar da a ka tsane
a zuba a yi ta juyawa, a rage wuta a bar ta ta turara a gefe
guda kuma ta hado mishi chips and salad wato hadin salad
me hade da soyayyan dankali, a bangaren abin sha kuma ta
hado mishi mango drink. Yana ci yana zuba santi, har ya
share abincin yanemi kari, tukunyar sukutum ta dire mishi
da yake irintasu da 'yan gayu ceme murukin roba da murfi
na tanaran launin kore (HappyHome) made in Germany.
in maida ni rumbu, wallahi kaman fahimta kai
rumbu ta'asss ne bama rumbu ba. Dariya yake sosai ta ce
Allah gaskiya na fada matarka sai ta shirya. Wallahi ko kin
yi gaskiya don in ba ta iya grki basaina lallasa ta har saista
iya din.aikin ku ke nan dai duka-duka ku daki mace košku
mare ta, shi ya sa har yanzu nake tunani anya ko ba da
gasken ne Safwanun bilkisu ba abokinku ba ne? don komai
naku daya ne.
A'a kar ki mana sharri ina muke karatun wannan
shirmen pallantana mu san wani safwan daga wasa kuma
sai a ara a yafa har ma ya zama makamin yakarmu. Ya
sauya maganar.
Wai ko dan Allah ina mara kunyar kawar nan taki
ne? ta bata rai wacce ke nan? Sameera ko samiha ko
menene. Ta galla mishi harara abin ya soma gangarowa ga
kawayera ne? ya ce a'a bahaka ba ne, yarinyar ce akwai
tsiwa, wai ko kinga san da ake rikicin nan wani gatsine da
aka dinga yi min da murgude-murguden baki kala-kala? To
ya ishe ka dai cin zarafin naku kuma kada ya ta6a yar
uwata. Ya yi murmushi, babu batun cin zarafi ni da za kiba
ni ita rna da na gode miki. Baki ta rike ni wa! Allah ya
51
tsare ta da shig ahannun irin ku, ni din ma da na riga na
fado addu'ar kubuta nake a kullu yaumin.
Shi ma bakin ya bude lallai kam an tsangwame mu
da yawa, me ya yi zafi haka har ake mana wannan bakar
addu'ar?
To duk ma daimu bar wannan maganar duk da
daina gano wayon kar a bani Samiran ne bayan ko Samira
ta Samiru ce a daura musu aure da Malam Sule dogo. Ya
fara rera wakar har da dan tafi. D riya ta saka bayan da ta
katse shi, ya isa da Allah za ka fara ko? Ya lura da kyau ta
saki jiki da shi, don haka sai ya ce, to shi ke nan ah yi shiru
din tun da wannan dinma ba a so. To ni sai a cika min
alkawarina a karashe min labarin BILKISU MAI GADON
ZINARE.
Ta saki fuska yauwa, to yanzu na ji zance, kanaji
ko..... ta fara ba shi labari tamkar tana karanto shi har zuwa
inda littafi na biyu ya tsaya. Ta ciji lebe ka ga fa irin cin
amanar taku, likitan ta ce fa? kai "Maza Ba Ku Da
Tabbas." Cewar zainab Lawan, kai hakika kam ta yi
gaskiya, wannan irin rashin tabbas haka? Hakika ya ci
amanar bilkisu. Kada kai ya yi.
Gaskiya kaım be kyauta wa bilkisu ba, to amma in
ke ce ya za ki yi? Ta dan yi nazari zuwa can ta ce sai kawai
in yi hakuri in ci gaba da tarairayarsa ina ba shi kulawa har
zuwa lokacin da zai karkato gare ni tun da dai ina son sa.
Ajiyar zuciya ya yi ya sami yadda yake so, ya kuma
fahimce ta muddun yana son ta sake da shi su yi hira toya
tabomaTahirar littafi, littafinma na hausa. Ya fuskance ta
babu alamun wasa a tare da shi, "Heedaya." Ya ambata
sunanta. Duban shi ta yi in miki wata tambaya mana. Ina
52
jin ka, ya ci gaba idan har za ki yi hasashen haka a dangane
matsalar bilkisu menene zai sa ba za ki jarraba wannan
hanyar ba a tsakaninki da maigidanki?
Hcedaya duk da kasancewar ki kankanuwar yarinya
Allah ya ba ki ilimime tarin yawa, kin fahimci matsalar
al'umma har ma kuna iya tsaya musu domin kare
hakkokinsu da kuma kwato musu 'yancinsu why? ba za ki
jarraba hakan akanki ba? abin nufi tsakaninki da
megidanki. Meye amfanin ilimi ne muddun ba za a yi aiki
da shi ba? ba shi da wani amfani. Ki bawa kanki amsa
karshe ma idan ba ki hankali ba ya kai ki ga halaka ranar
gobe kiyama.
Ki tsaya ki nutsu ki yi nazarin maganganuna kada ki
yi dubayya da abin da ya faru abaya ballantana har ki sako
shi a jerin abubuwan da ya hana ki kwantar da kai ki yi wa
mijinki biyayya.
Zama ne Allah ya riga ya hada shi ba fa wanda ya
isa ya datse shi sai fa ranar da Ubangiji ya so, idan kuma be
Kadarto rabuwar ba hakan muke fata, to ya za ayi ke nan?
Dole watan wata rana a hakurcewa juna, kila ma lokacin
Allah ya ba da albarkar zuri'a bayan ko a baya abin da yaka
mata a yi ke nan.
Shiru ta yi tana sauraronsa, mutane sun kasa
fahimtar ta ballantana su san matsalarta lefinta kawai a ke
gani bayan ko ta cancanci daukar matakin da ya fice hakan,
saboda babbar illar da inutumin ya yi mata da ba za ta taba
barin zuciyarta ta huta ba, ya riga ya gama yi wa zuciyarta
miki tun da ya zuba mata guba me wuyar sha'ani har abada
ba za ta taba mancewa da mutumin ba, ba za ta taba ganin
girman sa ba kamar yadda ta san ba zai taba ganin darajarta
53
ba tun da ya riga ya gama da ita, zamansu kam ba zai taba
yin armashi ba haihata-haiha......
Da ke nake Heedaya? Ya dawo da ita hayyacinta, ki
yarda ki amince wa zuciyarki ki so mijinki ki kuma
Kaunace shi.
Cikin tsananin Gacin rai ta ce, Never, sam-sam-sam
ba zan taba Kaunatar shi ba duniya da lahira, ba na son shi,
ba na son shi ba zan taba son shi ba, kama sheda mishi
yaba ni takarda ta na tafi gurin ne kaunata. Tahir nake so
shi kadia nake Kaunata don haka ba zai taba saınun farin
ciki daga gare ni ba.
Kallo kawai ya tsaya ya bi ta da shi cike da takaici.
ji yake kamar ya tashi ya kwada mata mari wannan
katobarar da ta yi. Kai wace irin kiyayya ce ke zukatan
mutanen nan? Kiyayyar ta yi yawa, in ka yi kamar za ka
shawo wancan sai ka ji har ma gwanda dayan.
Mikewa ya yi cikin bacin rai na tafi kuma ba za ki
kara ganina a gidanku ba, tun da kin kasa daukar shawarata
har ma kina wadannan maganganu marar sa kyau.
Tana fadin Samir, Samir amına ko ya juyo ya dube
ta, kuka kawai ta saka, babu wanda zai fahince ta ita kuma
ta yi alkawarin babu me taba nin wannan yankan kaunar da
ya yi mata ballantana a daina ganin zafinta.
Zaune take ita daya a ofis aiki ya kacame mata
sallama ta jiyo ta dago da niyyar ansawa, cikin
matsanancin mamaki ta buda baki tana kallon shi. Tahir. Tа
ambata haka.
Ya sami waje ya zauna, kina mamakin ganina ko?
kina tsamımanin duk inda kike bana tare dake ne? aiko ban
kasance da ke ba zuciyata na tare da ke Heedaya.
54
Heedaya na damu da ke na rasa yadda zanyi da kaunar ki dare da rana kaunarki ta hinaa ni sakat, ba na iya
baccin kirki, bana walwala bare nishadi tun bayan
rabuwarmu why Hecdaya kike neman saba alkawarin dake
tsakaninmu, zamanme kike yi ne har yanzu Heedaya? Ta
dube shi ya rame ya fada kai ya ma ba ta tausayi haka
kawai ana neman yi musu karan tsaye a rayuwa, ta ji wani
irin tausayinsa, "Ka yi hakuri Tahir ina bakin kokarina, ka
san shi komai lokaci ne idan lokacin ya yi babu mai iya
kara min ko da dakika guda ne, amma dai abin da nake so
ka bar zuwa saboda gudun zargin mutane ka san yanzu an
daina kiwon dabba sai dai fa mutum, duk abin da kake
mutane na halkance da kai.
Mikewa ya yi cikin 6acin rai to na gode Hcedaya,
na kuma fahimta kin daina kauna ta ko? Shi ke nan kawai.
Tahir! Tahir!! Da sauri ta shawo gaban shi, kada kai min
haka, idan ka yi min haka ka yi min rashin adalci da me zan
ji ne? kuka ta samasa, jikinsa ya yi sanyi ya sami waje ya
zauna,j to Heedaya ya kike so in yi ne? na ga ni ne kamar
kin daina kaunata.
Ba hakaba ne Tahir, kaunarka na nan daram а
zuciyata babu abin da zai sa ta raunana balle ma in daina
son ka, ka yadda komai lokaci ne, lokaci kuma nan nan
zuwa in zama mallakinka Tahir. Lumshe ido yayi lokacin
da yake kokarin tunano irin farin ciki da zai riski kansa a
wannan rana. Ina son ki Hecdaya, son da ban san adadin sa
ba, zan iya rasa rayuwata muddun na rasa ki.
Runtse ido kawai ta yi sarai ta san akwai rashin da
cewar zamansu ina ma lefin su tsaya a wayar, sai ta ji sam
ita da kanta tana jin cewa ba su kyaut aba.
55
Karfe biyu dai-dai an tashi daga ofis zo mu je in
sauke ki gida Heedaya. Ta dubeshi tana dogon tunani,
akwai rashin da cewar hakan, to amma ba ta son 6ata ranshi
sai kawai ta mike ya je ya sauke ta kawai ai ba lefi ba ne,
inma ba ta bi shin ba ya za ta yi, domin da kyar ta iya kawo
kanta zuwa ofis sakamakon imatsalar da notar take ba ta,
akwai matsala a cikin injin motar, haka nan sharp dinmotar
ya yi kasa. Ta kuma fada masa ko a safiyar yau amma ko
ya daga kai ya dube ta.
Yana tsaye a bakin motar yana kokarin budewa ita
kuma tana daga daya 6arin tana haramar shiga da zarar ya
bude suna daga tsayen suna tattaunawa a dangane da
rikicin auren kawarta Sameera ya shiga zolayarta ku dai
dukkaninku auren dole za ayi muku? Kai ma dai ka fada
bayan tuni an daina wannan yayin, kai gaskiya ba a yi
mana adalciba. Haka kawai ana shirin kashe mu da ranmu.
Ya Karashe nata, dariya ta saka shi ma dariyar ya saka.
Tahir ba ka da dama. To ina fa na gadamar tun dana rasa
Heedaya, dukkansu dariyar suka dada sawa.
Duk da kasancewar ayyuka sun kacame masa a ofis
haka ya kawar da komai ya nufi dauko ta ko ba ta fada
masa ba ya san motar ta akwai matsala mawuyacin abu ne
ma ta iya dawo da ita.
Rashin sani aka ce ya fi dare duhu, lokacin da
Waheed ya yi parking da motarsa dab da ta abokin
hamayyarsa, wani irin abu mai matukar tsini ya ji ya soki
kahon zuciyarsa, lokacin da ya yi tozali da su, suna hirar su
cikin nishadi har ma da kyakyata dariya.
Ta kadu kwarai da gaske lokacin da ta yi ido biyu
da shi to amma sai ta dake, sai menene don ya gan ta da
56
abin kaunar ta? Fakat ya sahale mata ta je ta auri abin kaunarta. Shi din ma ya lura da shi, kai ya ma riga ta ankara da shi amma sai ya dake ya basar ya ma shiga jan ta da hira duk dan ya cusguna masa.
Ya gama bude motar ya shiga ita ma ta shiga sai da
ya zo dai-dai saitin window sa ya dube shi da kallon raini
kana jin cewa ka mallake ta har ka aure ta ba ka san cewa
zuciya har ma da gangar jikin na wurin Tahir domin duka mallakinsa ne.
Daga haka be kara cewa komai ba ya ja motar cikin
matsanancin gudu, ko a jikinta kai Tahir din ma ya burge
ta, idan ya yi fushi ya kuna tabbata shi mai zuciyar ne ya sake ta.
Ko kafin su isa tuni har ya isa gidan, cikin
matsanancin Gacin rai ya zama dole ya dau mataki na
karshe a kanmara kunyar yarinyar nan. Tahir? Matarsa?
Hannu ya sa aka ya dafe, za a yi balbalin bala'i zai sake tan
don ya nuna mata ita ba wata tsiyar ba ce, to amma fa sai bayan ya gwada mata kaskancin da ya fi nata, cuta ce dại
an riga an yi mishi, iyayansa kuma suka ja masa, shi daman
tuni ya san yarinyar ba ta da tarbiyya kokankani.
Karar mota ya jiyo ko da ya leka sai abin ya ba shi
mamaki ita ce ya ajiye ta, ya tafi kamar ba ya so ba, abin
ma sai ya ba shi mamaki lallai ma ta tabbata yarinyar tantiriyar mara kunya ce, bayan ma zamewarta mara tarbiyya in ban da haka har ta iya dawowa gidan shi zai kwa gwada mata ko a cikin tsagerun ita kankanuwa ce. Tun kafin ta gama shigowa cikin ainihin baban
falonsu ya tare ta fuskar nan tashi babu sauran mutunci, ya
dube ta ina jin cewa gidan nan mallakina ne ba da uban
57
kowa na gina shi ba? ballantana har wani ya yi tunanin
akwai kason sa a ciki. Kau da kai ta yi ya ci gaba da ke
nake karamar 'yar iska me ya hana ki juyawa inda kika fito.
Ya je ya sa ma miki daki domin nan kin san ba bariki ba ne
balle ya zama dandalin 'ya'yan iska. Ta dueb shi ranta a
Gace kai bari ka ji ka kuma sani, abin da kake zargi hakan
ne? ba haka ba ne? duk dai-dai ne domin shi nake kauna shi
ne kuma zabina, saboda haka shi kadai ne wanda zan iya
mallakawa zuciya har gangar jiki baki faya..... ji kake
kauuuuuuuu! Ya wanke ta da mari. Ai ba sai kin yi hakan
ba za ki nuna min ke yarinya ce marar tarbiyya.
Cikin masifa ta ce, na ji na yadda to amma in ka yi
fushi ka sahale min, dominni dai na gaya maka na kuma
kara gaya maka bana son ka ba zan taba son ka ba, bana ma
fatan na so kan.
Ya nuno ta da yatsa, kin yi abanza domin kin da
nake miki ya shallake tunanin dan adam ki ji ki sani, ki
kuma sani kiyayarki a jinina take, shashashar yarinya mara
tarbiyya.
-Ta dada fusata, Eh daina ji ko me za ka ce na kuma
yi farin ciki da hakan, zan kasance cikin kaiconrayuwa
yayin dana fahinci burbushin so na a zuciyarka, to sai a ka
sami akasin haka, na kuma gode Allah, domin ba ni da
wani kaico a rayuwata, babu abin da ya fi kaico irin
soyayar mutumin da kai kake mutukar kiyayyarsa, kawai
ka sake ni ka hutawa kanka dama rayuwarka baki daya.
Ko ba ki fada ba na sani na kuma fahimta ba tun
yau ba manufarki ke nan har ma kike gwada min halayyar
rashin tarbiyiya, don haka na kudurcewa zuciyata ba zan
sahale mikin ba don kar na ba ki farin ciki, na fi so ki gasu
58
ki kuma gashe, har ma zuwa lokacin da masoyin naki z
daina yayinki tun da akwai wanda da suka fi ki a tare da shi, yanzu dai yana kan yayinki ne kafin ya gama sidin kwanon ya 6aro sabo dallele.
Karya kake na fi gaban haka gurin Tahir, duk
hassadarka sai deai ka buga ka kyale,. Dariya ya ska
yarinya na fi karfin na yi miki karya na gani da idanuna ne.
Ta hayayyako mishi sai dai ya sake ta so take ayi ta
ta kare hannu ya sa ya dakatar da ita, ke dakata, kar fa ki
dauka ke wata tsiya ce yaki ce ki ba komai ba ne, kar fa ki
manta babu fa wani abu da za ki yi min tunkaho da shi,
meye bakona ne? wane dare ne jemage be gani ba? Don
haka ki iya bakinki, ke da fankon ashana daya na dauke ku,
kin san ko fankon da ba shi ashana a cikinsa ba shi da wani
sauran amfani da