Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
3 / 8
shi shi ke nan tashi ka je dama na dauka ko wata matsala ce ta faru dana ga kwana biyu bana ganin ka. 31 Ta yi tsai tana nazari, wai me ya kawo haka ma? Mota da ba tata ba shi ya sa har zai gwada mata wannan gadarar banza da wofi, ya mance cewa ba daga gidan tsiya ta fito ba, meye ma dalilin da ya sa har yanzu ba a kawo mata motar ta ba ko dan kaucewa irin wannan wulakancin? Telephone kawai ta dauka ta nemi layin Dadinta, tun da handset din nata ya yi mata sanadinta. Sállama ta yi gami da gaishe shi ya amsa cikin tsananin farin ciki, ummina in ce ko lafiya? Kuna dai zaune lafiya ko? Ta yi kokarin tattara yawun bakinta lafiya lau Dad na kira ne in gaishe ka, in kuma ji lafiyarka. Dariya ya sa umıni 'yar gidan Dady, dadinki yana nan lafiya har ma da mom da Antinki Na'ima. Cikin shagwaba ta ce, af daman ina so in kawo maka karar Mom sam ta ki ta zo gidan nan har yanzu ita ma anti Na'iman sau biyu kacal ta zo su ko su fa'iza sai sun ga damar zuwa ko na yi aiken su zo ne. Yana dariya ya ce, lallai kam ba a kyauta wa ummina ba amma barizanyi maganin abin. Shi ke nan ummina? Ta ce uhm... uhm. Fadi mana ummina, akwai wani abu da za ki boye min ne? ta ji kwarin gwiwa daman Dad maganar motata ce, ina bukatar ta Dad ayyuka sun masa yawa ba ya samin zuwa dauka na da wuri, kin tabbata haka ne ba wata matsalar ba ce ko? Ta saki dariya haba Dad babu kormai komai fa ya wuce. Ya ce to kisha kuruminki galleliyar motarkiatana nan tafe a cikin kwanakin nan shiru na vieban gava don kar ki ishe ni da buge-bugen waya Ta sa kaa wayyo Dad thanks very much, I loye you nny Dad. Yana jin hargowarta ya kife layın yanka dariya kamar yadda ya fada a cikin satin motar ta zo wato 'Exclade Jap. 32 Ko da yake megidan nata ya ce a dankawa ba ta dai so hakan ba, amma dai tun da ta gidan ubanta ce babu yadda za a yi da ita, ranshi in ya yi dubu ya 6aci, wato ta gayawa mahaifinta ba shi da arzikin motar da za a kai ta ofis? ko ko ta gaya musu ya hana a dauke ta a motarsa? Don daure karya gindi shi ne aka turo mata da sabuwar mota, kowa za a gwada wa karyar arziki?" to ai dai sai ya yi ra'ayi za a hau tan za ta ga lalata ya ayyana hakan. Shiru-shiru har tsawon sati guda be ce mata komai ba, wannan dai ta gidan ubanta ce don haka tana da hurumin da za ta bi bahasin hakan. Ba ta taba shiga falon ba muddun yana ciki sai fa yau. Kerere ta tsaya a kansa, fuskarta a daure ta dube shi, Malam mai mota, na ga bakuwar mota a gidanka ina tsammanin kuma tawa ce, so in hali ya yi sai a ba ni, in ko ta yi maka ne sai na sanar a kawo minwa ta? Curarriyar maganar ta yi mi shi ciwo. Ya yi dai shiru bai ce komai ba Ba ka ji ba ne? Ta sake fadi, ina tarbiyya a gurin yarinyar nan ya ayyana hakan, tashi ya yi dan ya gawda mata iyakar ta, "Ke ko wani naki ba ku da arzikin da za ku ba ni wani abu na karbaj balle ma wata akwalar motar da ko jakin dawa sai marat galihu ne zai shige ta. Mari ta kawo nishi ya yi saurid tike hannunta, kanshi ya shiga girgiza mata, kin yi kuskure, ni za ki mara? to bari ki gani. Kafin ta ankara ya kawo mata wani wawan mari da har tsakiyar kanta sai da ta ji shigar marin, ta rikice sai akwai ta sa kuka ta zube a nan. Kanta ya zo yana karkada mata mukullayen motar, kin ga wannan haramiyarki ba dai a gidana ba, domin ni din nan da kika gani na fi karfin a zo a gwada min karyar 33 arziki, don haka ma nake shawartarki da ki yi gaggawar shawartar wadanda suka kawo miki wannan aimalanken su fitar min ita daga gidana domin gidana ba bola ba ne ballantana a nemi mayar min da shi jujin yasar da amalanke. Idan kuma har kin yi kunnan kashi da maganata na dawo na tarar da wannan amalanken to sai dai fa ke da itan ku tattara ki gidanku, ko da yake ko yanzu ma kofa a bude take, ya sa kai ya fice abinshi. Zuciyarta ta shiga ayyana mata a kan me za ta tsaya tana Gata lokaci kan mutumin da yake maketaci mugu me cin'zarafin dan'adam ciki ko har da iyayanta, za ta iya jurar komai amma fa ban da ya wulakanta mata iyaye: Shi wane ne ma? Gidansa din menene? Cikin Rankanin lokaci ta harhada kayanta sai kuma ta tsaya turus, bayan da ta tunano da rashin goyon bayan da za ta fuskanta daga wurin iyayenta, musmman ma Dadin, kai kila ma abin ya juyo kanta tun da tun farko sai da ya bincike ta ta kuma nuna masa babu wata matsala, mugun mutuinin kuwa yana iya yin duk wani abu da ya san zai kare kansa ya kuma tsunduma ta a ciki, harma a karshe ya hada ta da iyayenta kamar yadda ya faru a baya. Hannu ta sa a ka tana fadin, "Wayyo Allana." Kuka take har da kururuwa takaicinta ya zo ya riske ta a wanran gida bayan ya riga ya gaına yi mata gorin sa. Wani abu ta ji ya tsurga mata mai sanyi lokacin da tunano isoffin arzikin, wato iyayan mijinta, taboas su kzafai nc za su iya share mata hawaye. Kai tsaye gidan General Abdallah Usman ta nufa. A yadda Haj. Fatima ta aria ta san ba lafiya. Ita da Abdulwahab. ne a dakin yena dan zolayarta amıma sai ya lura ba ta cikin walwala, ya nutsu 34 lafiya anti to sarkin tambaya daga zuwan mutuin ba ruwa ba komai sai a cika shida tambaya. Cewar Haj. Fatima. Yana dariya ya ce, to a yi mina fuwa, momy na lura dai antin Yaya (kamar yadda suke gaya mata) ta kwace fadar kowa, a gurinki. Nan da nan ya cika da ta kayan kwalam, ya kuma zauna a gabanta, to Anti ci ko hankaliná ya kwanta, na ga duk kin bata ranki. Ya gutsuro cake ya mik bakinta ci Antina kada ki janyo mana jangwam wurin yayannu ya ce mun hana amaryarsa abinci, please ... Anti, pleasccee! Ya yi kamar zai yi kuka kawai sai ya sa ta dariya. duka ta kawo masa tashi ka ba mu waje. Ya fice yana dariya koke fa antinmu. haka kawai da kin hada rai kin san u damuwa, to ire-iren kulawar da 'yan uwan mijinta da ma mahaifansa suke ba ta ta wuce wai. ta nutsu tsam! Yata me ya faru ne? hawaye kawai ta ji na zubo mata, ta dada shiga damuwa, me ya faru ne Heedaya? Ni mahaifyarki ce kar ki rufe ni, wa ya taba min ke? Tiryan-tiryan ta labarta mata komai, abin da kawai ba ta bayyana mata Ba shi ne makasudin da ya hana ta zuwa ofis wato wayarsu da Tahir. Tafa hannaye ta dinga yi tana salati, kai... kai.... amma yaron nan be kyauta ba. Abdulwahab? Ta shiga kwalla mishi kira, yi maza, yi maza. Lafiya mum? Ya fafa a razane, yi maza na ce sarkin tambaya duk inda Abdul yake nemo mini shi. Lallashinta take yi har zuwa lokacin da ya iso yana ganinta jikinsa ya ba shi, tashi ta yi tsam ta shiga cikin fakin ko kalle be ishe ta ba. Yana Kokarin gaishe ta ta fara fadin, yau bana bukatar gaisuwarka, tun da kai yaron banza ne, zai yi magana ta dakatar da shi, kira mahaifinka a waya tukun 35 kafin na ji tsarin naka. Yana jin hakan kirjinshi yaba da dam,! Ya san 'yar iskar yarinyar ta fano mishi bom. har ma da bama-bamai.shi dai General din ba yanan yana can Kasar Slovacia don haka ne Haj. Fatima ta yi saurin sanar mishi don a yi gaggawar yi wa tufkar hanci. Yaji kain ba dadi gurin mahaifin nashi kamar yadda ya yi tsammani, ko kafin ya gama ajiye layin Hajiyan ita ma ta dauka, to inma ban da rashin hankali ina aka taba haka? Kai ba ka sai mata ba an kuma dauko an kawo mata sai ka hana ta abarta saboda ikon banza da wofi har ma ka bi ta da cin mutuncin iyayenta, to kai ina taka amalanken da ka sai mata? Mara kirkin banza kawai, maza tashi ka ba ni waje ka dau matarka ku tafi. Tashi ya yi ranshi in ya yi dubu ya baci ba wai fadan da ta yi mishi ne ya fi 6ata mishi rai ba, domin wanda dadin ya yi mishi nata lami ne ma. Takaicinsa yadda aka ci zarafinsa a gaban mara kunyar yarinyar wanda hakan na kara ba ta lagon raina shi. A kan hanyarshi ta fita ne ya ci karo da Abdulwahab da Ra'uf, wani kallo suke mishi na jin zafin abin da ya yi wa Antinsu ya kuma fahimci dalilin da ya sa suke masa wannan kallon, ashariya ya sakar musu ya kara uban wa kuke wa wannan kallon? Ko ni sa'an ubanku ne? da yake akwai 'yar tazara a tsakaninsu,babu wanda ya tanka masa, domin sun san haushin kaza wuce a kan dami kawai yake son yi musu bayan sunsan shi ya yi rashin kyautawar. Hajiyan ce ta shiga lallashinta ta je su tafi, ita dai kaın ba haka ta so ba a zatonta za ta yi wani kwakkwaran abu ne a kai (ya sake ta) sakamakon cin zarafin da ya yi wa iyayanta, amıma da yake ba za ta iya musanta mata ba sai ta 36 mike, ko banza a wanke mata wani bangare na daga takaicin da ya kunsa mata, tun da an ci zarafinsa kamar yadda ya ci nata. Kofar gidan baya ta bude ta shiga. Daga shigarta ya fisgi motar alamar har yanzu yana cikin fusata, har suka kai gida babu wanda ya cewa wani kala ta buđe murfin motar ta fita ta fara tafiya taku daya biyu, sai ta ji ya tsai da ita, ya fara fadin, kankanuwar yarinya kamar ki ba ki isa in yi miki karya ba ballantana har inmusanta abin dana fada, abin tambayar a nan me ya hana ki inda kika kai karar ki fadi musababbin rikicin ba (wato kama ta da ya yi tana waya da saurayi).; ci gaba ta yi da tafiyarta bayan da ta fuskanci inda ya dosa, koma dai menene ita ce a sama tun da ita ke da nasara. Wayewar gari ta nufi wurin aikinta a cikin dalleliyar motarta, tana jin wani irin farin ciki da nishadi tare da farin cikin nasara a kan abokin hamayyarta da ta yi. Mu je dai zuwa nan gaba kadan ni ke da bababr nasara. Ta ayyana hakan a zuciyarta. Kallon shi ya yi ya dauke kai, aikin banza ma malam, komaimutum sai ya yi wasa a cikinsa, in fa ba neman kudi ba ne in ba haka ba tun yaushe nake zaman jiran ka? Na dai ji ko ma me za ka ce. Ya fada yana dariya a lokacin da ya zauna, dama ka shirya zaman jira domin ni yunwa nake ji, mom ba ta gari ni kuma ba na iya cin abincin kazaman masu aikin nan, ka kuma azalzale ni ballantana na tsaya wurin abinci mai kyau in ci. Tabe baki yayi ai ka ga tsiyar gwagwaren ke nan inda kana da mace har ka tsaya neman abincin titi? Da dare ya yi kuma a shiga kame-kame, ni da kai dinmeye banbanci? Ya ba shi amsa 37 ya ci gaba,babu wani abu da ya banbanta mu, kana yawan gidajen abinci inayi, kana zaga gari har ma da bin dakunan yaran jama'a ni ma ina yi.... Tsawa ya daka mishi ya ishe ka da Allah malam, rufe mana baki. Kallon shi ya yi kana tsoron ta ne? ko kana tsammanin ba ta san-abin da kake ciki ba ne? Ban sani ba. yaba shi amsa da sauri ka rufen baki na ce kada anti amarya ta ji ta rufe ni da duka. To to na rufe ya sa hannu ya toshe bakinsa, kamar wani Karamin yaro, sai kuma ya ce, to ko za ka gayamata ta miko mina binci dan ko na gaya maka yinwa nake ji bana iya ko motsawa a nan da ka ganni. Ya dan saki fuska gami da sassauta murya za ka iya cin abincin kazamiyar yarinyar? Ya tambaye shi, kwarai kuwa, me ma zai hana? Kai dai ba da umarni kawai ka ga aiki da cikawa. Fuska ya daure don ya fuskanci wulakanci yake son yi mishi, ai ka san ba baiwarka ba ce? A'a kai dai fadi gaskiya tsoron takake ji, to sai menene? Sai kawai ka daina kira na da wanda ya yi yowa mata rakiya, domin kai rikon jaka ka zo yi musu, ka ga ko ka fi ni. Dauke kai kawai ya yi ya mayar da kallon shi ga TV muddun ya biye mishi zai dada curo mishi wacce za ta tafarfasa zuciyarshi. Ya mike bari ni na je na karbo abincin da hannuna, tun da ka san ni mace ba ta ba ni tsoro balle har in kasa unkarar ta har ma na zamo dan rakiayrta. Be ce mishi komai ba ya ci gaba da kallon sa fuska a daure tamau. Tana jiyo su daga falonta dariya duk ta bi ta gama cika ta, kai wannan mutum an yi shakiyi ashe bar abokin nasa ma be bari ba? sai kawai ta ci gaba da karatunta ta ma sha mur don kar ya kawo mata wargin da ya saba. Assalamu alaiki amarsu ta ango, amaryar da ba ta tsufa. Ya fada a lokacin da yake kokarin shigowa. Kishingide take hannunta rike da hausa novel tana karantawa. Ta dube shi cikin rashin sakin fuska suka gaisa, to ni fa yunwa nake ji sai a tashi a nemo min abinci tun da angor: naki marowaci ne yahana ni ko da dugon ruwa. Та bata ra. ga shi kuma babu ya za a yi ke nan? Sai kawai ki san yadoa za ki yi da ni. Ya ko zan yi da kai tun da babu? Zai kar amagana ta yi saurin katse shi gami da daga littafin hannunta, "Dan Allah Samir ka kyale ni bana son surutun nan, ka bar ni in yi karatuna kawai, ai kuwa babu yadda za ki yi dole ne ma yau na ci girkin amarya. Ta dada 6ata rai ta san halinsa sarai da naci ga rashin zuciya, ta dube shi yanzu saboda Allah sai ka hana ni karanta "BILKISU"? bilkisu! wace bilkisu? "MAI GADON ZINARE" ta ba shi amsa gami da nuno mishi bangonlittafin. Ya tabe baki ke ma kina karatun shirmen nan? ki bata lokacinki a banza a kan karance-karancen shirme. Ta galla mishi harara shirme ma? Karatun littafin shi ne shirme? To bari ka ji dubban mutane ne ke amfana su fadaka su kuma ilmanta daga ire-iren littattafan da ka kira su da na shirme. Har ma a wasu lokuta ka ga mutum ya shiriya ya bar abin dayake mara kyau, to a nan me za ka ce da wadannan littattafai da ka kira su da na shirme? Haka ko?" ya ci gaba, to in ma hakan ne ni kam ban gani a kasa ba. tamke fuska ta yi ta san shagube yake mata, ta sauya zancen, so yanzu dai mę zan kawo maka tun da ka rantse saika wahalar da ni? ko ma menene a kawo min. 39 murmu;shi ta yi to bari ka ga, yanzun nan zan hado maka irin kwamacalar "BILKISU". WACE BILKISUN? Ya kara tambaya "MAI GADON ZINARE" ita ma ta kara ba shi amsa, murmushi ya yi, to-to-to na gane cewa za ki min Bilkisu cikinlittafin Shirme. To nì dai don Allah kar a hado irin kwamacalar bilkisun, kin san ni cikina special ne, mikewa ta yi tana hararar shi, ka ma ji da shi, ni dai babu ruwa na kwamacalar bilkisun zan hado maka wato Indomie Jollop da akai wa hadi da baked beans salad creams and sirdine a gefe guda kuma ga tacaccen ruwaj inibi da strawberry. Ci yake yana zuba santi lalaoi ki ce "Kayataccen girkin" bilkisu zan ci ba kwamacala ba. ta dan saki fuska ah to na gya maka akwai alfanu a cikin littattafan da ka kira su da shirme. Lallai kam tun da ga shi ni mana amfana daga kayataccen girkin bilkisu. ta yi murmushi har cikin zuciyarta. Ya dai fahimci tana son littafin, sai ya ce, to ni ma a dan ba ni labarin BILKISU MAI GADON ZINARE na ji. Cikin dadin rai ta shiga labarta mishi, ya yi kasake yana sauraro, har zuwa inda ta dakata daga karatun littafin, ya dube ta to sai a ka yi yaya bayan ta gama dafa mishi indomin? oho ba kai ka datse ni ba ina cikin karantawa. Ya ce ayya lallai kam ban kyauta ba, so ina fatan next time idan na zo za ki karshemin labarin dan jin yadda za ta karke musu? Sai kuma ya ce, kai amma fa guy din nan ya yi wa sauran guys din keta, barin shi Aminun ko da yake ya burge ni ko banza ya yi maganin irin wadannan kucakan samarin da ba su kai su so yarinya ba har ma su ce za su gwada gogayya da wanda ba tsaransu ba. 40 Daure fuska ta yi ta san magana ya cillo mata. Ya fan yi murmushi domin ya san ta fahimci manufarsa. Ya mike tun kafin su fara hauro ta, ni zan yi gaba na bar angonki na jira na sai na dawo. Jin karshen labarin bilkisu. Ba ta cc mishi komai ba saboda maganar da ya cillo mata wanda ta taba masoyinta duk ko mutumin da zai taba masoyinta koshi waye ba za ta taba ganin kirkin sa ba kо me zai mata ko me zai ba ta. Har ya kai bakin kofa ya dube ta kin san meye? Ta ce a'a. yauwa to kin gane ko idan ni ne safwan a kai min wannan kwamacalar zane yarinyar zan yi. Ai ko za ku aikata, ko bakomai hali ya zo daya kai kila ma akwainasaba. Shi ya sa ma nake kokarin harhada inawainawa tun kan a kai wannan matsayin. Dariya ya saka ya fice yana fadin Barrister Heedaya. Wani banzan kallo ya sakar mishi banza marar zuciya yarinya na wulakan takata na kyarar ka amma kana wani shige mata har ma ka mance da abinda ke gabanka. Murmushi ya yi irin na tura haushin na, na dai ji ko me za a kira ni amma dai ni ban zana matsoraci ba ballantana har in zamanto dan rikon jakar mata. Sai kuma ya sauya maganar, wallahi kana ba ni mamaki Waheed, sam ka ki ka kwantar da hankalinka ka tsaya ku fahimci juna da yarinyar nan, kullum sai tsiya kala-kala kake tata mata, to ka dai bi a hankali in ba haka ba wata rana za ka yi ba wan ba kanin, ka yi batan 6aka tantan a lokacin ne za ka ga ME GARI YA WAYA? Alheri, alheri zai wayar min insha Allahu. Ya fada cikin zafin rai. Yanayin zamansu dai yana ci gaba da tafiya a haka, babu girma barc arziki babu kuma maishiga hurumin wani, 41 tana ji kamar a kan wuta take muddin yana gidan, haka nan ana sa bangaren yana jin wani irin tururi me zafin gaske a zuciyarsa yayin da ya tunkari gidansa saboda tunanin wacce zai je ya gani wai kuma a matsayin matarsa. Ba ya son yarinyar sam ba zai taba son ta ba. Al'amuransu da yake gudana a tsakaninsa da Zeenatu babu abin daya sauya takan debe mishii kewa harma wani sa'in ta mantar da shi duk damuwar da yake ciki, me kamar Zecnatu me zai yi da wata kucakar yarinya. A 6angaren ta ma babu abin da ya sauya daga cikin al'amarinta da Tanir kuilum cikin huduba yake mata ta kashe aurenta domin shine ya fi cancanta da ita, don haka take zuba masa rashin arziki kala-kala ko da yake yakan mayar mata da martani ninkin ba ninkin abin da take masa ko kankani ba ya ragamata. Zaman dai ya ki dadi domin tuni zukatansu sun riga sun tsumu da kiyayyar junansu. dadin rai a dalilin Yinin yau ta yi shiri ne cikin zuwan su Lubu sun saba da yaran tamkar tun fil'azal da sanayya a tsakaninsu, ita dai lubabatu daliba ce a Jami'ar Bayero (BUK) tana karantar Accounting. Shekarunta ba za su gaza ishirin ba, ita ko lubuna daluba cc a kwalejin tarayya (F.C.E) tana nazartar Hausa/SOS. Ita ma shekarunta ba za su gaza ishirin ba dan tazarar da ke tsakaninsu kadan се. Da yammaci a ka shiga girki. kala-kala saboda zuwan samarinsu, ita ko yayar tasu tia ta fi kowa zakewa, suna tare dukkansu ababban falon gidan, sanyie take da riga da wando na kasar Malesiya ta yi kyau ainun, halifa ne ya dube ta wato saurayin lubabatu,Lo antinmu kina burge ni kin iya karbar baki da karamci har ina nake addua'r 42 Allah ya sa kannannaki su yi koyi dake. Amir me son lubuna yace, gaskiya ne Antinmu akwai kirki sai dai kuma ina rokon a yi training kannanki yadda ya dace kosa zama masu kirki kamar ki. Kai-kai-kai, ku bar fa koda antin nan namu kada a yi rashins a'a yayanmu ya ji ya ce kuna koda mishi mata har ma ya fatattake ku, kunsan yayan namu akwai kishi. Cewar lubabatu. kuma yana mutukar kishin antin nan namu Kila ya hada mu da ku baki daya ya yi waje road da mu. Та yi nunı da hannutna zuwa bakkin kofa, ai ko ta nuno shi din a dai-dai saitin kofar fuskar nan tashi babu alamar annuri a tare da ita, ba su ankara ba dariya suke har da kyakyacewa, kai Heedayan ta fi kowa ma kyakyacewa. Ita da ta riga ta gan shin ne dai ta gan shi. Kai tsaye ya sa kai ya shigo.; to fa kowanen ya sha jininjikins yayinda surukansa suka yi gaggawar zubewa kasa domin gaishe shi, ba karamin daurewa ya yi ba ya iya amsawa saidai fuskarshi babu walwala bare fara'a, ita kam ko a jikinta, domin kalloma be ishe ta ba. sabanin shi da yake mata wani bala'ya'yan kallo don kar a fahimci wani abu da shi ta yi kamar ta bhi shi tsawon lokaci sannan ta dawo suka ci gaba da hira. Yana can ya kasa zuane ya kasa tsaye zuciyarshi sai tafarfasa take yana jinwani irin suya a zuciyarshi. Da ya rufe idonshi hango ta yake yi tana dariya yayin da kumatunta ke lotsawa, la66anshi ya hade ya cije yana jin wani irin abu bayan da ya hango fuskokin kyawawan samarin da sukai wa kawanya. Matata? Ya nana ta no, no, no hannu ya sa ya dafe kai bayan da ya tabbatar dai matar tasa ce. Why? Why? Why? Yake jin wani irin kishinta. 43 Tsaki ya yi saurin ja Allah ya tsare shi da kishinta. Abinda kake so shi kake wa kishi, shi ko ba ya sonota ya yi amannar hakan kai ba ma zai ta6a son nata ba. To amma why har yanzu zuciyarshit ake dafa azalzalarshi da wani abu me kuna kasancewar ta da wasu mazan, mazanma samarin kannanesa me ya sa haka? Ya tambayi kanshi. Awanni biyu cur da dawowarshi ya kasa barin gidan wanda da da ne ba zai yi wannan dadewar ba da ya yi wanka ya gama abinda yake zai fice sai kuma dare wani sa'in ma idan ya raba. Zuciya ta kawo shi ya nufi babban falon nasu da niyyar cin zarafinsu baki dayansu a kanmenene za a nemi mayar mishi da gida bariki saboda kawai ya auri yarinya mara tarbiyya, ba ta falon kai tuni ma ta yi ficewarta, ya iske su ana zuba soyayyar nan irin ta yaran zamani, lubuna na kwance a kirjin masoyinta ita ko lubabatu pillow ta yi da cinyar masoyin nata. Ashariya ya fara saka wa sai kuma ya shiga banbami mara sa mutunci masu ata yaran mutane, ku shige ku ba mu waje kar na kara ko ganin kafarku a gidan nan ko a can gidanmu, tun daku lalatattu ne marasa tarbiyya, ku fice na ce kar-kuma na kara ganin kafar kowanne dan iska a gidannan. A kan me? ta fada a lokacind a take kokarin shigowa harara ya galla mata nan fa ba gidan 'yan iska ba ne don me za a taramin karatai a na yi min shakiyancin banza. Murmushi ta yi kai haba da Alha kar ka bada ni mana, soyayya zamanin ce za ka ce ba ka sani ba? ca na ke anyi wanda ya fi haka. Kai wasu ma sun yi wanda ya shallake haka. Mari ya kawo mata saurin rike shi ta yi, haba dai wannan yayin tuni ya wuce to ma meye 44 abin bugu daga fadar gaskiya, soyayar zamanin ce ba ka sani ba? zan ko yi ınamaki idan ka ce ba ka san haka ba. Anti ki ba wa yayanmu hakuri abin da yake nufi ba haka ba ne. cewar khalifa masoyin lubuna. Ku je abinku babu damuwa ai ba gona da iri kuka wuce ba domin wasun gona da irin suke shigewa har ma su man ta su watsar da irin a wurin dabe dace ba. Tsayawa ya yi galala yana kallonta har matasan samarin suka fice ba tare da ya ce komai ba. Kansu ya yo da duka za ku ci ko ubanku a yau, rukunkume ta suka yi Anti ki cece mu, wallahi ba wani abu muka yi ba daga fa kawai munzauna waje daya. Kai da Allah ku sha kuruminku na gaya muku ba wuce gonada iri kuka yi ba ina ga masu wuce gona da irin? Cikin fusata ya ce wallahi zan hada har ke har su din in bab6alla yarinya, ko ki sake su. Ta dube shi sama da kasa tana wani irin dariyar tura haushi, ni kam na kan rasa tunanin wasu mutanen wani sa'in, wai ini tambaye ka mana? Shin ka mance da cewa abin da ka yi shi za a yi maka? To ina lefin suma su da ba su wuce gona da irin ba. ta yi

Chapter 3 of 8