Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
8 / 8
da ba ya iya boyewa ko a gaban waye ya ke. Su kuma Suwaiba ita da Hajiya Harira suna ta kulle-kullensu na ganin yadda za ai su salwantar da cikin Muneeba sun yi ta zaga gidajen bokaye da Malaman tsibbu suna narka masu kudi amma duk a banza ba su cimma nasara ba, balle da Suwaiba ta sami labarin hoton da akayi ance da namiji ne sai suka sake bazama gidajen bokayen don ganin kota halin yaya ta haifo abin da ke cikinta a mace tun lokacin haihuwarta bai yi ba. Ranar wata Asabar yana gida baije aiki ba kasancewar ranar hutu ce sai sha dayan safe ya tashi daga bacci ya shiga dakin Goggo suka gaisa yake tambayarta Muneeban ta ce ita bata ji motsinta ba tun safe da ta zo suka gaisa. Ya nufi dakin Muneeba bai isketa a falonta ba ya zarce dfakin baccinta a can ya same ta zaune a tsakiyar gado ta 191 WATA KUSAN З Rahmatu Hassan Zaria mimmike kafafunta da suka kumbura suntum. Ya hau gadon yana tambayarta "Lafiya yau baki fito ba, jikin ne? Ya kai hannu yana lallatsa kafafun nata". Ta се "Wallahi su ne gashi nan yau sun dame ni da ciwo da kyar nake tafiya", ba' an baki magani a asibiti ba da kika je"? Sun bani ina shafawa amma abin sai addu'ah. Ya shafo cikin nata, dad yayi zungurere ya ce, Gaskiya Muneeba girman cikin nan ya bani mamaki tun bai isa watan haihuwa ba gashi nan da kyar kike yin komai bari in Kira Dr. Aminullah in masa bayanin kafar nan ko akwai wani magani da za'a gaya mana mu siya. Ya kira wayar Dakta yayibmasa bayani sai yace zai zo anjima ya kawo mata wasu magunguna Mujeeb da kansa ya shigo kicin dinta ya hado mata abin karyawa ta karya sannan ya hada mata ruwan wanka da kansa ya kaita bayi yayi mata wankan ya shafa mata mai ya sa mata 192 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria १ kaya sannan yace ta dawo falo ta zauna kada ta kwanta. Da Karime ta zo ita ya sa ta gyara dakunan ta wanke bayi ta sa turarukan wuta, ita kuma ya ce koda ta yi aikin komai ta zauna ta huta. Bokan da su Suwaiba suka je gurinsa ya tabbatar musu lallai idan ta saki kudi to zai yi mata aiki na ban mamaki don zai tura wani iblishin. aljani ne ya bi dare ya sace dan da ke cikin Muneeba sai dai ta farka ta ga babu cikin kuma ya tafi kenan har abada. Murna ta kama su saboda jin wannan aiki mai sauki sai dai boka ya bayyana musu dole za a yi wa aljanin da zai yi aikin yanka ne na bijimin sa wanda a kalla ya kai dubu dari biyu shi kuma kudin aikinsa dubu dari, kenan zasu kawo dubu dari uku. Sun dawo gida cike da tunanin hanyar da za su samo wadannan kudade cikin 'yan kwanaki yunda dama aikin ba 193 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria 1 2 C C a k 2 h n y d s) b. a yi sai ciki ya shiga wata bakwai, kuma gashi yanzu ne a lissafinsu ya shiga wata bakwai idan ya wuce bakwai ba a yin aikin. Babban gwal din Suwaiba wanda ta siyo da suka je aikin Hajji shi suka kai kasuwa suka sayar dubu dari biyu da 'yan daruruwa. Ana neman cikon dubu dari. Haka nan Hajiya Harira ta saka filinta a kasuwa aka siye shi a wulakance Dubu Dari da Ashirin abinda ta siya Dubu Dari Biyu tunda abin na gaggawa ne. Sun hada kudin Dubu Dari Uku suka kaiwa Boka ya ce su je su jirayi abin da zai faru cikin kwana bakwai da za su Zo. Har akayi kwana biyar babu wani abu daya sami Muneeba lafiyarta samul m ranar Litinin ta je Asibiti Awo a can ne ai suka sake bata hoto saboda mamakin da watannin cikin ya basu, wai ciki wata bakwai amma girmansa ya wuce misali 194 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria 2 nauyinsa ma ya zarce tunanin tamkar na mai wata tara. Wannan karon 'ya'ya biyu aka gani a hoton wai ashe dayan ya kwanta akan dan uwansa ne sun dunkule suke bada mutum daya, yanzun kuwa ga su nan su biyu hoton. Tun a asibiti Muneeba ta Kira Mujeeb tana gaya masa Murna ya hau yi ya ce "Yanzu kina ina ne". Ta ce Gani nan a asibiti ni da Karime Jume na jiranmu zai maida mu gida ya ce Kice masa ya tafi gida gani nan zuwa da kaina zanzo in dauko ki, ya tafi da karimen". Ta dubi Karime ta ce "Ki je ki cewa Jume ku wuce gida ga Yaya Mujeeb nan zai zo ya daukeni ina jin wani guri za mu je, ki dafa min Indomi da dafaffan kwai yunwa na ke ji sosai". Ba su dade da tafiya ba Mujeeb ya zo asibitin sai da ya biya wani kudin aka sake yin hoton wai so yake ya gani da idonsa, ya kuwa ga 'ya'yan su biyu 195 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria kwance cikin koshin lafiya tun a asibiti ya kira ya gayawa Goggo an sake yi wa Muneeba hoto anga 'ya'ya biyu ai Suwaiba na jin haka ta ji tamkar za ta mutu don bakin ciki. Tunda suka dawo gida cikin Muneeba ke ta murda mata da ciwo 'ya'yan cikin nata sai watsalniya suke yi sun hana ta sakat zama dirsham Mujeeb ya yi yana kallon wannan iko na Allah mutum cikin mutum yana mata sannu saboda rintse idanun da take yi yace "ina ganin yamutsa cikin da akayi yau shi yasa kike jin ciwo. "Ta ce ni dama duk ranar da na je awo sai na yi wannan ciwon cikin amma na yau yafi na kullum kafin dare ciwon ya lafa mata har ta yi wanka ta ci abinci sai dai kadan-kadan ciwon ke mata. Tare da Karime suke kwana amma yau sai Mujeeb ya ce Karimen ta je gida shi zai kwana da ita in har girkinta ne to can take zuwa dakinsa ta kwana in ba 196 스 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria |Σ girkinta bane shine Karime ke zuwa ta taya ta kwana. Yau ma ba girkinta bane amma yace sam ba zai yiwu su kwana da Karime ba tunda bata da lafiya shi zai kwana da ita don baisan me dare zai haifar ba. Cikin dare Muneeba tayi wani mugun mafarki wai wani mutum ya biyota da wuka suna ta fafata gudu a dokar daji ba gida gaba ba gida baya har sai da tazo gabar wani kogin a rami ya ke sai ta fasa fadawa kawai ta tsaya. Mutumin ya iso ya kamata tana ihu tana rokonsa ya kwantar da ita tana gani ya sa wuka ya fede cikinya ta kwaso 'ya'yan cikin guda uku ne ba ma biyu ba tana ji tana gani ya tashi sama da su tana kallonsa har ya bace a sararin samaniya ita kuma ta kasa tashi sai ihu take tana neman dauki. Haka ta farka a firgice tana salati tare da fadin Innalillahi wa'inna ilaihir Rajiun Allahumma Ajumi fi musibati wa 197 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria akhlufni khairan minha sai taji cikinta wayan ba ciki ba alamarsa ta kai hannunta a firgice ta shafo cikin sai ta ji babu shi wayam. A firgice ta tashi Mujeeb dake kwance a gefenta tana nuna masa cikinta ganin babu cikin ya sa ya tashi shima a firgice yana tambayarta. "Kin haihu ne baki tashe ni ba? Ta girgiza kai ya ce, Bangane a'a ba to ina cikin jikinki? Tana kuka ta labarta masa irin mugayen mafarkin da tayi ai bata Ankara ba sai ganinsa ta yi ya tafi luuw yana sambatun fadin Innalilahi Wa'inna Ilaihir Rajiun. DOLE IN DAKATA ANAN DON NIMA KANIN SUMA NAYI TARE DA YIN TASBIHI GA ALLAH. KU BIYONI A LITTAFI NA HUDU WANDA SUKA FITO TARE DA NA UKU 3 TAKU RAHMAN ZARIA 080-6889-5555, 080-2843-4948 198 * * LITTAFAN MARUBÜCIYAR SANIN HALI 1,2,3 HUJJATA 1,2,3 MENE AIBUNA? ALKAWARIN DA CIWO 1,3 NA YI BIYAYYA 1,2 WA YA CUCE NI? 1,3 BAYAN WUYA 1,2 SAIHAМ 1,2 * MU YI HATTARA 1,2 * AUREN MANUFA 1,2 SIRRIN GIRKE-GIRKE 1,2 MIJIN ARO 1,2 ILLAR KUSANCI 1,2, DON MAʼAURAТA WATA KUSAN 1,2 MUHAMMAD SANI BOOKSHOP CHARANCI ROAD KASUWAR BARG 080332684404,07089897389 AL-MUSTAFA BOOKSHOR BAKIN RIMI GIDAN JUMA S/GARI ZARIA 08026570893, 08130616029 ABUBAKAR ABUB RABLL WUSE BOOKSHОВ Wuse market zone 1 Abuja. 08030777669, 08091331166 No Ag 1 Anguwar rimi market Kaduna 08023607345 HNARS BOOKSH Behind Kofar Doka Central Motor Park, Zana 08028341964. el Layi Na Hudu Bayan Masallacin Abacha A.A. Rimi Market, Kano Inside Club 69 Garejin Hayi-Hayl Sheik Abubakar Gumi CentralI Markat Kaduna. 07066708030,08029645801 Desia ZAZZAU VENTURES General Printing & Publishing 08028401199, 08035336868 Block A 36 Inner Idear T/wada Zaria. An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels

Chapter 8 of 8