Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
4 / 8
ya so ya tsunduma kansa a harkar neman mata tamkar yadda yaga wasu abokansa masu tashen naira irinsa nayi sun aje mata iri iri a 81 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Žařia waje duk wadda šuka yi marari ita suke dauka zuwa hotel su hole abinsu shi kam yana Kyamar hakan kasancewar irin wadannan matan sukan zama angulu ne kazar kowa, shi kam ko ba komai yana tsoron haduwar shi da Allah, sannan ga cututtukan da mazinata ke dauka masu hallakarwa in ma mutum baya tsoron Allah ai yaji tsoron daukar cuta. A kwance ya sami Suwaiba tana (Game) a wayarta sannu da zuwa kawai tayi masa sai taci gaba da yin (Game) dinta yace "Ina Waleeda ne? ta ce, "Gata can a daki tana bacci", ya ce, Ok to dauko ta ki goya ta zamuje anguwa ne yanzu". Ta bar game din tana kallonsa ta ce, "Anguwa? Za mu yi nisa ne in canza kaya? Ya ce, A'a bar kayan jikin ki sai dai kisa Hijab kawai bana son dan gyalen nan da kike sawa Ya fita zuwa dakinsa bai dade ba ya dawo ya ce ta fito ta dauko 'yarta suka fito taje tayi sallama da Goggo ta leka dakin Muneeba ta shaida mata za 82 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria su fiţa da baban Waleeda kuma tayi hakan ne don ta nunawa Muneeba itama fa miji na fita da ita ba wai sai ita ba" Tana barin dakin wani azabąbben kishi ya taso ya lullube zuciyar Muneeba har taa ayyana a ranta cewa shine ya turo Suwaiba tayi mata sallama don ta san sun shirya da matsąrsa in ma tana tunanin sun yi fada ne" Suna isa asibitin ya barta a inda ake jira kafin a aga likita shi kuma ya shiga ya sami likita da ya je gurinsa a wani (Private) asibiti yayi masa bayanin abinda yake so ayi mata wato Gwajin (H.I.V). A ka'ida kafin ayi maka gwajin ko kafin a baka sakamakon gwajin sai likita ya zaunar dakai yayi maka wasi nasihohi akan yin hakuri ga duk abinda sakamako gwajinka ya bayar ka dauki abin a matsayin Kaddarar rayuwa. Yadda likitan ya zauna yana yi mata bayani tare da nasihohi ne hakan 83 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria ya ganar da ita abinda mijinta ya kawo ta ayi mata wato gwajin cutar kanjamau tunda yana tunanin tan dauke da cutar dalili kenan da ya kaurace mata har na shekara daya da watanni. Likitan nasiha na gama yi mata har sai ya dauko sirinji tare da wata igiya yana kokarin daure mata hannu don ya debi jinin nata. Ta dakatar da likitan, "Tsaya likita nagane gwajin da zaka yi mini a bayaninka ka nuna idan za'a yiwa mutum irin wannan gwajin sai da amincewarsa to ni ba da amincewata za'ayi mini ba ban ma san me ya kawoni asibiti ayi mini ba, saboda haka ka gaya masa ban amince ba, saboda haka ban yardaba, ba na so, idan ya dawo ka ce masa na tafi gida". Ta mike tsaye ta goya waleeda likitan na mata wasu bayanan don ta tsava har mijinta ya dawo amma ina ko tsayawa ba tayi wajen sauraronsa ba ta fice daga Ofishinsa. 'Bata fito da ko kwabo ba hakan ne yasa ta dauki mota tayiwa direban bayanin sai ya kaita gida zata 84 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria shiga ta kawo masa kudinsa. Mujeeb na dawowa Ofishin likitan yaga babu Suwaiba, kafin nan ya tambaye shi ya soma yi masa bayanin yadda suka yi da ita har ta a tafi gida. Ran Mujeeb ya baci sosai, ya yi sallama da likitan ya fito ya figi motarsa ya biyo ta gidan a dakin baccinta ya sameta zaune a bakin gado ya watsa mata harara, "daga yau sai yau Wallahi kada ki kara zuwa kice mini na tauye miki hakkinki bana biya maki bukatarki ta aure, tunda kinki yarda ayi miki gwajin nan don ba zai yiwu naji da kunnena irin badalar da kika je kuka yi da bokanki ba sannan inci gaba da mu'amala dake ba tare da na tabbatar da lafiyarki ba. Wallahi tausayin Waleeda ne kawai yasa zan iya cigaba da zama da ke ba wani abu ba, in baya'ga haka da tun da na warke cutar da kika yi min sanadinta da na sallameki saboda haka kiyi ta zama a haka har sai ranar da kika amince aka yi miki gwaji Allah ma 85 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria ya taimake ni naje an yi min gwajin baki lakaba mini cutar komai, ke ma sai kiyi ta addu'ar kada Allah ya kaddaro cuta a kanki zabi ya rage gareki nikam babu wani hakkinki a kaina har sai ranar da na tabbatar da lafiyarki". Yana gama bayaninsa ya fice a dakin nata kuka mai Karfi Suwaiba ta saki saboda wannan hali na tsaka mai wuya da ta shiga kwarai tana cikin tsananin bukatar mijin nata don kuwa ita ba mazinaciya bace balle taje ta nemi maza a waje neman duniya ne ya kaita sallamawa boka kanta kuma a lokacin ta sami biyan bukata saidai tasirin abin baiyi tsawon lokaci ba gashi yanzun tashiga halin rashin madafa, ita kam tana tsananin tsoron gwajin da za'a yi mata kada ace tana dauke da cuta tunda kwarai ta sani bokaye nan fasikainc kuma yawancinsu suna tattare da cututtuka, ita kam a lokacin idanunta sun rufe biyan bukata kawai take nema shi yasa ta ba da kanta gashi yanzun lamarinta duk ya jagule ta rasa mafita. 86 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria Tayi kuka mai isarta daga karshe dole ta hakura don har ta yi ta gama ta kasa yardawar zuciyarta zata je ayi mata gwajin ta yarda zata iya hakurin zama a gidan haka nan, tunda hakan ne rufin asirinta don ta san idan ya tabbata tana da cuta to ba zai cigaba da zama da ita ba yanzu ko tana zauna babu abinda ta rasa babu abinda baya yi mata kuma babu wanda yasan meke tsakaninsu har yanzu ta san bai gayawa kowa ba, saboda zurfin cikin da yake dashi, kuma shi mutum ne mai rike sirrinsa yana barin dakin Suwaiba kai tsaye nasa dakin ya cuyce ya maida kofa ya rufe ya euce dakin baccinsa ya ruvbe kayan jikinsa ya wuce bayi ya sakarwa kansa ruwan shawa mai sanyi duk da irin sanyin da ake yi amma shi zafi ya ke ji saboda yanayin da ya tsinci kansa a cikin sannan ya rashin tudun dafawa. Ya kwace a kalla mintuna talatin ruwan sanyi na kwarara a jikinsa sannan zne fa ya sami yar natsuwa ya goge jikinsa da tawul ya saka jallabiya sannan ya 87 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria fito daga bayin ba'afi mintuna biyar ba wani irin zazzafan zazzabi ya rufesa ya lallaba ya haye gado ya lalubo bargo ya shige ciki yana rawar sanyi dare yayi nisa amma shi idanunsa biyu yana cikin halin matsananciyar zazzabi wanda ya galabaitar da shi matuka tabbas ya san yana bukatar taimako a irin halin da ya ke ciki tunda ba zai iya tashi ba balle ya nemi magani a dakin ya sha. Cikin matan nasa ya rasa wacce zai kira cikinsu kjasancewar kowa tana da laifin da ta yi masa kuma sune'suka yi sanadin shigarsa cikin wannan halin saukowa yayi a hankali ya rarrafa ya isa inda ma'ajiyar magungunansa suke ya nemo Panadol ya debi ruwa yasha guda biyu sannan ya koma ya kwanta bai sami yin barci ba a wannan daren har sai bayan da yayi Sallar subahi shinc bacci yayi awon gaba da şhi har tara saura tayi bai tashi ba, hankalin Muneeba na kansa a tunaninta ko yau ma ya shigo ya wuce Ofis bai nemeta ba, sai ta ji ashe ma bai shigo ba don 88 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria taji Goggo Hinde na tambayar Laminde "Hala Mujeeb har ya wuce gurin aiki muna can bayi? Laminde tace "Anya? Gaskiya bai shigo ba kila dai bai fita ba ko kuma ya fita din amma dai bai shigo ba Muneeba ta tashi ta je ta leka ta window dakin baccinta don gani ko motarsa na nan ko ba ta nan hakan ne zai tabbatar mata da ya fita ko. yana nan. Ganin motar ta yi a inda aka saba aje ta har ma jume ya wanke ta ya gogeta jiran mai ita kawai ake ya fito ya shiga. Ta fito daga dakin baccinta tana shaidawa su Goggo Hinde, Goggo ina jin fa bai fita ba donga motarsa can har jume ya wanke bari in dubo shi ko lafiya". Tana murda kofar falonsa taji a kofar a kulle da makulli tayi kwankwasawa shiru bai bude ba, sai ta dawo ta dauki wayarta ta kira wayarsa nan ma bai dauka ba sai abin ya fara tsoratata shin me ke faruwa ne? cikin 89 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria bacci yaji ana kwankwasa kofarsa ya taso da kyar yaje ya bude kofar bai tsaya ya duba ko waye a kofar ba kawai. ya juya yaje ya shiage cikin bargo ya kwanta. Muneeba ta biyo bayansa tazo ta zauna a bakin gadonsa tana tambayarsa, "Lafiya yau ba ka tafi Ofis ba? Munji shiru ne har yanzu ba ka fito ba shi yasa nace bari in dubo ka don naga motarka a waje har Jume ya wanke”. Lamo yayi cikin bargo bai bata amsa ba. Hannu ta kai tana taba jikinsa sai taji jikin da zafi, ta yi saurin hayewa gadon ta yaye bargon da 'ya lulluba tana cewa "yanzu ba ka da lafiya shine baka sanar da kowa ba in ma ni ba zaka sanar da ni ba ai ka gayawa Suwaiba tunda ita bata yi maka laifin komai ba ni ce kake fushi dan". Ya dan kalleta sannan ya lumshe idanunsa yace "Gani na yi ciwo na zai dami kowa ba shi yasa ban sanar da kowa ba, don bana bukatar taimakon kowa kuma ba na son kowa kusa dani". 90 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria Ya maida idanunsa ya rufe ta tsaya shiru tana kallonsa hakika abinda ta yi masa sam ba ta kyauta ba to yanzun me ya kamata tayi masa don ya sauko daga wannan dokin fushin da ya hau. Wani tunani da ya zo zuciyarta shine lallai kila sun sami sabani da Suwaiba ne don in ba haka ba babu yadda za'a yi ya shiga takura irin haka don tasan halin Suwaiba ba idan ta nemi biyan bukatar kudi-baiyi mata ba ta nan ta ke gasa shi bata san wannan karon matsalarsu ta wuce tunaninta ba. Duk da ba zata iya masa abinda yake so ba amma bari ta yi 'yan dabarunta don ta saka shi cikin natsuwa. Hakan kuwa tayi don bata bar dakin nasa ba sai da ta ga ya sami natsuwa yaje yayi wanka ya dawo ta hada masa Ti ya sha, ya sha magani sannan tace masa zata je ta duba su Bilal kila zasu nemi Nono. Ya rikota lokacin da zata fita yace, A kalla kinyi awa daya da zuwa dakin nan yanzun 91 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria idan kika koma me zaki gaya musu ya rike ki har tsawon lokaci haka? Kin dai san Goggo Hinde ta zuba idanu kanmu. a Tayi murmushi tace ka barni dasu ni na san irin tsarin da zanyi musu bari inje". Tana shiga dakin sukabita da idanu, Goggo Hinde tace, Lafiya kika je kika dade yara suna ta neman nono? Hala baya lafiya ne?. Ta ce zazzabi ne yake yi wait un jiya amma bai fada ba shine na tsaya nasa masa ruwan sanyi a jikin yanzun haka har ya fara sauka". Gaba daya suka hada baki wajen fadin "Subhanallahi" Laminde tace, "Shi Alhaji kamár yaro zai rufe kansa a daki cikin ciwo na ina ita matarsa da ba zata tsaya gurin saba sai ke mai jego?. Goggo Hinde ta tabe baki "Ba ma sai in ta san yana ciwon ba me wannan ta sani na kula da miji in banda tsinannan kishin banza ki ba yaran nono ki koma ki kula da lafiyar mijinki in har ita ba zata kula dashi ba jego ai ba zai hanaki 92 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria kula da lafiya mijinki ba Muneeba ta zauna ta shayar da yaran Nono ta mika su gurín su Goggo Hinde suka goye su sannan ta nufi dakin Goggo tab shaida mata Mujecb ba ya da lafiya ta isa dakin Suwaiba ta gaya mata, budar bakinta sai cewa tayi "Ba ya da lafiya shine ni bani da matsayin da zai gaya mini sai dai ya aiko a bgaya min, lallai ma mutumin nan to Allah ya sawwake idan kin koma ki gaishe shi Muneeba tace, Haba Maman Waleeda wannan wace irin magana ce nima fa ba gaya min yayi baya da lafiya ba, nice na ga shiru har kusan taran safe banga ya fito ba sannan ga motarsa a waje shine na je na duba ko lafiya sai na iske yana kwance baida lafiya tun jiya kuma idan zancen gaskiya ne aike ya kamata ace kin sanar damu halin da yake ciki tunda kece a tare dashi ko da yaushe don Allah ki yi hakuri ki daure ki dinga kulawa da al'amuransa don kada mu yi sake ya fada wani halin da bai dace ba" 93 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria Nasiha ce Muneeba ta yi mata a fakaice saboda lura da tayi da halin da mijin nasu ke ciki in ba'a saa aka ci ba Allah ya taimakesu tsoron Allah ya mamaye zuciyarsa yana iya kai kansa inda bai dace ba a dal,ilin rashin kulawar da yake samu. Allah ya sanbi tana son bashi tata gudunmuwar to amma tana jin nayin su Goggo Hinde kada su ga tana binshi su gano zakewarta ga al'amuran mijin nata alhalin tasan yana bukatar a kula da shi don ta riga ta saba masa duk rintsi zata kasance da shi in ita ke da kwana gurinsa. Suwaiban ma ta gano inda kalaman Muneeba suka dosa sai taс, "Ni fa ban iya wannan shisshigin gurin miji ba haka kurum bai neme ni ba in yi ta masa sintiri har ma ya kare ya wulakantani shine abinda ba zan dauka ba Muneeba ta sassauta murya "Haba dai ya wulakanta ki yanzun don mace ta je inda mijinta yake sai ace tayi shishshigi? Hakkinsa dake kanki zaki 94 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria sauke babu maganar kin yi masa shisshigi kulka da cinsa da shansa da gyara muhallinsa da biya masa larurarsa ta aure duk yana wuyanki mata biyu gare shi bai kai mata ace har ya shiga halin da yake ciki ba in ni ina jego ke me ya sameki da zaki barshi cikin larura?. Don girman Allah kiyi hakuri koma laifin me yayi miki ki bashi kulawar da ta dace a matsayinsa da mijinki don kada rashin hakan yasa yaje ya tsinduma kansa cikin hallaka sannan abin mu zai zo ya dama daga baya”. Suwaiba ta dubi Muncebas sosai tace, "Oh gaya miki yayi bana sauke hakkinsa da ke kaina? To bari kiji in gaya miki ni ban shiga hakkinsa ba shine ya tauye mini nawa hakkin kuma sai Allah ya sakamin don yanzun kusan shakara biyu kenan rabon da ya bani nawa hakkin tun kwanciyarsa ciwo har ya warke ga shi nan ke har kin sami ciki kin haihu ni ina zaune kamar ya aje hoto sai dai ya kale ni in zancen 95 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria gaskiya ne aini aka cuta shekara biyu sai kace an sassakani da ice". Zancen ya girgiza Muneeba ya kuma jefa ta cikin mamaki sai ta shiga ba Suwaiban hakuri don bata yi tsammanin al'amarin har haka bane, "Kiyi hakuri don girman Allah Wallahi ni bai taba gaya mini komai game da ke ba wannan ba halinsa bane ke ma kin sani baya hrar wata irin wannan da wata, wannan al'amariun naku sirri ne don Allah kada ki sake fadawa wani dolensa ya gyara in dai yana tsoron haduwarsa da Allah kiyi hakuri laifin da na dora a kanki ashe shi ya janyowa kansa shiga wani hali ki daure kije ki duba jikinsa isha Allahu zai gyara". Jikin Muneeba a sanyaye ta baro dakin a zaune ta sami Mujeeb da (Laptop) a gabansa yana 'yan danne danne ta zauna a gefensa tace, Ah jiki yayi sauki har an hau internet wane labaran duniyar ka samo mana?. Hankalinsa na kan Lato din yace "Labaran Lahira na samo matso ki ga 96 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria wa'azin dana karantawa jikina ya mutu Rwarai tunatarwa ce akan lahira da irin bala'o'in dake tattare a filin kiyama ita ma jikin nata har yayi la'asar tun kafin ta duba tunatarwar ta matso jikinsa sosai ta jingina da kafadarsa tana karanta tunatarwa kafin ta yi masa maganar dake cin ranta. "Abokin rayuwa wata magana nake so muyi ina son ka fahimceni kuma kada kace na yi maka shishshigi so nake kayi gyara don an sami baraka kuma daga gurinka 6arakar take shin don girman Allah Allah me Suwaiba tayi maka har ka dauki mummunan mataki akanta wanda zai iya jefa rayuwarta da taka cikin matsaya?. Ka fa yi hakuri kada kace nayi maka shisshigi so nake kai da kana ka yi gyara". Ya soma kada kai kafin ya dube ta yace. Gaya miki tayi mun sami sabani ni da ita, ko ko hasashe ne kika yi? tace, ba hasashe na ke ba zuwa nayi na gaya mata baka da latiya da shine ta ji haushin wai baka gaya mata ba, ni 97 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria kuma sai na dora laifin a kanta na yadda bata kulawa da kai don ya kamata ace itace zata fara sabin baka da lafiya bawai ni în gaya mata ba wannan laifin dana dora mata shi yayi sanadin da ta gaya min matsalar dake tsakaninku, abin ya bani matukar mamaki wai ka kaurace mata kusan shekara biyu kenan tun kwanciyarka ciwo, in har haka ne ka zalunceta ashe ma bata da laifin komai akan halin daka shiga. Ka sai dai rashin sauke, wannan hakkin yana kawo babbar matsala ga ma'aurata raini zai iya shiga tsakaninku da rashin daraja juna, in ma laifi tayi maka shekara biyu ai yayi yawa a matsayin Punishment, in ma horarwa za kayi mata ba'a so ya wuce na watanni hudu. Rufe Lato din dake gabansa yayi sannan ya juyo ya fuskanci Muneeba don yaji dadin yi mata bayanin dake bakinsa". Yanzu ita da kanta ta iya yi miki wannan bayanin don bata da 98 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria kunya? Wato duk yadda naso in rufe sirrin dake tsakaninmu sai ta sa na bankada shi kenan don in ban hakan nayi ba ke dinnan ba zaki yarda cewa bani ke danne hakkI ba tunda ta tsara miki nata bayanin kuma kinyi amman da bayananta dari bisa dari to bari kiji abinda banso kowa ya sani ba wanda shine ya zanío shamaki a tsakani na da ita" Ya warwarewa Muneeba hirar da ya/ riski Suwaiba nayi da bakuwarta Larai ranar daya fadi da abinda kunnuwansa sukaji har abin ya firgita shi wai shi Mujeeb matarsa taje tayi fasikanci da wulakantaccen mutum irin boka, sannan ta hada janabarsa da ta bokan duk hakan baiyi mata ba sai da ta ciyar dashi naman daya kwana a gabanta wannan alamari va bashi tsoro, ya firgita -da shalanín mata irin marasa tsoron Allah shi yasa da ya warke daga ciwo da ta zamo sanadinsa ya Kaurace mata sam yaji Kyamar kuşantarta yake yi harzya kafa mata 99 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria sharadin sai ya kaita an gwada jininta in har bata da wata cuta to zai iya yin hakurin ci gaba da zama da ita albarkacin diyarta Waleeda ita kuma taki yarda suje asibitin da yayi hikima ma ya kaita gudowa tayi shi kuma Wallahi ya sha alwashin ba zai taба iya hada makwanci da ita ba har sai ya tabbatar da ingancin lafiyarta in kuma bah aka ba to sai dai tayi ta zama hoto a gidansa shi bai zalunce taba itace ta zakunci kanta. Shiru Muneeba tayi tana aikin sauke numfashi kawai cikin tsananin mamaki da tsoron kila dukansu ma sun kamo da cutar tunda ai an gauraye da juna tun kafin ta bar gidansa tayi magana a tsorace "mu din yanzu ka tabbata mun tsallake siradin da kake ganin ita tana kai? Ko kai kana da tabbacin taka lafiyar?. Ya gyada kai kwarai ina da tabbacin lafiyata Kalau bani da wata cuta don nasa an gwada jinni na a zuwan da mukayi Egypt sai dana 100 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria tabbatar da hakan sannan naci gaba da mu'amalata dake zaki iya tuna hakan ta faru". Ta ce to me yasa ni bakasa an yi mini ba ka barni cikin duhu alhalin ina gidan nan lokacin da abin ya faru tunda shine masomin juya mini baya daka yi? Ya ce "Ke ma an yi maki gwajin a Egypt lokacin da suka yi miki gwajegwaje an kuma bani sakamakonki lafiya kaulau kike abinda yasa ban gaya miki ba don kada in tada miki hankali ko ki dameni da son sanin dalilin da zai sa ayi miki gwajin alhalin banason kowa yasan abinda Suwaiban tayi mini. Yanzu kuwa lokaci yayi da zan gaya miki tunda har ta a iya budar baki ta fadl cewa na tauye mata hakkInta alhalin nine tayi mini cutarwa da ba kowane namiji za'a yi masa ya iya hakurin cigaba da zama da irin wannan macen ba. Saboda haka, ki kyaleta duk lokacin da ta shirya cigaba da zaman aure dani to dole ta yarda muje ayi mata 101 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria gwajin, in kuma bata shirya ba to tayi ta zama haka na riga na bata zabidole Muneeba ta bar al'amarin a haka, dón kuwa ta san mijinsu yayi nan mijin kokari kuma yayi matukar hakuri a irin wannan badakalar da aka yi tafka masa wadda har ya iya juriya bai saki suwaiban ba. Al'amarin ya kada hantarta sosai na irin shige-shigen da Suwaiba ke yi ita da uwarta har abin na nema ya sa su kauce hanyar Allah sun ma riga sun kauce tunda abin har da bada kai ga boka da ba miji naman da ya kwana cikin gaba alhalin ance duk macen da ta wanke gaba taba miji ko ta bashi wani abu da ya fito daga gabanta kafin mutuwarta sai tayi ta tsigar gashin gaban nata har sai yayi jinni kuma a gaban mutane har hakan sai yayi ajalinta. To don Allah ko wannan kadai ma ai ya isa abin tozarci ga mace, balle kuma idan anje gaban Allah me macen data aikata irin wannan halin zata cewa 102 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria mahaliccinta? Don girman Allah mu tsare imaninmu muji tsoron Allah mu tsarkake zukatarmu mu yi yaki tamu kada mu yarda mu biye mata ta kaimu ga aikata sabo irin na Suwaiba ko makamancin akan ki mallakje miji ko kisa a wulakanta kishiya ko a koreta ki zauna ke kadai da 'ya'yanki. In kuma asirin baiyi tsawon kwana ba wani sanadi yasa ya karye irin yadda ya faru da Suwaiba sai abin ya juya kanki kinga baki sami riba yadda kike so ba, in ma asirin ya dawwama iyakacin a nan duniya kin gyara duniyarki tayi miki kyau kin 6ata lahirarki wadda itace matabbata, inda zaki rayu, rayuwa mai dadi ta har Abadan abandon. Wasu matan kuma gani suke ke duk baladar da suka aikata a duniya ai zasu tubane kafin su mutu, sun manta ita mutuwa bagatatan take zuwa wa mutum ba tare da yi shirya ba shi yasa ake son kullum kayi shirin tafiya kiyama kada kayi tunanin kaifa ba 103 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria yanzu ba alhalin a rana ita mutuwar tana kawo maka ziyara sau saba'in kuma kankanin sanadi zai iya saka mutu sannan ko ba ciwo ma zaka iya mutuwa saboda haka don girman Allah mata mu gyara al'amüranmu musamman masu kishiyoyi su sukafi daukar gidan bokaye da malaman tsubbu guraren kai kukan su sun manta cewa idan matsala ta dameki kika daure kika hana idanunki bacci kika gayawa Allah zaiyi miki maganin ko wace irin matsala ke gareki, amma fa idan kina da tsarkin zuciya tare da yakini, a zuciyarki don yawanci abinda yasa Allah baya amsar addu'armu kenan rashin tsarkin zuciya kullum burinka ka cuci Musulmi dan uwanka sannan rashin yakinin a zuciya sai ka dinga ganin idan kayi addu'ar shin zama ta amsu kuwa?. To wannan rashin sa yakini a zuciyar yanasa Allah yaki amsar addu'arka saboda haka sai muyi gyara akan al'amuranmu dogon nazarin da 104 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria Muneeba ta zauna kenan tana yi a zuciyarta. Ranar Munceba yini tayi tare da mijinta tana jinyarsa tare da bashi kulawa yadda ya kamata, ta so ta bar Suwaiba ta zauna tare da shi sai taga tana zuwa ta gaishe shi tayi tafiyarta bata sake dawowa dakin nasa ba shi yasa ita ta yi ta sintirin kula dashi. Ita kanta Goggo Hinde sai da al'amarin na Muneeba yayi ta bata sha'awa na yadda taga ta hana kanta sakat wajen kula da lafiya mijinta nata har suka dinga hirar da Laminde cewar Lallai in ba asiri ba wane namiji ne zai sami mace mai kula da al'amuransa irin Muneeba har ya iya juya mata baya yace baya sonta?. Shi dinma kulawar daya samu ne ya sa ya dada narkewa ba wai don bai ji sauki ba ya fi son yayi ta ganinta ne kusa dashi don hakan na kara masa samun natsuwa matuka. 105 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria ****** ****** ***** Kwana arba'in kenan cif da haihuwar Muneeba a wannan safiyar kamar yadda yake a al'ada anyi su waina fanke kosai harda su cincin da nakiya anata rabawa na yin arba'in Goggoninta nata guda biyu Goggonsu tan an gidan da kanwarta Goggo Hinde sune suke ta wannan hidimar da misalin biyun rana goggo Hinde ce ke zaune a falon Muneeba tana ta saka kayan sawanta da jume ya wanke ya goge ya kawo a Jakarta babba. Muneeba ta kara dubanta a karo da dama sannan ta sake yi mata magana wai don Allah Goggonmu da gaske tafiya zaki yi gobe". Ta soma kokarin zage Zif din Jakar tana cewa tafiya zan yi mana Muneeba kwana nafa arba'in a gidan nan can na bar gida sai yara da matar yayanku ayyukan gida sunyi mata yawa sannan ni ma aj na koma in kula da nawa gidan ko". 106 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria dafa kanta kuma babu wanda ya isa ya fada ki dage da addu'ar nemawa kanki da mijinki da 'ya'yanki tsari kullum kiyi addu'a ki tofa musu kiyi musu a ruwan shansu Insha Allahu Allah zai kareku. Muneeba dai sai da tayi nasara akan Goggo Hinde har ta a yarda zata kara kwana goma sannan ta koma Dukku. Tana ba Bilal Nono Mujeeb ya kira wayarta yake tambayarta Madan yau ko fa kira na baki yi ba tunda na tafi Ofis? Tace yi hakuri abokin rayuwa yau hidima tayi min yawa ne amma Wallahi kana cikin zuciyata kasan yau mukayi arba'in sannan ina nan ina fama da Goggo Hinde tace Gobe-gobe zata tafi Dukku yan zu dai na shawo kanta tace zata kara kwana goma Wallahi na riga na shagwabe komai yimin suke yi sun sangartani kofa nono su Bilal zasu sha idan ina Bacci ba za'a tashe ni ba sai dai a karasu a nonon su sha ga yanzun idan suka tafi dukkansu wa zai yi min wannan gatan? Wallahi ko Pant 109 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria na cire goggo ke wanke min wannan gatan aiba kowa zai min ba. Ya ce ni dinnan idan kika barni da ma zan nuna miki gatan da ya zarta nasu, don ni har goyaki zan dinga yi zan tarayyeki tamkar yadda naga kike tarairayyar su Hilal da Bilal har ma zanyi mii fiye da yadda kike musu ko akwai me iya goya ki yanzu in bani ba? Tayi dariya tana girgiza kai tamkar yana ganinta, "Wannan hirar tafi karfi na mu canza wata", au kinsan zata fi karfinki meye na gaya min su Goggo sun shagwabaki alhalin ni na fi kowa iya shagwabaki, ko

Chapter 4 of 8