Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
1 / 7
An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels ME GAR YA WWAYG ZALNAE KABIR BIROMAN MRS SUNIŞU BRISCOE) Sadiya Mukhtar Chairıman Asına'u Mukhtar Chairman GAISUWA DA FATAN ALKHAIRI GA: Fatima Aminu Baba (HAKA YA ISA) Allah ya bar zumunci, ya kuma albarkanci zuri'a, amin. GARGADI Ban yi wannan littafi domin wani ko wata ba, ban kuma ba da izinin amfani da slii ta kowacce siga ba batare da izinin marubuciyar ba. BUGAWA A NAʼURA Mubarak Ahmad Kurawa Yolawa Computers&Communications Email: almubrak@yahoo.com G.S.M: 08032929831 4 MAFARIN RIKICI ammacin ranar Asabar garin ya yi kyawu babu Y alamun zafi sai ni'imtacciyar iska da ke kadawa niai fauke da ni'imtaccen kamshi sakamakon korayen ganyayyaki da furrai da suka lullube zagayen unguwar ta masu fada a ji, unguwa mafi kyawu a duk cikin birnin na Dabo (Nassarawa G.R.A). Dan’adam zai kasance mai godewa Sarki. Allah a bisa wannan ni'ima da ya yi ımasa, alhalin a wasu kasashen ko kwayar gero ba ta iya tsirowa a Rasa t od iSannu a hankali motoci ne ke shigewa cikin lumana da kwanciyar rai, yanayin motocin da ke sakaraftu a kan shimfidadden titin kana kyakkyawa da ko a kasar turarai nisai haka shi zai dada tabbatar maka da cewa ba fa unguwa ce ta Ya-Ku-Bayi ba. A dai-dai junction (mahada) din in Ahmadu, Bello Way bayan an shige shataletalen Daula Hotel titin da zai sadar da kai har zuwa Tukur Road daga nan har Abbas Road, wata kyakkyawar mota ne fauke da Rofa daya mazaunin ma na mutum biyu ne kawai, motar da nigalibin matasan Turawa ne ke amfani da ita ta kunno kai, ilahirin glasses din motar masu duhu ainun a kulle suke. tk ,mo !dai-dai lokacin da. motar take kokarin karya kwana daga Ahmadu Bello Way zuwa Tukur Road a dai- dai kumay lokacin ne wata rantsattsiyar mota kirar m.Meroedesc 230), motar da akasari matasan 'yan mata yа yаn masu fada a ji suke kece raini da ita. Ta kuno kai Alaga, Tukur Road har suna shirin tawo mu gama da motar 5 da ta bullo daga Ahmadu Bello Way sakamakon gudun da kowannensu yake yı, ya zamanto ba za su iya shigewa a lokaci guda ba ke nan. Tilas sai daya ya budawa daya amma hakan ta faskara. Tsawon minti biyar motocin biyu sun kasa budawa junansu. Abdulwaheed da ke cikin daya motar da ta fara isowa wajen shi ke rike da akalar motar, dogon tsaki ya ja gani da waiwayar abokinshi, wai shin wane me takamar banza ne haka ya tsare mana hanya ne? Samir da ke gefe ya dube shi shi ma gami da dan jan tsaki, Ni ma tunanin da nake yi ke nan Waheed. Waigawa ya dan yi gami da duban hanyar. lallai ma ko waye ma ya kwaso wa kansa jidali, za mu kauce mu ba shi hanya ne alhalin mu ke bisa ka'ida? (wato su suka riga shi isowa wajen). A'a kila dai ko ma waye ke jan akalar motar yana da tawaya a idanunshi ne cewar Wahced. Koma waye? Ko dai ko dai wace ce?" da gani ba tambaya ka san motar mata ce, kila ma ta irin tsagerun yaran nan masu jiji da kai da fangimar tsiya. Tsakin ya kara ja gani da tabe baki ai ko ma wacece ni babu abin da ya shalle ni, zan kuma nuna mata kuskuranta, mutukar ba ta kauce ta ba mu hanya ba. A can dayamotar 'yar kyakkyawar matashiyar kana sarauniyar kyau (Quecn of Beauty) kamar yadda akasarin friends dinta kan kira ta, ta cika ta yi fam tare hanyar da take ganin an yi musu sautin kida ne ke tashi a motar kaset din Tony Branton cikin wakarsa ta "Look 4 Me'. Ta kai hannu ta rage sautin radio (volume) sannan ta gyara zamanta a jikin kujerar gami da kishingida bayan da take bin sautin wakar sannu a hankali, sameera dake gefenta ta dube ta sannan kuma ta mai da dubanta izuwa 6 daya motar gayu na tsiyarsu a garini nan, ji fa iskancin da mai motar can ya yi mana. Ba tare da ta dube ta ba ta shiga ba ta amsa, shi ya sa ni ma zan gwada mishi ni dai-dai da shi ce. Ta ci gaba da jin sautinta ba tare da ta kara cewa komai ba. Tsawon lokaci babu wanda ya yi kokarin kaucewa wani, ta fakaici idonta ta danna ham din motar har kashi uku. Samir ne ya sa hannu ya mayar musu da martanin hakan, ya lura da kyau ba su da niyyar kauce musu ya dube shi da Allah kau ce ka ba su hanya su shige kada su 6ata mana lokaci a banza, wani kallo ya sakar mishi sai ka bari yayin da sitiyarin motar ya dawo hannunka ka janye musun, tun da ka amince wa zuciyarka mata ka yowa rakiya duniyar, ya harare shi ba na son cin fuska, sanin kanka ne babu yarinyar da ta isa na jera da ita balle har na zamanto dan rakiyarta. Abu daya dai da nake so ka gane kuma ka san hakan, ba na wasa da lokacin da duk na san wata karuwa za ta same ni, don haka yanzu haka lokaci ne da yake da matukar muhimmanci a rayuwata, kauce ka ba su hanya dan Allah in ba so kake ka cuce mu ka yi mana sanadin da za mu yi missing makudan dollars din da suke shirin shigo mana ba, tun da kai na lura da kyau ba sa gabanka, sau tari ka kan yi wasa da damarka. Ya dube shi ka san Allah ko nawa ne za mus amu na gwammace wa asararsu da dai in kaucewa mamallakiyyar motar da ta gwada min gadara da isa, ya dada nutsewa cikin kujera, Samir ya dube shi yana dan gunaguni dole ma mu kauce mu ba su hanya in har su ba suba mun ba a kan me za ka cuce ni? Wata da watanni muna neman kwangilar nan takuma samu shi ne za mu yi wasa da damarmu? Sanin kanka ne ketare lokacin da aka diba mana ka iya sawa mu 7 kasa ganawa da Director wanda hakan ke nufin mun saki damarmu, a Jalilin me za ka cuce ni? Ya buda kofar gami da fita yayin da shi kuma ya bi shi da harara banza mayen kudi son kudi kamar tsohuwar karuwa. Ya ja ya tsaya gami da knocking glass din motar duk da cewa ba a iya ganin na ciki. Barrister Hecdayat ta daga kai ta dube shi gami da kau da kai, Sameera ce ta yi kokarin fita dan jin bahasin tsare musu hanya da aka yi. fuskarshidaure gami da yi mata kallon raini ya ce meye hujjarku na tsare mana hanya? Ta bi shi da irin duban raini, may be kanka ya dace ka yi wa wannan tambaya, amma dai bari in ba ka amsa, hujjarmu be wuce cewa mu mun isa har ma mun wuce kaucewa wani Guy ba ko shi wanene. Haka kika ce? Kwarai kuwa. Ta ba shi amsa. Tsawon lokaci suna ce-ce-ku-се. Waheed da ke mota duk haushin abokin nashi ya kama shi, dan menene zai tsaya kankanuwar yarinya tana bata musu lokaci haka? ya ja dogon tskai gami da ficewa daga motar cikin fusata ko 'yar uban wanene za ta gane kuranta. A cikin motar take ranta in ya yi dubu ya baci ta hasala ta fusata da wannan wulakanci ko kuma gadarar da ake gwada musu. Babar damuwarta be wuce batawa sauravinta lokaci da za ta yi ba, a dai-dai wannan lokaci suna hanyarsu ta zuwa Birthday partyi na fricnd dinta kana budurwar babban abokin amsoyinta. Duk kokarin da za ta vi na ta same shi a layi ta rasa samunsa completely wayar ta Ki shiga tabbatar network problem. Dauke da kallon ke ba ki isa ja da ni ba ya dube ta ya kuına dubi motar ya dai fahimta ba ita ke jan motar ba, ya kara yi mata kallon nan dai na raini, zai yi kyau ki 8 shawarci uwar gijiyarki ta ba mu hanya, domin ke na fahimta matsayinki be wuce na rike mata jaka ba ko?" ta galla mishi harara gami da jin dacin maganar shi. Ya gyara tsayuwarshi bayan da ya zira hannayenshi a aljihu ya yi irin tsayuwar nan ta isa da gadara sannan ya dan kwankwasa gilass din dai-dai saitin Driver, hankalinta ya dawo gare shi ta kalle shi tsaf sama da kasa a zahirin gaskiya ba ta taba ji m,o ganin matashin da tsarinshi ya yi mata ba irinshi, sanye yake cikin English wears irin nasu na 'ya'yan masu da shi kayan sun mutukar tsari da jikinshi tamkar domin shi aka saka kayan. To sai dai fa duk wannan ba ya gabanta ta ma ture shi gefe guda a memakon hakan sai ta riski kanta da jin tsanarsa, sakamakon gadarar da yake shirin gwada musu. Cike da jin kai ta fito daga ickin motar, a duk iya gane-ganensa da bibiyar 'yan mata da ya zamanto sana'arsu be taba katari da kyakkyawar yarinya me kyawun fuska har zuwa gangar jikinta irin wannan ba, dole ne ma ta yi jin kai da isa, ya ayyana hakan a ransa. Sanye take cikin French lace da ya amsa sunansa wato original din dan yadi daya naira dubu goma zani da riga me dogon hannu, (buba) kanta babu kallabi bare gyale sai fa uban gyaran da gashịn ya sha, wanda ya yi mutukar kara fito da kyawunta. fankwalin lace din ne ta yafa shi a gefen kafadarta yayin da kunne da wuya har ma da kafafunta shake suke da danyen gwal da babu sirki a cikinsa, kirar kasar Dubai a kafafunta hill shoe ne da ya kara fito da tsarin kwalliyarta. Ta dube shi ta kuma dubi abokinshi cikin kallon raini a kan menene za a tare mana hanya? Ta fada cikin daure fuska. Ya dube ta ya kara dubanta cikin kallon da ya 9 fi nata, ke ba ki kai ko matsayin da za a mayar miki da amsar tambayarki ba. Samir fin ne ya karashe mishi da cewa kuma ku yi kokarin janye motar nan cikin lokaci Kankani. Ini ba haka ba fa? ta fada cikin tsiwa. Za ki gane kuranki shi ma Waheed ya mayar mata. Ji nan malam mun fi karfin mu tsaya ce-ce-ku-ce da ku dan haka ku kauce ku ba mu hanya cewar sameera. Ai na zaci ke 'yar rikon jaka ce babu da abin da za ki iya tabukawa, ban sani ba ba haka ba ne ko ma menene dai ba a gabana yake ba so ku kauce ku ba mu hanya ina fatan kun gane. Ya matso gab da gab da ita ku janye motarku tun kan GARI YA WAYE MUKU. Ya waye mana har ma dare ya yi mana, in dai har a kan in kauce muku ne never, wallahi ba ku kai haka ba, kai ba ku isa komai ba ma. Ta fada cikin daga murya. "Ke wace ce? Wace ce ke? Ke 'yar uban wane ne za ki zo kina gwada mini wannan gadarar?. " "Ubana ya fi karfin a ce wanene? Ban san ba ko naka?" ya fusata ya kawo mata mari ya kuma kawo mata marin ya yi sa'a duk ya same ta. Cike da mamaki ta dafe kuncinta ta kuma dafe kuncinta sannan ta kawo mishi mari ko kafin ta kai tuni ya rike hannunta ya matse shi da karfin gaske ya shiga nuni da yatsa, da kin sake hannunki ya isa kuncina wallahi yau da kin gane kuskurenki, da kuma na nuna miki ke karamar mara kunya ce.' Ya yi facali da hannunta, ta zuciya ta kara kawo mishimarin, cikin sauri sameera tayi saurin rike ta, yayin da shi ma Samir yake kokarin rike shi, kan kace kwabo jama'a sun taru ana rabon fada zaginsa take tana fadin ko shi dan uban wanene a yau 10 din nan sai ya ga kaskanci me tarin yawa, za ta ga gatanshi, za a ga mutumin da zai iya kwatarsa. Shi dinma ban da an rike shi nufin dukanta yake waje yakacame da hargowa, yayin da go slow ya cika titin, w da duk sun tsare hanya, kowannensu kuma ya nace ya kafe ba zai janye motarsa ba, to fa yau fa ake yin ta ilahirin motocin da ke kan titin an saka su cikin halin ka-ka-ni-kayi babu dan ar gaba bare ja da baya. Police station da ke gundumar wajen nan da nan reporting ya iso musu ba bata lokaci suka garzayo da nufin sasantawa amma kuma daga Waheed din har Heedayan sun dau alwashin duk wanda ya taba musu mota zai gane kuskuransa. Nambar motocin kawai suka gani suka shiga taitayinsu, fadan na manyansu ne, lallai kam matasan ba banza ba suka kafe kai da ka ji ka san akwai abin da kowannensu ya taka. Idan ka ji ana fa dan manyan giwaye me iya shiga tsakani sai ko zaki da zakanya uwayen gijin naımin dawa. Abu wasa-wasa ya dauke su har tsawonsa'a guda, kowannensu ya kafe kan ra'ayinsa yayinda aka dau hakkin jama'ar da ke kokarin shigewa amma kuma babu damar hakan. Wani tunani ne ya fado mi shi nan da nan ya matsa nambobin Dad din Waheed domin shi kadai ne zai iya kashe rikicin, ita ma wannan tunanin ne ya fadomata cikin kanknain lokaci ta lalubi nambar Momyn Heedaya tunda ta san dad din ba ya kasar. Motocin gidajen biyu ne suka iso a lokaci guda a lokacin gudan ne kuma suka janye motocin da ake rikici a kansu. Bayan da kowannensu magabatansa suka sa aka yi awon gaba da shi. 11 Da isarta gida ta ci karo da Aunty Na'ima kishiyar mahaifiyarta, ta dube ta Heedaya lafiya dai?" ganin aydda take a hargitse wani irin kallo ta yi mata sai kuma ta ja tsaki ta shige abinta, kallon dai take bin ta da shi, kai wannan rashin tarbiyya har ina? matar ubanka kake wa wannan duba. Fadawa ta yi kan mamanta sai kuma kuka ya biyo baya, wallahi yau Momy wani mutum ya gwada mini kaskanci, idan dai har ina da gata a wajenku ya zama dole a nuna mishi iyakarshi, wai menene ya hada ku ne Heedaya?" Tiryan-tiryan ta labarta mata. Baki ta rike ya mare ki? Lallai kam zai ci kaniyarshi, yaron banza kawai, a kan me zai kama diyata ya buga?" A na me?" Zai gane kuskuransa kuwa. Bari Dadinku ya dawo ina sa ran zuwan nashi daga yau zuwa gobe. Ta dada narke mata yayin da ita kuma take ci gaba da sababin fada, dakata malam. Waheed ya umarci direban da ya tsaya dakata na ce, ya fada da karfi cikin fusata, Malam Mudi direban mahaifinshi wanda a haife ya haife shi har ma jika ya yi da shi. Ya ja ya tsaya fice kawai je ka abinka zan karaso da kaina. Ya dube shi cike da ladabi ya shiga fadin ranka ya dade Alhaji ne ya umarce nina dauke ka na kaika gida. Ya gargade ni kar na sake na bar ka. To ai ka rabo ni da wajen sai ka kama gabanka ka san dai ni ba yaro ba ne da sai an yi min jagora zuwa gida. Ala huci zuciyarka ranka ya dade, ya fada gami da mika mishi mukullun motar. Kai tsaye guest house suka shige, tsaki ya yi ya zauna gami da ciza lebe na jin haushin kansa na sakacin da ya riga ya yi, da bai tumurmusa yarinyar ba, ga Samir kuwa 12 ranshi in ya yi dubu ya faci sakamakon asarar da ya ja musu suna ji sunagani, sun saki wannan dama tasu kai ya cuce su. Banza kа cuce mu a kan wani dalili kankani, Allah ya isana. Ya kalle shi yana harararshi na cuce ka ko ka cuce ni da ka hana na lallasa mara kunyar yarinyar nan a kan son kudinka na banza? Mu yi mu tafi kada mu rasa kwangila ko? Key din motar ya dauka ya fice yana 'yan gunaguninshi na ta leko ta komar da abokinshi ya jaza musu. Zaune yake gaban mahaifinshi yana mi shi fadan sakarcinsa, "Ban da ma kai sakaraine har yaushe za ka tsaya fada da mace, macen ma da watakila ba ta fi sa'ar kanwarka ba, ni na rasa san da za ka yi hankali Abdulwaheed? Sunkui da kai ya yi Dadi ka bar ganin lefina wallahi yarinyar ce ba ta da kunya, haka kawai ta ja ta tsare min hanya, alhalin ni na riga ta isa wajen, to sai menene? Ba sai ka kauce mata ba faduwa ka yi idan ka yi hakan?" ya fan 6ata fuska Dad..... zai ce wani abu ya datse shi ya ishe ni bana son jin wani abu daga gare ka. Abin da kawai zan ce maka, ya kamata ka hada hankalinka ka san ka riga ka girma, har ma ka isa yi wa wasu fada, dan haka ne ma nake dada tunasar da kai akan maganar aurenka na gaji da ganin sa ban ga kaho ba, ya dan shafa keya yana murınushi, ka yi hakuri Dad komai lokaci ne, lokaci ne haka ne amıma kuma kai ka ki ka sa lokaci saboda kawai ka sa kanka a shashanci. Ya dago kai da niyyar magana, yi shiru kar ka yi min wata magana ko kana nufin ban san halin da kake ciki ba ne? na kyale ka ne idan tura ta kai bango zan yi maganinka. 13 Kamar ko yaushe ya dawo kasar cikin iyalinsa cike da nishiadi Haj. Kaltume ke gefenshi cikin isa da kasaita yayin da ta hannun daman nashi, ya ma fi soyuwa a cikin 'ya'yanshi ke gefen hannund amanshi ragowar yaran gidan kuwa suna warwatsc a falon tare da nuna farin cikin ganin mahaifinsu. Aunty Na'ima kuwa abokiyar zaman Hajiyan tana takure a gefen kujerar kuryar dakin ya rabawa kowa tsarabarshi kamar ko yaushe dai tsarabar 'yar gata Heedaya ta fifita, ya lura da kyau wannan karon ba ta murna da dokin zuwan nashi, ummina menene ya same ki ne' wa ya taba min ummina ne? ta 6ata rai Dad ba na sheda maka ba tun a waya na gani ne ka zo sam ba ka dauki wani mataki a kai ba. ya buda baki ah..., lallai kam shi kam wannan waye ya dakar mini ummi? Dady ni daiį kawai ina so ka sa a kama mutumin nan a nuna masa iyakarsa. A'ah ummi baa yi haka ba, ki dan bari zan ja kunnanshi, wai a ina yake? Dady ka san ko abin da ya yi min, mari fa Dady, ko ma menene a dai yi hakuri ummi. Haj. Kaltum ta katse shi a'a Alhaji a na me zai bugar nin yarinya a kyale shi? ai ya kamata a nunamishi kuskurensa. Ya yi murmushi, Kaltum ke nan ke kam wani sa'in kikan mance da shekarunki har ma ki kam biye wa diyar taki, ai babba da tsinkaye a ka san shi. Hajiya hakurin dai za a yi. Cewar Aunty Na'ima. Wani banzan kallo ta watso nata, me dauke da sakon ke fa ba komai ba ce sannan ta ce, "Ina jin dai a maganar nan dai ba a sako da ke ba ko?" cewar Hajiyan. Kai ta daga mata, to dan haka sai ki iya bakinki. Daga hakan ba ta kuma cewa komai ba ta ja bakinta ta rufe domin dai wannan abu ba bakon abu ba ne a gurinta, yara san babu tarbiyya sai abin 14 da suke so suke yi, ka fadi gaskiya a ga zafinka. To da kyar dai Alhajin ya iya shawo kanta. Misalin karfe hudu na yammaci Tahir El-Hussein ya iso cikin motarsa Hammer Jeep, kamar ko yaushe ya neme ta a layinta ya sheda mata isowarsa, ta san da zuwan nashi dan haka tuni ta gama kintsawa cikinleshin kasar Esphania (Spanish Lace) me matukar tsada ta yi kyau ainun ita kanta ta san hakan ba al'adarta ba ce sa ka mayafi don haka sai ta yafo shi a gefen kafadunta irin dai na 'yan matan zamani, ta bi ilahirin jikinta ta feshe da (palona picas). Sai kuma ta ja ta tsaya cak, sakamakon tunano karyar da za ta yi mishi ba zai yiwu ta bayyana mishi abin da ya hana ta zuwa Birthday Party ba. Saboda sanin zafin da yake da shi da kuma dan banzan kishi, kila ma abin ya juye kanta ba ta mancewa daga yamımacin jiyan har zuwa dare yana ta kiranta a waya amıma kuma sam ta ki dauka, saboda 6acin ran da take ciki, sam ba ta son bacin ranshi wanda muddin ya sani dole ne ma ta harzuko shi har ma ya shiga cikin damuwa ita dai kam tana son Tahir dinta so mara iyaka. Kwankwasa gilashin motar ta yi sannan ta ja ta tsaya domin ba ka iya hango na cikin motar saboda duhun gilashin. Kare mata kallo ya yi sama da kasa ta ko ina Heedayanshi ta hadu tana da kyau mai ban mamaki kai a tunaninshi ta zarce kowace mace a iya ganinshi. Ya bude murfin motar yana mai murmushi bayan da ya miko hahnunsa, harararsa ta yi gami da ba shi hanya ya fito fuskarshi dauke da annuri, suka jera zuwa Kayataccen lambun gidan (Garden) kamar yadda suka saba zama a 15 cikinsa, a duk lokacin da ya zo gurinta ya dube ta yana mai kashe mata zuciya. Heedaya kin sani cikin damuwa completely daren jiya, nakasa bacci na yi kiran wayarki kin ki fagawa why? Why Heedaya?" kin sani cikin damuwa Halisa kawarki da shi kansa failsa din wallahi sam lamarin be yi kyau ba, kin sani cikin damuwa kwarai da gaske. Ta dafe kai Tahir kai min afuwa na san ban kyauta ba amma akwai uzurin da ya hana ni zuw?. Menene shi kuwa? Ashe akwai abinda ya fi ni muhimmanci a gurinki? Ba haka ba ne Tahir. Haka ne mana na gode kawai daman dai kin yi niyyar gwada min iyakata ne. haba Tahir me ya sa kake fadar haka dan Allah ka bari kada ka sani cikindamuwa please... Tahir don't hurry. Ya harare ta cikin sigar so muddun kina so na hakura sai kin min wani abu guda, menene? Ta fada da sauri. Yauwa to zo ki ga da sauri ta kufce na ki wayon ta fada tana dariya. Ya dada tamke fuska shi ke nan je ki kawai ba tun yau ba na riga na soma fahimtar matsayina a wurinki, ya mike da niyyar tashi, dakatar da shi ta yi, Kа fahimce ni tahir ba haka ba ne. Ta dan harare shi dole man ka ce hakan bayan da ka sanı yin abin da ba na ra'ayi., Heedaya... ya ambata hakan cikinwani irin salo ya ci gaba kin san ina kaunarki ina yi miki wani irin so da ni kaina ban san adadinsa ba so why? Dan na gawda kaunata a gare ki za ki dinga ganin laifina? Ina sonki Heedaya son da baki ba zai iya fafarsa ba, kin kasance tauraruwa a cikin dubban taurari kowace mace ba a gabana take ba komai kyawunta komai matsayinta, ni dai na sani na kuma sheda Heedaya na kadai nake so. 16 Da irin wafannan zantuttuka ya kashe mata jiki har ma ta kasa katabus, ko dayake a yawancin lokuta ta kan kasa bijirewa umarninsa saboda tsananin kaunar da take mishi. ***** ***** ***** idaya Sa'ad Mohd, 'ya ce gurin Ambassador

Chapter 1 of 7