Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
3 / 7
zan siya ba duk gorin da za ka yi min, ina ni ina siyan wannan dankareriyar motar? ko ko nima kana so a tuhume ni da halin bera ne? Kallonshi ya yi kawai ya kau da kai idan ya biye mishi sai ya saka masa ciwon zuciya. Sam ba ya yin fushi da duk maganar da za ka gaya mishi yayin da shi kuma zai dinga lailayo wacce ka iya sa zuciyarka ta tarwatse saboda takaici. Banza mara zuciya mai naci sai ka rufe motar mu tafi. Yana dariyar dai ya ce, na ji dai ko ma menene da sauki tun da ba a tuhume ni da halin 6era ba. Be tanka mishi ba illa dogon tskai da ya ja, gami da kwada mishi wata muguwar harara, You are very stupid, you are very idiot. Shi ma ya mayar masa sai kuma gaba dayansu suka kwashe da dariya. 30 Wahced da Samir abokanai ne tun suna kanana haka suke a yi fada a shirya tun zamanin Kuruciyarsu haka nan kusan daukacin rayuwarsu, karatunsu kai, dama komainasu tare suka yi shi, makwaftan juna ne, haka nan iyayansu aminan juna ne don haka in ma ba sanika yi ba za ka ıya tsamınanin 'yan uwan juna ne. Sun sami ilimi mai zurfi har zuwa matakin Degree a fannin Engineering. Shi dai Waheed va yi degree ne a Bulding Engineering shi ko Samir bangaen construction Enginecring ya karanta. Bayan karewar karatunsu sun fara aiki da gwamnati na kankanin lokaci to daga nan ne suka bude kamfani na Kashin kansu na yini ginc-gine tare da taimakon mahaifansu. Mahaifin Waheed General Abdullahi Usman tsohon soja ne har mataimakin shugaban kasa ya yi a zamanin da ake mulkin soja a kasar nan. A yanzu haka shi ke rike da Ministantsaro (Defence Minister). Shi ko mahaifin Samir Dr. Salim Ibrahim Kwararren ma'aikacin gwamnati ne, ya rike manya da kananan mukamai a kasar nan har kawo yanzu da yake rike da matsayin MD. Na Bankin Arewa (Bank Of The North), mahaifiyarsa kuwa ma'aikaciya ce a ma'aikatar lafiya (Ministry of Health). Haj. Fatima wato mahaifiyar Abdulwaheed 'yar kasuwa ce tana gudanar da kasuwancin nata a tsakanin Saudi Archia dia kuma kasar ch ina, duk da cewa zamani ne da aka cigaba tana daga gida take gudanar da harkokin kasuwancinta ta cikin na'urar sadarwa ta zamani (Internet). Shi Waheed din shi ne da na farko a gurin iyayansa daga shi sai Abdulwahab, Abdurra'uf, Lubuna da kuma Lubabatu. 31 de to sh baste W [[**************** hea Suna tare da mahaifinta a babban falon gidan kowa da kowa na gidan ya halarta cikin walwala da nishadi in ka cire Aunty Na'ima da ke gefe cikin takurarko da yake in ba Ambassador yana nan ba yaushe ta ga fuskar zuwa falon, haka yake shi mutum ne me tattalin iyalinsa yana son iyalinsa yana kuma bakin kokarinsu wajen kyautata musu kowanne na rubuta list na abinudauyake bukataya duba yagani sa'annan ya zana vek yasmikawa Hajiyan kowanne a sai mishi abin da yake bukatay har su mardiyya a tambayi ra'ayinsu. Ya juyo gare ta, na dawo rgaré ki ummina ta dauke hannunta daga laptop computer ta main dad dubanta ga mahaifinta. ya fara magana ummina aikin nan ya isa haka kullum fatanki ki kare karátuoki lzáina cikakkiyar lauya sannan ki yi aure duk dai na bivra'ayinkiedon dai kada in tauye ki, amma kuma kehgal shinkina son bata min zuciya tun yaushe nake miki wannan maganar amma kuma ma lura yawo da hankatina kawai kike son yis 1 Dady yaushe zan so in 6ata ranka? Ai na ce maka tuni maganar ta shige na bayyana maka ra'ayina.... Da sauri ya katse ta ummi lamarinku davyaron nan ba mai yiwuwa banc, na nunamiki hakan tun darfarkoki dai sauya tunani in ba haka ba zan hada ki da duk wanda na yi ra'ayi. Ta buda baki domin ba ita san abin ya kai thaka ba, Dady wai don Allah mai ya sa ba kalson zabina ne? wallahi Tahir yana kaunata Dady dan Allah kaso shi tun da yana kaunar diyarka. Kai ya girgiza ummi ke yarinya ceiba za ki gane 32 abin da nake hange miki ba, kowane irin bayani zan miki ki dai yi hakurı ki cire yaronnan daga zuciyarki lamarinku ba mar. yiwuwaha ne. Kuka ta saka wayyo Dady ka cece ni don Allah ka so Tahn wallahi shi kadai nake so. Ta zo ta tsuguna a gabansa tana rokonsa. Kada kai ya yi ya fice ranshi a bace sam ba ya son bacın ranta ba aon ya gan ta cikin bacin rai balle har ya ga zubowar haw ayenta, yana yi mata wani irin fifikon so a duk cikin zurı arsa, ba kuma ya taba hana ta duk wani abu da take bukata daga gare shi. Ba ya fatan wannan rana, to sai dai fa ga ranar nan ta zo ranar da zai hana umminsa zabin ranta, sai dai kuma ya san hakan shi ne mafi alheri don haka nema bai cika damuwa ba. Cike fada kan da shagwaßa ta cinyar mahaifiyarta tana kuka, yayin da momin ke lallashinta ita kanta ba ta ra'ayin wannan aure, to amma tun da yarinyar ta kafe ta nace ba sai a ba ta ra'ayinta ba, tana son farin cikin 'yarta fiye da komai a duniya. Kukan dai take a cikin kuryar dakinta, dan menene Dady zai yi mata haka? me ya sa ne yake kokarin bijirewa abin da shi ne mafi soyuwa a gare ta? Abin da Dady be fahimta ba shi ne tana son Tahir son da ba za ta iya hakura da shi ba. Cikin talatainin daren ya kira ta a waya, "Hello my sweet heart how are you? Ya fada cikin taushin harshe. Da kyar ta iya ba shi amsa cikin rawar murya take ya fahimci tana cikin matsala cike da damuwa ya ce menene Heedaya? Wa ya taba min ke? Ta yi kokarin boye masa, ya ce a'a Heedaya kar ma ki rufe ni muddun kina cikin damuwa ko 33 da ba na dubanki sai na sani, kin san da hakan? Don Allah gaya min menene?, Kuka ta saka mishi, ya dada rudewa kwarai da gaske ta fahimci hakan nan da nan ta dada shiga cikin wani damuwar gami da tausaya musu a bisa kudurin da ake kokarin yi na shiga tsakaninsu, cikin muryar kuka ta ce Tahir Dad na son raba tsakainmu, ni kam ban san me ya sa ba ya son lamarinmu da kai ba, bayan ni nasan Dadin yana son duk abin da nake so. Shiru ya yi na wani lokaci ranshi in ya yi dubu ya Baci da kyar ya iya furta ni kaina na rasa dalilin da ya sa Dad ba ya ra ayina, ni kam in ya raba tsakaninmu ban san inda rayuwata za ta kasance ba. Heedaya ina son ki son da ban san iyakarsa ba, don Allah kar ki bari wani ya kwace ki daga gare ni. ya zan yi ne ni Tahir? Da ganin wannan rana gwanda mutuwa. Tofa kai ya kwance ya shiga yi mata surutai barkatai har ta yi dakacen gaya masa. Sai ya zamanto ita ce mai lallashin ma, da kyar da sidin goshı ta. lallaba shi suka yi sallama. Misalin karfe takwas da rabi dai-dai va sd ofishın nata wanda isowarta ke nan ma Masinjanta ta sa ya kawo mishi breakfast amma ko ya daga kai ya dube su, saboda damuwar da yake ciki. "Heedaya." Ya ambata hakan ta dube shi bayan da ta amsa mishi, "Idan dai kin amince kin kuma ba ni hadin kai a yau din nan zan turo magabatana gurin Dadinki. Meye ra'ayinki.?" Kada kai ta yi, "Ko kusa kada kai haka." 34 Π "Saboda ba kya so na ko? akwai wanda kike ra'ayi ko? To na gane na kuma gode." Ya tashi cikin Bacin rai da sauri ta dakatar da shi, “Zauna don Allah. dadina da kai saurin fushi, amma in ban da hakan kai da kanka har ka yi tunanin akwai wani namiji da ke gabana a bayan kai? Kai ma ka sani sai dai kawai ka so zuciyarka. Hannu ya sa ya dafa kansa, "Ya kike so in vi ne?" ta ce, "Yauwa ka gane ko kar ka yi garajen turo magabatanka in ba haka ba za a bata goma dayaba ta gyaru ba, ka dai bari na gama shawo kan Dady, ka san Dad na so na yana son duk abinda nake so don haka nake saka ran nan gaba kadan zamu cimma nasara. Ajiyar zuciya ya yi, "Na fahimce ki Heedaya, na kuma yarda da kaunar da kike min, sauran kokari duk yana gurinki, ki dage ki cije ki turjewa Dady Tahir finki shi ne ra'ayinki, zabinki." Kai ta daga mishi gami da murmushi. Yanayin dai yana ci gaba da tafiya a haka, yayin da Dad dinta ya dage ya cije sa'ilin ne wutar sonsa take dada ruruwa a zuciyarta, haka abin yake a Bangaren Tahir, yana ji kamar wannan lokacin ne ma ya fara son ta. Ana tsaka da bikin faisal da amaryarsa Amal yayin da Heedaya da Tahir dinta suka kasance kirjin biki, yau ita ce rana ta karshe wajen gudanar da 35 shagulgulan bikin a kuma ranar ne za a gudanar da cin abincin dare (Dinner) a Prince Hotel. Ta kintsa ta hade cikin net (first class) na kasar Faransa da akai mishi landing da saitin yard. Launin Kwanduwar kwai komai na jikinta ma launin kwanduwar kwai ne. hatta da yari da sarka da kuma abin hannu wasu tsadaddun fasion earring ne masu mutukar tsada samfurin 'Vivaldi.' kamar ko yaushe dai hill din takalmi ne a kafarta yayin da ta bi ilahirin jikinta ta feshe shi da 'Tommy Purfume). Tsayawa ta yi a mudubi tana kallon mimar da ubangiji ya yi mata, a yau kam ta dada gasgata sunan nan da ake kirantta da shi (Queen of Beauty) Barrister Heedaya ke nan yarinya me ji da kanta. Doguwa ce sambal me kyawun sura idanunta manya ne masu kyawun gani, gashin da ya yi wa kwayar idanunta rumfa su suka dada fito da kyawunta, haka nan tana da yalwar gashin gira, gazar-gazar gwanin ban sha'awa, haka nan tana da yalwar gashinka baki sidik sai dai yana da dan karfi to amma mayukan zamani da take amfani da su sun mai da shi mai mutukar santsi da sulbi, ta biyo kalar mahaifiyarta domin baka ce ba ta da haske ko kalilan ko da yake ko a cikin kanurin ba kasafai akan sami farare ba. To sai dai ko kai farin idan ka dube ta za ka yi fatan zamantowar launin fatarka irin tata saboda santsi da sheki gami da laushi dafatarta ke da shi. 36 Katafaren hotel din na Prince ya cika ya batse da zaratan samari da 'yan mata waje ne har waje da ya amshi bakuncin 'ya'yan hutu, 'ya'yan kuma masu da shi, waje tuni ya gama tumbatsa, domin tuni amarya da ango sun iso, a gefenta kuma babbar abokiyar amaryar ce Barrister Heedaya Sa'ad Mohd, gaba daya hankalin mafi akasarin guys da ke wajen ya tafi gare ta kai ita me kyau ce kyawun ma irin mai daukar hankalin jama'a, abin da kunnuwan Waheed ya jiye mishi ke nan, be wani kokarin juyawa kallon ta ba, ta'adarsa ce yarinya duk kyawunta duk matsayinta sai dai fa ta so shi ba dai shi ya fara furta yana son ta ba. Samir din ne ya zungure shi da kafa. Ya yi masa nuni da ido, Waheed ga fa mutuniyar taka can. Wa ke nan? Ya tambaye shi gami da waigawa lokacin ne idanunshi ya gane mishi fuskar sarauniyar kyawun. Baki ya bude cike da mamaki bayan da ya gane ta, kai hakika Allah ya yi halitta a nan, yana cikin wannan tunani ne ya dada zungurarsa. Meye ne haka kamar wani bakin maye kakura mata ido. Shafa kai ya yi gami da sunkui da kai Samir ina son yarinyar nan. Eh me ka ce? Abinda kunnuwanka ya jiye maka, kada kai ya yi tofa dara ta ci gida kamar yaya? ka fi ni sani ko da yake shi ma din ya jinjina lamarin? Meye shawara ne Samir? Ya dan yi nazari, kawai ka sa kai ka san da zafi-zafia kan bugi karfe muddin ko ka yi sake ni sai na saka kai, kai fa dan iska ne, ba a maganar kirki da kai dan Allah 37 ba ni mafita ka san ni dai ban iya wani zance da mace ba saifa ka kowa a yau din nan in ba haka ba sai dai idan za ka biya ni, ka san ni komai na kudi ne a gurina. Dauke kai ya yi gami da jan tsaki, ya ki ya gane lokacin wasa da lokacin da yake na zama serious. A bangaren amare kuwa Barrister Heedaya ce ta gabatar da jawabin amarya cikin tsararren turanci tamkar baturiyar Ingila. Zazzakar muryarta ta dada tafi da zuciyar guys din wajen ciki ko har da Abdulwahecd. An fara gabatar da duk abubuwan da aka tsara sai dai daga Heedayan har zuwa su kansu amaren rayukansu a bace yake saboda rashin isowar babban na hannun damar angon (Tahir). A dunıya faisal ba shi da abokin da ya fice Tahir, ko meye dalilin rashin isowar tasa? Wannan ne suka kasa sani, ta neme shi a layi amma kuma is not available, amma duk da hakan ta yi karfin hali wajen danne damuwarta ko dan kar ta dada saka amaren a cikin damuwa. Babu wasu masu kida da aka gayyata illa music da aka saki. An ci an sha an gyatse samari da 'yanmata suka fara dansewa wasunsu kuma suka fara kulla abota da sababbin 'yan matan da suka yi. Yayin da su Heedaya suka shiga hidima da da jama'a wajen rarraba musu gift da aka tanada samari da dama sun latsa ta amma ko ta kula bi ta ke tebir daya bayan daya suna raba gift din ita da Samira da kuma Najeeba 'yar uwar amaryar. 38 A can daya teburin da aka warcwa manya- manyan abokan ango Waheed ne da Samir suke tattauan yanda za su shawo kan abokiyar fadan nasu, barka da hutawa kuna bukatar abokin hira ne? wata kyakykawar yarinya ta fada, kai da ganin ta ka san cewa 'yar wani ce ban da ma kyawun da Allah yaba ta a lokaci daya suka daga kai suka dube ta kallo daya ya yi mata ya kau da kai gami da jan tsaki akara gaba dai mun gode, Waheed din ne ya fada. Ji ta yi wani abu ya tsirga mata, yayin da matsananciyar kunya ta baibaye ta, musamman da ta lura dariyar da guys din da ke kusa da wajen suke mata cikin mutuwar jiki ta bar wajen.. Dunkule hannu ya yi ya daki tsakiyar teburin. kai Allah ya isa Waheed, wulakancinka ya yi yawa, haba mai ya sa kai mata haka? Harara ya sakar masa donme ba zanmata haka ba, a bar ni man in ji da abin da ke gabana saikumaa zo a ishe ni da wani karuwancin banza, ka sani dai macen da take tallata kanta ba kasafai take burge ni ba. Amma dai ko mameye be cancanci ka yi mata haka ba, ko da yake sabonka ne wulakanta 'ya'yan al'umma, sai fa in kai ka yi ra'ayi. Ta gabansu ta zo ta shige amma ko kallo ba su ishe ta ba ta lura da su tun farkon shigowarsu kallo daya ta yi musu ba ta kara ko son duban su ba kai da ta san akwaiwata alaka a tsakanin su da shi faisal din da 39 ba babu abm da zai sa ta zo, duk da amincin da ke tsakaninsu da amaryar, to amma tsanar mutumin ta zarta komaia wajenta. Samir jibi fa ta share ni ko kallon kirki ba mu samu daga gare ta ba, ina shakkun tunkarar ta fa? Samir din ne yake mishi magana cikin rada-rada da Allah za namiji mana, meye kankanuwar yarinya za ta firgi ar kai haka... shawara ta a gare ka kar ka bari wannan lamar ta shige ka, maza je ka ga ta can sun zauna ita da waccan kawar tata. Kallon shi ya yi yavin da shi kuna ya kada kai. Hannunsa sanye cikin aljihun coat dinsa yayin da dayan yake a sake, ya isa teburinsu, barkanku da hutawa. Ya tarfa cikin daddadar muryar nan tashi maisace zukatan `yan mata Ta dube shi ta kara dubanshi sai kuma ta kau da kai, yayin da ita kuma samairan ta ce lafiya dai malam. Lafiyar ke nan ya ce ya ci gata na son magana da kawarki ne. ta dube shi ta dube ta sannan kunma ta girgiza kai, lallai kam lamarin babba ne.ya dan matso daura da ita, barrister Herdaya o zan sami mutsuguni a wajen nan? Wani irin abu ta ji nai mata yawo a tsakar kanta, tsana da kiyavyar nutumin ta motsa mata, ji yake jiya ma yau ce ya zo ya ci mutuncinta, to ai ko zai gane ЛҮА ВА YAU BA ce tun da zai amshi SAKAYYAR abin da ya yi mata da hannunsa. 40 Matsowa ya kara yi kusa da ita yayin da yake kokarin zama kusa da ita da yake kujerar mai cin mutum biyu, zumbur ta yi ta mike yadda ka san mutuwarta ce ta nufo ta, cikin shouting (daga murya) abin da ya janyo hankulan mutanen wajen ta shiga fadin, "Dan Allah malam ka saurara min, ka fita hanya ta, domin kai ba tsarana ba ne, ba ka kai ko ajin da zan tsaya dakai ballantana in kai ga yin soyayya da kai ba, ba na son ka na sha gaya maka ba na sonka to menene za ka dame ni?" cike da mamakin tuggun da take shirin kulla mishi ya buda baki da niyyar magana, cikin sauri ta tare shi, dama dai kada ka 6ata yawunka domin ba zai yi tasiri a gurina ba, dan babu wani dadin baki ko kalami da za ka yi min, domin bana son ka, kai din nan ba ka isa in soka ba. Samawa kanka lafiya ka sami dai-dai kai, ni kam na fi karfin tsayawa da kucaki ka na kazami kamar ka. Haaaaaaaaaa! Matasan wajen 'yan mata da samari suka kwashe da dariya, wasunsu ma har danuno shi da yatsa, musamman ma dai samarin da suka sa abokin adawar ubangidansu ne ko da yake yawanci abokanan faisal abokanan Tahir ne na kud da kud. musamman da yake shi maliya ne ba ya tausayin kudi ko kankani, amma kuma shi faisal din suna dan dasawa da Waheed din. A na cikin haka ne mai gayya mai aikin ya iso TAHIR DR. EL-HUSSAIN maliya sarkin ambaliya 41 kamar yadda akasarin abokanansu sukan kira shi, cikin isa da gadara ya iso wajen kai da ka gan shi ka san cewa wani ne kuma dan wani ne saboda tsadaddun kaya na fariya da ya sa a jikinsa, da ko Baturen sai isarsa ta kai isa yake iya saka su, ya dube shi da kallon raini da kaskanci a gefe guda kuma yana me mamaki gami da takaicin abin da ya' hada su da Heedayansa. balbalin bala'i ya ayyana hakan aransa, wannan karon kam Wahced ka yi kadan har ma ka yi kankanta na tsane ka, gabarmu da kai ba za ta taba karewa duk dai a zuciyarshi ya ayyana hakan. Ya mai da dubanshi gare ta Sweet baby yana mai dan bata fuskarsa,me ke faruwa ne a wajen nan? Ta dube shi da sigar so yayin da shi kuma ya hado ta da jikinsa tell me?" wani mutum ne dabba ko jaki zan kira shi, ya takura min na gaya mishi ba na son sa, ba na son sa, ya kasa fahimtar hakan, amma ban sani ba ko da gasken jakin ne ko dabban? ta nuno shi da yatsa ka shiga tsakanina da shi Darling Wani kallo ya sakar masa na nuna tsantsar tsana da kiyayya cike da raini ya shiga furta kakan, to kai ka ji sai ka gane ka fita harkarta tun da ba ta ra'ayinka. Zuciya ta kawo shi wuya ya fusata bayan da ya kawo mata wawan mari sai dai ko kafin ya ankara tuni har ta gama wanke mishi fuska har kashi biyu. Baki ya saki haaaaa kamar wani soko, wanda tsabar takaici da bakin ciki ya mai da shi haka har ma yake jin cewa kila jinin jikinshi ya riga ya gama sandarewa har ba ya tunanin sake motsa 42 ga6ban jikinsa, wannan shi ne kashedi na karshe, idan ka kiyaye ka taimaki kanka. Da fadin haka ta bi shi da ruwan lemon da ke hannunta zuwa fuskarsa, ta juya da zummar tafiya yayin da take jingine da kafadar Tahir, wani irin wawan raruma ya kawo mata cikin sa'a masu dan hankalin cikinsu suka rike shi amma duk da hakan hankoro yake na ya kwace sai zagi da ashare-ashare yake tamkar mutumin da ya zautu. Ita ko ko a jikinta, wani murmushi ta bi shi da shi, bayan da suka fice ita da Tahir dinta. To fa manyan na hannun daman Tahir suka shiga sowa, dariya har ma da tafi, barin kuma 'yan matan wajen musamman wadanda suke ciki da shi ciki ko har da yarinyar da ya bonsa yanzu-yanzun nan, tsakar kansa ta tsaya tana ta yi mishi dariya, har ma da shegantaka. Ga Samira ko tun da ta kifa kai a jikin teburin ba ta kara dagowa ba ranta in ya yi dubu ya baci hakika kawarta ta gwada haiin rasthin kirki, ba ta taßa sanin tunaninta ragagge ba ne irin yau, har yaushe za ka tijara dan'adam irin haka, shi kansa Samir din sandarewa ya yi a kujerar da yake zaune sakamakon kaskancin da aka gwadawa abokinshi. Karon farko ke nan da ya ji tsanar yarinyar, kai ko 'yar uban wace ce sai sun yi maganinta. Tun bayan rabuwarsu da Heedaya kai tsaye mashaya ya wuce domin nuna farin cikinsa kai anya ko akwai wata rana da ya taba riskar kansa cikin farin ciki haka? In ma da akwai to ba ko ta kai wannan ranar ba. Waheed ka shiga tara ka afka tarkona abin da na dade da buri kodonkai ya zame min dole ma in auri Heedaya. Shin akwai burin da nake da shi da ya wuce na kuntata maka? Ya taınbayi kansa duk wanda yake a mashayar a ranar a 43 cikin aljihunsa ya sha saboda mutukar muhimmancin ranar, ko da yake wani sa'in yakan yi hakan idan ya so nuna bajintarsa. A nata 6angaren ta kasa bacci tana jin wani irin farin ciki da nishadi, takan yi murmushi ta runtse idonta a duk lokacin da ta hango abin da ya gudana a dazun nan, musamman wajen da ta wanke mishi fuska, hakika ta yi bajinta ya ci kuma a yaba mata tun da ta yi nasarar kunyata shi kai har ma da kaskantar da sankacecen saurayin da yake mutukar ji da kansa ya kuma saka rayuwarta cikin kunci ba sidi ba sadada. Da wannan tunani bacci ya dauke ta. 44 <> bin da Waheed yake fada ke nan ga abekinshi, ya A daga dan yatsansa gami da nuni da shi wallahi Samir na rantse da sarkin da ya halicce ni sai na wulakanta rayuwar yarinyar nan za ta yi dakacen abin da ta yi min nan ba da jimawa ba. Ni Waheed a ka yi wa wannan? a kuma gurin mutumin da gaba da kiyayya ce a tsakaninmu? Ya yi kwafa Tahir zan maka illar da ba za ka taba mancewa da ita rayuwarka ba, za kuma ka gane kuskurenka a karo na biyu, ni Waheed wane kai Tahir? Ya ambata hakan da Karfi. Samir din ya yi shiru be ce komai ba, rashin kyautawa kam yarinyar ta yi har ma ta wuce mun shairin, to amma ya ci a ce an manta da komaí an kyale, domin su dai ba kananun yara ba ne, laifi ne kowa ya yi wa kowa, shi ke nan kalas! Kwana daya, biyu, shiru kai har tsawon sati babu Samira ba ta ko neme ta a waya ba, idan kuma ta neme ta a layi sam ba ta dagawa, matar da ba sa iya kwanaki biyu ba tare da daya ya ziyarei daya ba. Daga office gidansu ta wuce. Ta yi sa'a ta same ta domin ita mahaifinta ya ki lamince mata yin aiki ba tare da ta fitar da mijin aure ba, abin da kuma ya gagare ta, ba wai dan babu samarin ba a'a illa dai sangartar da ta tashi cikinsa a tunaninta aure ba komai ba ne face takura da tsangwama. Sun gaisa da maman Saınira Haj. Maryam, amma daga nan ta huce fakin mutuniyar tata, kai ta dago ta dube 45 ta sai kawai ta mayar da dubanta ga abin da take, hannu ta sa ta kwace magazine din da ke hannunta meye wani za kı wani kallę ni ki basar? Sakar min takardata, dan Allah Samiran ta fada fuskarta a daure, ba zan sakar miki ba sai kin fada min abinda na yi miki kike sha min kunu haka. Ta dube ta ta kara dubanta, sai kuma ta ja tsaki, kin ba ni mamaki Heedaya sam ban taba sanin za ki iya cin zarafin n n haka ba, haba me ya sa kikai wa mutumin nan hakа. Harara ta sakar mata, makure ni sai in gaya miki dalili tun da ba ki da masaniyar hakan. Ta fara magana cikin fada-fada aikin banza kawai ą kan wannan banzan mutumin har za ki dinga 6ata rai kina wani share ni, ko ma dai me za ki ce na ji dai na kuma fada na kuma kara ba ki kyauta ba, ba kuma ki nuna halin kirki ba. Karya kwana ta yi da niyyar fita, ni na tafi amma kuma kafin nan ina shaida miki ki je ki nemo kuma ki binciko duk inda mutumin nan yake sai ki so shi kuma ki aure shi, shi ke nan ko? Hankalinta a tashe ta shigo falon rungume da mardiya, gaba dayansu hankalinsu ya dawo kanta, Alhajin ne ya fara magana lafiya Na'ima?" me ke faruwa ne cikin muryar kuka ta ce Dady (kamar yadda sauran 'ya'yanta suke fada masa) mardiyya za ta mutu taimake ni don Allah suma take, da sauri Haj. Kaltum ta yo kanta ko kafin ta iso ma tuni su Heedaya da 'yan uwanta sun yo kanta. Mardiyya, mardiyya, me ya same ki? Ta fada a lokacin da ta karbe ta daga hannun Na'ima. Babu alamun numfashi a tare da ita. Cikin matsanancin hanzari ta zari key din mota ko kafin a yi wani abu tuni ta fice

Chapter 3 of 7