Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
7 / 8
mata rafar kud sababbi dal 'yan dubu rafa biyu yace, "Ga wannnan dubu dari biyu ki fara rikewa ko ince ki fara dasu, idan naga kin yi serious akan kasuwancin sai in kara miki wasu. Ta amshi kudin ta rungumje shi tana murna táre Da vi masa Godiva yace, "Muneeba ma zan bata amma ba yau ba don hakan shine adalci. Mota kuma zan saya mukun tare in yaso sai ta kayautar da waccan tsohuwar. 161 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria Ba haka Suwaiban ta so ba ta so ne ya saya mata ita kadai in yaso Muneeba ta ci gaba da hawa tsohuwar tata, ba ta san har yanzu soyayyar Muneeba na nan zaune dirshan a zuciyarsa ba. Da rana Muneeba na kicin dinta tana hada abinci me gidan sai waleeda ta shigo dauke da ledar nan ta leshin da ta aika wa Suwaiban, ta zo tana mika wa Muneeba. Ta amsa tana cewa,"Hala antinki bata kusa ne kika dauko kayan nan, kin ganki da barna." Ta duba cikin ledar lesunar 'ne guda biyu sai rafar kudl dauri biyu wadanda Mujeeb ya ba Suwaiban da safe. Ita da Kanta ta ba waleeda ta ce maza ki kaiwa mama tavi haka ne don Muneeba ta ga kudin da leshin ta san cewa ita ma yanzu miji ya dawo hannunta, ba ta san Munneba ta riga ta ganin leshin ba, kudin 'ne dai ta yi mamakinsa don ta san tabbas daga 162 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria J gurin Mujeeb suka fito don ga kamshin turarensa nan manne a jikin kudin, sannan ga sunan bankin da yakc ajiya nan rubuce a jikin takardar da ta yi rafin din kudin, kenan shin ya ba Suwaiba kudin. Ita kanta Suwaiba ta san kudin da kayan ba za su salwanta ba saboda Muneeba mutum ce sak ta kwarai shi yasa har ta iya ba waleeda ledar ita kuwa ta tabbata da hannunta kayan Muneeba da kudinnan suka zo to ruwa da iska ba zata maido su ba cewa zata yi bata gani ba kuma dole a hakura a hakan. Muneeba ta bar abin da take yi ta riko hannun Waleedda daya hannun ta riko ledar kayan tayi sallama ta shiga dakin suwaiba, dama suwaiban na tsaye ta window tana leken waleeda tun shigowarta har fitowarsu, da ta ga zasu shigo shine tayi saurin komawa bisa kujera ta zauna ta ci gaba da kallon da ta kunna. 163 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria Muneeba ta mika mata ledar nan tace, "Hala ba kya kusa ne Waleeda ta fita da ledar nan? Ta rike ledar tare da sauke ajiyar zuciya tace, "Kai kai lallai yarinyar nan sai na buge ki, ina can na shiga bayi bisa gado ta dauko ta kuma har da kudI masu yawa a ciki, tabdijam ai da kin fita dasu wani ya kwace da دو babanki dole ya sake bani wasu.' Munceba ta suri Walceda tana murmushi tace, "Sai dai kam ya sake baki wasu, amma ba zaki dukar mana ita ba, ko ni ina baki nawa sai inci girma nan gaba a bani. Munceba ta fadI hakanne don Suwaiban ta san ba ita kadai aka ba kayan ba in ma ta yi hakan ne don bata haushi to ba ta isa ba taga hushinta ba. Suka fice da walecdar suka barta cikin zurtin tunnai, "Lallai namiji ashe munafiki ne ashe dukkan su ta saya musu kudinnan kila ya bata shi da yace ba yau zai bata ba, lallai sai ta canza wata salon takun sabuwar kisisina a gidan nan in ba haka ba matar nan sai 164 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria dai tayi ta bata haushi a madadin ita ta bata. **** ***** **** Suwaiba kam ta sami kan miji irin yadda ta ke so yana yi mata sai dai duk abin da zai bata gurin bokaye take kaiwa da sayen magungunan mata suke karewa, bata jin kyashin kashe ko nawa ne ta saya kuma ta fi gane ta sayi wanda za ta tura a gabanta, a ganinta ya fi yi mata aiki cikin gaggawa. Don ko kudin da ya bata ta fara yin jari, bata yi ba dubu dari ta ba Aina'u aka kawo mata dan china kwalba biyu. Munecba idanu ta kawo ta zuba musu shi da Suwaiban, farin cikin ta daya yadda bai juya mata baya ba ita da 'ya'yanta yana sonsu fiye da komai, yana mata hidima ita da su dan basu rasa komai ba, illa ita da take hadiyar abubuwan da yake yi mata duk ranar da aka ce Suwaiba ce da girki to ya din rawar jiki kenan yana nan da Suwaiban 165 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria C sam baya son ya ga ta bata rai yanzu sai ya susuce yayi ta lallashinta ita kuma tana dada botsare masa. Babbar matsalarma yadda sam ba ya nuna mata zumudin kasancewa da ita, wani lokacin ma sai yayi fiye da sati biyu bai yi auratayya da ita ba alhalin tana kallonsa yadda yake rawar jiki da Suwaiba har dawowa yake da rana idan abin ya ciyo shi. Duk ta kawo idanunta zuba masa bata taba yi masa korafi ba, hatta ita Suwaiban ta rasa yadda aka yi Muneeban bata nuna jin zafinta, ko a jikinta sabgar gabanta kawai take yi. Maganar fara aikinta dama Mujeeb yace sai ta yaye su Hilal to Allah cikin ikonsa tun kafin su shekara suka fara tafiya shi yasa suna cika shekara ya yaye su. A lokacin ne takardar daukanta aiki ta fito, aka dauke ta aiki ta fara zuwa sai tana barinsu Bilal gurin Baba Hajjo fita aikin da take yi ne yake rage 166 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria mata radadin wasu abubuwa da ke faruwa a gidan nasu. Ko ba komai tana samun natsuwa bisa 'ga irin tsananin kauna da Mujeeb ke nunawa yaranta ta yadda ko gida ya dawo ba ya iya shiga dakinsa in ba ya gansu ba, har hakan na kunada zuciyar Suwaiba wani lokacin sannan gashi Kiri-kiri Waleeda ta gujeta ta koma dakin muneeba saboda su Hilal don ko bacci tayi idan ta farka ta ganta a dakin Suwaiba ta dinga ihu kenan ko mai dare sai an kaita dakin Muneeba. A wannan lokacin ne za'ayi bikin Isah, ya kamala karatunsa na digiri har Mujeeb ya sama masa aiki a nan Gombe, kasancewar matar da zai aura iyayenta 'yar asalin Dukku ne su ma aiki ne ya kawo su Gombe kuma Dukku za'a daura auren suyi shagalin biki a can sannnan a kawo amarya Gombe gidan da Mujeeb ya saya musu, shi yasa Mujeeb ya saya musu, shi yasa Mujceb yace aje can Dukku bikin idan 167 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria aka kawo amarya sai a dawo a karasa bikin a Gombe. Ranar alhamis Suwaiba suka wuce Dukku ita da yaran duka tare da mai girkinsu da karime da kuma Baba Hajjo, ita kuma Muneeba zata biyo su washe gari ranar Jumna'a idan ta tashi daga aiki tare da Mujeeb za su taho don shima sai Juma'ar zai tafi. Wani katafaren gida Mujeeb ya gina musu a Dukku mai dauke da bangarori manya guda uku nasa daya na Muneeba daya na Suwaiba sai na Goggo a can karshen gidan hade da na saukar baki. Baba hajjo da karime suka bude bangaren Munecba suka shiga tare da su Waleeda. Ba su zauna ba suka shiga gyaran gurin har sai da suka ga komai yayi tsaf sannan suka kunna turarukan wuta ko ina ya dauke kamshi kamar yadda suka ga tana yi. Washe Gari Munccba suka iso tare da Mujeeb amma kowa a motarsa, 168 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria ita a sabuwar Peugeot 307 shi kuma a tasa Mercedece C350. Ta Suwaiba na gida an rufe da tamfol don har yanzu ta kasa maida hankali ta koya. Da yake a satin aka saya musu motar ba kowa ya sani ba shi yasa 'yan uwa na ganinta da motar suka soma taya ta murna har wata cikin dangin su Mujeeb tace, "Ai Wallahi ilimin zamani na dadi kuma da naga mai ilmi ya bambanta da wanda bai yi ba, yanzu dubi daga fara aikinki har kin sayi mota inda baki yi iliminba ai sai dai ki kalla gurin masu ilimi." Muneeba tayi saurin cewa, bani na saya ba maigidan ne ya saya mana Suwaiba tata na gida don bata gama kwarewa bad a itama kunga tata. Matar tacc, "oh, kinga ikon Allah albarkacin kaza har kadangare kan sha ruwan kasko ke ai kin dade da hawa mota Allah dai yasa 'ya'yanmu a danshin ki komai naki acan-acan masha Allah." 169 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria Nan fa Suwaiba ta kullu iya wuya dama abin ke hana ta shiga cikin dangin Mujeeb kenan sun dinga yaba mata maganganu kenan sun fi kaunar Muneeba saboda saye su da abubuwan alkhairi da take musu, ita kuma ta sha alwashin in har sai ta basu abin alkhairi za su so ta ba tunda mijinta na sonta babu ruwanta da su. Duk wani abu na hidimar bikin nan a hannun Muneeba Mujeeb ya damka shi, don hatta lefe ita ya ba kudl yace ta hado masa, da ta nemi rakiyar Suwaiba don su je kasuwar tare sai cewa tayi tana da abin da zata yi taje kawai. Makullan bangarena na nan Dukkun duk suna hannunta, anan ne suka aje abubuwan da za'a bukata na hidimar bikin, sannan Munceba ma can ta tare kacokam sabo da Jama'arsu duk nan gurinta su ke makil. Takaici bai gama kashe zuciyar Suwaiba ba, sai da tag a irin suturun da Muneeba ta dinga sakawa tana fita, 170 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria C hatta Waleeda sai da Muneeba ta dinka mata kaya masu tsada kala shida, lesuna biyu atamfa super guda biyu sai shaddoji gezna da aka yi musu anko ita da su Hilal, har da 'yan hulunan dube aka saya musu yaran sunyi kyau tamkar ka sure su kagudu don kyaun da suka yi cikin malum-malum din da aka yi musu. Ita kuma Waleeda stone work aka yi mata a shaddojinta da lesunan, iri daya ne da na Muneeba. Suwaiba ta ji takaici kwarai don shawarar su ya nema cewa su zo ya kaisu shago su zabi duk irin kayan da ske so sai ita Suwaiban tace a ba kowa kudinsa ya sayi abun da ya ke so da yaki yarda sai Muneeba tace yayi Hakuri ya ba kowa kudin sai su sayi zabin a ransu ke so. Dubu dari-dari ya basu yaba yaron kowa naira dubu ashirin ashirin na waleeeda ma Muneeba ya ba yace ta saya mata kaya masu kyau don ta iya zaben kaya. 171 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria Nan ma Suwaiba ta ce ita sam a bata kudin 'yarta don ta gaji, mulkin mallaka ake mata kyauta da dan kishiya. Muneeba ta mika mata kudin, yace kuma idan an sayo a kawo masa na kowa ya gani don ba ya son karabitin kaya. Muneeba bata bi ta kanta da taje kasuwa duk sayayyar da tayi wasu Bilal tare da waleedan tayi musu bata yi la'akari da cewa suwaiba ta amshe kudin sayayyar waleedan ba. Sai gashi ita suwaiba bata sayawa Kanta komai ba ball ma waleedar, tsofafin kaya ta saka haka waleedan ma dake bangaren Muneeba tsoffin kaya ta bada tace a saka mata wai basu sami dinki ba sai telan ya kawo alhali ta. kai kudaden nasu sayayyar wajen bokaye. Sai kawai ta ga Waleeda cikiin sababbin kaya kuma tsadaddu, duk sai ta tsargi kanta ta ji ta muzanta har ta ma kasa hada ido da ko sahu da Muneeba, 172 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria don sai ta zamo tamkar yar aikin gidan, don 'yan aikin ma sun fita shiga mai kyau, Muneeba din kuma kala bibbiyu tayi masu karimen da baba hajjo da mai girkinsu na cin biki. Hatta su jume da baba mai gadi sai da saya musu shaddoji guda bibbiyu ta basu, tare da kudin dinki shi dai Mujeeb sai yaji suna gaya masa tare da yi masa godiya, anan ne ya fahimci alkahairin da tayi musu. Suwaiba saboda haushi da bakin ciki bata bari yamma tayi su bi ayarin da za'yi na tafiya da amarya ba, sai ta bi motare da za'a fara wucewa da su baba hajjo da yara tare da ladiyo, suka wuce Gombe domin yin girkin da za'a tarbi jama'a. Tu da suka koma gida suwaiba bata sake lekowa waje ba, balle ta baki, har aka kawo amrya bata fito an tafi da ita ba saboda tsananin haushin Muneeba da ta ke ji. Da su muneeba suka iso ne ta shigo dakin nata tace ta fito za su je 173 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria gida amarya sai tace su tafi kawai bata jin dadi. muneeba tace Allah ya sauwake ta debi jama'a a motarta suka tafi. ****** ******* ****** Shekar su bilal daya da rabi a lokacinn muneeba tana dauke da ciki wata biyu wannan karon tsananin laulayin da cikin yzo mata dashi ne ya fallasa ta kowa ya san tana da ciki har Suwaiban ta san cikin. Hnkalin suwaiba ya tashi Matuka ganin har yanzun a wani labarin ciki a tattare da ita, ballle yadda taga hankalin Mujeeb gaba daya ya karkata wajen kula da lafiyar Munceba bashi da wani sukuni sai tattalin ta. Wannan karon ma sun sake fantsama gidan bokaye don su so suke ko ta halin yaya muneeba ta bar gidan nan wutsiya zage kuma ko da mutuwa ce zata zama sanadin sanadiyar barinta gidan suna maraba ita da hajiyarta. 174 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria Suwaiba ta isa gidan kawarta Aina'u a wata yammaci, sun kule suna ta neman matsalolin gidan mijinta anan suwaiba ke tamabayarta ayauawa ina tabilet din nan da kika ce zaki bani masu kara girman nono don kin san tunda na yaye waleeda nawa sun koma kamr kokuma duk sun tamushe dama knsan básu da girama, ita ko tsinnanniyar har yanga take tana dada karakada masa su, can yake lalacewa gurin kallon su tunda ta lura yana sonsu. Aina'u ta mike ta bude wadrob dinta ta dauko tabilet tanacewa, "Aini autarki nake gani da har kuka zauna da mace mai dauara zani ta hannun dama ta fiki da wasu abu wanda kod Allah be wadata ki dasu ba zaki iya siya a kasuwa, in farin ne kawai mai in nonuwan ne akwai kwayoyi har da ne shafawa, in ma kwankwason ne tafi ki da su to ai duk akwai magungunan da bature ya kawo masu kara musu girma. 175 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria Don Allah dube ni? Da can haka nake? Ta yi juyi tana girgiza jikinta. Suwaiba ta girgiza kai ta ce, "Ba haka kike ba da ke siririya ce ba wata shef din arziki." Ta yatsina baki, "Ai dana lura da cewa mijin mai gane-ganene kuma na san abubuwa dake jikin mace, shi yasa na tashi tsaye ban zauna ba na tashi na siyo sinadaran kara jiki da kuma gyara su da kuma kara su to ba gashi na dawo irin macen da yake soba, ai mazan nan idan kika zauna sai wata ta zaune miki su. Kafin suwaiba ta bar gidan sai da ta bata magunguna na kara nono tare da maganinta da ta zo karba na China dan matsi tun ma a gidan Aina'u ta fara hadiyar na nonon. Tun daga ranar Suwaiba ta fara shan maganin sai fa nonuwa suka yi bula-bula gunin ban sha'awa har sai da Mujeeb yayi mata magana yake cewa ko ciki gareta tace bata da komai. 176 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassań Zaria Muneeba kanta sai da ta dinga mamakin canzawar jikin na suwaiba ta cika fam ta yi bul-bul nonuwa sun cika kirji, kowa ya ganta sai ta bashi sha'awa, sai muneeba ta dauko ciki gareta ita ma har take wa Mujeeb tsíyar ita da suwaiba kila lokaci daya za su haihu zasu yi masa rubdugu kowa na jego ya kada baki yace,"To meye idan kuka haihu lokaci daya? lyaka idan naga ba zan iya hakuri ba inyo amarya ku ku je ku ji da jegon ku ni kuma naje naci amarci dan ma ba zan aje ta gida daya da ku ba, gida daban zan saya mata. Munceba tayi shewa ta ce, "Aini dai zaka birgeni biyu ya kamata ka auro rana daya kaga biyu na jego biyu na cin amarci, ka leka nan ka leka canmu har hutu za mu dauka muei girma mu bar maka su duk ranar ga gishiri va sallace akan kaza sai ka neme miu, mu huma sai mun gasa masa gyada a tafin hannu idan ka dawo." Dariya sosai yayi sannan yace,"yi hakuri uwargida sarautan mata 177 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria bata ma da ciki balle tun yanzun ku fara tunanin yadda za su gasa min gyada a tafin hannu." Wata matsala da Suwaiban ta soma fuskanta shine wani ruwa mai yaukin da ya ke fito mata ta gabanta wanda kuma yake da wari da kuma doyi wanda sam bata iya zama sai tayi kunzugu da audugar mata in ba haka ba to duk inda ta zauna sai ya jike, gashi ruwan na da dan Karen wari duk sai gurin yayi ta wari. Idan kuma suka yi tarayya da Mujeeb gurin azabar zafi yake mata tamkar zata mutu, haka take ji daurewa kawai take yi, sannan yana mata korafin warin da yaji gabanta keyi a duk lokacin da ya kusance ta. Sai tana nuna masa ita sam bata jin warin alhalin ita kanta abin na damunta har yana son ya fi kartinta. Abu fa yayi tsanani har sai da ya kwantar da ita don tafiya ma gagaranta yake yi. Mujecb ya tsareta da tambayoyi,"so nake ki gaya mun 178 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria gaskiya me kike sawa a gurin nan ne yake wari ga kuraje duk sun fito a gurin ya tsatstsage yayi ja." Ta soma indainda tana hawayen azaba tace, "ni fa babu abin da nake sawa wannan ciwon ne kawai." Ya bata rai". "shikenan tunda ba za ki gaya mun ba in mun je asibiti su za su gano me ke damunki kuma zasu gaya mun, kuma zasu gano ko meye musabbabin ciwon ni kam bana raba dayan biyu ko ire-iren magungunan da kike mannawa don ki mallake nine sakamakon ya fara bayyana a jikin ki, ko kuma bin bokayen ki har kina basu tukwuicin kanki gurin da ya zamto halaliya ga mijin ki ne ya janyo miki wannan bala'in, nayi nadama da danasanin sake amince miki da na yi har na dawo ina tarayya dake alhalin na san ba za ki iya daina halinki ba, Ya daga hannu yana rokon Allah,"Ya Allah kasa wannan cuta da ke gabanta bata goga mini ba, in kuma ta goga mun ya Allah ina rokonka da 이 179 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria kasa ban goga mai baiwarka Muneeba ba don bata san hawa ba balle sauka akan wannan ciwon." Haj. Harira da ta iso ta ga yadda gaban 'yarta ya koma kuka ta saka mujeeb yana bata hakuri "kiyi hakuri Hajiya laifinta ne da ba ta jin magana tunda na hana ta saye-sayen magunguna nan gaya mata suna kawo ciwon daji amma bata ji ba yanzu wa gari ya waya? Sannan Suwaiba har boka ta tabа bashi kanta duk don ta mallake ni, gashi nan bata yi nasara ba ta sayo wakanta larurar da na sani. Haj. Harira ta fitittike tamkar batasan labarin ba ta cc "Don kuma lalura ta same ta sai ka hada mata har da sharri? Suwaiba ce zata je ta ba boka kanta kai wane algungumin ne ya gaya maka? Ya nuna Suwaiba yace, "Babu algungumin da ya gaya mini, gata nan da bakinta ta fada har kunnuwa na suka ji. ki tambaye ta gata nan, a dalilin 180 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria hakan da naji ne har na fadl na karye aka kaini aibiti. Suwaiban ta sunkuyar da kai kasa yin magana Haj. Harira ta hauta da sababin karya. "kin yi shiru kina ji ana miki sharri da yaushe haka ta faru?" Suwaiban ta kallí Hajiyar tata ce, "Ni fa ki daina min fada alhalin kin san komai, inma Ce keda Goggonsa ne kuka kaini gurin bokan har ya yaudare ni ya biya bukatarsa? Da baku kaini ba zan je ne? ai duk zunubin da na samu tare aka raba mana da ku don ku kuke yi min jagora." Bakin cikin yasa Mujeeb ya fice ya bar musu dakin don ba zai iya jin wannan irin ballake-ballake da suka yi ba kuma wai duk da uwarsa a ciki. Haj. Harira ta fita ta nufi' dakin Goggo Rahin ta same ta a kwance ta hau bala'I. "Au kenan kina kwance ne yarinya na can na fama da bala'in ciwon da har da ke aka yi sanadin da ya same ta? Eh, lallai duniya ba gaskiya, sannan ga dankin can ya ta sata gaba da 181 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria fada yanan cewa ai ya hanata wai yanzu wa gari ya waya. Goggo ta tashi zaune tana cewa, "Au ni kike son inje in yi jinyarta? Ai bani nasa ta zuwa tana sanye sanyen magunguna a gabanta ba ta na mannawa dan ta mallake min da ba, saboda haka kece zaki je ki jinyarta don ke kika haifi abarki." Haj. Harira tayi shewa ta tafa hannuwa tace, "A yau ne zaki ce haka? Mallakar danki kuma sau nawa aka yi? Ina ce ke da kanki kika fara ba da kudin da aka kai gurin boka don a mallaki dan naki? In yawon bin bokayen ne ai tare ta ruga ni da ke ko kin manta ne in tuna miki? Tunda wai kenan yanzu kin tuba a cewarki? To bari in tuna miki wani sirri da Kila kin manta vana lullube a fatala na kuma zan iya bankade shi dan naki ya ji. Wai Mujeebu ne yake cewa Suwaiba ta ba boka kanta don ta mallakeshi, to zan gaya masa ba Kanta faru ba ba ita kadai ta fara hakan a duniya ba kuma 182 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria 3 ba a kanta za'a daina ba, wasu matan sun dade da aikata wannan sabon kuma sun mallaki miji tun kafin shi Mujeeb din yazo duniya zan kuma iya bankada masa yaji ko su waye don ya sassauta ma 'yata a ganin da yake mata na wadda ta aikata babban zunubi don ba kanta farau ba, anyi da yawa a bayanta. Goggo ta mike tsaye ita ma suka fuskanci juna sosai da Haj. Harira sannan tace, "Au bankade-bankade ki ka zo yi? To bari ki ji in gaya miki Wallahi muddin wani labara na da ba kowa a duniya ya sani sai ke ba idan ya shiga kunnuwan dana sai na tozarta mutuncinki Wallahi" Haj.Harira tace. "Ai ni nan da kika ganni bani da wani sauran mutunei nawa da nake tattali. balie har invi tattalin na wani, kece kike ganin kina da mutunci har kike tsoron a bankade shi, to bari ki ji Wallahi yau ba sai danki yaji naki sirrin boyen don ya san 183 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassah Zaria bani dadiyata bane kadai mu ke da abin fada ba. Ta kama hanyar fita a fakin, ita kuma Goggon ta yo hanzarin biyo bayanta, amma kafin ta kai gareta sai jirin da ya mamaye idanunta 'ya kada ita, ji kake tim a kasa. Haj. Harira ta dawo da baya ta rike ta tana sallallami, yayi daidai da foitowar Mujceb daga falonsa, zai fita zuwa Sallar la'asar. Yana jin sallallamin Haj. Harira a dakin Goggo sai ya shigo ya iske abin da ke faruwa Goggon ce a kasa har bakinta ya jirkice yana dalalar miyau. Cak ya sure ta ya fita yasa ka ta a mota ya kira Muneeba suka wuce asibiti. Gado aka ba Goggon aka daura mata karin ruwa. Likita yayi masa bayanin ta sami mutuwar barin jiki don, bakin ta ya jirkice guri daya. Hankalin Mujeeb ya tashi sosai akan ciwon Coggo sannan ga Suwaiba dole ita ma asibitin ya dauke ta ya kaita 184 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria asibit. Ana yi mata gwaje gwaje aka gano ciwon daji ne ya kama gaban na ta wato (cancer) a dalilin magungunan da ta ke amfani da sun a matsi masu illa ne ba ta sani ba. Wata matsalar kuma nonuwan ta sai suka fara ciwo, wasa gaske sai gasu sun yi suntim har bata iya saka rigar nono, suma ana yin gwaji aka gano dajin ne ya kama su a dalilin kwayoyin da ta dinga sha musu kara girman nono. Goggo kam ta sami sauki har an dawo da ita gida, amma bata iya tafiya sai da sanda bakinta kuma bai dawo dai-dai ba ya riga ya nakasa. Nonon Suwaiba ya tsananta da ciwo har ta kai ga ya huje yana zubar da ruwa kuma duka biyun, kafin wani lokaci har ya fara tsutsa dole aka yi shawarar sai an vanke su in ba haka ba zata iya rasa ranta. A ranar da likita ya fadı hakan kwana suka yi kuka ita da Hajiyarta da ke jinyarta don kuwa dakin da take babu mai iya shiga sabo da wari, shi ma 185 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria gaban nata har yanzun warin yake yana fidda ruwa. Anyi nasarar yanke nonuwan gaba daya, suna nan a asibitin ana yi mata gashin gurin. Shi ma gabanta sai ya fara fitar da tsutsa wasu irin farare. Wannan al'amarin ya girgiza Mujeeb, Haj. Harira kuwa komawa tayi tamkar tababba in banda sambatu ba ta aikin komai. A wannna lokacin ne Muneeba ta haifo 'yan biyunta mata masu matukar kama da ita, ko da yake Mujeeb yace sam bai yarda ba da shi yaran suke kama, tunda ita ma Muneeban dashi take kama. Labarin haihuwar na shiga kunnuwan Suwaiba da Hajiyarta sai suka ji tamkar za su mutu sabo da bakin ciki, sambatun Haj. Harira sai ya dada karuwa har yada labarin haihuwar ya zauna daran a bakinta kowa ta gani sai ta gaya masa tana cewa kunji Muneeba ta sake haihuwar 'yan biyu ko? Daga fara haihuwar ta har ta wuce Suwaiba, 186 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria 'ya'yanta hudu yanzu suwaiba ko Kwaya daya dayar ma ta kwace ta rike wannan ai zalunci ne don an ga ciwo ya kama suwaibar." Muneeba suna dawowa daga asibitin su Bilal suka haye gadonta suka kewaye jariran suna kokarin daukarsu. Tana shigowa ta gansu tayi saurin sauko dasu daga gadon, ai sai suka saka ihu gaba dayan su, Mujeeb na jin ihunsu ya shigo da sauri yana tambayar abin da aka yi musu. Tace, "wai yaran nan za su dauka ina zan barsu ko wuyar da na sha ban manta ba." Ya dauko su dukansu ya rungume yana lallashinsu tare da cewa, "kuyi hakuri wadannan yaran na momi ne, ku bari zata sake haifowa Dadi nasa irinku masu kama ada ku sai in baku ku dauka kowa dava ko?" Suka gyada kai a tare. Ya dan dubi Munceban yace, "Na lura yaran nan dukansu za ki dinga yi akan 'ya'yan nan, wato kinfi son sababbi akan tsofaffi ko?" Tace, "Wannan 187 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria kuma ai kai ka raba, tun a haihuwarsu Hilal din kace in fara haifo maka naka sai in hifo nawa daga baya sai kuwa gashi Allah ya bani nawan ba dole inyi tattalinsu ba, kowa yaji da nasa" Ya dubeta, "Au haka ne? to shike nan kowa ya rike nasa za'a ga su waye 'yan gata." Tana Dariya tace, " Ai kuwa za'a ga 'ya'yan gata, yanzu ma kwashi naka 'ya'yan gatan ku tafi don kada su sake mini laifi ace na daki 'ya'yan gatan Dadi." Yana mikewa suka cangara ihu suka makale shi suna fadin Dadi! Dadi!! Dadi!!! Kowa ya daga hannu sai a daukeshi. Ya dauke su ya fice yana jin Muneeba na masa dariya tana cewa, "Haba wa ai mutum zai sha wahalar nasa `ya yan gatan indai su Hilal ne, sai sun hanaka fita otis, ni dai 'var kallo ce. Yaran an canza musu suna Hassana da Hameeda, Hussaina kuma Haneefa taron suna kadan-kadan aka yi shi sabo da majinyata da ke gidan ga 188 ا WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria Goggo a kwance, ga suwaiba ita ma an dawo da ita gida don an gama gasa ramin ciwon ya kame, matsalar tsutsotsin da ke fita a

Chapter 7 of 8