Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
1 / 8
An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels WATA KUSAN RAHMATU HASSAN ZARIA (Mrs. AbdultahtS. Polo) WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria *** *** **** **** Mummunan tashin hankali nan yayi tsananin firgita zuciyar Mujceb, shi ne har yayi sanadiyyar da ransa yayi balaguro na wucin gadi kafin daga bisani ya dawo gareshi cikin dakiku kadan. Ya bude idanunsa a hankali yana kallon Muneeba sannan ya sake rufewa. Hannu Muneeba tasa a gefen gadonta ta dauko gorar ruwa Faro da takesha duk dare sai ta shanye babbar gora, Allah yasa shi ba ya sa yawan fitsari kamar sauran. Ta zuba a hannunta ta shafawa Mujeeb a fuskarsa, ya bude idanunsa da suka canza launi ya sauke ajiyar zuciya tare da tsira mata idanu. "Munceba abin da kika gaya min shin gaske ne ko kuwa mafarki nayi? Ta ce, "ba mafarki bane gaske ne cikin jikina babu shi tun bayan da nayi mugun mafarkin dana baka labara, ya sauke wata nannauyan ajiyar zuciya ya lalubo wayarsa da ke aje gefen gado 3 ب WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria yana tunanin shin wa ya kamata ya kira don neman taimako a wannan rikitaccen lokaci? Dr. Aminullah? Kai wannan matsalar ta wuce da sanin Aminullah. To wa zai kira? Sai ya tuna da wani Malami da suka je gurinsa akan matsalar matar wani dan ofis. dinsu da aljanu suka hanasu zaman lafiya a aurensu, kuma cikin ikon Allah an dace yanzun suna zaunensu lafiya har ta haihu da kuwa ko batan wata ba ta taba yi ba., Yana da nambar malamin din sai ya shiga laluben sunansa yayi sa'ar ganin sunan Malam Abubakar ya latsa ya. kira shi tayi ringim ba'a dauka ba yayi kira har wajen sau goma sannan Malam Abubakar ya dauka suka gaisa sai ya ke gaya masa matsalar data faru da matarsa a talatainin daren nan. Ya ce "Ka kwantar da hankalinka Insha Allahu babu matsala yanzu ina matar ta ka? Ya ce, "Ga ta nan zauna kan gado Wallahi Malam baka ga girman cikin amma yanzun babu shi, 4 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria sai cikin yayi kamar jaka wadda ba komai a ciki. Ya ce "Aikin Jinnu ne ka barni da su duk wanda aka turo yayi wannan zaluncin yau zaiga zalunci akansa kwatantamin gidan inzo yanzun nan sannan kada ka barta ta sauka bisa gadon nan har sai nazo" Ya kwatanta masa gidan. A daren Malam ya iso ya kira nambar Mujeeb yace gashi a kofar gidan ya fita yaje ya sa mai gadinsu ya bude gate din ghidan Malam ya shigo da motarsa. Malam na shiga dakin baccin Muneeba sai ta soma wani irin gunjin kuka tana tirje-tirje akan gadon yasa hannu a aljihunsa ya fito da wata leda mai bakin mai aciki, ai sai kunjinta ya karu sosai tana nunowa Malam Hannu "Don girnan Allah kada ka samin wannan abin don kashe ni zaiyi idan ka sa min ka yi hakuri" Mujeeb tun daga nan ya fara tsorata Malam ya matsa zaisa mata a hanci Mujeeb cike da tsoro yayi 5 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria magana a hankali, "Malam yi hakuri kada kasa mata tace abin zai kasheta". Malam yace "Ba ita zai kashe ba wani takadiri ne, ai wannan ba muryarta bane kyaleni da shi koma kayi zamanka Mujeeb ya kasa zama duk sai ya firgice, ya tsaya tsuru yana kallon ikon Allah. Malam ya tsaya a gabanta a gefen gadon ita kuma taci gaba da gunjin kuka tare da fadin "Ka yi hakuri Malam Wallahi yanzun zan tafi”. “Aini bance ka tafi ba, ba kai azzalumi bane mata da cikinta har ya kusa isa haihuwa don zalunci ka zo ka sace mata shi to nima zan gwada maka zalunci ta yadda gobe ba zaka kara tunkaro inda take ba”. Ya kai maganin hancinta ta soma yinkurin tana ihu tamkar zata shede saboda azaba, aljanin ya ce "Wallahi na rantse maka tafiya zanyi ni dama turo ni akayi inzo in dauke abinda ke cikin in salwantar dashi kuma har yanka aka yi min na sha jini shi yasa nima zan saka musu da abin alherin da suka yi 6 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria min na cika musu umurnin da suka bani. Malam ya ce, "ni ban tambayeka me aka yi maka ba, bama na son ji wanda ya turo ka kayi wannan danyen aikin, ina son yadda ka dauke abin da ke cikin nan yanzu-yanzun ka maidoshi tun kafin in gana maka matsananciyar azaba, sannan in kaika kurkuku in kulleka tunda kai azzalumi ne ba ka da imani ko kai ba Musulmi ba ne? ya amsa "Ni musulmi ne? Amma shi ne aka hada kai da kai za'a zalunce ta? To yi gaggawar maida abin da ka dauka ko in kaddamar da żalunci akanka, ka sanni sarai nima azzalumin kaina ne in ma banyi maka da kaina ba zan iya turo 'yan uwanka ka sansu wadanda suka fika iya zalunci su lallasa maka azaba. Ya ce Eh duk na san haka yi hakuri zan maida yanzu". Ta soma juyi bisa gadon ta sa hannu a cikinta tana murzawa tamkar zata kwaso yan hanjinta. Mujeeb ya yi sauri zai taro ta 7 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria don a tunaninsa fadowa za ta yi daga gadon. Malam Abubakar ya dakatar dashi da hannu ya koma ya zauna akan kujerar gaban madubi Mujeeb yaga abin al'ajabi don dai bai Ankara ba sai gani yayi cikin Muneeba yana tasowa a hankali a hankali, bai gushe ba sai ganin cikin ya yi ya dawo yadda yake ta koma ta kwanta rigingine tana wani irin aje numfashi. Malam yayi magana,"In ka tabbatar ka maida to fice ta bakin ta kada in kara ganinka in ba haka ba kaima ka san sauran. Takwas Mujeeb yaga tayi a kwance tamkar mara rai ganin numfashinta da ke sauke shi ne zai baka tabbacin tana da rai Mujeeb ya mike ya iso gaban gadon daidai inda take ya dubi Malam yace "Sannu da kokari Malam Allah ya biyaka da gidan Aljanna nagode da wannan taimako naka yanzu shikenan sun maido cikin ba za su sake dauke shi ba". Ya ce 8 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria "Insha Allahu babu abin da zasu sake yi mata sai dai wani ikon Allah akwai magunguna da zan bata ta dinga amfani dasu da addu'o'i wadanda zasu zamo mata garkuwa tsakaninta da sharrinsu sannan akwai sharuďdan da zan shaida mata ta kiyaye akansu to tabbas idan ta kiyaye suma shaifanun za su kiyaycta. Yanzu ka barta tayi barci iya yinta har sai ta tashi zan yi addu'a a ruwa saika rufe idonta tashi ka bata tasha ta shafa a fuskarta da jikinta ko ina har cikinta idan ruwan ya bushe a jikin ta sannan tayi wanka taci gaba da amfani da sauran magungunan Insha Allahu kome zai daidaita kuma Allah ne ya taimakeka ka kira ni a lokacin da abun ya faru da ace an dauki lokaci to da wuya cikin ya dawo don suna dauka za suje su hallakar da shi ko su watsashi a teku. Mujeeb ya sauke ajiyar zuciya tunda Allah ya taimakeshi misalin karfe hudu da rabi na Subahi Malam Abubakar ya baro gidan su Mujeeb 9 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria lokacin ana ta kiraye-kirayen Sallah na farko. Mujeeb ya dawo zai wuce dakin Muneeba yaga Goggo tsaye A bakin dakinta tana ganirtsa tace "Lafiya tun dazun nake ta jin ana bude gate duk na tsorata ya ce, Mumeeba ce ba lafiya amma yanzų ta sami sauki. Ta ware idanu, "Ba dai nakuda ba? cikin ai bai isa haihuwa ba sai dai in bakwaini zata Haifa ko? Ya ce "Ba nakuda ba te, mu je ki ganta har ta a sammi sauki bacci ma take "Suka nufi dakin Muneeba tata tambayar shi, Ina ka je da talatainin daren nan? "Wanda ya duba ta ne dana kirashi a waya yazo yanzu shi na raka ya tafi dalili kenan da kika yi ta jin ana bude gate, suna shiga suka iske har vanzun baçein take yi a rigingine ciknta yayi wani irin tsini tamnkar yau abin da ke cikin zai fito duniya. Goggo ta ce, Me yasa kake bari tana irin wannan kwanciyar a rigingine alhalin dukanku na gaya muku yin 10 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria hakan nasa idan aka haifo yaro cibiya ta nannade shi karshenta ma in ba wanda ya iya cireta ta shake yaro ya mutu, tashe ta ta gyara". Ya đau bargo yana rufa mata saboda ganin yadda ta takure yatsunta shi a ganinsa sanyi take ji. Ya soma ba Goggo labarin abin da ya faru tun daga mafarkin da Munceba ta yi da yadda ta farka a firgice taga cikin ta wayam babu shi da zuwan Malam Abubakar da irin artabun da aka yi da aljanin da ya ce turoshi aka yi ya sace cikin da yadda aka yi cikin ya dawo. Goggo ta hau sallallami tana tafa hannu. "Eh kwarai kam wannan ture ne, lallai ni za a sace wa jikoki a ciki tun kafin su zo duniya to Wallahi koma waye zan dauki mummunan mataki a kansa don sai nayi ramuwar gayya. Mujeeb ya ce, "Ki yi hakuri Goggo ki kyale koma waye Allah zai yi maganinsa don girman Allah Goggo ki daina yarda ana cinye kudinki a iska duk makaryata. ne masu amsar kudi 11 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria suce za su yi maka abinda bai yi maka ba, a irin haka har sai a shammace ki a kaiki inda zała halaka rayuwar jininki ba ki sani ba. Gara kawai duk abin da ya sameki ki tashi cikin dare ki hana idonki bacci ki gayawa Allah to Wallahi zai duba matsalarki. Ta sauke numfashi "Humm" Ai na dawo daga rakiyar mayaudara nima na yi amanna da tsayawa gaban Ubangiji cikin talatainin dare saboda wani waʼazi da nake sauraro a gidan rediyo. Allah dai ya fisshemu kunyar duniya da ta Lahira. Mujeeb ya amsa da amen guri suka nema shi da Goggo suka zauna ita a bakin gadon shi a kan kujerar gaban madubi suka tsurawa, Muneeban idanu da ke kwance abinta lakadan tana sauke numfashi a hankali idan kaga yadda suka tsura mata idanu zaka ďauka Kidayar numfashin da take suke yi har aka soma kiran Sallah da za a yi Sallah ba ta farka ba Goggo ta dubi Mujeeb ta 12 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria ce. "tashi ka je ka yi haramar tafiya masallaci kada ka rasa jam'i idan ka dawo sai inje in yi tawa Sallar". Ya shiga bayin Munceba yayi alwalla ya nufi masallaci har ya dawo Goggo na zaune ya ce "Goggo je kiyi Sallah ki kwanmta zan zauna da ita har ta a tashi”. Goggo ta nufi dakinta shi kuma yaci gaba da zaman tsammani ba ita ta farka ba sai wajen bakwai na safe mika tayi tana salati idanunta karaf suka kai kan agogon da ke manne a bangon dakin tana ganin lokaci tayi saurin yunkurawa zata tashi tana cewa "SubhannAllahi abokin rayuwa wannan wane irin bacci nayi da har ban tashi nayi Sallar subahi ba kai kuma baka tashe ni ba? ta kare maganar tana kallonsa ya cc, yi hakuri nasan kina da larura shi yasa ban tashe ki ba Allah ma ya san kina cikin larura ba zai kama ki da laifi ba”. Ta kai hannu ta shafi cikinta tace "Ciki na ya dawo ko dama mafarki nayi 13 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria an sace min ciki? Ya ce "Ba mafarki bane da gaske an sace amma cikin hukuncin Allah an dawo da shi yi Bismillah ki sha wannan addu'ar ki shafa sauran duka a jikinki idan ruwan ya bushe sai ki je ki yi wanka ki yi Sallah". Ta amsa ta sha ta yi duk yadda ya gaya mata sannan ta dube shi ta ce "Duk jikina wani irin ciwo yake min cikin kuma ya kara nauyi tamkar an Kara min da dutse sam, sam bana jin dadi".". ya ce sannu ai yanayin jikin naki sai dai hakuri tare da addu'ar Allah ya rabaki da cikin nan lafiya. Suna zaune cikin mintuna kalilan jikinta ya bushc, ta tashi suka shiga bayi tare ya hada ruwan, wanka da kansa yayi mata wanka kamar yadda suka saba kullum saboda yanayin larurarta ga tsinin cikin sam ba ta Iya dukawa ta wanke kafarta da wasu sassan na jikinta don ko alwala zata yi shi ya ke taimaka mata idan baya nan 14 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria ga Karime shi yasa in daya ba ya kusa dole daya yana tsaye a gurinta. Ta idar da Sallah tana lazimi ne Goggo ta shigo suka gaisa take ce mata, Ashe kin tashi Wallahi baccin naki ya bani, tsoro". Ashe kin shigo ina bacci? Mujeeb ya ce "Tun hudu da rabi na darė muke nan tarc da ita Sallah ta tafi yi. Muneeba ta cika da mamaki "Ya aka yi ni ban sani ba? Me ya faru dani ne? Goggo ta ce, "Abin da ya faru da ke ne ya kira wani Malam Abubakar cikin dare aka yi ta artabu da aljanun da aka turo suka sace abinda kc cikinki da yake Allah ya fi su cikin ikonsa dolensu suka dawo da cikin ni abin al'ajabi ya bani ban taßa jin inda aka sace ciki ba, na dai san ana sace jarirai. Mamaki Muneeba ya Karu na jin abubuwan da suka faru cikin daren amma ita duk ba ta sani ba ta dübi Mujeeb, Yanzun kenan ina da aljanu yanzun?". Ya girgiza kai, sam baki da su shi ma aljanin da ya sace cikin turo 15 1 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria shi aka yi amma bai fadi wanda ya turo shi ba don Malam yace kada ma ya fada shi ba bukatarsa kenan ba. Ni kam tunda sun dawo da cikin ai mun gode Allah, Allah ya Kara tsare min ke da abin da ke cikinki koma waye ya turo din Insha Allahu zai ga Karshen sa". Goggo kam sai sauke ajiyar zuciya take tana jinjina kai don tabbas ta san babu wanda zai aikata wannan aikin inba Hajiya Harira da 'yarta ba, shi yasa take tsoron al'amuran Hajiya Harira ta san ita dinma ba kyaleta zata yi ba. kasancewar yanzun ta fara sakin layinsu ta soma gano kura-kuranta na irin kiyayyar da take nunawa 'yar Kaninta da uwarta alhalin basu yi mata komai ba balle danta da ake so wannan cikin sai ya wanke rabi da kwanta cikin kashi daya na irin kiyayyar da take wa Muneeba. kilama idan aka haifo jikokin nata kaunar su ta yi sanadin goge raguwar kwantan kiyayyar na Munecba. 16 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria Kiran Mal. Abubakar ne ya shigo wayar Mujeeb yayi saurin dauka tare da yin sallama Malam ya amsa ya gaya masa gashi nan a waje ya zo Mujceb ya mike yana cewa Goggo "Ga Malam đin nan bari na shigo da shi ya dubi Muneeba da har a lokacin tana bisa sallaya yace Maza ki sakaya Malam zai shigo ya sake duba yanayin jikinki yana fita ta mide ba tare da shafa maiba ta dauko doguwar riga ta saka dama sune kayanta koda yaushe kasancewar duk kayanta basa shigarta sunyi mata kadan sai ta karo doguyen riguna ta dinka wasu don tafi sakewa a cikinsu. A falo Malam ya zauna Goggo ta fito suka gaisa tayi masa godiytar irin gudunmmuwa da yazo cikin talatainin dare ya bada ya ce "Haba babu komai mun riga mun sabda irin wannan taimakon tamkar likitoci muke idan aka kawo mana za muyi gaggawar yin abin da ya dace in kuma munga dacewar muje har gida mu samu mai larura muna zuwa don wasu matsalarşu ta 17 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria wuce gaban a iya dauko su sai dai muje. Allah ya Kara mana lafiya ya rabamu da sharrin mutum da aljan" Duk suka amsa da "Ameen Ameen" Tambayoyi sosai Malam yayi wa Muneeba daga karshe ya bata shawarwari kamar haka". "Ina so ki sa a ranki wadannan magunguna da zan baki ba su bane za su warkar da ke, nima bani bane zan warkar da ke Allah ne kadai zai warkar da ke ya yi miki maganin dukkan larurorinki amma tare da taimakawa da shan magani saboda Allah da kansa yace bai saukar da cuta ba sai da ya saukar da maganinta. Kada ki yarda ki yi shirka ga Allah sannan kada ki yarda kokwanto ko shakku ko zargi ya auri zuciyarku ki dinga zargin ko wane ne yayi miki abu kaza shi yasa abu kaza ya same ki, ki kaddara cewa duk abin da ya same ki daga Allah ne ba daga wani ba saboda babu wata halitta da ta isa ta cutar da ke in ba 18 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria Allah bane ya bata ikon yin hakan kinga sai ki nemi waraka daga gurinsa. Ki kasance mai tsarkin zuciya kada ki yarda ki cuci wani daidai da kwayar zarra in ma mutum ya cuceki to ki barshi da wanda ya hallice shi in ma kinsan tabbas shi ya cuce ki to ki yafe masa tare da nema masa shiriya gurin Allah. Abu na gaba ki kasance mai kula da ibada kuma ki kyautata ibardarki ki dinga yin azkar ko da yaushe ki dinga yin itigfari a kalla sau saba'in a rana ko dari kada ki kuskura ki kwanta sai kinyi alwalla sannan idan za ki kwanta kiyi addu'ar kwanciya bacci kuma ki daina barin kanki a bude ki daina kwanciya tsirara daga ke sai zani don zai iya kwancewa ya barki baki sani ba, su kuma shaidanu sun sami hanyar shiga jikinki su cutar da ke. Ina fatan duk kinji bayanai na kuma za ki dinga kiyayewa? Ta ce "Na ji na gode Insha Allahu zan kiyaye ya bata magunguna yayi mata bayanin yadda za ta yi amfani da su babu fashi 19 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria ko tsallake har sai sun Kare sun fita tare da Mujeeb zai yi masa rakiya ya kawo rafar dubu hamsin ya mikawa Malam shi kuma ya ki amsa ya ce "Wadannan kudi sunyi yawa ka rage sannan in amsa ya ce "Ka yi hakuri Malam ba zan iya ragewa ba, saboda ni abinda kayi min ban isa in biya kaba sai dai inyi maka addu'ah kai da zuri'arka Wallahi kafi Karfin wannan kudin a gurina ihsani ne kawai nayi maka, Allah ne kadai zai biya ka. Da kyar Malam ya amsa sukayi sallama ya shiga motarsa ya tafi sun yi cewa da wata matsalar ta taso to ayi gaggawar sanar' da shi don rayuwarta na cikin hatsari amma da izinin Allah babu abin da zai faru. Goggo da kanta ta shiga dakin Suwaiba ta gava mata Munecba ba ta da lafiya, amma ba ta gaya mata abin da ya faru ba saboda sanin hali ya fi sanin kama. Da kyar ta iya shiga ta gaisheta saboda sam ba ta kaunar kallon cikin 20 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria na Munceba sakamakon wani bakin ciki da ke tokare kahon zuciyarta sai taji tamkar ma tayi ta naushin cikin har sai 'ya'yan da ke cikin sun mutu in ma so samu ne har uwar ta mutu babu ruwanta amma babu hali yin sata a lahira azo duniya a siyar. Goggo da kanta tayi waya Dukku ta shaida musu Muneeba fa bata da lafiya amma bata fadi matsalar da ta faru ba aikuwa washe gari 'yan Dukku suka yo mota guda suka zo gaisheta Innarta ma da Murja har da babansu sunzo a motar Mustafa tare da Mustafan. Murja ta dubi Muneeba lokacin su biyu ne a dakin ta ce "wai Muneeba kin sake yin hoton cikin nan kuwa don ni ban yarda da daya ne a cikin nan ba in kuwa daya ne za'a ga shirgegen da?. Munecba ta karasa shanve ruwan zam-zam mai kumshe da addu'a da ta tsiyaya a kofi duk Malam Abubakar ne ya bata sannan tayi magana, jiyan nan da naje awo aka sake yi min hoto ashe dai 'yan biyu ne kamar yadda mutane 21 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria ke ta fadi, sunce daya ne ya kwanta akan daya shi yasa idan anyi hoto ake ganin guda daya wai a dunkule suke guri guda" Murja tayi ihun murna na ta ce, Kai Alhamdulillah ina murna da jin wannan labara wai ya Mujeeb yayi da murna yadda naga yana dokin cikin nan kamar ma ya fi ki zumudi kan samun cikin nan? Ta ce kin san ina asibitin da na yi masa waya na gaya masa abin da scanning din ya nuna sai dai yazo ya gani da idonsa don zumudi ni kam ai nayi saranda na san ya fini zakewa don a gaban kowa zancen cikin nan da haihuwata yake yi ni ko ina zan iya". Dan halas din kuwa tana rufe baki yana śhigowa dakin kai tsaye gabanta ya nufo bayan yayi sallama ya jikin naki ko da yake kinga su Inna kin murmure sai murna kike yi ko nema na ba ki yi ba" ta yi dan murmushi ta ce Wallahi kana raina yanbzu nake tunanin in kira wayarka inji ko ka fita ne. 22 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria Ya ce Ina zan fita in barki'yau Ofís ma dole suka daga min dafa ce musu nayi ni da matata bamu da lafiya dukansu ita da Murja dariya suka yi Murja ta ce "Au ashe har kaima ba ka da lafiya ai bamu sani ba" ya ce "Gimbiya ta ba lafiya dole nima bani da lafiyar kallo na kawai kuke a tsaye ni tun yanzu ma har na fara mata nakuda, dama Goggo tace daga wata bakwai ake fara nakuda. Wata dariyar suka sake yi masa Murja ta ce, Shi kenan ke kin huta 'yar gata har nakudar ma tayaki za a yi ina Yaya na yazo ya dauki sabon darasi ya sa hannu yana mammatsawa Muneeba kafarta yana cewa "Na ga kafafdun kamar sun dan sabe yau? Ta ce, nima haka na lura har ciwon da suke yi ma sun rage. Murja ta ce h Mujceb ashe 'yan biyu za mu samu? Ya washe baki, "Wallahi kuwa har na riga kowa ganin su a kwamfuta, duka maza ita da take son mace gashi duka maza ne sai ki bari wata shekarar kya haifo macen bayan 23 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria kin'haifo min Mazaje na. ta danyi masa harará ta ce "Ai Insha Matan zan Haifa tun das u ma asibitin a hasashen suka yi babu tabbas tunda sun sha cewa na miji a haifi mace ko suce mace a haifi namiji mace ko suce mace a haifi namiji ko suce 'yan biyu a haifi daya ko suce daya a haifi 'yan biyu duk karya suke idanb har kaga an haifi abin da suka ce to dama can hakan Allah ya kaddara za';a Haifa ni kam Insha Allahu mataye zan haifo wata shekarar na haifo maka mazajen. Ya ce bakinki ya sari danyen kasha ai baki isa ba ki dai fara haifo min nawa naki sais u biyo baya in kuma ba haka ba inyi tar okon Allah su zama 'yan hudu biyu mata biyu maza kjin gas hi kenan rigima ta Kare". Munecba ta watsa masa idanu tana shagwaba, Ni ni Wallahi yaya Mujeeb kada kayi min wannan addu'ar in azan kai 'ya'ya hudu Allah ma kada ya amsa wannan addu'ar aid a shikenan na zama Allah sarki biyun ma yanzu sai 24 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria zullumi nake yi naga masu goyon daya ma suna wai waiu balle biyu bare kuma hudu ai sai dai ka aje aiki muyi rainonsu tare ya ce “Ai in dai zaki haifo hudun sai in aje aikin don samun 'ya'yan ni ya fi min samun aikin tunda gashi nan shekaru nawa ki ka kwashe bamu samu ba sai yanzun gara kawai kiyi uku uku ko hudu, hudu kiyi ki gama. Ta soma shagwaba, Ni dai Wallahi bana son addu'ar nan taka nasan halinka baka san wasa yanzun kana iya hana idonka bacci kayi mini wannan addu'ar. Murja dai tana jinsu tana musu dariya har Mustafa ma ya shigo falon aka ci gaba da hirar dashi, har lokacin ya fiyarsu yayi suka tafi tare da yi mata addu'a Alllah ya raba ta lafiya da cikin jikinta. 25 WATA KUSAN 4 Rahmatu Hassan Zaria **** **** **** Tun da cikin Muneeba watan ya shiga haihuwa sai wahalhalun ciwo suke tsananta a gareta yau nan ke ciwo gobe can har ta kai bata iya yin komai sai anyi mata don ko sujadar Sallah bata iya dukawa daga zaunen da take Sallar sai dai koma a zaunenta ke yi saboda girma da tsinin da cikin yayi abin ya euce tunanin duk wani mai tunano idan ta zaune shima cikin zama ya ke a kasa dirshan in kuwa a kwance take to shi ma kwanciyar yake a gefe guda duk mai imani da ya ganta a wannan halin sai ya tausaya manta balle Mujeeb wanda ya fi kowa tausaya mata ya shiga tsananin damuwa

Chapter 1 of 8