Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
3 / 8
tunda an roki Mujeeb ya barta ta je wankan gida yace sam bai yarda ba ko dakinta na Dukku ma yace bai yarda ba gara su zauna a Gombe tunda ga Goggo nan in yaso a samo wata cikin 'yan uwa da zata zauna das u tana musu wanka. Yanzun wa kike ganin a nan Dukku zata je ta zauna da masu jegon saboda kula da su wajen kwana da yi wa Muneeban wanka nan dai zan tura Laminde zata dinga sa musu ruwan wanka da yin wasu yan ayyukan. Innarsu Muneeba ta ce 'yanzu Goggonsu Hinde ta taho ita zata zauna a gurinsu zata dinga yi mata wanka da yiwa jariran wanka kinga ita Laminden sai ta dinga sa ruwan an gode Allah ya kara zumunci" Ta ce Ameen Allah ya raya mana su ya ba uwar su Lafiya. Tun da Muneeba ta dawo gida kullum gidan cika yake da jama'a yan uwa da abokan arziki tamkar a ranar 53 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria ake yin taron suna sai aka samo wata Kwararriyar mata ita ce ke yin girkin gidan Suwaiba ta ce ba zata iya girki mai yawa ba gara a nemo wadda zata yi. Muneeba tana jin dadin zaman Goggo Hinde tare dasu saboda yadda take kula dasu ita da jaririranta don idan dare yayi cewa take Muneeba tayi baccinta ta barta dasu ko kuka suke yi bata tashinta don ta basu nono sai ta kyaleta ta basu ruwan dumi da gulukos ta goya daya ta saba daya tayi ta jijjigasu har suyi bacci shi kanshi uban 'yan biyun kulawa ta musamman yake nuna musu ita da 'ya'yan in har yana gida to yana nan manne a dakin baccinta tare dasu ko 'yan barka ne suka zo ba ya fita sai dai akai musu varan falo Goggo Hinde tun tana korarsa tana masa tsiyar. wannan binbini har taa hakura ta kyaleshi. In kuwa ya shigo da daddare bayan Sallar Issha to sai ta gaji idanta ga Goman Dare ta wuce tace masa ya 54 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria Gyaran da ta yi wa fuskar ta sai ya maidata yarinya danya shakaf har sai da Goggo Hinde ta tanka kai 'ya'yan zamani sai a barkü yanzu danyen jegon naki kika zauna kike irin wannan kwalliyar don jawo wa kai jidali ko? Ni nan uwarki sai da kika birgeni balle shi wanda kika yi dominsa Wallahi ki kula da kanki ki tausayawa yarannan don mazan nan ba kunya gare su ba duk hanyar lallaba sun santa iyakaci idan kika biye masa kika sami ciki ke zai bari da wahala babu ruwansa gara ma ki sani ni kam na gaya maki. Jikin Muneeba yayi sanyi tace "Ni fa Wallatni Gaggo ba don shi nayi kwalliyata ba, na dai riga na saba ne, kuma ina nake binshi kinja gani dai shi ke zuwa nan kuma akan idonki 'ya'yansa yake biyowa ni ba ruwana don bana ma zuwa dakinsa". Goggo Hinde ta murmusa tace In ma 'ya'yansa yake biyowa ke ma ya kusa ya biyoki in dai namiji ne ba yaga 67 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria kinyi garau ba kwadai ji da shi ni babu ruwana. Munceba ta fara kukan shagwaba tana cewa "Ni dai babu ruwana gara ma ki hana shi shigowa nan din 'ya'yanma idan yana son ganinsu ga Karime nan ta dinga kai masa su dakinsa kwalliyar ma daga yau zan daina yi. Laminde ta ce, "Ki kyaleta kawai ta yi kwalliyarta Hajiya Hinde tunda gidan nan wa kika ga tana masa kwalliya inba ita ba, mazan nan na zamani gara da hakan yadda yake ganin mata iri-iri a gurin aiki ko cikin gari gara idan ya dawo gida shima ya sami nasa abin kallon ya ji dadi shi jego ai bazai sa ka zauna ba kwalliya ba. Kina dai gani da ya dawo gidan nan sai yazo ya ganta ita 'ya'yan han sannan ya ke samun natsuwa in da basa kwalliya suna birgeshi yaushe ma zai damu dasu, nan fa idan yazo ya makale sai kin kore shi yake tafiya hakan inace kulawa ce? Ki barta kawai taja hankalin mijinta gareta?. 68 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria kuma nayi daga zuwa na an watso min wannan uwar hararar mai makon ki tare ni da murna".. Ta juya suńa fuskantar juna sannan tace Ai Wallahi kin kyauta yanzu tsakaninki da Allah yau nme ya kamata kizo? Jiya fa mukayi zaki zo don ma kada in dameki shine har da kashe waya, ba komai zan rama". Murja ta riko hannuwan ta ta ce, Afuwan aminiyata Wallahi laifin yayanki ne tunda ya ga na matsu in taho jiyan sai ya hana ya fake da cewa Innarsu ba lafiya ('Yarsa) in bari ta kara samin sauki zuwa yau zazzabi ne a kawai kin dai san halin mazan nan da kulafuci gay a can waje sai da ya biyo ni Muneeba ta kai mata duka lallai yarinya yayan nawa kike cewa haka. zan kuwa gaya masa". "Gaya masa din ai ba zai iya ragewa ba dọn ni din ba ta wasa bace suka yi dariya., Murja ta tashi ta shige cikin dawayen Munecba 57 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria dake cike da gidan sukaci gaba da gudanar da abubuwan da ya dace. Ranar Suna yaran an canza musu suna Hassan ya ci sunan Bilal Hussaini kuma Hilal sunaye ne masu kyau na sahabban Annabi Muhammadu (SAW) kowa ya san Bilal Babban Bawan Annabi ne kuma mai kiran Sallah'a masallacin ka'aba shi kuma Hilal wani sahabi ne cikin Sahabban Manzon Allah. Mujeeb ne yake yi wa su Goggo wannan bayanin. Suna kam ya kayatar fiye da tunanin mai tunani don musamman Mujeeb ya ba da odar yin abinci nau'i goma sha biyar a wani hotel sune suka kawo abincin a motar din tare da ma'aikatansu, su suka dinga rabawa abincin ga jama'a babu nuna bambanci duk abin da kake so shi ake kawo maka tun daga abincin zamani har dana gargajiya irinsu dambu, fate, danwake, birabisko da sauransu. Hatta fura da nono sai da aka zuba shi cikin wasu robobi a damensu ake rabawa dasu 58 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria kunun gyada dana gero da na shinkafa abubuwa masu sanyi kuwa basu da iyaka na kanti da na yin hannu kayan Sobeniyos kuwa wata babbar jaka ce tamkar tirabilin bag jakar yin tafiya mai dauke da hotunan 'yan biyu an shade cikinta da tarkace a kalla kala goma sha biyu duk masu dauke da hotunan yaran haka ake ba kowa babu wani bambanci duk itace dai jakar mai kaya a ciki ake ba kowa. Muneeba. da 'ya'yanta kaya masu asalin kyau da tsada suka dinga sawa dama ta bada shaddoji da atamfofi masu tsada da Maman Dijah kawarta zasuje Dubai da Mijinta aka dinko mata su rantsattsun dinkuna masu tsada aka yo mata tun kafin ta haihu shine bata sa ba ta bari sai da ta haihu., Ai kuwa ranar suna ta sha kallo da tsegunguna musamman gurin dangin Suwaiba wata Kawar Hajiya Harira da ke aure a Yola take cewa Suwaiba "ke sakarya wannan kishiyar taki tasha gabanki gurin Miji dubi fa suturun 59 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria alfarmar da take sakawa tana fiddawa leshina masu tsada akalla kowanne daya ya tasamma dubu saba'in jibi shaddojinta suma gezna ne masu tsada atamfofi ina lura sufofi ne Exclusive sai Super Sheraton da Aura ko Holland banga ta saba ga dinkunanta duk irin wadanda ake yowa daga Dubai ne ke kina nan kina fama da atamfar Ingila. Shin wai ke kina ina da har zai kashe mata wannan dukiyar ke bai yi miki ba? Lallai Suwaiba ke sakarya ce dubi gwal din wuyanta a kalla yayi dubu dari biyar, dubi wuyanki kina fama da dan kunnin SAUDI du kina naki 'Yan Dubai din. Suwaiba tayi tsuru-tsuru don kuwa nata sunci kasuwa kudaden na gidan bokaye, wannan fan Saudia ma na Hajiyarta ne ta ara mata, gashi tsinannun bokaye sun cinye mata kudi sunci moriyar jikinta babu wata nasara, ko da na sararma ba'a dadewa tasirin abin yake karyewa ita kam ta gama yawo don bata yi tunanin kayan jikin 60 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria Muneeba masu tsada har haka bane, kwarai ta yarda masu tsadane da adadin kudadensu da kawar Hajiyarta ta fada tunda mijin ta mai hali ne itama surutu masu tsada ta ke sa wa. Ta dubi Hajiyar Yola (Yadda suke kiran kanwar Hajiya Harira kenan) ta ce, "Wallahi Hajiya bani da wata fawa yanzu a gidan nan matarnar ita ce a gabansa, balle yanzu da ta haifo masa 'yan biyun nan Wallahi tamkar ya hadiye su yake ji ita da 'ya'yan har fa Ofis yake kin zuwa yana can yana kallon 'ya'yan tamkar ba'a taба yi masa haihuwa ba sai fa ya wuni a dakin ba ma na sanin yana gidan sai idan naga motarsa idan dare ne can yake bacci har sai Goggonsa dake zama dasu tace ya je ya kwanta zasu rufe kofa sannan zai bar dakin in dai asiri ne suka yi masu Wallahi ya ratsa jikinsa sosai yayi tasiri kafin in shawo kansa zan sha wahala. Ta soma matsar kwalla Hajiyar Yola ta ce "Ke kwantar da hankalinki idan an kwana biyu ki riko kudi kizo ki 61 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria sameni a Yola zan kaiki inda za'a share maki hawaye, ita din banza Wallahi sai ta raina kanta sai sun zamo tamkar kasha ita da 'ya'yanta a cikin gidan nan mu za a yi wa haka du kina Yaya Harira take ake yi miki wnanan cin kashin a tsakarka? Ai mu duk zuri'armu ba sa boranci dole ne ki zama mowa a gidan nan lallai Yaya Harira ta yi sanyi ruwa ya doki Babban Zakara. Suwaiba tace Wallahi tayi iya kokarinta da nice ke fada aji ana damawa a gidan nan tsautsayi ne ya afko ya karya asirin da mukayi tunda har korar ta yayi a gidan nan ta kusa shekara a gidansu sanadin kwanciyarsa a asibiti ne ta dawo shine fa al'amura suka chanza sam yanzu asiri ba ya kama su ita da shi., Hajiyar Yola tayi Kwafa tacс, Karyarsu tasha karya zamu kai sunansu inda za'a karya lagonsu sai mun cire Imani akan aikin da za'a yi musu ke dai ki yi kodari kizo Yola ki same ni”. 62 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria Ba su sake firgita da al'amarin ba sai da aka debo jakunkunan Sobeniyos guda dari aka kawowa Suwaiba akace gashi nan ta rabawa jama'arta da suka zo har ma da wadanda basu sami damar zuwa bad a suka bude jaka daya suka ga irin kayayyakin da ke ciki sai da Hajiyan Yola ta zunbduma ashar "Kan jakar Uban nan lallai Suwaiba sai kin mide tsaye akan matar nan don ta yi miki fintinkau akwai babbar tazara a tsakaninku ta sami mijinku irin yadda ake so, ko tana aiki ne?. Ta girgiza kai fuskarta cike da damuwa ta cc, "ba ta fara aiki ba ta dai gama Karatunta duk wannan hidimar shi yayi tunda yanzu yana samun kudi sosai fiye da da, kin san sun fara kasuwanci a Kasashen waje shi da abokinsa, sannan ga aiki yana yi, baya da matsalar kudi a rayuwarsa nice dai ya daina yi wa hidima, amma Waleeda babu abinda baya mata don ita ma akwati guda yayi mata na kayan sawa da haihuwar nan, ni kuma ya bani 63 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria zannuwa gudaa biyar duka masu tsada ne ban amso su gurin dinki ba kudin daya bani na dinki na kashe bani da wasu shi yasa ban amso ba". Hajiya ta ce "Ai wannan duk bai yi min ba dole sai na sa an yi maki gyaran bawul a gidan nan sai an sabunta kinyi tasirin gaske a zuciyarsa in kuwa bah aka ba kin dinga zama mi ara koma baya kenan". Taron suna an yi lafiya an tashi lafiya ba yadda 'yan tsegumi da hassada suka so ba duk wanda yazo taron sunan nan sai da ya koma gida cike da farin ciki kuma dauke da kayan arziki niki-Niki. Jarirai biyu Bilal da Hilal kuma suna cikin koshín lafiya su da mahaifiyarsu Mujeeb kam harya shige sabon Ofis dinsa a matsayinsa na shugaban ma'aikatansu Karin girman da ya samu ya samo asali daga irin jajircewan da kwazo da tsayawa gaskiya da Mujeeb din yayi akan girmama duk wani na gaba dashi ko da 64 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria Gyaran da ta yi wa fuskar ta sai ya maidata yarinya danya shakaf har sai da Goggo Hinde ta tanka kai 'ya'yan zamani sai a barku yanzu danyen jegon naki kika żauna kike irin wannan kwalliyar don jawo wa kai jidali ko? Ni nan uwarki sai da kika birgeni balle shi wanda kika yi dominsa Wallahi ki kula da kanki ki tausayawa yarannan don mazan nan ba kunya gare su ba duk hanyar lallaba sun santa iyakaci idan kika biye masa kika sami ciki ke zai bari da wahala babu ruwansa gara ma ki sani ni kam na gaya maki. Jikin Muneeba yayi sanyi tace "Ni fa Wallahi Goggo ba don shi nayi kwalliyata ba, na dai riga na saba ne, kuma ina nake binshi kinja gani dai shi ke zuwa nan kuma akan idonki 'ya'yansa yake biyowa ni ba ruwana don bana ma zuwa dakinsa" Goggo Hinde ta murmusa tace In ma 'ya'yansa yake biyowa ke ma ya kusa ya biyoki in dai namiji ne ba yaga 67 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria kinyi garau ba kwadai ji da shi ni babu ruwana. Muneeba ta fara kukan shagwaba tana cewa "Ni dai babu ruwana gara ma ki hana shi shigowa nan din 'ya'yanma idan yana son ganinsu ga Karime nan ta dinga kai masa su dakinsa kwalliyar ma daga yau zan daina yi. Laminde ta ce, "Ki kyaleta kawai ta yi kwalliyarta Hajiya Hinde tunda gidan nan wa kika ga tana masa kwalliya inba ita ba, mazan nan na zamani gara da hakan yadda yake ganin mata iri-iri a gurin aiki ko cikin gari gara idan ya dawo gida shima ya sami nasa abin kallon ya ji dadi shi jego ai bazai sa ka zauna ba kwalliya ba. Kina dai gani da ya dawo gidan nan sai yazo ya ganta ita 'ya'yan nan sannan ya ke samun natsuwa in da basa kwalliya suna birgeshi yaushe ma zai damu dasu, nan fa idan yazo ya makale sai kin kore shi yake tafiya hakan inace kulawa ce? Ki barta kawai taja hankalin mijinta gareta?. 68 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria Goggo Hinde tace Ai na barta tunda kin bata goyon baya Allah ya Kara so da kauna. Basu dade da gama zancen ba sai ga dan Halas dın yayi sallama ya shigo dakin ya gaidasu Goggo sannan yasa hannu ya dauki Bilal dake hannun Laminde ya rungume a kafadarsa yana cewa "Goggo yaran nan naga sunyi kiba sosai nonon ya amshe su kenan? Tace "Eh Nononta na da kjyau, amma dole za'a hada musu da madara don wannan Karamin yana da tsotso fiye da dan uwansa kaga ma ya fi shi kiba ruwan nono ba ya isarsu yace "Ok to zan tambayi abokina likita inji wace madarar ya kamata a fara basu sai a siyo musu. Yana maganar amma idanúnsa na kan Munecba wadda ke ba Hilal Nono don tun ana masa shafa yake neman nono shi ne ana gama sa masa kaya Goggo ta bata shi tace ta bashi Nono. 69 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria Ya rankwafa yana liken fuskar Hilal din ganin haka ya sa Laminde tayi saurin barin dakin Goggo Hinde ma sai ta suri bahon da ta gama yiwa Hilal wanka ta fice a dakin hakan ne ya bashi damar kai baki ya sumbaci yaron sannan ya dawoi ya sumbaci kirjin Muneeban ta dago idanu tana harararsa cikin sigar soyayya ta ce, Ka fara ko? Ya kyalkyale da dariya "ban ma fara ba zan dai fara kinga irin kyan da kika yi yau kuwa? Gaskiya jegon nan ya amshi jikinki fatarki tayi luf-luf tayi kyau ni fa na kosa 'yan tsofafaffin nan su barni da ke don Goggo Hinde tasa ido sosai a kaina". Ta ture hannuwansa dake jikinta ta ce, "Au korarsu ma kake yi? Su kuwa suna nan sun dage suna gyara maka mata da 'ya'ya to zan gayawa musu gara tun wuri sai su fara hada komatsansu. Yayi saurin cewa "Don Allah rufa min asiri da Goggo Hinden ai ni ban san gyara min ke ta ke yi ba shi 70 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria yasa na ke sonta wallahi ta san duk wasu hanyoyi da za ta yi wa jininta yaji dadi a duniya ki tambayar min ita in ma ana budatar kudi don siyan kayan gyaran naki zan bayar don bana son inji kin canza min. Ta sake dubansa "Aika fini kusa da Goggon Hinden gata can a waje sai ka je ka tambayeta don ba zan iya isar da wannan aiken naka ba ya ce "Kin san zan iya kuma ce mata zan yi in jiki kince in bata kudade akwai abubuwan da za ta siya na gyaran da take maki. Ta riko hannuwansa da ta ture tana bashi hakuri "Don girman Allah kada ka je na san zaka iya kuma Wallahi za ta iya yardan don yar kwalliyar nan da na yi yanzu cewa tayi ina neman janyowa kaina jidali, ba kunya garc ku ba ku mazan zamanin nan ya kame baki ya ce to fa! Yanzun daina yimin kwalliyar zakiyi? Ta cе "Haka ta ce nima na fara jin tsoro kwada kiran sallaar Magriba da aka yi shi ya dakatar dashi abin da yake son 71 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria fada bayinmta ya shiga ya yo alwala sannan ya fito ya wuce masallaci tun da ya dawo Sallar issha'i bai shigo dakin Muneeba ba yana can nasa dakin yana cike wasu takardu da yazo das u, amma rabin hankalinsa na kan Muneeba surorinta na ta yi wa fuskarsa shawagi kyan da tayi na ta dada dayatuwa a fuskar tasa ya tsaida abinda yake ya dauko wayarsa ya kira Ikayinta tana dauka sai yace "Ki sawa yaran nan kayan sanyi sosai yanzun zan zo mu je asibitinsu Dr. Aminullah za'a duba su don a san madarar da ya dace a soma basu". Ta ce, "Garin akwai sanyi me zai sa ba zaka bari sai gobe ba yaran nan fa basu da kwari, ya ce ba zan bari sai gobe ba yanzu nake so kiyi sauri kada ki batamin lokaci ganinan zuwa" Babu yanda ta iya dolente ta tashi tá đauko kayan sanyi masu kauri sosai ta mikawa Laminde dake rike da Bilal tana bashi ruwa tace "Asa masa kayan sanyin nan wai asibiti za mu je a 72 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria daren nan "Laminde tace "asibiti wani ne ba lafiya? ta ce "kowa lafiya za'a kaiwa likita sune wai ya duba su yaga wace irinb madara ya kamata a fara ba su". Та се "Gara kam a fara ba su madarar don mijin nan na Hajiya Hinde sai da madara". Goggo Hinde kuwa fada ta dinga yi wai don meye za a fita da yara da daren nan alhali lokaci ne na sanyi don kawai a kwaso musu sanyi. Ita dai Muneeba tana jinta ta san tunda yayi niyyar fitar tasu to ruwa da iska babu mai hana wannan fitar ko da kuwa Goggoce. Tana sakawa Hilal Safa ne ya shigo dakin cikin sallama kallo daya tayi masa ta kawar da kanta, saboda irin kyan da yayi mata cikin wasu sabbin Kananan kaya wando da riga shirt long slip sai ya kawo bakar jaket ta sanyi ya dora bisa shet din saboda sanyi sai ya koma dan saurayi abinsa. Ita ma sai ta dauko katuwar rigar sanyi ta saka sannan ta saka dogon 73 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria hijjabi ya dauki Bilal ya rungume shi ya rufe shi da babban bargo ya salami su Goggo Hinde ya fita. Ita ma tan ade Hilal a nasa bargon ta rungume shi tana cewa su Goggo sai sun dawo Goggo Hinde ta dubeta tace "Kai wannan zamani yanzun sai goyo dai ya zama tsohon yayi sam ba kwa son goya ‘ya'yansu ji dumin jikinku alhalin hakan na kara dankon soyayya tsakanin iyaye da 'ya'yansu ta ce "Gani na yi mota zamu shiga shi yasa ban goya shi ba, amma ai na rumgume shi a kirjina zai ji dumi goggo. Taja tsaki "Ni wuce ku tafi ku bani guri, yara kun sangarce da kuya kawai, ku an yi ta goyonku amma ku kiri da muzu ba zaku dinga goya naku 'ya yan ba.mu zamaninmu har da goyo kwana mukeyi. Munceba dai ta wuce ta bi bayan mijinta tabar goggo Hinde na ta korafi. A bayan motar ta iske ya kwantar da Hilal ya lullube shi da bargonsa ganin 74 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria ta tsaya tana kallon yaron sau yace "Shima kwantar da a bayan ki rufe su zan kunne hitar mota ba zasu ji sanyi ba. Та се, "Ni na so ne in rikesu duka a jikina don Goggo tace, in dinga rungumesu suna shan dumin jikina hakan na kara soyayya tsakanin uwa da dfanta ya amshi yaron a hannunta ya kwantar dashi kusa da dan uwansa shima ya rufa masa bargon suka shiga motar suka bar harabar gidan. Sai da ya hau titi sannan yayi mata magana "Ni kam yanzu na lura son yaran nan yana neman ya ture gwamnatin tawa soyayyar, in bayan haka su kadai ne wadanda zasu sha dumin jikinki ko ko ni ba'a gaya miki ya kamata ki bani kulawa bane? Shziru tayi masa ya kai hannu ya damki nata hannun yace "wai ba kiji abinda nace bane kika min shiru? Tа се "to idan na ji me kake so ince maka? Ni kadai ke gareka balle kace baka da madafa?" 75 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria Ya ce Ok haka ne fa bake kadai ba ce har kin tuna mini shike nan nagode da tunatarwa tun daga nan bai sake cewa komai ba har suka isa asibiti yayi wa Dr., Aminullah bayanin abinda ya kawo su ya kira wata Nos yayi mata bayani tare da gaya mata abinda sukeso yace ta kaisu inda ya dace. Gurin likitan yara ta kaisu aka duba yaran sannan aka rubuta musu sunan madarar da za su sayawa yaran. Sun koma gurin Dr. Aminullah suka yi masa sallama sannan suka bar asibitin wani (Super Market) ya kaisu anan ya sayawa yaran katon din madarar ya sayawa Walceda Katan din Cerelac da ta ke sha sai kayan kwalama da ya saya musu da wasu abubuwan bukatar ya kashe kudi sosai sannan suka nufo gida. A hanya sai da ya sake tsayawa ya saya masu gasassun kaji suna isa gida ya dauki Hilal ya rungume tare da wasu ledojin ya ce mai gadinsu ya kwaso sauran kayan ya biyo shi da su. 76 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria Ya dubi Munceba ya ce, ki sameni dakin a Hakan da yace ta san neman jidali yake yi" Suwaiba ta hanga ta labulen windonta tana lekensu hakan ne yasa kawai ta bi shi dakin nasa don ta san Suwaiban ta ji umurnin da yayi mata na cewa ta same shi a dakinsa kila shima ya ganta tana lekensu ne yasa Muneeban shigowa ya maida kofar falon nasa ya rufe da makulli don ya san halinta sarai zata iya biyo su don taga me za su yi. Kuma kullum yana gaya mata ta ragewa kai daraja ne ka dinga bin kwakkwafin sai ka ga me miji ke wa kishiyarka alhalin ko kin gani ba ki isa ki hana shi ba sai dai ki karawa zuciyarki takaici ya hanata shigo musu tsulum ba sallama amma tayi kunnen Rashi taki dainawa shi yasa in dai yana tare da Muneeba yake sawa dakin makulli ya rufe ba wai don tsoron kada ta ga me suke yi ba a'a baya son ta dinga katse masa abinda yake yine in 77 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria bayan hakla ta zo ta yi ta gani ita ce za ta sha takaici. Ya wuce kan doguwar kujera ya kwantar da hilal ya isa gareta ya amshi Bilal shi ma ya kwantar da shi sannan ya dawo itama ya ja hannunta suka zauna bisa (2sita) ya kwantar da kansa a kafadarta yace. "Wai laifin me dakin nan yayi miki rabonki da shigowa tun ranar su Bilal a kalla sati biyu kin daina zuwa gaishe ni sai dai ni in zo inda kike meye hujja yajin da kika yi wa dakin nan?. Ta soma nokewa saboda abubuwan da ya ke mata sannan ta ce, "Yaushe ne zan yi ta biyo ka alhalin kana zuwa ko da yaushe kana dai gani 'yan tsofaffin nan idonsu na kanmu ko zuwa dakina ka yi basa jurar suji mu shiru a daki idan ka daďe ma korarka Goggo Hinde ke yi, ka yi hakuri kawai har su tafi tsanani ai bai wuce su yi arba'in biyu ba'sannan su tafi". Ya watso mata idanu "wane irin arba'in biyu? Kina hauka ne? lallai in 78 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria baki yi wani abu akan faruwar hakan ba to zan nuna rashin hakuri na karara don Wallahi na shiga halin takura". Та kalleshi cike da mamaki "Ni fa kana bani mamaki wai shin me yake amfanin aje mata biyu a gida ina ce idan daya nada larura mutum ba zai shiga matsala ba tunda ga 'yar uwarta. Gaskiya idan ma kace kana cikin takura kai ka so hakan tunda babu wani shamaki a tsakaninku in ma rigima kuke Wallahi gara kaje ku shirya ni kam bani da abin da zan yi maka" Ya manneta sosai a jikinsa sannan ya ce, "Kina da abin da zaki yi mini, amma fa idan kika so in kuma baki so ba sai in kyaleki tashi in raka ku". Ya mike ransa a bace ya soma kokarin daukar Hilal ganin ransa ya baci sai hankalinta ya tashi don sam bata son bacin ransa ko ya ya nc. Tayi saurin isa gare shi ta rungumo bayansa tana cewa "Ka san dai jego nake `yi me kake so in yi maka? "ya sha kunu sosai ya ce "babu 79 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria komai inma akjwai na hakura sake ni in daukar miki yaron nan dare nayi kada Goggo Hinde ta ga kin dade don na lura ka'idojin sosai take kafa maki a kaina gara ki dinga kiyayewa". Kalamansa ya nuna ya ji haushi sosai akan abinda ta yi masa, sai ta shiga lallashinsa tana bashi hakuri amma ya basar ya ce ya ji ya hakura su je kawai ya rakata. Ya dauki Hilal ita kuma ta biyo shi da Bilal har dakinta ya kwantar da yaron ya koma dakinsa ya debo ledojin da suka dawo dasu da kwalin madarar yaran yazo ya aje mata su Goggo Hinde kawai yayi wa sai da safe ya fice abinsa. Shirin kwanciya kawai tayi, suka kwanta ita da yaranta amma fa ta yi bacci ne zuciyarna cike da tunanin halin da mijin nata yake ciki shin ita wai meye laifinta don ta ce jego take yi kuma shi ina amfanin aje mata biyu in har wata ba zata iya daukc masa 80 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria matsalarsa ba shine fa abin yin fushi meye laifinta anan? Washe gari tana dakin baccinta tana jinshi a falo ya tsaya suka gaisa da su Goggo Hinde ya duba yaransa sannan yayi musu sallama ya ce ya wuce ofis, su kansu sun yi mamaki da bai nemi Muneeba ba kuma bai leka dakin gurinta ba. Wunin ranar sai abinda yayi mata yayi ta damunta da kyar ta samu ta saki ranta har ta manta da abin shima abin ya yi ta damun zuciyarsa sai dai ya yanke kansa shawarar yau dole ya kai Suwaiba asibiti don a auna jininta a tabbatar masa da lafiyarta ko ya sami madafa don kuwa ba zai iya jure har nan da kusan wata daya yana juriya ba alhalin yana da wata matar. In har ya tabbata suwaibar garau take to zai lallaba da ita don babu yanda zai yi shi kam ba

Chapter 3 of 8