Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
6 / 8
"Kinga uwar bari ne yanzu? Ai 134 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria na dauka kina da juriyar da zaki iya zama haka nan tunda kina samun komai na jin dadin rayuwa? Kije zan neme ki duk lokacin dana shirya? Ta marairaice "Ni dai yau zaka kaini don Wallahi na gaji da juriyata ta kare ni ba dutse bace ni mutum ce kamar kowa ina bukatar samun natsuwa kamar yadda kake samu kanada madafa. Ok laifi na kike gani ko naki? Dama ni ba zan damu ba tunda ina da inda zan kai bukata ta, ke dinma da kinso ai zaki iya zuwa gurin abokin masha'ar na ki don kila baki tuba-ba". Ta soma matsar kwalla munafunci don girman Allah kabar tuna mini wannan mummunan al'amarin Wallahi nayi dana sani ya fi cikin Kwando kuma Wallahi tallahi bantaba ba kowa kaina ba in ba wannan kaddarar ta auko kaina ba saboda wata biyan budatar duniya amma nayi nadama ba zan sake aikata hakan ba ina rokonka ka yafe mini na tuba zan hakura da matsayi na na rashin 135 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria so na da baka yi zanyi ta addu'a har Allah ya karkato da zuciyarka gareni kamar yadda zuciyarka ta karkata ga Muneeba tana maganar tana hawayen munafurci yazo ya dafa kafadarta ya shiga lallashinta abinka ga mata da miji al'amarinsu sai Allah nan da nan ta karyar masa da zuciya yaji tausayinta dama hakan take so ta faru" Kiyi hakuri ki bar kukan na san ba halinki bane bin maza tunda zan iya bada shaidar na aureki a cikakkar mace amma bansan rudin duniyar da ya kwashe ki har idanunki suka makance kika ba Boka kanki ba in kinyi haka ne don in soki fiye da kowa kin zalunci kanki don ni bance miki bana sonki ba, sannan ina kamanta adalci a tsakaninku da yar uwarki wani lokaci ma ita ce ya kamata tayi korafi akan irin fifikon da Goggo kesa ina nuna miki fiye da ita amma duk baki gani ba shin wane irin so kike son in nuna miki bayan wadda nake nuna miki ke da 'ya'yanki. 136 a WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria Ajiyar zuciya ta shiga yi "Ni bance ka so ni fiye da kowa ba, ina dai son ka dinga yin adalci ne a tsakaninmu akan komai ka sakani cikin duk wasu al'amuranka kamar ita, kayarda dani tamkar yadda na ga kana ammanna da komai na ta nayi maka alkwari zan دو canza duk wasu dabiu da baka so". Yaja numfashi ya sauke sannan yace "Kayya Suwaiba kinfa riga kin 6ata rawarki da tsalle kina ganin da gaske kike kuma kinyi alkwarin zaki watsar da makamanki za ki rungumi gaskiya da samar da zaman lafiya da zaman amana a gidan nan? Ta gyada kai nayi maka alkawari in har ba zaka sake juya min baya ba don ina tsananin sonka in kishinka sosai inhar baka mayarmin da martanin soyayyata to komai zaí iya faruwa ina fatan ka canza kamar yadda nima nayi maka alkawarin canzawa. Ya ce"Duk abinda ya faru laifinki amma mu manta da abinda ya faru mu fuskanci abinda ke gabanmu ki 137 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria tabbata kin rike amanata dake hannunki ki tsaremin kanki bana son na sake kamaki da yiwa aurenmu kwamacala ki ji tsoron Allah ki ji tsoron duniya in ba haka ba to zan dauki mataki da ba zai yi miki dadl ba saboda haka sai ki kiyaye tayi masa alkawurra masu dama amma duk na bogi ne saboda ita da kanta a zuciyarta tana tunanin anya kuwa zata iya kyale bin bokaye don anan ta ganin sai da taimakon su take samun wasu nasarori a gidan aurenta. Shima a nasa 6angaren yayi mata alkwarin canza yanayin zamantakewar su tare da yin adalci a tsakaninta da Muneeba bayan Sallar Magriba ne yayi kiranta a waya yace ta shirya gashi nan dawowa daga masallaci za su je asibitin da saurinta ta tashi ta shirya Walceda ta shirva kanta ta zauna jiransa yayi sallama ya shiga dakin nata a falon ya sameta tana sanyawa Waleeda rigar sanyi yarinyar sai Ihu take yi ya isa ya dauki yarinyar yana tambayarta me mamana tayi miki kikasa min ita kuka? 138 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria Tace "Wai rigar sanyi zansa mata shine bata so sai dai a kyale da 'yar karamnar riga ga da nomoniya" Ya amshi rigar yana Karasasa mata tare da tambayarta "Wa ye ya doke ki? Ta nuna Suwaiba "Anti ce ta doke ni takI goyoni, ya dorata a bayan Suwaiban yana cewa "Oya dauko zani ki goyata ko nima in rama mata dukanta in rama maki?. Ya tambayi Waleedar ta gyada kai ya kai hannu ya dan bugi bayan Suwaibar yace "Na rama miki yi shiru ki kyale Anti ba. zan goya ta ba". Suwaiba ta sauko da Walecdar daga bayanta ta dora a bayan Mujeeb din tana cewa "Sauko min a baya na shi sai ya goya ki tunda nima yace ba zai kara goya ni bа". Ya manne yarinvar a bayansa yace "Oya sa hijjabi kizo mu tafi bari in kaita gurin mamanta ta zauna gurin kanninta har mu je mu dawo". Taso a'a sai kuma ta tuna da yakin zamba da zata soma a gidan sai ta fasa ta kyale 139 ta WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria shi yana rungume da Waleedar yar kimanin shekaru uku ya shiga dakin Muneeba ya sike ta gabansu Hilal da ke zaune suna koyon zama cikin kekunansu tana basu (Prisocream). Ya aje Waleedar yabi yaran yana sumbatarsu yace "Suna kuwa shan abinnan sosai kuwa? Naga sunfi son Madara? Ta soma ba Waleeda da ta wangame mata baki wai itama zata sha sannan tace "Suna sha sosai saidai sunfi shan madarar don tafi yi musu kama da Nono shima wannan din zasu saba. Bilal ya soma miko masa hannu yana zillo don ya daukeshi ya ciro shi daga keken ya daga shi sama yana masa wasa sannan ya maida shi cikin keken ya dubi Muneeba yace "Ga yarki nan ta zauna guren kannenta za mu je asibii da Suwaiba". Tace Subhanalallhi bata da lafiya ne ban sani ba" yace "Lafiyarta kalau gwajin nan za mu je mu yi yau ta ga dama bari ba shegiya bace tana da ubanta Munceba tace sai kun dawo Allah ya tsare ya jishshemu 140 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria alkhairi yayi dabara ya fice don kada yaran su ganshi sun yi saboda da shi sosai indai ya shigo zai fita muddin suka ga fitarsa sai sun yi kuka. An yi wa Suwaiba gwajin H.I.V sakamako ya fito nan take bata dauke da cutar (NAGETIVE) suka gani a jikin sakamakon nata ". A gaban likita tayi tsallen murna ta rungume Mujeeb tana murna likitan shi ma taya ta murna yake yi Mujeeb ma yayi murna da ganin sakamako amma zuciyarsa ta kasa natsuwa sai da ya sake kaita wasu asibitoci har guda biyu bayan wannan aka sake yin mata wani gwajin duka sakamako iri daya ne bata dauke da cutar. Daga asibiti na karshe sun fito zasu taho gida, sai dabarar yadda za ta yi ta cusawa Munceba Haushi a wannan fita tasu tamkar yadda take jin zafi idan suka fita ta zo mata ta dube shi ta ce Don Allah mu dan biya gidan kawata Aima'u bata da lafiya tun rannan ta kirani yayi magana ba tare da ya dubeta 141 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria ba Dare fa yayi za ki ce mu je gidan mutane dubi agogo yayi mata nuni da agogon motarsa ta duba ta ga tara saura minti takwas tace ai dare bai yi ba tunda goma bata yi ba don Allah ka yi hakuri mu je tunda akan hanya ne ya ce יי "Shi kenan sai mu je tunda kin matsa. A harabar gidan ta barshi ta shiga ta tura masa mijin Aina'un don suyi hira duk cikin shirinta nason su dade wanda shi sam bai dago wannan shirin nata ba. Suna can sun kule a dakin Aina'un suna kullawa da kitsawa ta yadda Suwaiba za ta zargo zuciyar mijin nata a wannan karon ta hanyar Kissa da kisisina ba wai sai ta hanyar boka ba ko malai ba. Aina'un ta kara da cewa "Ke sakarya yanzun an daina yayin zuwa gurin teacher don basa wani tasiri kiyi mai gaba daya ne ki tsaftace shegiyar in zaki sha giya ki sha ta dubu ki yi tatil sannan ki ki kanainaye shi da kisisina na iri iri sai kifi samun kansa amma 142 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria yaushe ne za ki tsaya gurin ticocin zaure ai gara kiyi mai gaba daya haihuwa da 'ya'yan hanji sukayi shewa suka tafa suwaiba tace shi ya sa kike burgeni kin hana ko wace shegiya shigowa gidanki ta gidan da kika samu ma kin yi waje road da ita ta gudu ta bar ladanta 'ya'yan har yanzu suna can makarantar kwana?. Ta yatsina baki tace dukansu suna can don ba zan iya jidali ba sai hutu suke zuwa, shima hutun can kauye nake kada su gurin kakarsu a cewarsu wai can ya fi dadin zama munafukai ai ba zà su iya zama gidan nan ba don aiki kadai ya ishesu hana masu aiki yin komai na ke yi su suke yi shi ya sa wuya ke korarsu su tafi can karata su bare min daga ni sai mijina da `ya'yana na biyui, wadda ta vave ma tana can nasa ya mayar mata don ba zan iya rainon dan kowani mata ba na ma gaya masa. Suwaiba tayi shewa tace, "haka nake son ki tawa kina birgeni kuma 143 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria dole ya yarda ya maida ta? Ta kara yatsina baki saboda dabi'arta ce yin hakan tace, ba dolen shi bani umurni, kawai nake bashi tamkar uwa da danta da na ce haka za a yi iyakarshi yace to gimbiyata. Suka saki shewa suka tafa Aina'un taci gaba da cewa, "shima ya san sauran idan ya ki bin umurni na fuska kadai zan hade sai ki ga ya soma rawar jiki yana lalllashi na, ai ni namiji dan in ja akalarsa ba wata tsiya bace ina da wanda ya tsaya min." Suwaiba tace, "shi yasa ai nace mu biyo don na san baza ki rasa shawaran da zaki bani ba, sannan idan 'yan sinadaran da ake birkita kwakwalwan Alhaji a bani yau nima na birkita nawa mijin, ni ban san irin shi ba duk kyan maganin mata idan nayi amfani da shi bana gane ko yayi ko bai yi ba don ba zai nuna ba sai yayi mirsisi na rasa gane gabansa." Aina'u tace, Kyale shi Wallahi karyan miskilanci yake yi yau zan baki 144 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria wanda zai yi ta kwara miki ihu kuma sai ya manne miki tamkar cingom, kece da shi yau ko? Tace, "Eh, nice amma babu tabbas din ko zai yi wani motsi don miskilancin na kansa sai yayi ra'ayi." Aina'u taja dogon tsaki au ke kuma sai ki kyaleshi, baki san dabarar da zaki yiu ya afka ba? To bari kiji ni ko bani ke da girki ba idan ina jin tsiya ko ina da muradinsa na san yadda zan masa ya fado tarko na kawo kunne ki ji," Ta yi mata rada a kunne suka kece da dariya suka yi shewa suka tafa, suwaiba ta ce na gode miki tawa kin bani liked ai matar nan ta higa uku har ,, ita ta shigo tarko na. Aina'un ta tashi ta zuge zif din wata jaka ta dauko wata 'yar karamar kwalba tamkar ta mai ta nuna ma suwaiba tana mata karin bayani, kinga wannan maganin daga China muka bada sako aka taho mana da shi naira dubu hansin kenan duk kwalba, dan 145 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria kadan zaki lakuta ki manna ba zance miki komai ba ina jiran wayarki don ni ranar dana fara amfani dashi kin ga wannan." Ta dauko makullin mota dake aje bisa kan madubi tace, "makullin motar da ya bani kenan da safen, waccan tawan yace in hada ko inyi kyauta da ita bayan wasu kyaututtuka da suka biyo baya. Humm! Ai ni yanzu bana sanyi da wadannan abubuwan don suna biya min bukatu sannan ga boka Duna ya tsaya min, ki zo in kaiki." Tace, "ki sha kuruminki zan zo mu je kudi ni da bani da shi, amma yanzu idan ya zo hannnuna na san zan sami kudi don ba kananan kudade mutumin ke samu ba yanzu ni ina zaune cikin rashi." Ta dibar mata maganin cikin wata 'yar kwalba. Mijin Aina'un yayi sallama ya shigo yana cewa, "yace ki fito ku tafi dare nayi ga garin da sanyi." Ta mike tana gyara hijabinta suka biyo 146 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria bayan Alhajin Aina'u na sake yi mata rada a kunne har suka fito. Anan ne Mujceb ya gaida Aina'un da jiki ta amsa tamkar ciwon take yi da gaske, sannan suka yi sallama suka wuce. Ta dan marairaice masa tace, "Don Allah baban waleeda ka tsaya ka saya mana ice cream." Ya dan dubeta yace, "kin fa san dare yayi za ki sa muna tsaye-tsaye ki bari gobe na siyo miki." Ta kara narke murya."kayi hakuri ina ce a kan hanya ne? bai ce komai ba sai gani tayi ya tsaya Mr. Biggs, ya shiga ya siyo ya zuba ledojin a sit din baya Ana zuwa wata kwana kuma ta sake kashe murya."Baban Waleda don Allah ga gasassun kaji, Wallahi yunwa nake ji ban ci komai sabo da zullumin zuwa asibiti nan." Ya dan Harare ta, "wai ke wane irin kwadayi ke damun ki tamkar wata mai ciki, kince ice cream an siya yanzu 147 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria kince kaza ai ko me yaron ciki sai haka. Tayi dan murmushi, " Ni dai ayi hakuri a siya mana ciki kam ai ka san na dade ban bi hanyarsa ba, amma kwanan nan zamu hadu insha Allahu." Girgiza kai kawai yayi lokacin da yake yin fakin din motarsa. Ya fita yaje ya siyo kajin suma suma ya bude sit din baya ya aje ledojin sannan ya ja motar suka tafi. Suna daf da kwanar da za ta kaisu gida ne ya dube ta yace, "Ga mai soya kifin ruwa can shima za'a tsaya a siya ne? ta san tsokanarta yake yi shi yasa tace, "A'a na gode da wanda aka saya mu je gida kawai da dai ciki gareni ka san dole sai an tsaya an siya. Ba su isa gida ba sai goma da kusan rabi. Suna fitowa daga motar ya amshi ledoji hudu biyun yace ta wuce masa da su dakin ta gashi nan zuwa.. Can ya sami Muneeba a dakin baccinta tana zaune bisa abin Sallah da 148 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria hisnul muslim a hannunta tana karantawa. Ya aje ledojin da ya shigo da su yana cewa, "kin gammu sai yanzu ko? Wallahi asibiti uku muka je, na farko sunce bata da ciwon, amma ban sami natsuwa ba sai da muka sake zuwa wasu asibitocin kinga result din. Ya fiddo takardar daga aljihunsa ya mika mata ta amsa ta duba sannan ta maida masa tana cewa, "Ai an gode Allah da sakamakon ya kasance haka, Allah ya kara tsarewa", Yace, "Amecen". Ya dubi su Hilal dake bacci bisa gadonta Waleeda na can bayan su yace, "yarannan duk sun yi bacci har Walecda? Tace "Tuni suka yi bacci dare ai yayi, Bilal ne ma yau bai yi da wuri ba, Waleedan kam tun tara saura ta bingire tunda ta cika cikinta da riso". Ya yi dariya "yarinya da kwadayi sam yanzu ba ta cin abinci sai abincin yara taci zamaninta za ta ci na su.' 149 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hạssan Zaria Ya nuna mata ledar da ya aje, "Ga ice cream nan da gasassar kaza, daga zuwa aibiti mun bige da siyan kayan kwadayi har da cakulet a ciki." Ta dau ledar tana dubawa, "An gode Allah ya amfana yace, " Akwai wani abu ne zan je in kwanta baссі nake ji gashi ko Sallar isha'I banyi ba" Tace, "Babu komai Allah ya tashe mu lafiya." Har ya juya zai fita sai tace "Waleeda nan zata kwana mu rufe kofa ko? Ya juyo yace Wallahi na manta da ita ki barta ta kwana nan tunda tayi bacci". Bai jira abinda zata ce ba ya juya ya tafi yana kara yi mata sai da safe kishi kummalon mata nan da nan ya taso ya lullube zuciyar Muneeba take ta soma karanto addu'ar yaye kishi. a zuciya don ba taso yayi tasiri a zuciyarta duk da zallar zúmudi da murna da tagani karara a shimfide a fuskar Mujeebu wanda ta rasa gane cikin abu biyu wanne ne ya saka shi 150 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria cikin murna tsallake siradin da Suwaiban tayi ko murnar yau zai kasance tare da matar tasa bayan shafe kusan shekaru biyu rabon da wata mu'amular auratayya ta hadasu ta dade zaune tana yan tunane-tunane da, 'yan canke cankenta daga karshe dai ta watsar da komai ta tashi ta je don ta rufo kofar falonta dake bude. idanunta karaf akan Suwaiba dake tafiya zuwa dakin Mujeeb tana sanye da wata 'yar yaloluwar riga da bata boye sirrin komai a jikinta ba, iyakacin rigar guiwarta kuma ga dukkan alamu rigarce kadai ke jikinta Allah ya sa ba su ga juna ba bayan Suwaiban kawai ta hanga da cewa za ta yi Muneeba lekensu tazo yi jikinta a salube ta rufo kofar ta zo ta zauna a bakin gado tayi shiru yau kam tsakanin Suwaiba da Mujeeb sai Allah an dade ba'a hadu ba banufe ya ga Koko shi ya sa ma yace ta bar Waleeda ta kwana gurinta wato don kada ma ta kawo musu cikas sauri tayi ta fatattaki wannan tunanin daga 151 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria zuciyarta don in ba ta yake shi ba sai ya nemi dagula mata tunani ya hana ta bacci mai dadi tayi addu'o'i ta tofawa yaran dukansu ta ja bargo ta shige sannan ta latse fitila mai haske itama ta karanto nata addu'ar ta tofa miyan ya dawo jikinta sannan ta soma baccinta mai dadi. Suwaiba lokacin da suka dawo wanka ta yi sauri ta shiga don ta san kaidar mijinsu ba'a kwanciya da shi sai kin yi wanka kuma ya jiki kina Kamshi tana Sallar Isha ya shigo ganin tana Salah sai yace idan ta gama ta sameshi dakinsa ya juya ya fita tana idar da Sallah ta saka yar rigar baccinta ba tare da tasa komai a jikinta ba, ta shigo bayi ta manna maganin da Aina'u ta bata, sannan ta fito ta feffesa turare ta suri ledar data shigo da shi ta fita ta rufe kofofinta ta nufi dakinsa. Shima har yayi wanka yana Sallah ta same shi hakan ne ya bata dammar dauko filet ta juyc kajin nan ta dauki robar Ice Cream guda daya tana 152 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria sha tana kallonsa har ya idar da Sallar ta dauka filet din ta kawo gabansa ya dubeta yace "Ba zan iya cin komai ba bani Ice cream din matsowa tayi ta debona hannunta ta kai bakinsa yayi murmushi "Yau dai na ga so kike ki shagwabani miko min wannan nasha na hutassheki" Ta turbune fuska "wai ni meyasa komai na yi maka sai ka gwale ni ne sam bana birgeka da Muneeba ce ai ba zaka ki sha ba". Yace "Kinga matsalata dake ko? Ke dai bakinki ya zama sai kinyi korafi kin kawo zancen wata ki daina irin wannan babu kyau”. Sai dai ta fadi hakan ne ita ma taga sakarcinta da take son 6ata nishadinta da suke ciki tun yamma cin yau hakan kuma zai iya bata al'amarin da take fatan ya wakana tsakanin su don kuwa tayiwa daren nan shiru sosai ta langabe kai cikin kisisina "Shikenan kayi hakuri ba zan sake sako sunan kowa ba idan huna tare yi hakuri kasha" 153 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria Ta kai cokalin Ice Creamn din bakinsa bai ki ba ya amsa yasha. A haka tayi ta bashi har suka shanye sauran ta je ta saka Firij dinsa ita kadai ta ci kaza daya kadan ta rage saboda yunwar da ta ce tana ji daga nan al'amura suka fara canza salo shi kam yace bacci sosai yake ji amma sakat din da ta hana shi shi yasa ya sallama mata suka raya daren cikin nishadi irin yadda take mafarkin samu shi kam har tausayinta ya dinga ji na rawar jikin data dinga yi lallai ya yarda ta dade cikin kewarsa da kyar ya iya tashi ya tafi Sallar Subahi saboda taki barinsa yayi bacci duk. cikin kisisinar data shirya ne don tana son tasa shi ya makara wajen zuwa Ofis don ta Kunsawa Munceba kishi a zuciya ana idar da Sallah ya kasa zama yayi karatu a masallacin kamar yadda ya saba Allah - Allah yake ya dawo ya iske Suwaiban da wata sabuwar bukatarsa don kuwa tayi rugu-rugu da tunaninsa a daren jiya ta canza masa tamkar ba ita ba ko dakin 154 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria Goggo da Muneeba bai shuga ba kamar yadda ya saba idan ya dawo sallar subahi yana yi. Ta sake kanainayeshi ta nuna masa tamkar baida kowa inba ita ba har sai da ya zo yana tuhumar kansa yadda ya kasa saurara mata abin tamkar tishin karatu wani irin nannauyan bacci ne yayi awon gaba da shi wanda ya kaishi har kusan tara safe san nan ya farka a gaggauce yayi wanka ya soma shirin zuwa office a makare ya tashi Suwaiba da ke shara baccin ta hankali kwance yana tambayarta abin da zai yi breakfast da shi tayi mika babu wani salati idanunta na kallon agogon bangon dakin murna fal cikinta da ganin lokaci sannan tace "Ni yanzun me zan iya yi maka yadda nake a gajiyen nan kaje gurin mamansu Bilal na san ba za ka rasa abin da zaka ci bа`. Jin abinda tace sai ya soma shiri a gurguje don ya shiga gurin Muneeba yayi break sannan ya wuce Ofis Muneeba ita kuma tana can tana fama 155 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria da Walceda dake rigima tana ta kiran anti ko tace Baba tana neman Suwaiban ita kuma babu halin ta je ta kaita dakin Mujeeb din tunda har a lokaciun basu fito ba kada su yi zuwan nata fassarar lallashin yarinyar ta dinga yi har dai ta hakura ta saki jiki tana wasa da 'yan kunnenta Mujeeb ya shigo dakin nata tare da sallama ta amsa masa amma hankalinta na kan yaran dake wasa ta soma gaishe shi ya amsa tare da cewa "Yau nayi lattin zuwa Ofis ko zan sami abin break fast?. Mamaki abin ya bata na sakaci irin na Suwaiba kin iya kwana gurin miji ki kainainaye shi amma ba zaki iya bashi abinda zaici ba ta kalle shi cike da mamaki tace "Abin breakfast tace akwai a kicin bari na kawo maka na dauka ka tafi Ofis ko ina bayi lokacin Yace "Ban tafi ba wani, bacci ne tamkar na asara ya same ni tunda na dawo Sallar Asubahi Allah yasa ya zamc min alkhairi". Tace "Amcen ta wuce kicin dinta ta kawo masa kunun 156 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria gyada da soyayyan dankali da kwai ta barshi zaune gurin yara a falo ta shige dakin baccinta ta kama gyaran durowar kayan su Bilal hakan nan ta tsinci kanta da yin wannan aikin da bata shirya ba kasancewar bata son cigaba da zama gurin Mujeeb saboda kishi da ta ji yana yunkuro mata na ba gaira ba dalili mutum da matarsa me za su fasa? Har ya kammala karinsa bata fito ba ya tashi ya shiga dakin ya sameta yayi mata magana cike da kulawa 'Ni zan wuce Ofis koda wani abu da kuke so? Ta girgiza. kai "Babu abinda muke so Allah ya tsare ya bada sa'a ya amsa "Ameen" ya kai hannu ya shafi gefen fuskarta sannan ya juya har zai tafi sai ya dawo yace "Abincin yaran akwai saura da yawane tunda naga har waleeda ma sha take yi'. Tace "Ina jin saura gwangwani biyu cikin kwalin zuwa jibi za'a iya siyo musu wani yace Ok zan aiko direba da shi anjima ina son ki yi min 157 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria kunun alkama ya taho min da shi tamkar zata ce masa meye aikin Suwaiba fa da ba zata yi masa ba sai dai ta fasa tace "Sai ya zo". Ya juya ya fice ta bi bayansa da kallo tana girgiza kai misalin daya da rabi na rana direban Ofis dinsu ya iso har bakin falonta mai gadinsu yayi şallama ya shaida mata an aiko direba ta saka hijjabi ta fito suka gaisa ya mika mata kwalin Prisocream din yara tare da wata babbar leda yace; "Ga shi nan inji yallabai yace ki kirashi yanzun kafin in tafi". Ta amshi kayan ta koma falonta ta dauki waya ta kirashi yana dauka tace, Direbanka yace kace in kira ka yace "Ki bashi kunun ya kawo mini sannan ga wasu kaya nan ki dauki kala biyu ki cirewa Goggo biyu sai ki ba Suwaiba guda biyu mun fita da abokina yawale ne zai yi wa matarsa sayyaya ta haihu shine na ga kayan sun bani sha'awa Allah ya sa sun yi miki. Ta amsa sunyi kyau sosai Allah ya kara budi mun gode". Suka yi sallama kowa ya aje wayar ta dauki 158 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria Filas din kunun ta saka cikin wani basket tare da kofuna da cokula ta zo ta duba lesunan ta cire nata kalolin da take so ta cirewa Goggo don ba ta nan ta zuba na Suwaiba a ledar gurin da aka yi siyayyar ta ba direban tace ya je ya kai wa Suwaiban. Lokacin da ya kai mata yace inji yallabai don haka Muneeba tace yaga ya mata yana fita ta duba ledar tayi tozali da rantsatssun lesuna 'yan dubu arba'in arba’in, don haka taga kudinsu manne jikin ledar kasancewar a Super Market aka sayesu. A tunaninta ita kadai ya siyama tukuicin fadawa tarkon da ta dana masa ya afka a daren jiya ta dauko wayarta ta nemo Ainau ta soma labarta mata irin wainar da suka toya a daren jiya ita da mijin nata wanda sai da ya aje wani miskilanci da jin kansa ya dinga kodata abinda bai taba yi mata ba ta kara da cewa kin san yanzu ina zaune sai ga direbansa na Ofis ya aiko a kawo min galla gallan lesuna yan dubu Arba'in 159 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria Arba'in na san duk tukuicin abinda nayi masa ne" Aina'u ta kyakyale da dariya tace "Me na gaya maki an gaya miki ni ta wasa ce to kada ki kyale shi don so nake ki kanainaye shi da sabon kisisina ki tatso wasu kudade don ki bada akawo maki naki kin daiga aikin maganin sha yanzu magani yanzun ne kada kiyi wasa da wannan dama da kika samu ina jiranki gobe in sake jin wani cigaban da za'a samu. Cikin daren yau ma bayan sun gama nishadantar da junansu sai ta narke cikin jikinsa tana masa 'yan koke-koke na kisisina, nan da nan hankalinsa ya tashi saboda cikin daren nan guda biyu jin al'amuran Suwaiba yake kamar me........ya dan dago fuskarta dake narke bisa kirjinsa yana kallonta yace "Me kuma ya faru muna cikin nishadi zaki tada min hankali? Ta Kara marairaicewa "Ni kam gaskiya na gaji da zama ba wata sana'a jari nake so ka bani in fara sayan kaya ina saidawa 160 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria ko in bayar a sayarmini sannan nima ina son in fara hawa mota kamar sauran mata tunda dai Allah ya hore maka bawai baka da hali bane". Ya. sauke ajiyar zuciya yace, "Wadannan 'yan bukatocin ne za su saki-tada hankalinki? Ki bari zuwa da safe zan san abin yi. Tun bai bata kudaden ba ta shiga yi masa godiya. Da safe kamar yadda yace tana zaune gefen gadonsa, shi kuma yana saka kaya, yana gamawa ya mika

Chapter 6 of 8