Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
2 / 8
acewarsa bai taba ganin macen da ciki ya wahalar irinta ba. Mujecb ya shigo dakinta cikin shirin bacci a wani dare kasancewar tunda cikinta ya shiga wata tara gurinta ya koma kacokan da kwana da suwaiban ta soma tawaye sai yayi mata matashiya da cewa ai dole ne a ramawa 26 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria kura aniyarta tunda ita ma duk haihuwarta da tayi guda biyu da watan haihuwa ya tsaya dakin ta yake komawa da kwana. Da ya gayawa Goggo take ta goyi bayan hakan ita ma acewarta ai dama kyan cin tuwon kishiya ramako. Hakan ya bakanta ran Suwaiba na yadda kiri da muzu Goggo ta ke so ta maida Muneeba wata yar gaban goshenta kawai don zata haifo yan biyu dadin abin dai kafin ayi daran akayi kwandi ita ta fara haihuwa har biyu kafin Muneebar na mijin ma itace ta fara balle ayi, mata wani kan kajere haka ta dubi tsabar idon Goggo ta gaya mata. Mujeeb ya zauna a gaban Muneeba cike da tausayinta karara a fuskarsa ya cc“Sannu da kokari ya jikin na ki? Ta lumshe idanu, jiki Alhamdulillah bacci nake son in shiga ciki inyi amma tun dazu na kasa tashi kafafuna sun rike. ya ce to ba sai ki kirani a waya ba bako na yi ina can 27 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria waje hankali na gurinki". Ya mikar da ita tsaye a hankali ya riketa suka shiga dakin baccinta sai da ya tabbatar ta kwanta sannan ya je ya kullo kofofinta ya dawo ya zauna gefen gadon yayi mata magana kin yi bacci ne? ta ce ido na biyu a yan kwanakin nan ban cika samun bacci ba ya ce wata shawara nayi tunda kinki yarda in fita da ke wata Kasa ki haihu a can to ko asibitin zan kaiki ki zauna can ana kulawa dake har ki haihu don ni ka mina tsoron kada ki haihu a gida ko nakudar tazo miki cikin dare mu rasa yadda za mu yi da ke". da Ta tashi zaune ta jingina Allon gado, sannan ta ce, Gara dai ka barmi a gida kai kanka zaka fi samun natsuwa idan ina gidan kuma a yadda suka ce a asibiti da zarar naji ciwo ko yaya ne muyi gaggawar zuwa asibit ka yi hakuri kawai Insha Allahu babu wata matsala da za'a samu zan haihu lafiya. Shi kenan tunda kince haka zamu ci gaba da addu'a Allah ya saukeki 28 A WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria lafiya ba ta sami bacci ba sai da yayi ta mammatsa mata jikinta da kafafunta sannan ta samu yin bacci. Da asuba sun shiga ba yi zata yi alwala tun a gurin fitsari taji wani abu na mata zugi da radadi a gabanta sai ta gaya masa yasa cocila ya haska sai yaga ashe wani dan kurji ne ya fito mata a bakin gaban دو nata. Ya gaya mata abin da ya gani amma yace dole da safe suje asibiti don kada a sami matsalar sun sami ganin likita tayi wa likita bayanin matsalarta Allah yasa mace ce likitar shi yasa ba ta dar da lokacin da ta umurceta taje gado ta kwanta zata duba ta sai da likitar ta taimaka mata wajen hawa gadon don kuwa kasata tayi. ji Likita ta duba kurjin ta ga yadda yayi daga bisani ta rubuta mata magunguna da zasu siya ta sha don ya noke in kuma bai noke ba to zaiyi ruwa sai suzo a yanka shi a cire kwayar. Tun a mota Muneeba ke addu'ar Allah ya sa ma ya noke din kada yayi ruwa ace 29 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria za'a yanka ta kila kafin ya warke zata haihu in kuwa haihuwa tazo ga yanka a guri ai ba karamar azaba zata sha ba. Tun da ta fara shan magunguna sai kurjin ya soma nokewa amma duk da haka yana mata zogi tamkar yana duran ruwa data gayawa Mujeeb sai yace ta bari ta shanye magungunan in bai daina zugin. ba sai su koma asibitin har ta a shanye maganin zugin bai daina ba sai suka sake komawa asibitin wani maganin aka sake bata. Cikin dare ranar wata laraba ne ta fara nakuda amma ciwon ba sosai ya ke mata ba shi yasa take ganin tamkar ciwon bana nakuda bane ciwon bai yi mata tsanani ba sai bayan da ta idar da Sallah Subahi. Wani abun mamaki da ta gani lokacin da ta shiga bayi shine marurun da ke gabanta yayi wani irin girma tamkar an hura balam-balam ya rufe duka gabanta don tayi kokarin ta nemi wata kafa a gaban nata taji babu. Tun a bayin ta kwalawa Mujeeb kira a guje ya shigo bayin kuma a 30 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria tsorace yana ganin yadda marurun yayi sai abin ya tsorata shi da sauri ya fita yaje ya gayawa Goggo suka dawo tare itama taga wannan abun al'ajabi tayi salati tana cewa 'Wannan ai babbar matsala ce saboda yadda take nakudar nan idan haihuwar tazo to fa babu kofar da 'ya'yan nan zasu fito marurun ya rufe ko ina ruf". Mujeeb ya sake tsorata ya ce "goggo taimaka mata sai muje asibiti kawai" ya soma harhado kayan da ta shirya don zuwa haihuwa Goggo ta dube shit a ce"Kira suwaiba don bata sani ba sai mu tafi asibitin da kai ita sai ta zauna a gida", shi sai a lokacin ne ma ya tuna bai gayawa Suwaiban ba. Yadda tazo ta iske irin yanayin matsalar da akace Munceban ta samu sai ta nuna damuwarta a zahirance amma a can cikin zuciyarta murna ta dinga ganin hakarsu zata cimma ruwa. Suna tafiya asibiti Suwaiba ta koma daki tana rawa tana juyi ta dauko wayarta ta kira layin Hajiyarta cikin 31 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria murna tace "Hajiya yau dai burinmu zai cika akan tsinanniyar matar nan gata can tana nakuda sun tafi asibiti "To da suka tafi asibitin me ya faru? Abin da boka yace mu zura ido mu sha kallo ya faru din ne? Hajiyarta ce ta tari numfashin Suwaiba ta ce "Ai kuwa ya faru kurji na nan ya fito ya rufe gabanta babu inda 'ya'yan za su fito kinga sai dais u mutu a ciki. In kuma aka yi mata aiki aka ciro 'ya'yan aida sauran rina a kaba. "Au kin manta boka ya ce muddin aka yi mata aiki ko aka yanka kurjin jini ne zai tsinke mata yayi ta zuba har ta a mutu 'ya'yan ne kawai zasu rayu? Ta се. "ban manta ba amma don ta mutu ai an kashe macijine ba'a sara kansa ba ke da muke son ita da 'ya'yan duk su mutu a huta shine har zaki yi murna don ita ta mutu 'ya'ya na nan da ransu. Suwaiba tayi ajiyar zuciya to yanzu me ya abin yi Hajiya ta ce Abin 32 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zarja yi kawai ki san yadda zaki yi ki ba mijinki shawarar kada a yadda a yanka kurjin nan kice kin taba ganin wata ta yi irin shi da zata haihu ana yankawa jinni yayi ta zuba har ta mutu, kinga idan ya bi shawararki shikenan ita da 'ya'yan sai buzunsu mun rabu da alakakai. Suwaiba da hanzarinta tayi saurin kiran Mujeeb a waya tana tambayarsa wai Muneeba ta haihu ne ya ce "Ba ta haihu ba marurun da ya futo mata yayi girma har ya toshe kofar da 'ya'yan zasu fito yanzu haka ana tunanin aiki za'a yi mata. "Aiki? Gaskiya kada ka yarda ayi mata aiki don ni na taba ganin wata kanwar kawata irin haka ne ya sameta da ta zo haihuwa sai aka yi mata aiki daga ita har 'yar cikin nata mutuwa sukayi wai ashe ba'a sawa marurun wuka abin kamar iska ne ka ga abin akwai tsoro gara dai a jira kila a sami kafar da 'ya'yan za su fito. Jin kalaman Suwaiba sai Mujeeb ya tsorata shi dama sai da yayi tunani 33 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria ko dai aikin jinnu ne tunda babu irin badda bamin da ba sa yi shi kam da ya rasa Muneeba gara ya rasa 'ya'yan tunanin kiran Malam Abubakar yazo ransa ya lalubo wayarsa a aljihu ya kira layin Malam din bayan sun gaisa yake shaida masa matsalar data sami Muneeba. Malam Abubajar ya ce "Yanzu haka tana ina ne? ya ce mun kaita asibiti sun mace idan ba ta haihu ba nan da awa daya zasu yi mata C.S. sm yasa nace bari in gaya maka ko da ani taimakon da zaka yi mana ni kam bana son son su yanka ta". Malam ya numfasa akwai abinda zan taimaka dashi Insha Allahu kuma za'a dace in dai ba'a sami miskila ba wajen debo abin akwai wani ganye vana fitowa ne a tsakanin duwatsu kuma ya kan fito ne daga sha biyun rana zuwa daya na rana sai ya noke ya koma sai kuma gobe zai sake fitowa shi zaka je ka debo Insha Allahu idan aka murjeshi ruwan za'a shafa mata akan 34 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria marurun zai fashe da kansa ba sai an yanka ba kuma zata haihu lafiya ba sai an yi mata wani aiki ba. Mujeeb ya ce "Yanzu Malam a ina za'a debo ganyen na san kila ka taba debowa? Ya ce "wane asibiti kuke sai inzo in sameka muje kafin sha biyun tayi anfi son ya fito a idanunmu Mujeeb ya gaya masa asibitin sannan ya fito harabar asibitin yana tsimayin jiransa ganin har sha daya saura a lokacin Malam din na zuwa suka tafi a motarsa can bayan gari suka je wajen wani dutse suka zauna a daidai inda suke tsammanin ganyen zai fito cikin ikon Allah sha biyun na yi da minti daya ganyen ya fara yin tsiro yana fitowa Malam ya taba Mujeeb ya nuna masa Mujeeb yayi tsiru-tsiru yana kallon ikon Allah har ganyen yayi fala-fala kore shar sannan Malam yace yasa hannu ya tsinka Mujeeb yayi Bismillah yasa hannu ya tsinka, sannan suka tashi a gaggauce suka bar gurin suka koma asibiti Mujeeb yayiwa Goggo bayanin 35 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria ganyen tare da shaida mata yadda zata yi har ta a je ta shafawa marurun inda Allah ya taimakesu har da kawar Munceba cikin masu amsar haihuwar ta wato Sister Hadiza ita Goggo taba ganyen tayi bayanin komai cikin ikon Allah Sisiter hadiza na m ruza ganyen ta shafa ruwan a kan marurun sai ga shi ya fashe ruwan da ke cikin duk ya tsiyaye gurin sai ya koma tamkar babu wani kurji har an sami hanyar da zata haihu lafiya. Tamkar jira haihuwar take yi kurjin nan ya fashe sai nakudar ta taso gadan-gadan ba a fi mintuna talatin ba Muneeba ta sauka lafiya ta haifo kyawawan yaranta maza guda biyu kuma babu wani jinkiri tsakanin haihuwarta su don cibiyarsu ma a hade ta ke sune (Identical Twins) masu tsananin kama da juna. Tana kwance bayan ta haihu tana kallon Nosis suna ta aikin gogewa yaran jiki ita kuma har an gama yi mata duk abubuwan da ya dace amma sun ce 36 WATA KUSAN 4 Rähmatu Hassan Zaria sai an yi mata dinki don ta sami karuwa da yawa. Ta so tace musu bata son dinki. saboda irin wahalar datasha amma sai ta tuna a littafin DON MA'AURATA data karanta an nuna muhimmancin yin dinki ga matar da ta karu a lokacin haihuwa don in ba'ayi ba mace zata iya samun matsala da mijinta yayin da ya dawo gareta bayan tayi arba'in don zaiji ta ba daidai ba shi yasa gara ka tsaya a dinke karuwar da kayi daga nan kuma sai ka kara da gyara na musamman. Su gogon dake waje tare da Inna Amina da su Khairee da suka zo daga baya duk hankalinsu a tashe yake don basu sake ganbin wata cikin Nosis din da ke karbar haihuwar Muneeba wata ta fito ba balle su san me ake ciki ta haihu ne ko ba ta haihu ba. Sister Hadiza ce ta fito ta nufu su duk suka tsura mata idanu ganin tana cike da fara'a yasa suma suka tarbe ta da fara'a suna tambayarta "Munji shiru ta haihu ne? Ta fadada fara'arta 37 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria "Barkanmu da arziki Goggo ta sauka lafiya kun samu mazaje Goggo ta Hassan Mama kuma mun baki Hussaini. Hamdala su goggo suka dinga yi babu ma irin Inna Amina tafi kowa murna su Khairee kuwa wani irin uban ihu suka saka na murna Inna Amina ta dube su ta ce "Kai kuna da hankali kuwa? Dubi yanda kukasa hankulan mutane ya dawo kanmu haka ake murna in banda shashanci. Sisiter Hadiza ta ce "Ai abin ne abin murna mama ni yanzu ina baban 'yan biyu inyi masa albishir don na san zan sami babban goro? Inna Amina ta ce "Yanzu yaje yin Sallah a masallaci Wallahi-Wallahi maza ki bishi ki amshi Babban Goro nima ga nawa goron albishir din" Inna Amina ta balle fosta din hannunta ta zaro 'yan 'dari biyar biyar sababbi dal ko kirgawa bata yi ba ta mikawa Sister Hadiza ita ta ce. Haba Mama Wallahi ba zan amsa ba, ko shi ma da ika ji nace haka ai ba 38 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria masar zan yi ba ni Muneeba ai ta wucе kawa a gurina yar uwa tace. Dole Inna Amina ta maida kudinta jaka tan a hararar Khausar data miko mata hannu cikin tsokana tan ace, Mama miko mana tukucin tunda bataso ba'a maida hannun kyauta baya. Sister Hadiza tana shirye-shiryen barin gurin sai ga Mujeeb ya karaso duk sai sukayi shiru suka kyaleta ta fara sanar masa da haihuwar ta tare shi da Congratulation kawata ta sauka lafiya an sami (Identical Twins) masu kama da kai. Hannuwa Mujeeb ya daga sama "Alhamdulillah" Masha Allah ina godiya mara iyaka gare ka ya Allah da ka azurtani da wadannan 'ya'ya Allah ka albarkaci rayuwarsu ka ba mahaifiyarsu lafiya". Wata irin murna da bai taba ji b a rayuwarsa ita yaji a yau don ko lokacin da aka Haifa Baffa baije irin wannan Murnar ba a ganinsa dila don Muneeba ta dade ta haihu dashi bane 39 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria yasa yake wannan murnar ko kuma dalilin irin son da yake mata ne". Ya dubi Hadiza yace, Sannu da Kokari Hadiza mun gode kwarai da irin kulawa da gudunmmuwar da kika ba Kawarki Wallahi na` fidda raid a samun rayuwarta ita da 'ya'yan da ke cikinta yanzu a masallaci kuka na dinga yi da hawaye ina gayawa Allah matsalarta tare da rokonsa ya kawo mata dauki ya raba ta da cikin nan lafiya har mutanen da ke cikin masallacin suka yi ta kallo na. da kuzar na baro masallaci saboda zuciya ta da sami yakinin tabba Sallah ya amshi addu'ar ta ashe gaske ne sai gashi kun tare ni da wannan daddadan labarin lallai Allah abin godiya ne kuma abin dogaro ne". Ya zura hannu a aljihun rigarsa ya fiddo kudade da bai san yawan su ba 'yan dubu dubu ya mikawa sister Hadiza yace "Ga tukuicin wannan daddadan albishir da kika yi min. Ta hade hannuwanta guri guda tana girgiza kai Haba Haba gaskiya ba 40 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria zan amsa ba ai ka wuce nan kabar kudinka, ya bata rai ai kema kin wuce nan kuma kinfi karfin kudin nan a gurina wannan na yi maki ne don in nuna irin jin dadi na da nuna godiya ta ga Allah da wannan arziki da yayi mini ke din nan kin cancanci in yi miki komai kece kika fara sanin Muneeba na da ciki sannan yau ke ce kika fara sanar da ni ta haihu kinga kuwa ai kin wuce kyautar wadannan kudi don girman Allah ki amsa kada mu yi haka dake". Jin ya hada ta da girman Allah yasa ta amsa tare da yi masa godiya tare suka karasa gurinsu Goggo nan fa suka shiga yi wa Juna barka, Inna Amina ta dubi Sister Hadiza tace idan an gyara yaran don Allah akawo mana su mu gansu "Ta ce Eh ai za mu kawo su na barsu ana gyara su në ita kuma don Allah idan an fito da ita ku barta ta yi bacci ta huta sosai saboda data sha wahala da yawa "Ai dole mu hana kowa shiga gurinta su dai yara shigansu 41 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zària ita kam dole a'barta ta huta gajiyar da ta sha". Inji goggo Mujceb na can zaune bisa wata kujera yana ta sanar da 'yan uwa da abokan arziki haihuwar da aka yi masa Suwaiba kam daya gaya mata Kiris ya rage ta zabga kururuwa sai Allah ya taimaketa ta kashe wayar sannan ta zabga ihu tana cewa yau na shiga uku na lalace! Muneeba ta hangi 'yan biyu? Wallahi sai na yi ajalin 'ya'yan nan tunda ita ta gagareni ita dimma ba zan kyaleta ba sai na ga bayanta. Tana kokarin kiran Hajiyarta ta shaida mata wannan Mummunan labarai (Acewarta) sai kiran Mujeeb ya sake shigowa wayarta ta ja uban tsaki sannan ta dauka yace, Baki ji abinda na gaya maki ba Munceba ta hangi 'yan biyu maza ki gayawa Waleeda da ta sami kanni yanzu ma zan turo Direba na Ofis ya dauko ku sai ku shirya kafin ya niso. Cikc da bakin ciki ta yi magana "Kada ka turo shi yanzu girki nake ban 42 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria gama ba idan na gama zamu taho da Rabe Direba yana nan ya dawo yace 'Ok to don Allah ki haďo duk abubuwan da suka dace maijegon sai ki yo mata kunun gyada da farfesu saboda ta sami ruwan Nono. Hum! Kawai ta fada sai ta kashe wayar tare da yin wani matsiyacin tsaki tana fadin "Ji wani kitifi har sai an jaddadamin in kawo abubuwan da suka dace "Ki yo mata kunun gyada da farfesu saboda ta sami ruwan Nono" Ta kwaikwayi muryarsa lokacin da ke bata umurnin sannan tace in ban yi ba sai ayi yaya dani? Kawai zan yi mata ne don in ramawa kura aniyarta tunda ni kam tayi dawaniya da ni a haihuwar Baffa da Waleeda amma in ba haka ba shi ma ya san in banga dama ba ba zan yi ba kafin Sallar La'asar jama'a sun cika asibitin nan Musamman mutanen Dukku wadanda tamkar jira suke yi a fadi haihuwar su taho irin su Murja da Mustafa da su Adda fadima duk sun iso asibitin a wannan lokacin ne aka fito da 43 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria jariran cikin wasu nagartattun kayan sanyi ‘yan biyu waje kalar sararin samaniya mai haske saiti ne tare da abin daukarsu. Sister Hadiza ce da wata Nos suna fitowa aka soma rige-rigen amsarsu Sister Hadiza tana murmushi tace kuyi hakuri gurin babansu zan fara kaisu sai in dawo muku dasu". Murja tace "Haba Sister yadda muka kosa mu ga yaran nan shine zaku yi mana kwalele 'ya'ya ai sai ya gaji da ganinsu mu tafiya zamu yi mu bar shi da su. Ta ce Eh haka ne amma dai yanzu kuyi mana hakuri mu fara kai masa yanzu zamu dawo muku dasu Mujeeb shi da Mustafa ne a zaune a lokacin da suka kai masa yanzun za mu dawo muku dasu" Mujccb shi da Mustafa ne a zaunc a lokacin da suka kai masa yaran sai bai amshesu ba Mustafa ne ya amshi daya sai ya nade saboda su Goggona kallonsa ya ce "Ga su Goggo can su ya kamata ku fara basu kada su nayi rashin 44 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria kunya ku maidasu can don Allah kada muyi laifi. Yana maganar amma idanunsa na kan fuskar yaron da Mustafa ya amsa Godiya ga Allah kawai yake yi a zuciyarsa saboda azurtashi da yayi da wadannan kyawawan yara masu tsananin kama da shi don ba'a taba haifo (Photocopy) dinsa ba irin wadannan yaran, sai ya ji tsananin son su ya kara darsuwa a zuciyarsa. Mustafa yayi wa yaron hannunsa addu'a sannan ya tambayesu "wannan wa ye na dauka? Don na ga kamar tasu tayi yawa". Hadiza tace wannan shi ne Hassan ga Hussaini nan ka duba gaban rigarsa mun manna sunansa don kada a shiga rudu kamannin yaran akwai rikitarwa mu kanmu da muka amshi haihuwarsu sun so su rikita shi yasa muka mannawa kowa sunansa". Ya mika mata Hassan ya amshi Hussaini Shi ma ya yi masa addu'a ya miko musu yace Don Allah ku kaiwa su Goggo kallonmu suke yi tayi kada mu yi laifi. 45 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria Mujeeb yace "Don Allah Hadiza zan iya ganin Muneeban don ni ita na damu in ga halin da ta ke ciki ta сe Ok zaka iya ganinta tunda na san ba zaka dameta da surutu ba, su ma Matan ba wai mun hanasu bane ba ma so aje a tsaya a gurinta ne ana ta surutu muna so ne ta sami isashshen bacci ta yadda za ta huta sosai ku biyo ni in kaiku gurinta sun kaiwa su Goggo yaransa, suka shiga dakin da Muneeban take ita dasu Mujeeb kowa ya amshi yaran nan sai ka ji ya ambaci masha Allah saboda kyan yaran gasu da girma tamkar ba 'yan biyu ba. Nan da nan su Khausar suka fara daukansu hotuna a tsadaddun wayoyinsu (Iphone) suka saka hotunan a cikin (Whatsapp) dinsu. Mujceb na shiga ya iske Muneeba kwance bisa gado daya dake dakin idanunta a rufe ga alama bacci take yi ya tsaya daidai kanta yana yadda ta rame rana daya kacal dagani ka san ba Karamar wahala ta sha wajen haihuwar nan ba tausayinta ne karara 46 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria ya bayyana a fuskarsa har ta kaiga ya kasa jurewa sai da ya risina ya sumbaci fuskarta sannan ya kai hannu yana shafar gashin kanta yana mai dashi baya. Sam bai ji kunyar Mustafa ba da ke tsaye kusa da shi kila ma ya manta da shi ne ta yi alamun zata bude idanu sai kuma taci gaba da baccinta sun dan jima a dakin sannan Mustafa ya shafa cikinsa yace "kai ni fa hantsi yadubi ludayi 'yar Gusau nake ji kaina ga ba ma kajin yunwa murna ta kosar da kai". Ya shafa nasa cikin shima yace "Karka tunamin wai ance da mahaukaci ashe ya daina duka ya ce har kun tunamin Wallahi sam na manta da wata yunwa amma yanzun tunda an haihu lafiya na kuma ga matata tana lafiya to Muje mu nemi wani gidan cin abinci nan kusa muci don gaskiya ba zan iya komawa gida ba sai na yi ido hudu da matata":. Ya yi murmushi yace in ma nan zaka kwana babu mai hanaka ni dai mu 47 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria je mu ba ciki nasa hakkin. sun fita gurin cin abinci su kuma su Inna Amina suka dinga shigowa suna ganin Muneeba suna fita saboda har a lokacin bacci take yi ga dukkan alamu ma allurar bacci akayi mata tun a gurin cin abincin nan Mujeeb ya soma sadaka ya siye kaf abincin da ke gurin cin abincin yace a raba wa almajirai da gajiyayyu da ma duk wanda ke da bukata. Kafin su bar gurin har ma'aikatan gurin sun soma raba abincin Muneeba ba ta farka daga baccin da take yi ba sai gab da Magriba a lokacin Mujeeb ne ke dakin don kuwa ya kasa ya tsare ba zai bar asibitin ba sai ta farka, ya tsaya a gabanta yana mata sannu da ya ga tana dodarin mikewa sai ya kamat. Zaunar da ita yana ta faman yi mata sannu ya tambaycta "Mc zaki ci? Akwai kunu akwai Ti ga farfesun can Suwaiba ta yo miki da kunun gyada mama Amina tasa anyo miki kunun alkama da farfesun kaza wane zaki ci? Dama da wata irin 48 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria mahaukaciyar yunwa ta tashi sai tace zan sha kunun alkamanm da farfesun kajin amma ka bani ruwa zan wanke baki na. Yayi sauri yaje ya kawo mata ruwa da burosh da makilin ta wanke bakinta, sannan ya kira Inna Amina tazo ta zuba kunun ta sa wadatacciyar madara ta soma sha. Inna Amina ta ce sannu da kokari Allah ya kara miki lafiya, bari a kawo yaran idan kin gama ki ba su nono don tun dazun suke tsotson hannu suna neman nono sai ruwan dumi da glocouse kawai ake basu". Muneeba ta dan 6ata rai "Mama tun yanzu za'a fara ba su nono inace sai gobe? Mama ta harareta "Inji waya ce maki sai gobe? Ai ana haihuwar yara da an wanke su ake soma basu Nono kema don kina bacci ne aka kyaleki to in ba'a basu nono me za'a basu?. Tace "Ruwan dumi mana mama Amina tayi tsaki ta kyaleta tan agama shan kunun ta zuba farfesun kajin a filet 49 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria ta mida mata ta ce "Gashi nan ki cinye duka ki bani filet din, sannan a kawo su su sha". Та се "Mama duka wannan ai yayi min yawa a rage? Ta ce ni ba zan rage ba don banga yawan da yayi ba in za ki dage ki dinga cin abinci sosai ki. dage shayar da yara biyu bana rago bane in ba haka ba ki kanjame saboda tsotso". Ba ta sake yin musu ba ta amshi ferfesun ta cinye shi tas kasusuwa kawai ta bari a filet din su Khairi suka shigo da yaran suka dora mata su bisa cinyarta suna tsokanarta "Bude nonon ki basu" Ta Hararesu ta ce 'Idan na ki fa? Mu gayawa Mama gata can waje ita ta turo mu ko mu haďoki da babansu kinga kuwa yadda yake son yaran nan Wallahi kamar zai hadiyesu ya wani. rungume su dukansu sai sumbatar kumatunsu yake yi shine Mama ta ce mu amso su Magariba ta gabato amkawo su ki basu Nono. 50 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaría Bude kawai ki basu kada mu tara miki jama'a azo aga kukanki don Wallahi tsotson farkon nan akwai zafi ni kuka riris na dinga yi? Kausar ta harari Khairi da tayi magana tace Ok to zuga ta kina cewa da zafi Wallahi sai in kira mata Goggo. Muneeba na jin haka ta fiddo nonon tace to Antis dina a bani ruwa in wanke nonon sai azo a koyamin yadda zanyi musu. Maganarta ta basu dariya khairi ta shiga bayi cikin dakinta ta debo ruwa a karamin baho ta kawo mata ta wanke nonon sannan suka taimaka mata ta soma ba yaran suna cafka a take ta ji wani zafi tamkar zata kwala ihu ba ta yi ihun ba illa rintse ido da tayi har suka sha nonon ba'a salami Munceba sai washe gari da ta haihu a ranar Mujceb yayi barin kudi wajen vin sadaka ga nakasassu da kyauta ga jama'ar annabi mabukata da yan uwa bar sai da Suwaiba ta tare shi da maganar wannan irin barin kudl da yake yi". 51 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria "wai baban Waleeda ba'a taba yi maka haihuwa ba ne da kai ke ta barin naira haka? Ko dai ni da na fara aje maka kwanka a duniya a ranar banga kayi wannan barin kudin bako su nawa ba yayan so bane yanzu ne aka haifo maka 'ya'yan so tunda matar so ce ta haife su? Ya girgiza kai yana murmushi yace Duk 'ya'yanda aka Haifa mini babu wanda bana so kuma babu wanda ba zan nuna masa so ba tunda jinni na ne, amma kin san kyautar 'ya'ya biyu a lokaci daya babbar kyautace kuma dole ne in nuna wa Allah godiya ta. Shin akwai aibu ne idan nayi sadaka don in nunawa Allah godiya ta? kasa-kasa tayi magana cikin kunkuni, ni bance da aibu ba. amma gani nayi tu yanzu zaka fara nuna bambanci tsakanin 'ya'yanka ya cc "Eh kece dai kike ganin haka amma ni ban gani don banga abin da nayi ba korafi ne kawai zirin na ki da ba ya karewa bai ci gaba da sauraronta ba ya fice ya bar mata dakin. 52 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria Inna Amina ta kira Innar su Muneeba don su yi shawarar wadda zata zauna da Munceba

Chapter 2 of 8